🧠MIJIN BUZUWA🧠 BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM MUNA GODIYA GA ALLAH DA YA BAMU DAMAN RUBUTAWA DA KARANTA WANAN LABARI UBAGIJI YADDA MUKA FARA LAFIYA MUKAI KARSHEN SHI LAFIYA . KISHI DA BUZUWA SAI KA KWANTAR DA HANKALI KA KAI AIKI DA HIKIMAR KA WAYEWA DA ILIMI BAI FITAR DAKAI A GARESU, , , , GODIYA GARE KUMA KARANTA NOVEL DINA DA KUKE KOKARIN DAUREWA DA HAKKURI WURIN KARANTA LABARAINA WANDA ABUBUWAN DAKE YAWAN FARUWA A NAHIYAR MUCE MUKE TABOWA DON HASKA KAN YAN UWA DAMA MU DUKA. NOVEL DINA NA KAUYAWA NE BABU YAWAN KARAYAN ARZIKI A CIKIN SHI SAI DAI ABINDA LABARIN YAZO DASHI BABU FAYYACE FITSA A FILI YADDA WASU KE SON IN SAUYA ZUWA HADI DA FITSARA NA KASANCEWAN MACE DA NA MIJI A GADO A HAKKAN KUMA NAKE DA DINBIN MASOYA MASU KARANTA SHI A HAKAN, GODIYA GARE KU HAR KULUN MASOYA DA MASU KAUNA NA. GAMA SU SON NOVEL DIN ZAKU IYA KIRA NA DA WANAN LAYIN DON NEMAN KARIN BAYANI DARI UKU NE GA MAI SON BIYA TA WANAN ACCOUNT DIN 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK 09026931792 KO 08036959257 Hadari ne ya hade garin sosai baka ganin komai sai walkiya da kara kainan motoci a lokacin wanda suke haskawa don ganin gaban su. A daidai wanan lokacin ne motoci guda uku da suka karyo titin a jera wanda ke nuna wani mai akwaine tafe a lokacin yadda mutane suke ta kaucewa a titin suna basu wuri. Wasu daga bakin titi ke fadin yanzun haka ma ba maigidan bane tafe wanan fitsarariyar matan tashine haka da bata ganin kowa da mutunci a idon ta. Wani gida motocin suka shiga a lokacin gini ne na zamani motan ne suka dan tsaya da alama magana akeyi da wani a cikin gidan. Ba a dade ba suka wuce zuwa cikin gidan kai tsaye security ne suka fito don bude motar nan naga wata farar mata buzuwa ta fito tasha ado na fada da gani daga saman ta har kasanta kwaliya ne. Doguwa ce sosai ga fari sai dai idan ka kura mata ido zaka iya gano farin ne kawai ke aki yake rudin mutane don kyau akwai kyau inda bamu matan mu na Nigeria masu kyan asali da dire bayan farin da gashi da kuma tsayi babu abin da suka dara matan Nigeria dashi na fannin kyauwo. Tana wani tako ta shige ciki zuwa part din ta ta dan jima ciki ta fito tana kwala ma wata mata mai suna Labara kira da karfi . Da saurin matar ta iso gareta tana dukawa tare da fadin hajiya barka da zuwa an dawo lafiya yaya han, , , , Dakata tace wa matar yaya naga witan part din can a kunne ko mara zuciyar nan ta dawo ne kuma ? Matar ta dago kai a hankali tace wa hajiya babba kike nufi waye hajiya baba ina nufin fatima matar wancan shiyan ta fada a fusace jin an kira uwar gidan nata da hajiya babba taji haushi. Eh ta dawo laraba tace ai tun ranan da kuka wuce washe gari ta dawo kutawa tayi tare da juyawa da karfi ta shige part din ta a hasale. Anan tabar laraba da kallon mamaki ta nisa tana fadin ikon Allah mata da mijin ta kinzo kin hana zaman lafiya a tsakanin su haka ? Ita kuma a daki sai faman huce takeyi ita daya nan ta dauki waya ta kira mijin nasu da suka rabu yau ya tafi waje yin wani aiki. Duk da tasan dare ne a duk inda yake amma bai hanata kiran shi ba a wanan lokacin saboda tsananin kishin dake damun ta a lokacin. Kiran farko ya tsunke bata hakkura ba ta sake kira a karo na biyu bai daga ba sai wayan na gap da katsewa ya dauka da alaman barci yake a lokacin . Murya irin ta masu barci ya daga wayan tare da fadin Nafisa lafiya kira da dare haka yanzu fa kin san dare ne nan sosai a wanan lokacin. Bata jira ya gama magana ba tace watau munafuntana zakayi ashe kasan matar ka ta dawo shine baka fada min ba tun muna tare sai kawai in dawo in samu ta dawo gidan. Ajiyan zuciya ya sauke tare da fadin tadawo fa ni ban san ta dawo ba don basu fada min da cewa zata dawo ba ma kit ta kashe wayan. Ta wurga a gefen gadon ta tana fadi a fili duk sai nayi maganin shegun tsofin don sai auren nan ya mutu inga ta bakin naci irin nasu. A daidai lokacin ne kuma aka turo kofan side din nata wata matace cikin dogon riga ta dora hijjab a saman rigan nata. Fuska da murmshi tace mutanen Abuja ashe kuna tafe yanzu ne an sauka lafiya yaya hanya fuska a daure ta juyo tana fadin eh muna tafe ko idan zan dawo sai na sanar da wani akace ko ma ? Ke yanzu don baki da zuciya dawowa kikayi duk da maigidan ya nuna baiyi dake saboda rashin zuciya irin naki sai da kika dawo kamar ana zama dole ne. Matar tadan sake murmushin dabai kai ciki ba tace nake ganin ke nan haka amma ni nasan yana yi dani har gobe ke ce dai ganin ki ke rudin ki ga hakan don ko na bar gidan shi bamu rabuba don ga diya ga zumunci a tsakanin mu. Fati ke nan zakiko ga abinda ba daidai ba wallahi in dan kin nace sai kin zauna min da miji don sai na rami ya fiki shan iska a gidan nan tunda haka kika zaba wa kanki sannu sugar mai iyali ko tasbi sarkin zumunci shida bakajan da daya bai biyo ka ba . Murmshi tayi Allah na tare da mai gaskiya dama jin kin dawo ne yasa nazo taron ki da dawowa ba wani abu ya kawo ni ba a huta lafiya bata tsanmanin ta amsa mata ta fice daga dakin . Zuciyar ta yana ciki da mamakin fitsara irin na Nafisa wanda sam babu kunya a cikin shi ko kadan sai zallah cin fuska da fitsara filli. Daki ta nufa a daidai lokacin da ruwa ya gauce sosai a garin na kaduna kamar da bakin kwarya da sauri ta isa ta rufe mirrow da sauran abinda baison walkiya a dakin saboda tsaro wanda ba kowa ke wanan ba a wanan lokacin sai masu sani da hakan a baya suka saura rufe irin wa yan nan abubuwan a daki yayin da ruwan sama ke zubuwa daga samaniya don kariya daga fitinan walkiya. Falo ta dawo ta zauna tare da yaranta dake cin abinci a wanan lokacin ido ta tsurawa yaran biyu sai da ba wai don tana kallon su hankalin ta yana gare ta ba ne tunane takeyi a zuciyar ta na irin rayuwan da ta tsunci kanta a ciki yanzu. Tun shigowan Nafisa cikin su komai na rayuwan ta da mijin nata ya sauya sallo a lokaci daya ba yadda suka saba gudanar da rayuwan su ba suda yaran su da sauran yan uwa. Hatta yaran yanzu a matse suke da zama gidan mahaifin nasu sun fison zama a gidan kakanin su da zaman gidan nasu saboda matsin da suke ciki a yanzu. Ita dai tasan aure ne a tsakanin ta da mijin ta na soyayya tun tana karama soyayyan su ta samu asali don gidajen su basu da nisa da juna shi din abokin yayan ta ne. Kuma akwai zumunci na makwabtaka da ya koma kaman na jini daya a tsakanin gidajen su tun kakan su zumunci ya kulu a tsakanin gidajen biyu. Wanda yakai bako ba zai iya banbanta tsakanin su ba sai wanda yasan tushen abin koda ta girma bai daina kulata ba cikin yan uwa haka ya kai har aure ya kullu a tsakanin su. Tayi haihuwan farko lafiya ga cikin na biyune ya samu aiki kano suka koma can sun koma bada dadewa ba ya hadu da Nafisa yar mutan Niger da suka shigo Nigeria neman kudi da iyayyenta ta lake mai tun bai kula ta har ya soma kulata don suna sayar masu da abinci a bakin ma,iakatar su ne. Yaron ta ne dayazo inda take zaune tana tunane ya katse da da fadin mama daddyn mu bai dawo bane naga anty ta dawo. Shafa kan yaron tayi taja sauke ajiyan zuciya tace bai dawo ba Affan da kaga ya shigo nan ai anty ce ta dawo ita kadai. Yaushe daddy zai dawo mama yaron ya kara jefa mata tambaya kuma tace Affan ban sani ba idan ya dawo ai zaku ganshi. Bai barta ta huta ba ya sake jefo mata tambaya again yace mama ai anty ce bata bari mu ganshi ko munje wurin shi sai tace mu fito muna damun shi yana hutawa. Murmushi tayi tace kai Affan ba yana zuwa nan ida muke kuna ganin shi ba to may kuma kake so shiru yaron yayi kamar yana tunane a zuciyar shi. Sai kuma yace ni mama ban ma son ya dawo saboda may Affan uwar ta tambaye shi yace saboda idan ya dawo sai ki ta kuka mama su kuma suna dariya da anty kuma su fita tare. Affan ban son yawan surutu fa ka faye surutu ina jin tsoron wanan bakin naka kullu naji ka kara fadawa wani matsalan mu sai na yanke ma kunne daya. Shiru yaron yayi yana tunanen kada uwar ta yanke mai kune kamar yadda tace din kayan da sukaci abinci ta kawar ta gyara wurin suka shige dakin kwanan su. Da safe bata fito ba sai da ta gyara part din nata ta nufi kitchen don dafa ma yara abincin zuwa school sai ta samu kitchen din a rufe. Dakin kwanan laraba mai aiki ta nufa a nan ta samay ta tace yau laraba lafiya naga kitchen a rufe Labara tace aikin hajiya karama ne hakan. Nima na fito zan gyara tace na barshi taja kofa ta rufe nayi tunanen zaki fito don saboda abincin yara gashi kuma ta kulle kitchen din. Dan jimm tayi tana tunane a ranta wai may Nafisa take nufi da ita ne haka abinci dai na kowa ne a gidan amma haka take mata idan ta bushi iska sai tace wai ana barnan abinci da yawa gidan. Bayan abinci ma da take ita daya sai ta ba wasu balle yanzu da ya samu karin girma sosai a wurin aikin shi basu da talaucin komai a rayuwan su. Muryan Laraba ne ke fadin sai hakkuri hajiya idan mutum ya ci gaban ka sai dai bi wallahi gama tana ganin ta samu miji a hannu sai abinda tace a gidan. Ba komai Laraba na gode badin tura su can cikin gida wurin hajiya su karba haka ta juya ta wuce zuwa part din ta tabar Laranba a wurin tana jin tausayin ta. Daki ta koma ta shirya yaran ta fito dasu da kanta ta mika wa kanin mijin su dake zaune dasu a gidan ya kaisu cikin gida wurin hajiya a basu abinci. Yace yau kun makara ne tace eh salis koda na tashi har gari ya haska sosai wallahi kaga idan nace zan tsaya dafa masu yanzu sai su makara. Ta koma ciki ya kwashe yaran zuwa gidan su dasu don duk a unguwa daya suke zaune da iyayyen nasu gida uku ne a haka kuma Nafisa ke tsula tsiyar ta a gidan. Don tafi son zaman kaduna saboda anan kawayen ta suka fi yawa da yan yaren su na buza da suke kara zugata tana iya shegen. Salis na shiga gidan kafin ya isa part din mahaifiyar mijin nasu da yaran matan gidan suka fara magana a, a su Affan ne haka yau da safe nan. Salis yace eh maman su ta makara ne yau bata tashi da wuri tayi masu abin karyawa ba shine zasu zo nan su dauka. Murmushi hajiya kubura tayi tace Fatice zata makara da safe kawai dai yar bakin halin gidan su ta dawo jiya akwai da wata a kasa. Ba an mayar da Fati bata san tadawo ba shine ta dawo ta samay su bakin halin nata na banza ya tashi yanzu ta soma ke nan har sai ta kure ta ta tanka mata. Allah dai ya sauwa dayar matar gidan ta fada daga daki tace shi kuma da yazo sai ya biyewa iya shegen nata ba daga daki suke magana. Sun shiga gun kakan su tana ganin su tace ai na sani ba yar iskan yarinyar nan ance ta dawo jiya ba nan yanzu tsiya zai tashi a gidan wanan karo ko ba zan saurara mata ba wallahi. Salis yace cewa tayi makara tayi fa bata samu dafa masu abinci ba yau yaya maganan ku yazo daya da na mommy ne ? Hajiya bata iyayin magana ba sai jan yaran datayi zuwa cikin part din ta ta zuba masu abincin da tayiwa yan marayun jikokin ta da suke hannun ta. Bayan ta gama sallaman yaran ne ta dauki waya ta kira Fati din tace wai may ke faruwa ne yau a gidan naku cikin fara a ta fara gaida surukar nata da bata ko tsaya gaisawa da ita ba. Amsawa tayi sama sama dakyat tare da maimaita tambayan ta a gare ta tace hajiya makara nayi tace jinan fati na san komai walahi nasan abinda yar banzan yarinyarin nan zata iya. A sanyaye fati tace hajiya ba haka bane makara nayi yau din ban samu dafawa ba kashe wayan hajiya tayi badon ta yarda ba. Kashe wayan nata yayi daidai da shigowan hajiya kubura wurin ta tace sai gasu Affan na ga sun zo karban abinci kuma ? Bari hajiya Kubura duk da uwarsu ta boye min na san akwai wata a kasa wallahi bai yuyuwa haka kawai taki tanadarwa yara abin zuwa makaranta. Nan suka zauna suna maganan hajiya kubura tace idan ita fatin bata iya magana mu ba kyalewa zamuyi ba ai ana horo da yuwa ne kuma ? Kai hajiya ta dafe tace Allah ya kawo muna karshen wanan yarinyar a gidan nan hajiya kubura tace amin tana mikewa tare da fadin bari mu gani zuwa rana idan har sun dawo nan kin ga hasashen mu ya tabbata ke nan ta rufe kitchen din nasu ke nan. Ta fice ta bar hajiya a cikin bacin rai tana tausaya ma wanan rayuwa da yayan nasu suka tsunci kan su a ciki na bamin auren buzuwa da ya dorawa rayuwan shi yana zaune kalau da matar shi ya jajibo masu wahala haka. A gidan Fati kuma bata karya ba tun safe ba tunanen kanta takeyi ba a yanzu sai tunanen idan yaran sun dawo may zata basu idomie ne ya fado mata arai ta sayo ta dafa masu suci. Damay zaki dafa wani zuciya yace mata tsaki taja tana tausaya masu a ransu take tunanen da can baya lokacin tana ita kaida ya fado mata a rai. Abinci sai wanda ransu ke so zata dafa da ita da yaranta da maigidan ta har sai taba makwatab wani lokaci yau kuma gashi a sanadiyar kishi da buzuwa har horo yakai ga a rufe store da madafar abincin gidan baki daya. Babu wanda zata kara kai kara gareshi tunda baji mijin nasu keyi ba ko ta fada karshe ma ya dawo ya hauta da masifa gashi ita ba son masifa take ba a rayuwan ta. Haka ta taso da tsoro sam bata fada ko kadan saboda ruwan ciki irin na matan hausawa da ta taso a cikin shi wanda a cikin tarbiyan diyan hausa yake. Kamun kaina a diyan hausawa rasgin hayani da fada da mutane barkatai wanda akasarin matan hausawa hake ne ke cutar su a gidan mazaje su da gun kishiyoyin su yan bana bakwai. Tana tuna yadda Nafisa tazo gidan daga ita sai ghana most go din yan kayan ta a ciki amma yau ta koma kamar wata hamshikiya a gida. Auren ta da aka dauro ba tare da sanin iyayyen su ba can bariki suka dauro auren su da ita inda ta tare a gidan da yake a lokacin a kano. Sannu a hankali har ya samu iyayyen shi suka hakkura ta fara shiga cikin su inda take baiyana harin ta na zahiri a hankali. Da farko ta yaudari mutane inda taja yan uwan miji a jikinta duk suka yarda da ita ta gama jin sirin su kaf kafin daga baya data bunkasa ta fara fitar da kalan ta ga mutane. Inda yanzu kowa ya gama gane ta wasu masu zuciyar imani sun gujeta masu kwadai kuma har wanan lokacin suna tare da ita duk da abin hannun ta bai ban baruwa wasan dadi sai kayi mata bauta kafin kaci abu daga gare ta. Don haka take kallon kowa a wullakance sai uan uwanta dakan zo jefi jefi cin arziki wurin ta wanda ba a wuce wata daya basu zo gidan ba. Tazo da wata yarinya da take cewa wai kaunar tane sai da tafiya yai tafi aka gane cewa yar tace ta cikin ta yarinyar. Nafisa zata girmay ma Fati ga shekaru haka yasa tafi fati wayo sosai har take jin tsoron ga fin karfi ga sihiri don bata shigo haka kai tsaye ba sai da ta shirya ta shigo gidan . Shi kan shi maigidan ba a banza ta barshi ko yanzu kuma bawai ta fasa abinda takeyi din bane sai ma abinda yaci gaba a cikin halayen nata. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU🧠MIJIN BUZUWA🧠 2️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU NOVEL DIN NAN NA KUDI BIYA DARI UKU KO KATIN DARI UKU TA WANAN ACCOUNT DIN 2254380105 ZAINAN IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KI KIRA TA WANAN LAYIN 09026931792 KO 08036959257 ASHA KARATU LAFIYA Hayaniyar yaran da suka dawo daga makaranta ya dawo da ita ga tunen tace shike nan nawa ta samay ga Affan da dan banzan wayo kawai na shiryasu zuwa cikin gida wurin kakanin su tasan idan sunje can sa samu abinda sukaci a cikin su. Yaran suna shigowa suka fada mata a jiki suna fadin mama mun dawo yunwa nakeji sosai wallahi karamin ya fada take taji gabanta ya fadi don hakan halin su ne . Sai subar abinci a cooler makarantarsu su dawo dashi kuma suce yunwa suke ji halin yaro ke nan oya a cire uniform kuje cikin gida wurin su hajiya kwaci abinci a can banson yawan hayaniya yau. Acan cikin gida kuma dawowan yaran gidan makaranta yasa hajiya ta kasa kunne taji shigowan jikokin nata da take zaman jiran tsamanin su tunda safe. Ba afi min ashrin ba ta fara tsinkayo hayaniyar su daga kofan shigowa gidan tace a ranta nasan a rina dama tabbas hashe na ya tabbata ke nan wanan yarinyar har takai can. Yaran suka shigo dakin da murnan su don anan kawai suke samu su sake suyi yadda suke so batare da wani tsangwama ba. Suna shiga Affan ya cire rigan jikin shi ya rage daga shi sai singlet yana fadin hajiya maman mu tace muzo nan muci abinci a wurin ki wai yau bata son damuwa. Yar ta Aisha ta kwala wa kira tazo ta basu abinci sai gata ta fito daga daki tana saye da dogon riga a jikin ta tana ganin yaran tace a a su Affan ne yau da rana tsaka anan zakuci abincin rana ke nan ? Hajiya tace zuba masu Abinci don Allah ki kawo masu nan ta wuce kitchen cika umurnin mahaifiyar nata da sauri sai gata dauke da plate din abinci ta kawo masu. Hajiya na zaune gefe ta kurawa yaran ido tana kallon yadda suke cin abincin gwanin ban tausayi dasu tunane tayi aranta da yau babu ita fa kamar yadda babu ran kakarsu ta wajen uwa yaya Fatima zatayi da wanan ukuban haka ? Hajiya kubura da take matse ita tunda rana sai gata ta shigo wurin hajiyan da mamaki a fuskanta tana fadin yaya kin ga hasashen yana son ya tabbata a kan yarinyar nan ko sai ga hajiya karima uwargidan su tashigo a bayan su tace tabbas maganan mu ya zama gaskiya. Ya tabbata ke nan ta ki bari yarinyar nan ta girka abinda zasuci a gidan abin har ya tashi ga ta hana mai aiki yi masu girki suci ya koma ta hana masu abinci. Sallama ake daga kofan shigowa dayar yarinyar gidan ta leko daga kofan hajiya karima tana fadin sannu da zuwa yaya Suraj. Bai amsa mata gaisuwa ba sai tambaya yayi ba kowa a gidan ne ina sallama gidan shiru tace suna dakin hajiya mama ina gani can yanufa dakin don yasan idan sunyi irin wanan taron akwai abinda ke faruwa da ya shafi dayan su ne don don iyayyen nasu nada hadin kao sosai a gidan. In ka debe ko wanan ya kasance amaryan su Asiya bata gida ne a lokacin da su hudu zasu hade a dakin kofan ya nufa yana saye cikin uniform din shi na sojoji. Sallama yayi a bakin kofan daga ciki suka amsa mashi mahaifiyar shi hajiya karima tace kamar muryan suraj nake ji a kofa yace nine ummi. Dakin ya shiga kallo daya yayiwa iyayyen nashi alokaci guda ya gane akwai wani matsalan da suke fuskanta wanda ya shafi hajiya mama a gidan. Gaida su ya fara yi a cikin ladabi kamar ba soja ya samu wuri ya zauna bayan sun karba mai gaisuwa. Duban hajiya kubura yayi yace mommy akwai matsalane su Affan dake cin abincin su hankali kwance ta nuna mai tana fadin wanan fitinaniyar matar uban tasu ce kila ta rufe dakin girkin gidan ne yau ko da safe a nan suka dauki abincin zuwa makaranta. Yanzun kuma kaga uwarsu ta turo su nan su da sauri yace ita Fatin fa may zataci to ya tamnaya yana kallon fuskokin su gason jin amsan su. Mommy tace ai shi muke tunane a nan dafe kai yayi yace wanan mata ban san abinda take nufi ba a gidan nan tana son mayar muna da dan uwa binan. Kada kaga laifin ta ai shine mai babban laifi mama ta fadi a hasale sai mummy tace ba yin kanshi bane yaya bar irin shuuman matan nan wallahi. Suraj ya mike a hasale yana fadin yau sai naci mata mutunci idan haka gaskiya ne wallahi ko a gidan maza ana ma mutum horo da yunwa ne balle gidan brother za a ce anyiwa mutum haka. Ko maigadin gida ai yana iya kyauta da abinci tunda bai rasa ba balle diyan shi ummi ta kalle shi lokacin da yake shirin fita daga dakin tana fadin ina zaka ? Kai tsaye yace gidan zanje wallahi idan na samu gaskiya ne yau sai tabar gidan nan wallahi ummi tayi saurin cewa dashi kaifa mahaukaci ne na sani a dai karbe key din ka bude wurin shike nan. Kasan yadda dan uwanka ke son ta hakan zai iya kawo matsala a tsakanin ku yace wallahi sai dai ya kawo ummi wanan wani irin bakin haline haka ? Ai haka suke mommy tace mashi abinda ake mai gudu ke jan tun farko bai gane ba basu son kowa sai kan su da yan uwan su kawai wanan halin su ba wai ba. Mama dai ta rike goshin tada hannun ta sai wanda duk yai magana cikin su ta bishi da ido kawai shine nata yayin da zuciyar ta ke mata soya a ciki tana jin wani irin ba dadi a ranta. Yana tsaye daga kofa mommy tace bari muje tare dakai zaifi da sauri ummi tace haka zaifi kan don wanan kin san mahaukaci ne ya shawo Alluran shi ja sojoji kar yaje ya sauke wa yar mutane a kai. Ai da zai sauke din haka zai fi gani take duk ta gama da kowa a gidan babu wanda bata iya takawa shiyasa take abinda taga dama inji mama. Yanzun dai bari mu tafi idan munje ni zan fara shiga wuri ta inji ba asin yin hakan da tayi sai asan abinyi sukace yayi kyau hakan mikewa tayi zuwa dakin ta ta dauko hijjib din ta ta saka suka fice da suraj din a motar shi suka karasa gidan. Daidai lokacin Abba ya dawo shi da anty amarya daga asibiti da dan ta da bai da lafiya ganin motar suraj ya gilma ya nufi gidan dan uwan nashi yasa suke mamaki. Anty amarya ke fadin yau suraj ziyara zaikai gidan Abdul ne haka mahaifin nasu yace kila yazo ya samu Fati ta koma dakin ta ne zai dubuta. Sai da suka shiga gidan ne suke jin abinda ke faruwa karban key anty Amraya tayi bata shiga dakin taba ta bar yaron wirin uwar gidan nata ta mara masu baya. Sun samu kofar gidan a rufe wai taba maigadi sallahu cewa kada ya bari kowa ya shigo gidan ya damay ta don yanzu ta dawo da yarta daga makaranta zasu huta. Da kyat ya bude masu kofa sai da suraj yayi mashi jan ido wanan abin shiya kara harzuka suraj din rashi ya baci sosai kusan a tare suka shiga gidan da anty amarya don samun delay din shiga da sukayi. Bin gidan Suraj yayi da kallo daga sama har kasa kafin ya karasa fitowa daga motar shi cikin hasala mommy tace ashe kun dawo ke nan take cewa anty amarya tace mun dawo ina shiga ake fada min abinda ke faruwa nace barin biyo ku don ba mutunci ne da ita ba. Anty tasan ida take rashin mutunci ta ai nika yau idan tayi min wallahi balbalata zanyi in daki banza sai dai mu rufe da mijin ta ai mun saba. A tare suka shiga gida jin karan bude get din gida ta fito a fusace tana fadin maigadi wani dan bura, uba kabudewa, , , , , ganin su mommy yasa tayi shiru ta juya da saurin tana zaton basu ganta ba suko sun ganta. Kafin su iso ta wuce part din ta ko da sauri don tasan ba bakin ta bane na Fati ne don ita suke zuwa gidan su . Tunda ta sallamay sallah la,asar take zaune saman sallaya ta tun tana addua ta koma tunane ga tunanen ya bowayeta don yunwan da ke cin ta. Sun shiga da sallaman su aka gaisu tace mommy kune tafe ashe mune fati har kasa takai tana kara gaida su cikin mutunci suka amsa mata ta dago tana fadin yaya Suraj marmari daga nesa. Ke kin ci abinci yau ko baki ci tambayan da ya jefo mata ke nan a lokaci daya tayi murmushi tace kajika da wani magana kuma ba a gida ka samay ni ba zakai min wanan tambaya haka ? Mommy tace Fati ba tambaya muka zo yi ba don mun san abinda ke wakana a gidan ko yau dai bakici komai ba tunda garin Allah ya waye haka ne ko ba haka ba. Kai ta sadda kasa tace hakane mommy tace to akan may Fati zaki zauna ana maki horo da yunwa dake da diyan ko haka abincin nan akwaishi ba babuba kuma. Mommy yau fitina take ji tun jiya data dawo ta samu na dawo gidan ta fada min bakaken magana har tana ikirarin sai na rami ya fini shan iska a gidan nan. Shine yau da safe zan shiga kitchen na samu ta kulle komai tunda asuba wai kada a dora girki a gidan ta fadawa Laraba ni kuma ban koma ta kanta ba tunda nasan don ni tayi hakana. Haba Fati sai ki zauna da yunwa ai zaki kashe kanki ne idan kina haka yanzu bari muje mu samay ta muji may take nufi wai. Suraj bai bisu ba ya dan tsaya ganin Fati din yana kuma tambayan ta may zataci yaje ya sayo mata tace duk abinda ta samu yace kayan tea fa tace suna store acen muke ajewa fita ya yi ya mara masu baya. Sun shiga da sallama cikin isa ta karba masu sai suka tsaya gaisawa da ita tunda iyayye ne su bayan gama gaisuwan mommy tace munzo ne dama muji dalilin rufe kitchen da tsore din gidan da akayi wa mutanen gidan. Hajiya nan fa gida na ne ina da daman da zan rufe ko ina nake son don Abdul bai bar abinci da Fati a gidan nan ba tunda bai cata dawo ba ta dowo don haka sai ta jira idan ya dawo ya bata abinci ita da diyan ta suci. Karya kike yi munafukar Allah kuma baki isa ba wallahi muryan Suraj ne da batayi tsamani ba ya fado dakin yana zazzare mata ido a cikin hasala yake magana yana huci. Tare da daka mata tsayawa yana fadin ban makulin nan tun ban balbalaki yanzu a wurin nan in kuma sa sojoji suzo su kwashe ki sukaiki barikin mu su daure har ranan da miji ku ya dawo inji shiku idan shiya ai horo da yunwa haka. Kallo da tayi wa Suraj raga fuskan nan nashi ba imani a cikin sa zai iya aikata abinda yace a kanta tsoran ta Allah tsoran ta soja da sauri ta mike ta shige dakin ta yabi ta da harara. Yadawo da fuskan shi kan yar ta dake cin abincin da tayo masu take away a hanyan dawowanta gida ya watsa ma yarinyar harara da sauri ta noke kanta kasa ta kasa cin abincin da tun shigowan su dacin abincin ta take yi bata ko gaida su ba. Da sauri tafito daga dakin dauke da key din a hannun ta tana mika mashi cikin ladabi ya fisge a hannun ta har ya fara tafiya su mommy zasu bishi sai kuma ya juyo yana fadin. Ina ne kitchen din da tsore suke ki taso muje yau za a yi ta ta kare and idan bayan tafiya ko harara naji kin ma yar uwa wallahi yau ba ubanda zai hanani daureki a garin nan jiki na rawa ta bi bayan shi zuwa tsore din yace ta bude da kanta ta bude. Laraba da mai masu aikin gida namiji da ta dauko dan kabilar su can garin su wanda ya zama kamar CID din ta ga komi a gidan ko tana nan ko bata nan ya kira. Komai na tsore din aka fito dashi waje aka kasa uku yace Fati ta kwashi kashi biyu ita da diyan ta kashi daya ta dauka nata ne. Ga abin magana ba halin yi don tsoron soja da ke zuciyan ta tun da zasu shigo Nigeria sojoji suka latsu a hanya take tsoran soja inda duk ta ganshi. Yana tsaye a rike kunkurun shi da hannayen shi biyu yake tambayan fati akwai wani tsore da kitchen a gidan tace eh akwaishi a part din ta wanan nata ne ita fatin suke amfani dashi in generar. Kwashi naki kikai part din ki da sauri taja wani kwali da kyat tana fadin kasiye dauko mun sauran ta matsu tabar wiein wanan dan banzan soja mara hankali dake gabanta. Dama tun zuwan ta gida da ta fara ganin shi aka nuna mashi ita a matsayin sabuwar matar wan shi bai yi murna da ganin ta ba a fili ya nuna hakan kowa ya gani. Don shi kyamar irin su yake yi bai dauke su wasu cikakkun mutane ba a idon shi, yafi daukan mayaudara aduk inda ya gasu haka yake kallon su a yatsune. Shine dan uwan shi ja jini ya auro ya kawo ta cikin zurian su take juya mutane yadda ta ga dama a gidan da takaicin ta ya juya tafi bai shiga gidan nasu ba a lokacin mommy tare da anty Amarya suka koma gida bayan sun yiwa Fati nasiha kadan. Nan suka tafi suka bar Fati da tsoro a zuciyar ta fam sai dai abinda bata sani ba a halin yanzu Nafisa tafita shiga tashin hankali don tsoranta Allah tsoron ta Suraj soja. Wanda ta hango mugunta zalla cikin kwanyan idon shi abinda ya fadi tasan karamin aikin soja ne yayi shi ya aiwatar da abinda ya fada din dole ga magana nacin ta da zata fadawa Fati a yau sai dai babu halin yin hakan gare ta dole ta kawo ido ta saka mata a gidan tana jiran dawowan mijin nasu wanda zata sa ya ci fuskan Fati din a gidan. Ai idan sun san wata basu san wata da makirici zataci galaban su gaba daya don ta gane yan uwan mijin da iyayyen shi duk munafukai ne a kanta. Can gidan su hajiya sun koma kumshe da dariya a cikin su sai da suka shiga mota suka fara dariyan abinda suraj din yayi wa Nafisa . Yanzu sun gano takon ta Suraj ne zai dinga mata hukunci irin nasu na sojoji na rashin imani sun shiga gida nan suke bada labarin abinda ya wakana a gidan. Mama taji dadin har cikin ranta ko banza Suraj ya kwantarwa Fati incin ta yau wanda inba shi din ba, ba wanda ya isa yayi haka a zauna lafiya da ita tunda tayi niya. Maganan mommy ne ya dakatar da ita da taji abinda Nafisan ke fadi a lokacin shigan su gida da take fadin wai babu rabon su Fati da yayan ta ga abinda maigidan ya bari a gidan. Lalaima wanan matar tantiriya danta ya dauko mata ba kwai ba donge amma har take ikirarin cewa wai ba abincin su a gidan. Wani zafi na bakin ciki irin wanda iyayye ke ji a gamay da diyan su idan sun yi abu ba daidai a cikin alumma wanda sai uwa ko mahaifi suka san da irin zafin da mama taji a lokacin. Haka dai ta shige daki a dadafe bakin ciki da takaicin da matan dan nata ke kumsa mata a zuciyar ta yayi yawa kuma dan nata ya sani amma bai iya daukan wani mataki akan hakan. Wunin ranan haka suka kare shi da maganan Nafisa wanda hakan ba bakon abu bane agurin anyi sau tari da yawa sai dai na yau din ya banbanta da sauri don ta fito ta nuna masu karfin iko da izan da take dashi a cikin kan dan nasu . Wanda suka haifa suka tarbiyartar da hannun su kuma ya tashi da tarbiya suke saka ran samun farin ciki a wurin shi kamar yadda duk wasu iyayyen ke fata ga diyan su idan su samu Amma lokaci guda Nasifa ta shiga rayuwan dan nasu wanda ya watsar da duk wani rayuwan farin ciki da suke hasashen samu daga gare shi. Gashi a yanzu yana a cikin ganiyan samun duniyan shi wanda bai zauna ba tsaye yake wurin neman na kanshi a rayuwan wanda ba komai yakawo hakan ba sai addun mahaifa da yawaita ta sadaka akan diya yake bibiyan shi a yanzu. Don a baya in zata iya tunawa bata da aiki sai yawai ta sadaka fiye da kowa a gidan in anyi magana sai tace ba neman duniya nake wa kaina nemawa na baya nake madogara. Ga yawan taimakon na kasa da ita tundai idan ance yaro maraya ne sai mama tasan yadda takai alherin ta ga yaron ko ta saka yayan ta suyi mai alheri daga abinda suke dashi na jikin su mai kyau wanda zai farauta ran yaron da za a ba abin. Don Allah iyayye mata mu kula kada muyi sakaci da wanan dama akan marayu da muke gani zaki iya dafa kan yaro maraye zai ji dadin hakan da kikai mai har a cikin ranshi. Bawai duka maraye bane zai bukaci taimako wasa ma da dariya a gare su sadaka ce dan abinda zai farauta masu rai sadaka ne Allah ya bamu ikon yi ga maratun dake a kusa damu. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU🧠MIJIN BUZUWA🧠 3️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU NOVEL DIN NAN NA KUDI NE BIYA DARI UKU KO KATIN DARI UKU TA WANAN ACCOUNT DIN 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KI KIRA TA WANAN LAYIN 09026931792 KO 08036959257 ASHA KARATU LAFIYA YAN UWA. Tsaye take gaban mirrow tana gyara rigar da ta sa a jikin ta na tampha wanda akai mata dogon riga dashi mai wani launi kamar jikin damisa brown colour. Dinkin mai dan kwala sai da wuyan rigan V neck akayishi wanda yasa gaban ta ya fito dakyau daga cikin rigar kasan rigan ma an bude shi free yadda zata iya walla kafafuwan ta ba cikin matsuwa ba. Turare ta dauka ta feshe jikin ta dashi ta juya ta dauko gyalen ta dake saman godo gefe ta fesa mashi turare ta mayar a hand bag din ta dan kwali ta dauko ta dan daki lokaci tana daurawa take fuskanta ya fito tsonen a jikin mudubin. Duk wanan shirin da take yi ranta ba dadi don bata son zancen zuwa kaduna a zuciyar ta tafi son tayi rayuwan ta a gidan ubanta dake a cikin garin Minna. Inda gidan su yake a kwangila road asalin su su hausawa ne zamane na kakan ni ya kawo su garin minna har suka zama yan ainihin gari baza kace su bakin gari bane yanzu don kowa nasu anan aka haifeshi. Daga wajen gidan wanda irin ginan da can bayane na siminti wani murya ya kirata da fadin Khadija kina makara fa a cikin irin hausan mutane Niger shiba kananci kuma ba hausa pure ba do ya dan hade da surkin harshe. Muryan Khadija ne ke fadin mama shiri nakeyi gani fitowa yanzu da sauri ta karasa shirin ta jawo dan trolley din da ta sa tufafin ta a ciki tare da rataya handbag din ta a kafada ta fito waje. Kallon ta mama tayi wace zance a wurin ta khadija ta debo kyau da na saba kafin in ga mahaifin ta farar mace ce doguwa yar kabilan gwarin may kunkele dake a cikin minna din. Kallon yar nata tayi tace kin fi son ko yaushe kiyi tafiyan marance mama nina fison in shiga da yamma yafi ba wanda yasan zuwan ka sai dai a ganka. Maimakon tayi haraman tafiya sai ta ja kujera roban dake gefenta ta zauna kallon ta uwar tayi tare da fadin yaya haka kuma ? Banbara nake jira na aika a sayo dashi zan tafi bana son in mising din shine idan naje ke dai yanzu na gane baki son zuwa wurin yar uwan naki tunda kika girma kika fara karatun jamia . Ta dan ya motsa fuska mai kama da sallo ko yanga wanda ba haka bane kusan yanayin yan garin ne haka suke maganan su da kamar sallo da yanga tace ni nafison in yi hutu na a gida. Amma ita ya Amina kullun sai tace sai mutum tafi wurin ta hutu yanzu kuma ba da bane ban son ina missing din gida sosai murmushi kawai uwar tayi don tasan halin yar nata. Ba ajima ba mahaifinta ya shigo gidan yana ganin ta yace a Khadija an fito ke nan eh baba zan tafi hannu yasa ya fara laluban aljihun shi sai ya fito da dubu biyu ya cire guda ya miko mata. Kai ta girgiza mai tace baba ka barshi kawai kudin da anty ta turo min zai ishe ni na gadone a daidai lokacin yaron da ta aika ya sawo mata banbara ya iso da leda a hannun shi yana mika mata da canjin karike canjin tana bude ledan ta debo banbaran ta mika mai ta mike tana gyara jakkan ta yaron ya taima ya fita mata da kaya ida ta tare Napep zuwa Abdulsalam garej . Tana isa saura mutum daya ta biya suka shiga suka kama hanyan garin kaduna yamma lis suka shiga gari lokacin kuma akai hadarin marancen nan da Nafisa ta dawo ta samu Napep din da zai kaita unguwar da yar uwar nata ke aure wanda kusan rabin zaman ta a baya a nan tayi shi sai data girma ta koma gida karutun da take yi Abuja yanzu shine silar mayar da rayuwan Khadija gida Niger state. Tun ranan da khadija tazo kaduna bata fita ba tana daga daki sai falo indan ta fito ko kuma ta shiga kitchen tayi masu girki a gidan. Yau da yamma ya Amina ne ke kwala mata kira tana zaune tana cin banbara da tayi worming din shi kamar yanzu akayi shi bai kwana ba. Ya Amina gani ta fito tana fadi cikin ranshin kallon fuskanta don Allah zo ki shiga gidan su mommy ki karbo min sako tace yanzu in tura a karbo min. Fuska khadija ta ya motsa tace ni ban shiga ba tunda nazo banje na gaidasu ba Amina tace wai khadija may ke damun ki ne haka ? Ke a rayuwan ki sam baki son shiga jamma a ban san inda kike dauko wanan rayuwa naki ba haka cikin bacin rai ta juya dauko gyalen ta kayan da tazo dasu garin ta kara sakawa a jikin ta. Yaran anty nata biyu ta, ta kira su rakata gidan da aka aike ta din fitowan su bakin get din gidan yayi dai da zuwan wata mota a guje ta watso masu ruwan dake kwance a wani dan rami saman hanya. Cikin bacin rai Khadija ta dago kai tana fadin you are very stupeid bakya gani ne kika watso ma mutane ruwa haka. Horn kawai Nafisa tayi masu ba tare da ta tsaya khadija tabi motar da hararan takaici tana dan kakabe riganta da ruwan ya dan taba a lokacin. Raina yayi matukar baci haka muka doshi gidan mutane ina mita wani saurayi dake tafe a bayan mu naji yace yar iskan buzuwan nan ne haka take tuki kamar mahaukaciya wallahi. Dan juyawa nayi na kalli mai maganan nace sannu yace yawa bata dai zuba maku ruwan sosai ba ko nace kadan ya taba mu inayi har lokacin ina kakaban ruwa a jikina. Gidan muka shiga wanda har lokacin raina a bace yake da buzuwar da naji saurayin nan yace min da sallama muka shiga gidan. Wanda sai kawuce kofan falon gidan kabi wani dan siririn hanya da zai sadaka da cikin gidan da muka shiga wanda babban gida na ba yau bane farkon shigana gidan don duk zuwa nayi sai anty ta aike da gidan ina shiga akai akai yanzu tunda na girma bani shiga idan nazo sai da wani dalili. Sallama mukayi inda kofan uwargidan ne fara isa sai na mama daga can ciki sai kuma wasu biyu dake kallon nasu din na mommy dana anty Amarya ke facing din su. Hajiya ummi da yaranta nake jiyo hayaniyar su daga kofan part din ta na dan matsa daga kofan dakin ina gaida su dakyat aka amsa min ban tsaya ba na wuce. Lekowa akayi daga dakin ummi don ganin mai gaidasu din da bai shigo ba bata gane ni ba alokacin har nakai kofan mama shiyasa ban son shiga wanan gidan don yawan dake garesu kuma sai kabi kowa kagaida shi dole don hadin kai irin na matan gidan. Koda baka gaida mutum ba wanda kaje wurin shi zaice dakai ka ko gaida mutanen gidan sanin haka danayi yasa na fara binsu daga daga ina gaida su. Dakin mama ma a kofa naja na tsaya ina fadin ina kwana mama ta amsa min daga ciki tana fadin waye shigo mana ciki. Dole na shiga daga cikin dakin tare da kara gaida ita inda nakai gwiwana duka biyu a kasa irin gaisuwan mu na mutanen Niger. Daga kuryan dakin ta aka fadin muryan wa nake ji kamar khadija Adamu da sauri mai maganan ta fito falon ida nake wani irin ihu ta sake a lokaci daya tare da kwalawa binta kira tana fadin ga khadija Adamu ashe tana garin nan mukayi maganan ta jiya. Murmushi nayi ina dagowa daga gaida mama da nake nan suka shiritar dani nace anty ta aiko ni wurin mommy. Bayan nagaida amaryan su ne na wuce zuwa dakin mommy ta tareni da fara anta mun dade tana jana da hira wanda ni ban iya sake jiki dasu muyi hiran sosai saboda mutunci da girma da nake gani a idona. Sakon ta dauko min na fita mukai sallama dasu nan suka rakoni suna dan taka min in baki mantaba mai karatu na fada maki a nan kaduna nayi rabin rayuwa na. Kamar abin tsokana wanan motar dai ne na dazun ta dawo a guje ta kara yin facali da ruwa a take nace wanan wani irin iskanci ne wai haka ? Har motar ta wuce sai ta dawo baya a hankali zuwa gare mu a lokacin zainab ke fadin Nafisa ce fa ta dawo zai tai muna cin mutunci kila taji zagin da khadija tayi ne. Gab damu ta tsaya tare da sauke glass din motar wata farar mata nagani ciki tare da wata zaune a gefen mai zaman banza. Tace wace yar iska ce cikin ku take zagina shiru naji sunyi suna soke kai kasa nan san lokacin da nace mata kece dai yar iskan da baki san darajan mutane ba kika gudu da mota haka a wulkance cikin gari kamar yar koyo. Ke tafadi a zafafe tana kokarin bude kofan motan da sauri naji su Binta da zainab na fadin yi hakkuri anty bata san ke bace . Cikin zafin rai nace ke wacece da zaki watsa ma mutane ruwa kice kada ayi maki magana wallahi ko diyar shugaban kasa kike sai nayi maki magana . Karasa fitowa tayi daga motan tana fadin ke yar gidan uban waye a garin nan take raina ya kara baci nace kedin yar gidan uban waye da baki da tarbiya fada min naki in fada maki nawa. Fisgan hannu na Zainab keyi ni kuma ina turjewa don ban ga wani kimar ta da suke gani ba idons a lokacin don sam ban da tsoro akan gaskiya na. Ke yar waye da zaki tsaya kina fada min magana son ranki nace ni yar gidan ubane ke kuma cewa akai titin na gidan ubanki ne da zaki dinga gudu kina watsa ma mutane kura da ruwan titi. Yadda taga ina yi sai ta tsaya tana kallo na kafin ta mayar da fadan akan su Binta da zainab din tana fadin zamu hadu da kune wallahi don nasan da sanin ku take min hakan. Nace wai kun san wanan banzan ce da kuka tsaya tana fada maku maganan banza saman hanya haka ? A harzuke tace nice banza nace an fada maki idan ba banza kike ba may kike zaki tsaya kina ma mutane son raki ke gaki mai kudi ki takamu ki wuce lafiya kin taki banza ko ? Zaki gane kurenki wallahi wani kallon banza na watsa mata nace sai dai mu gane kuren mu amfada maki don kina da kudi zanji tsoron ki ne ko may kudin ki bai damay ni ba tunda ban taba zuwa wurin ki neman wani abu ba. Matar da take cikin mota ne taji abin yayi yawa kuma dukkan mu munki bari ta bude mota ta fito tana jan ta tana fadin haba Nafisa zaki tsaya kan wanan karamar mara kunya kuna raba hali a saman hanya ai sai ta ja maki raini ga jama, a. Kuta tayi ta watsa min harara na mayar mats ta shiga mota tana fadin zaki san kin shiga hurumi na nace inga alheri . Fisgan mota tayi sai da yayi wani irin kugi suka nufi hanyan cikin gari zainab tace wai Khadija kin san kowacece ita din ? Wacece kuwa banda kila matar wani ko wata kusan gwaunati shike nan don muna kasa sai ta rena mu Binta ce ta katse ni da fadin matar yayan mi ne kishiyar anty Fati. Inda motar yabi nabi da kallo nace yanzu wanan matar matar dan uwan ku ne wallahi na dauka irin matan bariki din nan ne masu zaman kasu nima ban san yaya akayi idona ya rufe haka ba naci mata mutunci. Nan nake fada masu abinda tayi muna da zamu shiga gidan su yanzu kuma ta sake maimaita muna shiyasa raina ya baci don naga kamar da gaiyya tayi hakan amma kuyi hakkuri don Allah. Binta tace ai mu yau kin muna daidai wallahi don ba karamin dadi naji ba da kikaci mata mutunci nan a gaban mu. Mun da jima a tsaye dasu karshe mukai sallama muka shige gidajen mu har lokacin ina da zafin matar nan a raina. Nafisa ko sai fada take kawar ta na bata hakkuri tana fadin ban son ki biye mata ba tunda kinga kannen mijin ki a wurin may yuyuwa tasan ki ke baki santa ba. Zanyi maganin ta wallahi sai ta rena kanta zata san ba a taba ni a zauna lafiya ko wacci tuwo dani miya ya sha na san dai ba yar gidan uban kowa bane ita. Su zainab na shiga gidan su suka fara bada labarin arangaman mu da matar yayan nasu nan mutanen gidan suka fito suna sauraren su. Mommy tace kai amma wanan yarinyar wallahi ta burge ni sosai yau da haka Fati ke daurewa ta mayar mata da martani da abin nata ya rage. Anty amarya tace ai ba zata iya ba ne don ta riga tasa mata tsoron ta a zuciya kuna ganin a banza ta bar mutane ne haka da kowa ke shayin ta. Ummi tace kwarai ai irin su ba a banza suke barin gida ba sai sun kama bakin kowa sun daure yadda ba mai iya motsawa a kan su. Sai lokacin mama tayi magana tace aini wanan yarinyar ta gama shereni wallahi tayi min daidai yanzu zata san in ta daure bakin wasu bata iya daure na wasu. Nikan da muka shiga gida ya Amina tana daki mika mata sakon nayi a cikin wani dan leda wanda ban san abinda ke ciki ba dakina nakoma na fara rage kayan jikina. Na mayar da dan riga mai karamin hannu da bujen body hook dana cire sai hula dana dora a kaina kitchen na nufa don dora abincin dare saboda yamma yayi. Kafin wani lokaci har na kammala na gyara wurin na mayar da kauan da nayi aiki a inda suke daki na kofa nayi wanka kafin a kira sallah na fito na canza kayan jikina. Kananan kaya na kara sawa a jikina don idan ina gida sune kayan sawa na wayata na jawo ina duba sakon dana samu daga abokaina da muke karatu dasu. Lokacin sallah yayi na mike na gabatar da sallah ban daga ba sai da na yi har isha,i na nike abin sallah na fito din in ba yaran anty na abinci. Anty ce ta fito daga dakin kwanan ta muryan ta naji daga baya na tana fadin har kin fito eh kawai nace mata ba tare da na juya ba ina zuba abincin a plate na mika ma yaran dake zaune suna jirana. Juyowa nayi inda nake tsanmanin take zaune nace in zuba mata abincin yanzu ne kallo na naga tanayi cikin mamaki tambayan da ta jefo min a lokacin ban zaci ji ba. Khadija may ya hada ki da buzuwa yau kin ko san waye buzu kin san ko matar waye don Allah ki rufa min asiri tunda nake unguwan nan ban taba fada da wani ko wata ba ina jin tsoron rashin tsoran nan naki wallahi. Kara daure fuska nayi nace ina ruwa da wata buzuwa ko baturiya take ba zan yarda ta wullakantani ba ga banza don tana takama tana da kudi tunda ba kudin ta nace ta bani ba. Don Allah dai ki bari ban son irin haka ni na dauka kin bar halin nan naki yanzu da kika girma ashe halin na nan baije ko ina ba. Mijin ta fa na iya sakawa a kore mu a unguwan nan wallahi don suke fada aji yanzu a garin don Allah dai ki bari. Kamar zan yi magana sai nayi shiru ranan banci abinci ba saboda haushin buzuwan nan dake ci min rai haka na kwana da tunane kala kala a raina. Hajiya mama haka ranan itama ta kwana tana tunane a ranta kan yadda zatayi da danta akan buzuwan da ta zama masu fitina da masifa a cikin zuri,an su. Dan ta ya zubar mata da mutunci da kimar da mutane ge gani nata duk a kan auren wanan matar da bata darajja mutane da halin ta. Da safe nafito na hada breakfast har na gama ya Amina bata fito ba tana daki na gyara ko ina na gidan sai na koma na shiga wanka na fito na shirya tare da hayewa gado in dan huta. Sai lokacin na fara jin hayaniyar su a falon gida alaman sun tashi ke nan daga barci hakan baisa na fito ba sai kara lafewa danayi saman gadon barci ne ke son dauka na a lokacin. Muryan ya Amina naji na bude idona a hankali ina kallan ta daga inda nake kwance nake mata ina kwana murshi tayi ta karaso gare ni tana fadin. Har kin gama kin kwanta yau barci ne ya dauke ni tana fadi tana kaiwa zaune a saman gadon da nake kwance jin banyi magana sai naji tayi murmushi . Tace khadija fushi kike yi akan maganan da nayi maki jiya akan buzuwan nan bata da mutunci ne khadija shiyasa kowa ke tsoron shiga tsabganta don mijin ta zai iya keta ma kowa a kanta yadda yake son ta. Dagowa nayi nace OK shike nan don mijin ta na da kudi ko mulki ba zanyi fada akan dama na na dan adam ba murmushi naji tasake yi tace khadija ina raba ki da shiga tsabgan irin mutanen nan. Kai na kawar gefe ina hade miyau takaici da yazo min a lokacin haka abin yai ta cina har na gaji na sake na manta da wata can a zuciya. Jin shiru da su Binta sukayi yasa su ranan biyo ni gida a falo suka samay mu dukkan mu nan muka zauna har anty muna hira suna min korafi wai kullun ina gida kumshe ban fita. Zainab tace kodai kina tsoron haduwan ki da Nafisa ce nace waye Nafisa kuma tace matar yayan mu mana da kuka kwasa ranan . Oh kuce mi buzuwa mana ai sai in gane ba Nafisa ashe sunan ta ke nan ni na fi gane ma buzuwa ai Binta tace ai bata son a kira da buzuwa shiya sunan ya mutu a bakin mu. Ranan da ra kai kara wajen yayan a gidan bakiga irin fadan da yai muna ba ni tun lokacin gidan ya fita raina wallahi. Ashe ya zama mijin buzuwa ke nan yar sani in fika wai agola da rabon gida ina kika san yar sani in fika ne ai sai kin ga yadda ta mayar da anty Fati a gidan. Ita da mijin ta yanzu ta koma yar kallo a gidan ko dan aikin gidan yafi ta daraja a gidan kwanan fa sai da ta fito aka maida ita kin san may ? Da ta koma bata gidan tana dawowa sai cewa tayi wai uban wa yace ta dawo gidan sai ta kama kitchen da komai tarufe na gidan ta hana ma anty Fati da yaranta. Sai lokacin anty dake gefe ta saka baki a hiran da mukeyi a falon tace amma samun wurin nata yayi yawa wallahi nace wai wace anty fati kuke magana haka ? Wanan da ta taba haihuwa har mukai fati daku a baya dan tunane nayi nace nagane ta itace mijin ta ya auri wanan matar wallahi itace inji Binta zainab dai sai dakilan wayanta takeyi tana charting. Anty ce tace yanzun yaya akayi akan abincin nan dai take fada muna yadda suka kwashe da suraj anty ce ke dariya ni banga abin dariya ba tunda ba dukan ta naji yayi ba. Sun kai wani lokaci suka ce zasu tafi na mike na dan taka masu har bakin get din gidan anty na na dawo ciki. ZAINAB IDRIS MAKAWAYau ta tashi tana ta farin ciki maigida yace zai dawo garin sai abubuwan taron shi akayi ita da kawayen ta a gidan. Fati bata san abinda ke wakana ba sai dai gani tayi mata da maza suna ta shige da fice a cikin gidan nasu wanda duk girman shi bai hana a jiyo ihun da suke yi ba a lokacin wai duk cikin murna ne hakan. Hajiya ce ta aiko gidan a tambayi Fati mai ke faruwa ne gidan nasu amce anga mutane na ta shige da fice a gidan. Fati tace itama ba ta sani ba itama dai haka ta gani suna shiga suna fita kawai a gidan amma bari ta tambayi laraba taji ko ta sani zuwa tayi ta kira Laraba take tambayan ta abinda ke faruwa tace wai maigidan ne zai dawo shine ake shirin taron shi. Mamaki Fati taji a lokacin tace yanzu dawowan na yaya Abdul shine shine akewa wanan hiddimar haka ikon Allah ikon gaskiya. Hajiya mama ma da taji fada tai tayi tana zage zage sai da hajiya ummi da mommy suka ce ta sa masu ido ga duk abinda take yi wani abin saboda neman baki take yin shi. Ran hajiya ya baci sosai daki ta shige saboda bata son yawan surutu abin kunya abin takaici wai dan da ta haifa da cikin ta a gaban idon su tantirai ke wanan wasan a gidan shi. Yau ina tarbiyan da tai mai a matsayin dan ta na fari a matsayin shi na jikokin malaimai bu sanadin mace ya samu raini a rayuwan shi macen ma shu,umar mace da tafito yawon barki. Muryan mommy ya katse ma mama tunane tace nazo ne in ji haka zamu kyale Fati ita kadai a cikin tantiran matan nan. Mama ta nisa tace may zanyi hajiya karima mommy tace ni a gani na yaran nan suje suma su zauna a dakin Fati din kin ga ko suna da niyar mata wani abinda ba daidai ganin idon su zai sa su fasa. Abinda kuka yi shawara akai sai ayi ni banda abincewa don wanan yaron ya gama bada tako ina mommy tace kada kice haka yaya kowa yasan ba halin shi bane juya shi akayi ya koma haka. Murmushin takaici mama tayi tace haka dai kuke cewa amma har da raayi kin san shi tun farko da son farar mace ai doguwa. Shine dai abinda ke rudin dan naki kawai ba wani asiri wallahi yaya mudai bishi sannu har a samu ma fita yaran ta kwala ma kira duk suka hadu nan take fada masu tana son su shirya gobe idan yayan su zai dawo su je su zauna da Fati a part din ta sai ta sake cewa ina ganin zamu biku ni da antyn ku amarya zan buga waya sauran uan uwanku suzo ba zata zamuyi mata kamar yadda tai muna bazata itama bata fada wa kowa da shafe shi ba. Nan dai suka taru sukai ta shawaran abinda zasu yi bada sanin buzuwa ba don su rama abinda take shirin masu din na iza masu takaici ta nuna masu su ba kowa suke gare shi ba yanzu. Muna falon antyna zaune karatu muke da yaranta ita kuma tana duba littafinta na islamiya don tana hadda a wata makarantar matan aure dake unguwar su. Wayan ta ne yai kara tace dan ta dake kusa da wayan ya miko mata jin ta ce hajiya karima mun wuni lafiya yasa na gane da mommy take waya don aminiyar ta ne sosai mama kuma a uwa ta dauke ta a gidan tafi shiri dasu su biyun. Bandai ji may suke fadi ba bayan gaisuwa da sukayi sai ji nayi antyna tana fadin kwarai kuwa hakan yana da kyau sosai mommy in Allah ya yarda goben zan shigo dani da khadi tunda tana nan sai muzo a cika taro da mu muma. Dagowa nayi na kalli antyn nawa don jin abinda tace bayan sun gama waya ne take ce min ikon Allah wai dan gidan hajiya mama ne ya samu karin girma bai fadawa yan uwan shi ba sai gani sukayi matar shi tana ta shirin buki ita da kawayen ta. Haushi naji a raina nace shiya sani mana duk wanda ya wullakanta iyayyen shi ai kan shi yai wa wasu ma suna can suna neman iyayyen ido rufe basu samu ba. Shi ya samu Allah ya bar mashi nasa a raye shine zai wullakanta su antyna tace ai shi na gani nima wallahi. Shi fa dama haka yake kamar mai tsoron mutane yake hadewa da buzuwan nan da yayi sai abin ya kara bulakucewa mai. Yanzu hajiya karima ta kirani ne tana fada min wai gobe tana gayyatan mu zuwa gidan nashi don suma zasuyi nasu taron a part din Fati. Kai amma suma dai basu da zuciya wallahi akan may ba zasu saka mashi ido suga iya gudun su ba ai mutum baiyi sai da nasa. Ni dai ba zan je sai kun dawo don babu komai wurin nan sai tarin takaici tace a a don may bazaki ba ba gaiyyatan mu sukayi ba muje mu mara masu baya a cika taro da mu muma. Ban iya bata amsa ba sai ma cewa da nayi da yaron ta kana jina ko muci gaba da karatun mu dajin wanan abin takaicin. Duk abinda muke sai na gaza yi sai cewa nayi da ita wai mashi wani irin mutum ne haka wai tace ai zaki ganshi gobe idan munje gidan. Washe gari ko da wuri anty tasa muyi aiyukan da muka saba a gida muka gama komai akan lokaci. Tace mu shirya zuwa karfe uku mushiga gidan su mommy din raina bai so ba haka na shirya dole cikin wani buje dariga na atampha da nayi dinki shi a abuja atamphan pink ce don haka shirgan pink colour nayi na ni kaina nasan kayan sun karbe sosai don sun fitar min da sura na fili. Muka fito muka rufe gidan muka nufi gidan da kafa saboda ba nisa sosai abin mamaki sai samu mukayi duk yan uwa da abokan arziki sun hadu a family house din nasu. Mun dan shiga dakin mommy ita kirjin abin nikan ganin duk matan aure ne a ciki yasa naja yaran anty muka wuce dakin mama wurin su zainab. Ba wasu mutane a dakin sosai sai ita da yaran ta kuma da alama kamar wani magana mai muhiamci suke a lokacin sai naji na tsargu ga yadda na gansu din a lokacin saboda kar na takura masu dana gaida su sai na mike zan fice daga dakin. Muryan mama din naji tana cewa a a dawo abinki ki zauna ai ba wani magana muke yi ba cikin muryana da yake kamar sallo da yanga nace No bari kawai na tafi daga waje ai. Binta ne ta fito daga cikin daki tace muryan ki naji yasa ni fitowa yanzu wai rangas wanan irin kwalliya haka ai sai ki sa kallo ya koma kan ki. Guntun murmushi nayi nace da ita silly girl ina zainab ashe tana kusa da mama zaune saboda cika min ido da sukayi ne banganta ba tace gani nan bakiji ina cewa khady ba da kika shigo. Binta ne tace mu shiga daga ciki mu zauna sai maman tace a a tazo nan ta zauna abinta ki sakata ciki kamar kunshi matsa min take yi wai nazo na zauna a kusa da ita ban hau kujeran ba sai na zauna a kasa kusa da kafafuwan ta. Ina zama tace da yaranta masu aure mutum biyu kun ganta nan ranan ta burge ni da ta tsaya taci wa yar iskan yarinyar nan mutunci ido rufe akan titi taso ta kawo masu rainin hankali a saman hanya ita ko ta wanke ta tas wallahi. Anti fauziya tace kin min daidai wallahi dama ai ganin ana daga mata kafa ne yasa takewa mutane iskanci wai ita a dole matar mai kudi. Nan dai suke ta maganganun su a wurin kamar daga sama muke jiyo haya niya wata ta leko tana fadin ga yaya Abdul nan ya iso kuma nan ya fara shigowa. Fita suka kama yi a raina nace ashe shiyasa yake maku abinda yaga dama saboda hakan da kuke mai nidai ina zaune a kusa da hajiyan tasu. Ganin yaran nata sun fita yasa ta mayar da hankalin ta a kaina tana fadin dada dai yanzu khadija gudun mu kikeyi baki ko son shigowa gidan nan in kin zo na dan yi murmushi nace no mama ba haka na bane kawai dai daurowa ne. Nan take dan jana da hira cikin rashin sakin jiki nake dan bata amsa a hankali ganin dandazon mutane sun nufo dakin nata ne yasa na mike zan bar wurin tace dani koma ki zauna abinki yanzu fita zasuyi idan mun gaisa. Wani farin mutum ne ya dumfaro kofan zai shigo kamshin turaren shi kawai ya isa ka dago kai kaga ko waye maishi nan dandazon yan uwa suka dare a kofan dashi da wani suka shigo dakin kawai ba wanda ya shigo bayan su sai ni da mama da yaron anty na da muke zaune a dakin a lokacin. Mayar da hankali na na nayi ga wayana dake hannu na a lokacin ban daga na kallesu ba suka zube kasa suna gaida mama din cikin girmamawa. Tace dashi bayan sun gaisa ashe kana tafe baka fadawa kowa ba harda samun abin arzikin da kayi bamu kai girman da zaka sanar damu hakan ba a yanzu sai dai muji ga shanun talla ana fadin wai ka samu karin girma a ma aikatar ku. Yace ba hakkana bane mama bari nayi sai nazo in fada maku dama ashe ma kun riga da kunji abinda ba a ko rantsar dani ba tukun . Daidai lokacin na dago kai cikin jin haushi na watsa mashi wani irin harara ban sani ba ashe idon shi yana kaina a lokacin cikin rashin sani na nayi saurin dukar da kainanajigina da kujeran da mamake zaune tare da mayar da kaina ga wayana da nake duba. Wanan wata yarinyace haka miskila har da zata iya hararana da nuna min ko in kula yace a ranshi in dai zaka sake hali wallahi kasake mudin dai mune iyayyen ka ba wasu ba. Yanzu ka duba fadin gidan nan kaf yan uwa ne da abokan arziki da mommyn ku ta gaiyato suka zo don ka idan ba a zumunci waza ka gani a nan yanzu kai hakan ma da sukai maka bakaji dadin shi ba. Ace mutum babu nashi wanda ya ja a jiki sai dai yan duniya masu maka rudi da duniya kaina na kada alaman fada mashi dai mama na tabe baki na. Wayana ne yai kara a lokacin baba nane ya kirani da sauri na dauka cikin kashe murya nace daddy yau kaji ban kiraku ba ka kirani yanzu nake son kiran ka a yanda nake magana da mahaifina cikin sakewa da walwala kamar ina magana da wani sa a na sai mutum ya saurara zai iya jina don kada in damay su in hana su maganan da suke yi din. Muryan su naji yana fadin mama zan shiga gida in huta don ban isa can ba nan na fara shigowa in gaida ku. Har lokacin yanayin ta ba dadi Allah ya sauwaka naji ta fada masu tace Yusuf ashe kuna tare yusuf din da ya dukar da kan shi tunda mama ta fara mai fada sai a lokacin yayi magana yace eh mama tun da ya bugo min zai dawo ai naje abujan taron shi. Mikewa sukayi zasu bar dakin tace kaji an mayar da Fati dakin ta ko hakan yasa shi tsaya yace naji mama. Wani sabon hararan na dago in aika mai still muka kara hada ido yasha toka a lokacin yace zamu tafi Allah ya tsare ta kara maimaita mai suka fita dakin. Ajiyan zuciya na sauke bayan fitan su mama din tace kin ga yayan ku ko yau khadija nasan kila baki san shi ba. Murmushi kawai nayi mata nan sauran diyan suka shigo suna fadin su mommy sun fita ance gidan ya cika da mutanen Nafisa don haka mu zamu wuce can. Kafin ya gama ganawa da baba su zainab suka fito suka ce in tashi mu tafi Allah ya gani da zasu bar ni in zauna wurin mama da zai fi mun dadi don ban son hayaniya da yawa ga matar gidan da mai gidan da nake kule dasu a raina. Ganin mota zamu shiga yasa na dauka gidan yana da nisa sosai ashe ma ba wani nisa muna shiga mata yan duniya ne birjit a farfajiyan gidan zazaune saman kujeru farare sai kidan dj dake tashi kamar wani buki akeyi mai muhinmanci a gidan. A raina nace kudin banza a bazan suke tafiya mommy na gaba ita da anty amarya muna biye da yawan mu a bayan ta muka shige gidan. Nan naga duniya a cikin gidan sai kace ba a garin kaduna muke ba part din Gatin muka shiga a sama suke dukan su mun samu tayi kwalliyanta ba laifi nikan a nan falon ta na zauna zainab ma da namu yazo daya sai ta zauna a wurin. Anan wasu suka zauna basu shiga dakin ta ba su anty na kan an shige daki nace magulmata a raina jefi jefi muke hira da zainab muna dan dariya . Sai gasu sun fito suka ce a sauka kasa a falon kasa zamu jira shi koda muka fito ba kowa a falon sai zuwa can Nafisa da mutanen ta suka fito cikin mamakin ganin yan uwan shi da na Fati wanda bata zaci haka ba yasata daure fuska atake ta nuna kinshin ta karara a wurin. Gashi kuma har ya iso gida a lokacin nan su mommy suka ja Fatin zuwa taron shi daidai kofan shigowa falon gidan mai dan karen girma da tsaruwa. Duk abinda su mommy suka ce tayi shi tayi a wurin aka dauki ihu da tafin yan uwa itama tazo da nata tawagan sukayi iskancin su da sowace sowace irin na yan duniyan mata shiko yana wani washe baki yana runguman matan nashi. Ranan dai naga kishi kara don buzuwa a gaban kowa ta kwace hannun mijin su daga gefen Fati din ta rungumay shi ita kadai. Juyawa nayi wurin zainab nace wanan tsohuwar may take nufi ne haka wai tsuhuwar da nace yaba sauran yan matan da muke tare dariya duk aka kwashe da dariya. Ido rufe ta kallo mu tana rugumay dashi a jikin ta kamar wani soko sai lumshe ido yake yi tace kada ku kawo min iskaci a gida na don ban gaiyace ku ba. Ai ba gaiyyan ki muka zo ba mu wane mu da gaiyan ki kin ga mun yi maki kama da mutanen banza ne duk wurin akayi tsit ana kallon mu . Wai wanan yarinyar yar gidan uban waye a garin nan nace yar gidan ubanki ne a garin nan tsaye kowa yayi yana kallon mu ta fara fisge fisge wai zata zo ta dake ni a wurin . Ko dar banji ba na ce da turanci too hell with you wallahi don ba don ki muka zo gida idan kikayi gigin tabani yau sai kin raina kanki wallahi . Anty Fauziya tazo ta jani da mommy suka hau sama dani shi kuma sai cewa yake ta bari bai son fitina ita fa ta tara mutane tace ba gaiyyaci kowa naka ba don nasan halin su ba sona sukeyi ba. Saman yabi da kallon mamaki yadda karama dani na iya tsayawa a gaban su nayi wa yar lalai matar shi tas na barta nan tana hargowa. Anty na duk ta tsure sai fadi take ku bari mu tafi gida khady dama nasan halin ta bata daukan wulakanci tun tana karama. Kowa a wurin fadin albarkacin baki shi yake yi mun dade a dakin kagin mu fito zuwa gida muka bar wasu anan sai da su Binta sun fito tare damu sai nuna ni abokanta sukeyi da muka fito. Niko ko a jikina don ban damu ba ban biya gidan su ba gida muka wuce mommy taba anty wani leda dake da kaya a ciki ni har nayi gaba a lokacin har muka kai gida ba wanda yayi magana a cikin mu. Sai bayan mun yi sallah magariba da ishai muka fito falon har lokacin ban sake ba raina a bace yake da abinda ya faru dani. Zaman mu shigowan su zainab da Binta da Amira suna shigowa suka saka dariya gaba dayan su anty tace dasu yau ai ni naga abin mamaki gun khady mata da gidan ta ki ce zaki fadan karfin hali. Nace anty wallahi ko ba yau ba wanan matar tai min ramawa zan yi haka kawai zan tsaya tana zagina akan may wata tafi asali. Ni dai don Allah ki rufa min asiri a garin mutane khady ki koma gida lafiya wanan abin da may yayi kama Binta tace anty mu ai tayi muna daidai wallahi. Baba ma da yaji cewa yayi wai waye khadija din nan har cewa yayi a kiraki mukace kin tafi gida. Anty tace kinji ko wallahi khadija ki rage wanan girman kan naki don ba zai kaiki ko ina ba wallahi tace ai bayan dawowan mu ayin fitina sosai a gidan dasu anty Fauziya da suka tsaya suma sai da akai rashin mutunci dasu yau. Wuri ta samu mana shiyasa takewa mutane rashin mutunci son ranta inji zainab ai yau naji mamaki da bai biye mata ba da dane ai rama mata zaiyi. Sai lokacin nayi magana nace ashe na manajo ne yayan naku cabdi dako yau yaji magana wallahi binta tace da zaki iya ramawa nace mai zai hana iyaka dai yasa a kama ni ko zainab tace wane shi. SEENABUA raina sai mamaki nake wai wanan matashin da nagani wanda bai wuce ace yanzu zaiyi auren farko ba ke da mata har biyu haka. Buzuwan nan dai da za a zauna a fadi gaskiya tana iya girmay mashi daga shi har matar shi sai idan ance yanayin jikin su kawai da ba a gane hakan. Ita kuma Fatin baka ce sai dai da zata zauna ta gyara jikin ta banga abinda buzuwan nan zata gwada mata ba sai dai kasshh yanayi irin namu na matan hausawa yana cin rayuwan ta da haka nake hango buzuwa ta kwace mata miji . Yau da gobe sai Allah dama sati uku zanyi don hutun ba yawa shiyasa ban so zuwa kaduna ba a wanan lokacin amma anty na ta dage sai nazo ita kadai ne a gida mijin ta yayi tafiya. Ashe kuma da rabon mu kwasa da matar mulki ne a garin ya kawoni don haka shiri nake inda ba komai nake shiryawa sai kayana don ban daukan provition da ga gida sai na tafi can nake saya. School zan wuce direct sai nakwana biyu zan shigo mina in masu weekend in kwashi abinda na samu in koma bayan kwana biyu don haka nake ta shirin komawa makaranta a lokacin. Kwatsan da safe muna karyawa saura kwana biyu tafiyana sai ga wayan mommy ta bugo ma anty wai Fati ta dawo gida yanzu haka tana nan gidan su naji anty na fadin o o Allah yanzu matan nan da karfi da yaji sai ta raba wanan auren take nufi. Banji may mommy ta fada mata ba nadaiji tana fadin gaskiya haka nane idan abu yaki sai ayi hakkuri kada zumunci ya baci idan abin ya sake shi inda rabon komawan ta gidan sai ta koma. Bayan ta kashe waya tace mummy tace ki shiga kafin ki wuce kada ki tafi baki sallamay su ba nace haba anty may yasa kika fada mata zan wuce ai sai yazama kamar roko idan naje sallaman su. Kai ta girgiza min tace ba haka halin su yake ba dauka na sukeyi kamar wata ta gida a gurin du duk zuwa kikayi kika wuce sai sunyi min korafin hakan. Shiru nayi sai tace o Allah sarki wanan buzuwan dai ta hana Fati zama gidan mijin wai yanzu kuma ta kara fitowa tace bazata koma ba. Dudufa baifi wata da ta koma gidan na yanzun kuma ta kara fitowa jiya wai sai dai na shiga inji may kuma ya hadasu fada yanzu. Takaici bai barni nayi magana ba sai dai a zuciyana nake bankawa mijin zagi da rana su binta suka shigo gidan mu anan muke jin labari wai tunda ya dawo buzuwa taki bari ya ke be da fati hakan bai isheta taja Fatin da fada har tana fadin sai ta kashe ta. Shiya ba Fati tsoro tace barin gidan yafi mata nace shike nan ta samu galabanta ai ta kashe ta din idan ta isa mana. Gaskiya matan nan ta samu wuri da yawa wallahi nace shiko sokon yayan naku fa may yayi a kai tace jiya baban mu ya kirashi sai cewa yayi shi yagaji da halin fati tana bata mashi suna. Ai wallahi idan da nice tace sai ta kashe ni da na nuna mata hauka ke matsorata ne fa iskancin abaki yake masu kawai Fatin dai ne wallahi she is to slow . Anty tace khadija baki san aure ba fa shi wanda ake abin a kansa bai nuna wani feeling din shi akan ta gara dai da ta hakkura ta basu wuri. Zata tafi nace barin bisu daganan in masu mommy sallama tun ranan da mukai fada da buzuwa ban sake shiga sai yau da zan tafi sallaman su da anty ta matsa min. Tsab na shirya na fito cikin wani dogon riga mai hannu shara shara shara da gyalen shi na yafa akaina sai turaren da na fesa a jikina. Mun shiga gida inda na fara zuwa dakin mama na gaida ita sai na fito naga anty amarya a waje anan na gaida ita har zan wuce tace khadija ashe haka kike ina ganin ki shuru shiru dake ashe ke ma jaruma ce ban sani ba. Dan guntun murmushi nayi nayi kasa da kaina kawai dakin mama na nufa ina jin suna maganan a waje da mai masu aiki na shige wurin mama in gaida ita. Tana zaune a falon ta tana waya haka yasa na samu wuri a kasa gefeta na zauna ta gama wayan ta dago kai cikin fara a tana fadin yau khadija ne gidan nace mama ina kwana. Ta amsa min fuska a sake nace mama nazo in sallamay ku gobe zan koma school tace a a har hutun ya kare wanan karon nace eh mama. Ta sake cewa gida zaki ko Abujan zaki wuce aa zan wuce school ne daga nan tace barin baki tsaraban yan makaranta ko nace mama da ki barshi ai ba zan dauki kaya daga nan ba sai naje can saya. Tace a a wanan kan zaki so dambu ne da akai ma yayan zai tafi dashi kin san yana son dambun nama sosai shine na aikai mashi shima gobe zasu tafi. Ta mike ta shiga daga ciki sai gata da roba dan madaidaici ta fito da kudi a hannun ta ta miko min nayi godiya namike zan fita ko ba a fada ba yanzu na sheda wanan kamshi ba kowa bane sai dan ta Abdulsamad mijin buzuwa. Zai shigo ni kuma zan fita ban yi tunanen in kauce mashi ba a lokacin dole suka jaye a hanyan na fita ashe da buzuwa suke tana bayan shi. Mama ce naji ta kwala min kira sai na dawo wanan karon sai da na bari sun gama shiga na shiga dakin nima na karasa wurin ta gwiwa na biyu a kasa na zube ina fadin mama gani. Buzuwa ke gaida ita ta tsaya amsawa ta dago tana cewa dan ta gobe ne zaku tafi din ko yace insha Allahu mama yanzu ma mun zo mu sallama ku ne don goben sakko muke son yi dan zan shiga office. Ta juya gare ni tana fadin gobe sai ki shirya su tafi dake indan zasu wuce gaba na ya ba da damm da sauri nace a a mama ba tafiyan safe zanyi ba ni. Khadija yayan ku ne fa ki shirya ki bishi yafi shiga motar kasuwa su wuce da ke shidai baiyi magana ba ya rike goshin shin da hannu guda . Sai buzuwa ne tace motar tamu ai a cike take dayan ni dashi ne sai driver dayan kuma na masu aiki mun ne su larba sai na security din mu . Naku zata shiga don ita din ba bare bace yar gida ne kaji na fada maka tau mama yace ta shirya da safe din kada ta makara sukuku na mike tare da fadin mama na gode. Fitana dakin mommy na tafi ina nuna mata abinda hajiya mama ta bani tace ai yaya tafi danan ban fada mata zancen bin mijin buzuwa da tace in yi ba a lokacin itama daki ta shiga sai gata ta fito min da wani bakin dogon riga da takalma cikin na sayarwanta tace ga wanan a samu na sakawa. Binta ce ta shigo dakin tana dariya mommy tace maynene kuma tace khady nakewa dariya mommy mama tace da yaya gobe su tafi da ita. Ga buzuwa can tana fada bayan fitar mama daki wai bata yarda ba bata san mama ta jita ba shine mama ta fito tana fadin har ta isa tace ga abinda take so tace ita bata yarda ba yaya ce shi baice ba zata bisu ba ai. Juyowa mommy tayi ta kalle ni nace nifa ban iya bin su gaskiya don idan tayi min wallahi nima yi mata zanyi gara ko kada in bisu din. Dariya take min mommy tace akan may kin samu sauki bazaki bisu ba ai shi Abdulsamad baida hakana tunda har yaya tayi mai magana da bai daukan ki tun a nan zaiyi magana balle yanzu da yasan yaya tana hake dashi ai ba zai so ya bata mata rai ba kuma. Daga cikin dakin mommy anty Fatine ta fito tana saye da wani hijjab har kasa fuskan ta duk ya kode alaman tasha kuka har ta gaji. Gaida ita nayi ta amsa kasa kasa ta zauna a daya daga cikin kujerun falon mommy tace kin tashi tace eh mommy tace ga mutanen ki can sun shigo sallaman mu zasu koma gobe wai. Shiru tayi batayi magana ba sai mommy ta kara cewa kin san yaya da son jan magana wai cewa tayi gobe su wuce da khadija da zata koma makaranta goben. Wai ai ba zata bari ba wallahi bata son kowa ya rabe shi balle wanan da take gani mace haka maikyau kuma gasu da wata a kasa daman. Aiko banyi niyan binsu ba da amma yanzu sai na bisu tunda abin haka inga yadda zatayi a motan dani idan na shiga. Murmshi mommy tayi tace ki shirya da wuri don shi da wuri yake tafiyan shi idan zai tafi tashi nayi nayiwa mommy sallama muka fita da binta ta rakani. Naje gida na nuna ma ya Amina tsaraban da suka bani don da zanfito anty amarya taji zan wuce ta dauko min wani set din turare mai kamshi ummi ce bata ban komai ba a cikin su. Sai can muna hira nace ya Amina kinsan wai mama cewa tayi in shirya gobe in bi mijin buzuwa da buzuwa idan zasu koma. Da sauri tace may ne ? Nace wallahi da banyi niyan binsu ba amma tunda ta nuna bata son haka zan bisu din inga yadda zatayi dani a hanya . Nidai wanan zuwan wai damay yazo muna haka ne da tarihin buzuwa ko damay yanzu ke binsu din zakiyi, ba zaki hakkura kibi motar kasuwa ba. Don mama ne kawai zan bisu kada in bata kunya tunda tana sin gwada masu ikon ta ne a kan su da kuma ita buzuwan zantafi. Da yamma sosai na fito zan shiga gari in karbo dinkina da nakai ina fitowa bakin get sai ga motan shi tundaga nisa na kawar da kaina don ban san wanda ke cikin motar ba sun kawo kusa dani na gane su ne na watsa mai harara na kawar dakai. Yusuf wacece wanan yarinyar wai da nake gani a gurin mama yarinyar bata da kunya ko yanzu baka ga wanj harara da ta watsa muna ba kullun shi take min fa har a falon mama da muke haduwa. Dariya Yusuf din yayi yace amma kuma tana da kyau gaskiya koda yake kai yanzu baka ganin kyaun mace gaka da buzuwa a gidan ka. Wai Yusuf may ya kawo wanan magana haka daga tambayan ka yarinya idan baka santaba kace kawai baka santa ba period. Dariya Yusuf din yayi yace kai ke nan da anga mace mai kyau kace kada ayi magana wallahi yarinyar ta hadu sosai shiya take da jan aji da yawa. Nafisa fa tayiwa rashin kunya a gida na ka sani kuma kake wanan magana yace a a suka dai yiwa juna ta zage ta ta rama don uba baifi uba ba. Matsalan Nafisa tace kowa zata juya don tana takama mijin ta na da kudi kaji dai abinda yarinyar tace mata ai batazo roko wurin ku ba zumunci ya kawo ta. So tayi ka kama mata kuyi wa yar mutane cin mutunci a banza. Yace ai don na ganta a wurin mama ne yasa na kyale ta amma da ba zan yarda ta shigo min gida tayi min tujara ba for what ? Matar ka ce yar cin mutunci ai ya furzo iska daga bakin shi yace matsalan ta ke nan wallahi cikin ina tsawata mata ta bari ke nan ma. Yanzu dai kun kori Fati kun huta tabar maku gidan yace ta dai kori kanta amma ni ban kore ta ba ai ban san irin Fati ba wallahi . Bandai san irin ka ba malam buzuwa ta hanaka ka ba Fati da yara hakkin su kai kuma ka biye mata ranan fa a gaban kowa ta banbare hannun Fati a jikin ka kuma ka yarda. Wallahi idan zakai ma kan ka fada kayi tun baka makara ba kana ganin su Affan idan suka girma sukaga kanawa uwar su haka zakaji dadin su ne. Kai wa kan ka fada wallahi akan buzuwan nan kada ka tashi ranan lahira da bari shayaye . Bugu yakai ma abokin nashi yace Allah man abinda akace yana samun masu karkata gin mace daya ke nan na fada ma tun farko ban yarda da ita ba yanzu kaji abinda hajiya ta fada muna ranan. Nisawa yayi yace ai Fati ta riga da ta hadani dasu har baba fushi yake dani a gidan da sauran yan uwa. Yusuf yace buzuwan ka kuma tana jin dadi ba ta kori yar masu gida an bar mata gida tana yadda take so ita kadai tayi hankali wallahi da iyayyen nan namu. Shiru yayi yana nazarin maganan abokin nashi baice komai ba san cen yace kasan hajiya don jan magana cewa tayi gobe da wanan yarinyar zamuyi tafiya. Ina Yusuf ya tambaya da sauri yace wai Abuja zamu tafi a can take tace nowarder idon ta yake a bude haka bata da tsoro da ganin ta ai. Na karbo dinki na dawo na shirya kaya na bayan na gama komai na zauna ina tunanen yadda tafiyan mu zai kaya a goben. Ya Amina ta ban abinda zata bani taja min kunne don Allah kada in kula buzuwa har mu isa nace ni ina ruwana da ita su dai kaini su sauke kawai. Da safe ya Amina ta tana dani da wuri na shirya jiran kawai nake ace in fito mu tafi ya Amina tace in dauki jakkana da sauran kayana inje dasu gidan su mommy nace ai wanan ya zama tonon asiri haka . Ni madai su wuce idan haka ne dole ta kyaleni don ba yadda zatayi dani na gama komai har da karyawa ya Amina ta sani yi da safe don tafiyan da zamuyi din. Can sai ga su Binta sun shigo wai in fito da kayana ga su buzuwa nan sun fito suna ciki suna sallaman su mama zasu biyo nan su dauke ni inji mama. Tashi nayi na fara fito da kaya na waje suna tayani fitarwa kofan gida sai ko ga motan su ya tsaya suna baya dashi da buzuwa gaba zan zauna dani da driver su. Ina jin ya Amina tana gaida su binta ta bude min na shiga duk da kamshin turen su amma nawa ya karade motar har na shiga na zauna ban yi masu magana ba ina daga wa su ya Amina hannu muka tafi. Tsayawa sukayi suna bin motar da kallo Binta tace yau akwai tafiya a wurin nan jifa yadda anty Nafisa ke cika tana batsewa kamar ta fashe. Zainab tace suna daidai da khady ai ta fita iskanci daidai zasuyi a motar niko saida aka fara tafiya na dan juyo nace dasu ina kwanan ku murya can ciki bai fita. Ina kokarin cire airpies dina na sa a kunnuwa na tare da sake kira, a a wayan na lumshe idanuwa a hankali ban kara bi ta kansu ba kuma. Tun ina bi sai dan barci ya dauke ni ina yi ina falkawa na gyara zama tare da dan satan kallon su ta karkashin idanuna na naga yadda suka zauna manne da junan su sai dai aiki yake a laptop din shi. Ita kuma tana gyangyadi daga zaune da yake lafiyayun motoci ne kafin wani lokacin har mun kusa isa Abuja driver yaiwa magana yatambaye ni ina za a sauke ni . Ya juyo idanuwa suna lumshe ya dan taba sit din na bude ido tare da cire airpies din dake a kunne na yace yallabai yace a ina za a sauke ki ne ? A hostel nake zaune na bashi amsa ya juya gun ogan nashi yana fadamai abinda nace mai bai kara magana ba har muka shiga gari. Ban ankara ba sai naga suna shiga jerin gidajen dake asorock a wani gida motar ta danna kai suka shiga katon gida ne mai wani babban get ginin gidan sai mutum yace a turai yake sai lokacin na cire airpies din kunne na naji buzuwa na fadin ita a ina za a sauke ta banji may mijin ya fada mata ba nidai ban fita motar ba su kuma sun shige ko godiya ban masu ba. Driver ya shiga masu da kaya ciki ni dai sai bin gidan nake da kallo a raina nace shiyasa yake abinda ya ga dama ashe yasan abinda ya taka, Ga wasu manyan motoci gudu uku a fake wata katuwar jeep ta dauke min hankali har ina satan kallon ta a wurin motar sai sheki take tana daukan ido da gabin ta sabuwace. Sai dai ga daular duniya matashi dashi amma ya kasa auren yar kasamu suci arziki a tare sai wata bare ce buzaye ne gidan naga suna fitowa daganin su kasan yan uwan buzuwa ce ba sai an fadi ba nace mijin hausa ke nan inwar giginya na nisa ka more ka. Driver ne ya fito tare da wani dan saurayi buzu a baya shi yana dauke da tire da drinks yace gashi mai gida yace a kawo maki No na gode na fada tare da juyawa da kaina gefe a can cikin gida kuwa fitina na tsakanin buzuwa da mijin ta. Wai sai dai in shiga motar haya akaini hostel bata yarda ya wuce su sauke ni ba dole yasa driver yakai ni sai ya dawo ya kai shi office daga baya. Mun kama hanya driver ke cewa kai matar oga akwai kishi yanzun haka ta rike shine ciki wai bata yarda ya fito atafi kai ki dashi ba. Murmushi nayi nace mahaukaciyar banza kawai itake nata haukan ni ko a jikina yace nayi mamakin yadda ta yarda aka dauki ai nasan shi take ma fushi har muka zo ba shiri a tsakanin su. Surutun nashi ya isheni don haka nakawar da kaina gefe kamar ina kallon titi don abokin gulma yake nema da alama ganin na kyale shi shima yaja bakin kishi yai shiru har muka isa gidan da nake ba a cikin hostel sai dai gidane na haya da yan makaranta ke kamawa. Driver shi ya taimaka min da kayana har zuwa bakin gidan namu ya shiga min dasu sai dai bai shiga ciki ba kudi ya miko min yace gashi oga yace idan na sauke ki in baki. Dan jimm nayi kamar bazan karba ba sai dai nasa hannu na karba tare da fadin kace nagode sai dai ban faye karban irin kyautar nan ba kallo na yayi ganin na fara jan trolley dina yasa shi wuce yana mamaki na a ran shi. Dakina na bude wanda mijin ya Amina ne ya kama min hanyan shi dakine ciki da falo da bandaki a cikin sa sai inda mutum zai danyi girki daga waje haka dakunan suka a jere har dari da wani abu. Dakin yayi kura dan sati biyar din da nayi ban ciki daga kofa na aje kayan da na dawo dashi na fara gyara dakin tukun sai da na sharo ko ina na dakin. Na mayar da komai yadda nake son shi na fito ba zan iya fita ba haka yasa na kwanta don in sauke gajiyan dake jiki na a lokacin. Ba wanda yasan na dawo do haka na rufe kofa na kwanta abina sai barci mai nauyi ya dauke ni a cikin barci sai gashi wai muyi mumunan fada da buzuwa mijin kuma na tsaye yana kallon mu baiyi magana ba. Falkawa nayi don kiran wayana da akeyi na lalubu wayan da kyat saboda barci da yaci idona ya Amina takirani. Ina dauka naji muryanta tana cewa ina kika shiga ne haka waya nata kara baki dauka ba cikin muryan mai barci nace wallahi barci nakeyi anty. Tace yaya kuka sauka shine koki kirani hankalina ya kwanta nace wallahi lafiya kalau muka sauka tace badai wani matsala ko ke da buzuwan ki ? Naja guntun tsaki nace suna can gidan su muka sauke su driver su ya kawo ni hostel ni komai bai hada mu ba a motan bayan gaisuwa. Tace to barin barki ki huta an jima zan kira son naga yanzu barci yaci karfin ki nace ai na tashi yunwa ma nake ji yanzu tace to ki samu abinda kikaci kin san kina da ulcer nace yanzu zan tashi. Baki sayo komai ba ma ke nan nace yau na gaji ne anty ba zan iya zuwa ko ina ba sai dai gobe idan na fito lecture. Allah yakai mu tace muka kashe waya ina jin dadin yar uwa ta sosai saboda kulawan da take bani na musanman shiyasa nima nake mata komai kamar ita ta haife ni. Mafalkin da nayi ne ya fado min a raina lokaci guda yake dawo min dan dariya nayi nace ikon Allah wanan buzuwar kamar manya ta tsaya min a rai haka ? Sai a lokacin kudin da driver nan ya bani ya fado min a rai na jawo jakka na daga kwance na kirga kudin ido na zaro ganin har dubu hamsi ya bani nace wanan yasan zafin kudi kuwa ? ZAINAB IDRIS MAKWA SEENABUBai yi mamaki shigowa ya samu abinda ya gani ba a gidan don ba yau bane farkon yin haka gare ta don a duk lokacin da ta ganshi ya rabi wata mace ba aita ba ko kannen sa da suke uwa daya ko uba daya ba hakan take mashi wannan haukan a gida. Don sani yadda suka rabu da ita kafin yaje office akan kawai mahaifiyar shi ta bashi umurni ya bi na su rage min hanya zuwa abuja kuma a motar shigan su. A hankali ya kusa kai cikin falon su na sama ga tarin gajiya a jikin shi daya kwaso yau ga na tafiyan da sukayi ga ya zo ya samu aiki a office. Hankalinshi yayi matukar tashi saboda ganin yadda tayi kaca kaca da falon komai ta har gitse ta fasa na fasawa ta watsar dana watsarwa a kasa. Hatta tv bango ta tarwatsashi ga crystal glass da aka aje don decoration din falon a folon a kasa ta tarwatsa duk komai na falon a har gitse kamar ta haukace. Tsayawa yayi a daga kofa yana bin ko ina da kallon mamaki a ranshi kuma yana mamakin irin zafin kishin Nafisa. Wanan wani irin kishine haka shi bai da dama ya sake da wata mace a rayuwan shi sai ita duk da tasan neman mata ba halin shi bane. Wanan wani irin rashin hankali ne ko kishi haukane kinshi Nafisa ba ba bai san yadda zai fasarashi ba don abin baiyi kama dana mai hankali ba. Shi dai tun farko bai fada mata da ita kade zai zauna ba a rayuwan shi kuma tasan yana da mata tayi ta nacin sai da ya yarda ya aure ta. Amma kuma shigowan ta ta hana shi zaman lafiya da iyalin shi da mahaifan shi gaba daya halin Nafisa idan ya motsa sai yaji nadaman auren ta dayayi. Amma kuma idan komai ya wuce sai ta koma kamar ba ita ba shi dai wanan abin yana matukar damun shi wallahi. Dakin barcin su ya nufa inda ya hangota takure a wuri daya tayi kuka tagaji ta ba kanta hakkuri jin an shigo dakin yasa ta dago kai cikin fushi don taga ko waye ya shigo mata daki. Daga kofa ya tsaya ya kare mata kallo da kyat ya bude bakin shi yace wanan wani irin rashin hankali ne ko kishi haukani a garin ku ko kwakwalwan ki ya tabo ne da zaki min hassara irin haka don bake ke saye ba ko ? Ya ka maganan cikin fushi yana hararanta a harzuke ta dago tana huci tana fadin eh hauka nake kuma a kan ka wallahi kadan ka gani duk kace zaka hadani da wata mace a duniyan nan abinda zan ma sai yafi wanan. Yace oh ashe kina da aiki kuwa don dai ni namiji ne mijin macd hudu so zan iya aure a duk sanda nayi raayin hakan. Cikin wani murya tace wallahi karya kake baka isa kace zaka hadani da wata kishiya can ba ni ni kadai ne matar ka, ka sani. Oh dama tunanen ki ke nan amma kafin ki shigo kin samay ni da wata matar ko amma sabods zafin kishi irin naki ki hana mu zauna lafiya da ita. Kaima kasan abinda ba zai yuyu ba ke nan ka hadani da wata mace may na rage ka dashi a duniyan nan wani irin kulawane baka samu a gare ni da sai ka hango wata a waje. Cikin mamaki yace wana na hango a yanzu din kuma wa kika gana kula haukan ki dai ke nuna maki hakan mahaukaciyar banza kawai. Indan kai ba baka hango ba ai mahaifiyar ka ta hango maka ita in bashi ba may ye nace wa sai wata ta biyomu a motar mo inba son hada fitina ba. Yace Nafisa rashin hankalin naki har yakai ga mahaifiyata haka tanan kika biyo kuma Nafisa kan mahaifana tace in ba haka ba ne may take nufi yasa ta hado mu da ita ? Yace cikin daka tsawa karki kuskura ki kara fadin wani maganan banza akan haka rakin zai baci sosai a gidan nan daga haka ya juya zaj bar dakin sai kuma ya juyo yace. Ki tabbatar da kin gyara dakin nan da kan ki kuma ki mai da komai da kika fasa in ba haka ba wallahi zaki ga bacin rai na a yau din nan. Sannan wani magana guda kada ki kuskura ki kira wani dan aiki yazo ya kwashe wanan barnan da kikayi ke da kan ki nake son ki kwashe shi daga haka ya fice ya shige wani daki a gidan. Bin shi tayi da kallo don tasan ya hau sosai ga abinda tayi din sai yanzu nadama yazo mata a rai ga abinda ta aikata don tasan gaskiya ya fada mata kuma zuciyar tane kawai ya bata hakan ta hau ta zauna akai. Gashi ta jawa kanta aiki don abinda ya fada har cikin ranshi ya fada duk dan aikin da takira ya gyara mata tasan abakin aikin maishi yake. Gashi duk yan uwanta ne na jini babu wanda zata so a kora a cikin su haka yasa ta mike dole a cikin daren nan ta fara gyaran duk inda ta bata din. Dakin yake yayi wanka ya sauya kayan shi zama yayi tare da dauko laptop din shi ya duba sai dai ya kasa aikin da yake son yi a lokacin tunane halin Nafisa yake yi. May take nufi dashine ya tun haduwan su na farko da ita a bakin ma aikatasu yazo shigewa ta miko mai hannu tana fadin baba bani kuddi. Kallon mamaki ya tsaya yana mata tare da waigawa baya ko da wani take magana bashi ba sai yaga babu kowa a wurin sai shi kadai tsakanin shi da mutane akwai nisa ta sake mika hannu tana fadin baba bani kuddi. Yace kudin may zan baki tayi mashi alama da hannu abinci zataci alhalin su ke sai da abincin dayake shi mai tausayi ne kamar yadda mama ta koyar dasu na taimaka ma nakasa dasu sai ya ciro dari biyar ya mika mata da sauri ta karba har kasa tana mai godiya. Ta nufi rufan sai da abincin nasu ta mika kudi yana kallo aka bata abinci ta koma gede tana ci a haukace kamar mai yunwa. Tun wanan ranan idan yazo zai shige zata taso tana fadin baba bani kuddi sai ya mika mata dari biyar taje ta karya dashi. Har shakuwa ya shiga tsakanin su mai karfi ko bai ganta ba zai aje mata dari biyar din nan kudin karyawanta yakawo mata yace ga kudin abinci nan. Tsaki yaja ya rufe laptop din tare da kai kafadan shi saman gado ya kwanta rigingine yana ci gaba da tunane shi mutum na farko da ya fara warning din shi akanta shine Yusuf. Yace kasan fa irin mutanen nan kudi suka fito nema ido rufe da maza ya kamata ka daina bata kudin nan kar mutane suyi zargin ka akanta. Shiko tausayi take bashi baiga zai iya kin taimaka mata ba don taba bukatan taimako aa lokacin har yakai sun fara kyaabewa da ita. Alokacin kallon yarinya yake mata don bai dauka ta haihu ba ma sai da yaje da zancen ta gida wurin su mama nason ya taimaka mata. Mama ta kafe ba zai dauko mata fitina cikin zuri,anta ba anyi anyi da mama tace ba zata yarda ya dauko buzuwa ba yadda take ganin a na kwashewa dasu a gidaje da suke. Ga fati bata rage shi da komai ba tana mishi biyayya don auren gata akai masu shida ita tun yana karami sosai saboda an ga taso yazo daya da ita aka dauka soyayya suke yi dashi aka hadasu aure tare. Ido ya runtse a haka barci ya dauke shi cikin barcin ne yaji ta a jikin shi don bata zuciya dashi duk yadda ya iya fushi da ita bata yarda fushin nasu yai nisa. Tea na tashi na hada don yunwa ke damu na na debo danbun da mama ta bani ina hadawa dashi ina jin kida na tashi a gidan alaman adawo da yawa ke nan hakan bai sa na fito ba don har na rufe kofana a lokacin. Na gama nayi shirin kwanciya na don kada in makara da safe ina son shiga school tunda safe in gama komai don zan tafi shopping da yamma. Washe gari bakwai na gama komai na fito don zuwa cikin makaranta ina rufe daki ne makwaciya na ta gani tace ashe kin dawo dama naga haske jiya a dakin ki sai kuma ba sake gani ba nayi zaton idona ne ke gizo kawai. Nace eh nadawo jiya nan dai na tsaya muka gaisa sama sama da ita don ina sauri a lokacin na samu napep da zai karasa dani cikin school tunda ajike nake da kudi yanzu. Naje na gama komai har na samu shiga lecture a lokacin sai karfe uku na juyo zuwa gidan mu a hanya na tsaya sai da na sai abinda zanci na wuce zuwa gida. Sallah na fara yi don lokaci ya shige sosai koda na dawo wanka nayi na dan huta sai na shirya don zuwa sayo abincin da zanyi amfani dashi na wanan time din tunda ina da waddatacen kudi a hannu na saboda wanan tafiyan a saa nayi shi nake gani. Don ga kudin da ya Amina ta bani wanda dama ita ke sallama na idan zan dawo sai dai kudin bai kan isheni sai na je gida na dan kara roro abinda ke akwai in kara kafin time ya kare. Sai gashi wanan karon na samu a wurin mama da kuma dan su mijin buzuwa da ya driver ya bani dariya nayi don tuna sun da nayi nace jamgwangwan ke nan. Ai sune maganin mazan dake ketare matan kasan mu su auro su don kawai ace buzuwa mutum ke aure ko may ko kuwa jaraba ne irin na mazan Nigeria oho ? Na watsar da maganan su na mike na sabala jakata na rufe kofana na nufi bakin titi don samun abin hauwa a lokacin sahad yana tashe sosai a cikin abuja do haka na yanke shawaran zuwa can in sayo komai da nake so a saukake. Ban samu wani matsala samun abin hawa ba ni kadai na dauki shata har can bakin sahad mai Napep ya aje ni na karasa shiga ciki. Ban tsaya wani feleke ba abinda ya kawo ni na fara yi inda na dauki basket na fara zagayawa ban gare su indomie da taliya wanda shine abincin dan makaranta. Sai shikafa karamin buhu dana dauka da su kayan miya yadda zai kai min time kada yazo ya kare in rasa mai taimaka min. Bayan na gama da wayan nan sai na nufi bangaren kayan tea madaran Nidor na dauka na gari dan madaidacin gwagwani na juya zan sa a basket din da nake tara kayan a ciki . Kamshin turaren mijin buzuwa ne ya daki hanci na kaina na kasa ban dago ba sai takalman mutumin da na gani bakake a kafan shi hakaya na dago kai na dan kalle shi. Mijin buzuwa ne tare da Yusuf suke sayayya a shagon su ma dan daburcewa nayi da ganin su kamar ba zan gaida su ba sai wata zuciya tace min ko dan kudin da ya baki ai kya gaida su. Sannu ku nace dasu tare da juyawa na fara tura keken kayana Yusuf din ne ya amsa min tare da fadin a a yar garin mu ke ce. Ummm kawai nace dasu na wuce abina na karasa saura sayayyana na dungura keken zuwa wurin biyan kudi na aje a gaban wanda ke lissafi ina jiran inji ko nawa na kashe a cikin shagon in biya. Ya gama lissafi kaina yana akan wayana ya dago yace thirtythree thousand five hundred nace OK na bude jakkan dake makale a kafada na zan biya kudin yace ai an biya maki kudin ga canjin ki ma ya rage yana miko min kudin. Yana kokarin miko min ledojin yaron shagon ya mike da sauri yana karba da mamaki nake kallon shi ina kallon kudin da yake miko min din. Waya biya nace mai duk da nasan ba wanda ya sani in ba mijin buzuwa da Yusuf dana hadu dasu yanzu ba a ciki. Yace gasu can suna fita su suka bada kudin sukace indan kin gama sayayya a biya maki suka tafi da sauri nabi bayan su har na samu sun tayar da motan su suna ribas a lokacin. Ganina Yusuf ya tsaya na dago da zuman fadar wani magana kuma sai na kasa yaya akayi yar garin mu nagan ki a sukwane ko hanya zamu rage maki ne ? Nace murya a tausashe aa nazo inyi godiya ne mai shago yace kun biya min kudin kayan na mika mai canji nace ga sauran kudin daya rage nan. Nuna min mijin bazuwa yaya yace bani na biya ba ogana ne ya biya maki albarkacin ki na yar mama mun yasa ya biya maki ban san sanda nace mijin buzuwa na gode ba. Ido ya waro waje jin abinda na kirashi dashi shiko Yusuf dariya abin ya bashi yace kwarai kuwa mijin buzuwa ne abokiyar fadan ki ko ? Sai nayi kasa da kai kunya ya kamani nace ga sauran canji ina mikawa Yusuf din kudin kai ya girgiza min yace ai shi bai kyauta ya karba jeki dashi Allah ne ya baki sai a kara ayi provition ko don naga alaman sayayyan yan makaranta kikayi. Kallon ledan da yaron ke biye dani dasu nayi nadan yi murmushi nace na to gode kai mun godiya wurin mijin buzuwa zai ji yace dani. Ai da kizo mu sauke ki don naga gaki da kaya dayawa abin hawa zai maki wuyan samu a nan da sauri mijin buzuwa yace amma dai kasan sauri nakeyi ko ? Haba baka gani marance yayi ina zata samu abin hawa mu sauke ta mana sai mu tafi aiba dadewa zamuyi ba a can ko may kace yana bukatan jin ra ayin shi. Da sauri nace a a zan hau napep a bakin titi zaku iya tafiya na gode yana kokari bude mota yace a a ai ba zamu bar yar mama a nan na shiga kawai mu sauke ki kada ki fada ma mama mun ganki muki rage maki hanya tayi muna fada. Ya fito ya bude booth din motan yake magana ban da yadda na iya dole ina kallo yasa mun kayan a booth din su ya bude min bayan hangamaymay jeep din su na shiga sanyi da kamshi kawai ke tashi a cikin motar. Ya shigo ya tayar da motar muka fara hanya shiko mijin buzuwa ko ta kan mu bai yi ba sai faman aiki yake a sytem din shi saman jukin shi. A hankali yake tukin motar mun dan bar sahada din Yusuf yace mijin buzuwa sorry fa mun bata maka lokaci ko ? Ban son iskanci yace a harzuke sai kuma ya juyo gare ni yana fuskanta yace and ke kuma duk na kara jin kin kirani da wanan sunan sai na bata maki rai wallahi. Da sauri nace ni kada kaga laifi na haka naji kowa na kiran ka da mijin buzuwa bani na fara fada ba ina magana ina jujuya idanuwa na manya. Dariya Yusuf keyi muna yace a a mijin buzuwa da haka kowa ya sanka a layin mu don ta fada yanzu shine zakaji haushin ta nace ai shi nagani nima. Yace dakyau yar mama har lokacin wani kallon takaici yake min yaja tsuki ya mayar da kan shi ga abinda yake yi ya fita batun mu da Yusuf din. Yace yar mama ke may sunan ki sai naji mijin buzuwa yaja wani uban tsuki yace kai malam kafa san aiki nake yi ka samu yarinya kana biye mata don wauta. Kasa kasa nace wai yarinya yarinyar dai tafi buzuwan matarka yasin ban dauka maganan duk sun jini ba a motan sai gani nayi ya rufe laptop din ya dafe kan shi da hannu daya. Shiko Yusuf cewa yayi a sosai ma yasani ai gashi yana gani a gaban shi yace kai Yusuf tsaya in fita motar nan don Allah kun isheni wallahi ban son damuwa kasani. Maimakon ya tsaya kamar yadda yace sai ya kara ma motan wuta ya harba saman titi da sauri shi yana dariya ya sake cewa baki fada min sunan ki ba mana. Khadija nake yace suna mai kyau a uni ke karatu ko ina nace eh anan nake yace dakyau aji nawa yanzu nace ban dade da farawa ba biyu muka shiga yanzu. Kai amma kinyi kokari nake ganin ki yarinya ashe yarinyar da kwazon ta yace may kike karantawa anan ? Ban kai ga bashi amsa ba yace yaushe ne kazama dan jarida haka Yusuf ban sani ba wanan tambaya ai yayi yawa haka yace ai ba zaka san na zama dan jarida ba sai na karasa tambaya na tukun. Kawar da kai yayi gefen window motar yana kallon titi Yusuf din yace baki bani amsa ba nace bari in ogan ka ya fita bai san ni nafishi rashin son magana ba ma . Yace aini naga alama shi ne dai kamar bai ga hakan ba ke nan zan bari sai next haduwa mu sai mu dora a ida muka tsaya tunda ku dukan baku son hayaniya jin nayi shiru yasa ya dan juyo yana satan kallo don jin banyi magana niko ina kokarin ciro wayana daga ciki jakkata da ake kirana. Bayan na dauko naga baba nane ke kira da sauri na dauko ina fadin daddy i miss you ina mama yace gata kusa dani jiya anty ki tace kin dawo makaranta nace eh daddy amma ban zan zo minna yanzu ba sai dai hutu ina gani. Mun gama watan da naji Yusuf yace ashe ke yar Niger state ne nace eh ni yar minna ce yace a cikin garin minna kuke da zama ? Ohh god wanan wani irin abune haka for god sake in kana son jin kwab ne basai kuje gidan redio ba kuyi wannan abi damay yai kama don Allah. Ku ajeni daga nan don Allah zann karasa da napep don ma mun kawo kusa da inda nake ai a haba ke ko baki son muga a inda kike ne don watarna idan za a bamu sako mu baki. No I no wan wahala ne ji yadda yake ma fada ban son in ja maka matsala gun ogon ka ne don naga kamar bai so dauka na da kayi ba beside nima din ban son shiga mota dashi don takurawa. Ke yace yana kallo na a zurke yace ka neman min rai ni a wurin wanan yarinyar Yusuf harta kalli idona tace ina takura mata. Ya kara yana jan tsaki don Allah yaya Yusuf ka tsaya in sauka anan tun bai yi ball dani waje ba don ban daukan irin wanan na karasa fadi a hankali. Ina zamu bi don mun kawo unguwar Yusuf ya ke tambayana nace wancan layin zaka bi anan gida jen namu suke ya dan gangara kadan sai nace wancan get din zaka tsaya nagode ina kokarin mikewa ya ja ya tsaya get din a wagale yake a lokacin. Bai bode motar ba sai yace a nan kike da zama ke nan eh kawai na bashi amsa yana sake bin gidan da kallo sai can ya bude mota nima na bude gefen da nake na fito. Ya fito ya fara fitar min da kayana daga cikin motar ina tsaye gefe har ya gama ya dago yana cewa kona shigar maki dashi ne ciki. Abinda yasa ni murmushi ke nan har dimple dina ya dan lutsa kadan yace ko maza basu shi nace ko haka na gode Allah ya saka da alheri kai min godiya wurin mijin buzuwa. Dariya ya kwashe dashi ya shige mota yana dariya ina tsaye a wurin suka ja motar suka wuce na sauke ajiyan zuciya a hankali na duba tarin kayan dake gaba na a lokaci. Shiko yana shiga motar ya sauke ajiyan zuciya yana fadin kai yarinyar ta hadu wallahi ga kyau ga zakin murya kamar dai ita tai kanta ji idanuwa karmar ita ta tsaya ta halici kanta wallahi. Tsakiya yaja yace wai yaushe ka koma haka ne don Allah ka koma kamar wani sabon shiga a ganin mace mai kyau. Wanan din kyaunta na daban ne ai dole ne a yabata wallahi don komai akwai zamzam wanan sai irin gidajen ku ai. Gidan wa ya juyo da sauri yana fuskantan shi cikin alaman tabaya a fuskan shi yace ban ga laifin Nafisa ba da ta haukace min jiya a gida. Hauka fa kace yace hauka mana don kawai mama tasa mun rage ma yarinyar nan hanya take ta hauka wai mama na son shirya wani abune akai. Jiya koda na koma gida gaba daya duk ta hargitsa komai na falon sama da daki wai tana kishin wanan din. Kaji ba Nafisa tasan abinda ta gani anan ita ke nan ma mace taga inda kyau da fari ke aiki ba farin bane kawai irin nata. Yace cikin gatse gashi fa in akwai kyau ba gashi may akayi yace kasani ko duk ta hada kai dai ka kwantar da hankalin kasha kallo kawai a nan. No warnder Nafisa take fadin bata yarda dakai ba ashe tana da gaskiya yau kaine da bakin ka kake fadin inso wata bayan ta ni wata mace kuma zan so yanzu nidake da Nafisa a gida na. Baki Yusuf ya tabe yace ai ko baka kai namiji ba idan ka buge ga wanan buzuwa ke nan ka zama mijin buzuwa da gaske. Lumshe ido yayi da Yusuf ya fadi hakan yace yarinyar nan ma ta raina ni wallahi da ganin ta bata da kunya dama don dashi ta tare ni. Wallahi yarinyar ta hadu ne kai dai kawai ka mace ga son yar buzuwa baka ganin sauran mata da gashi yanzu. Ina mukayi yace mashi yana kallon shi don son ji yace kaini gida kawai murmushi yayi tare da fadin buzuwa tayi kira ke nan ? Bai ce dashi komai ba sai lumshe idon da yayi mai kawai yana sauka yace to mijin buzuwa sai gobe ke nan ko don nasan in kashiga ka shige ke nan . Harara ya watsa mai yana tafiya yana gyara jakkar laptop din shi cikin hasala da abokin mashi. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABUAgidan su kuma Nafisa ne ke waya da kawar ta da ta baro kaduna wace suke kira da madam a cikin su tantiriyace ta kwarai na fada. Da mijin ta sai dai kamar itace mijin ba mata ba don sai yadda tayi da mijin a gidan idan tace kada ya zauna bai isa ya zauna ba. Atakaice dai ya zama mijin tace ga madam ko kawayen nata zasu iya aiken shi ya tafi komai nisan wuri koda da kafane sai yatafi yadawo. Itace Nafisa ta kira tana son fada mata abinda ya faru da ita bayan barin su kaduna ta dauko wayan ta madam ta soma nema a wayan sai dai wayan nata ringing ba a daga wayan ba takaici ne ya kama Nafisa. Ta ja tsaki ta na fadin yar iskan ko gidan uban wa ta shiga waya nata ringing haka bata dauka ba har ya katse bata dauka ba kin sake kiran layin tayi a lokacin sai taci gaba da tunanen ta tanayi tana kada kafan ta daya dake har de. Babu abin da take tunawa sai irin shirmay da ta tafka jiya din akan bakin kishin dake damun zuciyar ta akan mijin ta wanda take mashi son daba taba yi ma wani abu ba sai dai kuma a kasan zuciyar ta ba so bane can na har abandan don da zai iya shiga wani halin jarabtan rayuwa a yanzu tsaba zata iya gudun shi ta koma wa mai maski. Wayan nata aka kira ya hanata karasa muna jin birnin zuciyar sai ta dan sake guntun murmushi tana daukan wayan nata tare da fadin Aloh ina kika shiga nake ta kiranki baki daga waya ba. Cikin muryan barci madam din tace tana hamma baki hangale bata fasa magana duk da tana hamman tace wallahi barci nakeyi tunda rana. Tsuki Nafisa taja tare da fadin barci sai kace wata mai ciki ko kasa ni don Allah watseke fuskan ki kiji ni magana nake son muyi dake ki ban shawara. Madam tace ina jin ki matar manya dadi Nafisa take ji idan su madam na fada mata wanan sunan madam din ne tace ke nake sauraro fa. Wallahi ke dai madam kin san ko sai da munafukar tsohonwan nan ta hadamu da yarinyar da nake fada maku tace mu rage mata hanya ? Don Allah ki bari madam ta fada itako tace sosai kuwa ai saida muka dauke ta a mota daya mukai tafiyan. Tace yaya kika bari haka ya faru don Allah kin ko san iein mijin ki neman su mata keyi ido a rufe nasha fada maki ki nisanta shi daga ko wace mace in ba muraharamin sa bace har kika yarda hakan yafaru dake. Ke dai bari madam nanu mashi rashin yarda na ga hakan amma ya rufe ido yace shi yace umurnin mahaifiyar shi ce dole ya bi. Madam tace yaya kukayi a motar injin baki basu daman sakewa da juna ba a motan ? Tace ai in fada maki ban yarda ko daga kai yayi ya kalle ta ba kuma nima ban sake ayi hakan ba sai dai mun kwashi rikici dashi sosai da muka iso gida wai zai tafi office a sauke shi sai a wuce da ita. Bude mashi wuta nayi sosai in fada maki sai da mukayi kaca kaca dashi na kuma hana shi fita sai da aka kaita a ka dawo san nan ya tafi. Da haushi da bakin ciki ya kamani duk na farfasa kayan falon nan gaba daya don in nuna mashi bacin raina don gobe kada ya kara min haka. Madam tace kash aike kinji matsalan ki ke da zaki bishi da lalama ki nuna mai ba wata mace sai ke a duniya daga baya sai mu sake shirya wa tace. Madam idona ya rufe a lokacin da kishin ganin wanan yarinyar a kusa dashi amma da ya fahintar dani shi irin su ba su gaban shi shi yanzu wace mace zai kalla ta bashi sha,awa sai naji hankalina ya dan kwanta a lokacin. Madam tace amma kin so ki bada mu wallahi kai kin ma dai kwafasa wallahi yanzu ke ko irin matan abujan nan ya lalubu maki har ki ta da hankalin ki haka mudake da wuka a hannun mu nama kawai muke jira. Kawai yanzu idan ya dawo kije ki bashi hakkuri akan abinda kikai mai din don kada ya zarge wani abu a gare ki. Kin ga zaki ji a bakin shi ko ita wanan yarinyar wacece a garesu kin dai san yadda zaki bugi cikin shi ai muji komai a saukake. Tace zanyi kamar yadda kika ce din amma ba yanzu ba zan dai saka ido in gani idan suna tare ko basu tare sai musan abinda zamuyi daga baya. Sun dauki lokaci suna maganan akaina ana ta kulla sheri da tugu akan mazajen su kafin suyi sallama madam tace zata kira zuwa gobe taji indan da wani matsala kuma. Na gama shiga da komai daki na da taimakon wata yar gidan namu da ta dawo tagan ni da kaya ta tsaya taimaka min. Kayan jikina na fara cirewa san nan na fara gyara kayan ina aje komai a inda nake bukatan shi na gama na zauna ina tunane a raina. Bakomai nake tunane ba sai mijin buzuwa da Allah ya jefo a rayuwana a dan lokaci ya taimaka min yau gani da kudi a hannu na wanda yakai dubu dari ta dalilin mijin buxuwa da iyayyen shi duk na samay su. Waya na dako a cikin handbag dina ina neman layin ya Amina don in fada mata abinda ya faru don komai ya faru dama nakan kirata in fada mata. Kira uku ta daga wayan ina ji bata kusa da wayan ne a lokacin mun gaisa nake tambayan yaranta tace suna lafiya sun tafi islamiya. Nace anty kin san wani abu da ya faru yau tace ina zan sani Khady nidake kaduna zaune kina abuja ke. Nace anty yau na hadu da mijin buzuwa danaje sayayya tace kun sake haduwa kuma again nace wallahi anty wai duk wanan uban kayan da na sawo nazo biya sai ake ce min ai ya biya bayan da suka sauke ni ranan ya ba driver dubu hamsim ya bani. Kai da gaske khadija nace wallahi anty kuma su suka kaini gida sai dai shi bai so su dauke ni ba sai abukin shi ne yace saboda mama ne suke min haka. Dariya tayi tace to Allah ya saka da alheri ki dai bi a hankali inda duk kuka hadu don buzuwan nan ba imani ke gare ta tana iya komai akan mijin ta. Ya Amina ni inama zan kara ganin shi kuma Allah dai ya tsaga rabona daga Aljihun shi wanan karon mutumin da ko yaushe take a cikin hade fuska banda gaisuwa may zai hada ni dashi kuma. Daga haka muka kawar da zancen shi muka dauko na iyayyen take fada min cewa sunyi waya da baba yana fada mata kudin su na ritaya ya kusa fitowa kwanan nan. Ihun jin dadi nayi don murnan iyayyen mu zasu fita acikin hali talaucin da suka shiga na ritayan da mahaifin namu yayi muke cikin halin kaka nakayi. Tace ai zan riga ki ji idan kudin sun sauka don haka sai abinda kika samu daga baya nace ai ni indai daddy zai samu bukata na ya biya ke nan. Yanzun ma shawara nakeyi inje banki gobe in tura mai kudin da mijin buzuwa ya bani don akwai kudaden da zasu isheni a hannu na tunda ina da abinci waddatace . Tace haka akeso mutum idan ya samu ya tuna da iyayyen shi dama dako kin kyauta wallahi dama sallaman ki ya hanani tura mashi kudi wanan watan. Haka dai mukai ta hira da ita daga karshe mukayi sallama na kashe wayan tare da mikewa na jona electric dina don in dafa dan abinda zanci da dare. Kira, a na saka a wayana ina aiki ina bin kira a don ni gwanace a wurin iya hadda tun ina yar shekara sha hudu na sauke alkurani mai girma na sake maimaitawa yakai kashi uku yanzu don duk wanda yasan yaran minna ya sansu da ibada da kamun kai ga girmama na gaba dasu a duk inda suke. Da wanan halin namu nake shiga ran mutane farat daya kowa tsakani na dashi gaisuwa ne na mutunci da sani girman wanda ya girmay mun. Na gama na zuba a plate na dauko ledan ruwa guda cikin wanda na sayo na aje a dakin na zauna don in fara cin abincin sai ga kiran waya ya shigo min. Binta ce ta kirani a lokacin na dauka kafin wayan ya tsunke hiran mukayi sosai ranan da ita har nake mamakin ko nawa ta sa awayan ta haka don da mun sake wanan hiran take dauko min wani. Har take fada min yadda akayi ranan da zamu wuto da buzuwar yayan su tace bazata shiga mota dani ba mama ta dage daya zo mata da maganan kan lalai sai sun tafi dani. Nace kin ko ga tunda muka kama hanya batai min magana ba nima ban masu ba daga ita har mijin ta. Tace wanan ai dama shi miskili ne magana kamar aiki yake ganin sa a gare shi zai iya zama da kai kuyi awa daya baice uffan ba haka kuma matar shi anty fati itama take shiru shiru bata magana. Nace aiyanzu sun samu mai magana a tsakanin su haka yasa ta samu daman musguna mata yadda take so ai. Tace ke kin ko san halin wanan matar shu,uma ce wallahi ta karshi da farko da tazo boye halin ta tayi kamar wata mutumiyar kwarai da ita. Sai daga bayane ta fitar da kalar ta kowa ya sani bata kaunan ko dan uwan yaya ta ganshi a gidan nan wallahi. Nace wuri ta samu wallahi ni kar nake kallon ta don banga abin tsoro ba anan ku dai na fahince ku kuna bata girma ne don mijin ta yana da hali a cikin ku. Tace ga tsiya nace eh mana haka din ne amma in bashi ba ta yaya zaku zauna wanan matar ta dinga raina maku hakali har tace wai idan tana wuri kada ayi dariya . Tace ina ma kika sani khadija ai sai wani lokaci da mukaje hutu wurin su a abuja ba girma muka dawo gida kwanan mu biyar ko sati bamu kai ba matsi yai muna yawa a gidan. Muka matsa ma yaya zamu dawo ga yan uwanta nan muna ganin yadda take ji dasu amma mu ko falo ta hana mu fito muka koma kamar wasu bare ba yan uwan maigidan ba. Dariya nake mata sosai tace Allah ko magana mai karfi wai ba ai mata a gida tace ba kallo ba komai sai zagi da hattara ga anty Fati damu da ita duk muka koma daya. Bayan mun dawo sai ga anty Fati ma ta dawo wai a kaduna zata zauna bata iya zama da buzuwa a abuja bata bari ko miji ta gani idan yana gida. Nace ke ki bari don Allah ashe ba karamar shuuma bace tace baki santa bane Khady wanan fa ko kashe mutu tana iyawa fa. Nace wanda Allah yabata ikon kashewa ba wani kan ai yafi karfin ta wallahi ba abinda zata iya wanda Allah bai tashi yi da bawan shi ba. Ni don Allah har kin ban haushi da wanan maganan naki don ba a gidan ku nake ba wallahi da taga tsiya a guri na nifa irin matan barikin nan haushi irin su nake ji. Zako kiji nata don bata da hali mai kyau ko kadan akan mijin ta zata iya yiwa mutum komai musan man ma ce ko waya tayi da wata ranan sai sunyi jidali sosai da ita ke ta zama mai kaya ko shi yanzu bai da yadda zaiyi da ita ne kawai wallahi. Nace ya dai ga dama ne Binta idan ka ganshi ga mutum har mutum amma baida kuzari gun mace tir yayan ku ya zama mijin hajiya wallahi. Haushin abinda na fadi taji da fada muka karasa wayan a rana na kashe ina mata dariyan shakiyanci na gama na wanke kayan na samu wuri na kwanta. Washe gari da wuri na fita don ban yarda in makara in ba wani dalili ya tsayar dani ba mai karfi shi kadai zai sani makara kawai. Ban da yawan kawaye sai mutum biyu yan department din mu kosu shirin mu dasu don sun ga nafisu kawo wuta sosai a class din shine likewan su dani. Banda wasa ga abinda ya kaini abujan daga school sai gidan mu sai ko idan wani dalili zai sa na fita a ranan zan fita. Yau ya dawo a gajiye don daga wurin aiki ya wuce wuri wasan polo da suke yi don dan wasan ni ne sosai wanda yana daya daga cikin abinda ke kawo mashi kudi a lokacin bai dogara ga aikin shi ba yana buga buga irin na maza gida da waje shike sa yana samun mahaukacin kudin da yake riko. Wanka yayi yana saka kaya a jikin shi ta shigo dakin dan juyawa yayi ya kalle ta ya kawar da kan shi yaci gaba da abinda yake yi. Karaso wa tayi gare shi tana wani rangaji na daukan hankalin shi ta sake abinda yake so ya sauko mata har mazaunan ta. Cike da sallo ta iso gare shi sai dai tsiyan shi da ita duk gayun ta bata damu da saka kamshi ba kuma har yanzu ba gwanewa tayi ba da iya kwalliya shine ma yake kokarin wurin gyara mata idan tayi wani kwaliyan zasu fita. Gata da son karya sai dai ko bokon kasar su bata samu ba kuma babu na Allah a tare da ita abin ya taru yai mata yawa amma hakan bai hana shi son abin shi ba. Rungumoshi tayi ta bayan shi ya sauke wani ajiyan zuciya yana dan murmushin jin dadin ganin ta tace yau ina ka shige haka ne ta dawo ta gaban shi suna fuskantar juna. Bai ce komai ba yadan jajeyeta ya dauko turare yana fesa ma jikin shi tace har da daren ma sai an feshe jiki da turare ko fita zakayi ne haka ? Sai lokacin yayi magana yace sai zan fita ne zan saka kamshi a jiki na ke baki son kamshine ashe yasa baki sakawa . Taji zafin maganan amma ta daure don in da sabo ta saba da gorin saka kamshin da yake mata din ko yaushe kuma hakan bai sa ta saba da sakawa ba. Tace muje kaci abinci yace na koshi ta dubeshi da sauri tace tare da fadin ban gane ba yace mun ci abinci da Yusuf kafin in dawo. Juyawa yayi ya nufi saman gadon su yana jawo laptop din shi tasan idan ya fara dakilan laptop sai ranta ya baci kafin ya gama. Idan tayi magana kuma yace business yake a ciki shi ko wani abin dariya tayi ya dago yana duban ta na lafiyan ki kalau kuwa ? Sai yaji tace maganan turaren da kayi ne dai yaban dariya har na tuna da yarinyar da mama ta saka mu dauko ranan. Bakaji wani irin kamshi tiraren da takeyi ba kamar tayi wanka dashi yace tasan kan ta ne yasa ta saka turaren haka don kada a raina ta. Tace shi saka turare kuma har wani sanin kai ne dashi wai ma may ye alakan ta da mama ne data nace sai mu dauko ta wai ? Yana bude laptop din yace sai yanzu kike son jin halakan su da mama da kishi ya rufe maki ido baki tsaya tambayan ta ba da farko. Tace kayi hakkuri cikin yanayin tausasa harshe tace nasan ban kyauta ba kishin ganin ka kusa da wata mace nakeyi tundai irin wanan yarinyar dake cikin ganuwan kurciyan ta ga kyau kuma da gani tana kuri da ilimin ta. Ina tsoron ka hango kyawon tane wallahi kazo kace zaka dauko min ita a gidan nan wata rana son ka nake har karshen zuciya ta ka sani. Ya tsaya yana mata wani irin kallo yace don kina kishina sai ki min hauka mata nawa nake gani a rana da ina raayin mata ne zaki san lokacin da zan nemay su ne. Har kina fada min cewa mahaifiya ta da biyu ta hadamu tafiya da yarinyar don in so ta kika haukace har kina fashe fashe a gida. Kwantowa tayi a jikin shi ta dan shafi kan shi tace kai min afuwa don Allah haka ba zai sake faruwa ba a tsakanin mu. Yaji hakkurin da ta bashi har cikin ranshi yace ki rage kishin nan nake don ni din mijin mace hudu ne watarana. Da sauri ta rufe mai baki tana fadin don Allah ka daina fadin haka don kana sa zuciya ta tana bugawa da wanan zancen kishiyar da kake min. Yace idan lokaci yayi ai yi zanyi sai dai ki tausasa zuciyar nan naki bakiga mahaifina matan shi hudu ba kin sani ko in gado shi nima ? Kuka ta soma mashi tana fitar da hawayen munafunci a idon ta dariya yayi mata yace akan kishiya kike wanan kukan haka fati fa ba kishiyar ki bace kin ga ai ko yanzu kina da ita ke nan. A bar maganan Fati tace don ni kaina ma kunya nakeji ace wai ita din kishiya ta ce balle kai ace matar ka ce Fati ta sunna. Ohh kin fison indan zai ne ma yanzu in nemo wace idon ta ya bude sosai don itace ta dace dani tace ba haka nake nufi ba don Allah mu bar zancen kishiyan nan haka na. Tambayan ka nayi cewa wacece wanan yarinyar ne sai ka dauko min wani dogon zance kuma akan kishiya ? Yace nima ban san ta ba a gurin mama wanan zuwan da nayi na fara gani ta koma waye dai ita nasan alakar ta da mama mai muhinmaci ne sosai. Shiru tayi tana nazarin maganan shi daga karshe dai data ga ya fara aikin shi ta kwanta tana ci gaba da tunane kala kala a zuciyar ta. Yanayin damana yanayi mai cike da albarka yayin da ban gare guda yake burge alumma ko babu komai yanayin da daminar kan haddasa jamma,a sha,awan ta saboda ire iren abunda damanan kanzo wa jamma,a dashi musanman musan nan abuja da ba noma suke ba amma yanayi yana kawatar da jamman cikin ta yayin da damanan ta fara mikewa zaka ga tsirrai iri daban daban dake kara kawata garin. Wanan yanayin yakan saukar min da nishadi sosai musanman idan naga garin ya gaure da hadari kasan ba wuya ruwa ya sauko masu. Yau ma na fito daga aji ke nan naga yanayin garin ya sauya nasan bamu nisa da samun ruwan sama ke nan kusan kwana shida ke nan ana zuga muna ruwa a irin wanan lokacin. Tafe nake a hankali nake takawa daga cikin haraban makarantan zuwa hanyar da zai fitar dani daga cikin makarantan sai dai zuciyana cike yake da tunanen rashin kudin da ban samu fita zuwa turawa daddy ba har yau ko da zan fito hadari ko ruwa zai tare ni gashi ban son inyi missing din lecture da safe. Abu biyu ne yake damu na yanzu yunwa da tunanen daddyn mu saboda banci komai ba tunda safe da na fito don yau na makara ban tsaya na karya ba. Saboda nacin karatu da nake dashi a raina don koda dare haka nakan raba dare ina karatu ni kadai a daki sai na gaji zan dan taba barci asuban farko kuma in tashi in fara nafila ina kusanta kai na ga Allah idan na gama kuma karatu zan dan dasa a wurin sai zuwa haskawan gari zan tashi in wanka in karya in kama hanyan shiga cikin makaranta. Yau sai aka samu akasi na makata ban tashi da wuri ba har rana ya fito hakan ne ya hanani tsaya in karya wanan tsarin dana dauka yana matukar wahal dani . Amma ni ina aganin shine daidai don iyakacin abinda ya kawo ni kenan a garin indan ban yi ba may zanyi. Domin karatu na bar gidan mu na bar dangina da kowa nawa a gida nazo nan idan ban mai da hankali ba mai zanyi sai shiririta ke nan kamar yadda naga sauran dalibai suna yi. Don a ganina karatun shi yazama min dole dashi na dogara dashi nake saka ran samun ci gaban rayuwa na dana iyayyena nan gaba . Buri na ne burin iyayye na da yan uwa na ya ta,allaka ne akan karatun don haka babu dalilin da zai sa in zauna ina wasa dashi. Nikan zauna in dinga tunanen yadda nake ganin wasu dalibai suna wasa da daman su ta hanyar zibar da abin da ya kawo sai in rika mamakin su ina tausaya masu don nayi imani da cewa suna cutar da kansu ne sun kuma ha,inci iyayyen da suka turo su karatu . Ire iren su gasu nan da yawa sai yadda suke so sukeyi a cikin makaranta kwata kwata basu damu da karatun ba sai idan jerabawa yazo ne ido ya rena fata duk dadai wasun su ne suke damuwa da hakan. Wasu ko iyayyen su ko samarin su suna masu hanya su haye ire iren tunanen da nake yi ke nan ina tafiya saman dogon titin da zai sada ni da gidajen da muke ciki. Ido na zubawa wata dankareriyar motar jeep dake nufo inda nake a hankali ba ka gane wanda ke cikin motar dan glassen motar da ya kasance masu duhu baka gane na cikin motar balle ma wana sani ni anan. Ta gefen ido nake kallon motar har zuwa lokacin da motar tayi gaba kadan dani ta tsaya a gaba na ban dauki komai a raina ba don a gani na wani abin maishi ya tsaya yi. Nazo zan wuce motar ne naji muryan kamar wanda na sani yana cewa yar garin mu yanzu nake tunanen ki da hanya ya biyo dani ta wurin ku. Don sheda muryan maishi da nayi yasa ni sakin dan murmushi kadan nace kaine kuma yau a wurin namu yace wallahi aiki ya biyo dani tanan din kuma ashe da rabon ganin ki. Murmushi nayi na fara gaida shi ya amsa yana fadin ummm Khadija ko nace eh ashe baka manta da sunan yar garin naku ba dai. Murmushi yayi yace ina zan manta da yar mama baki tambaye ni mijin bazuwa ba yau murmushi na kara yi nace kace dai miskilin mijin buzuwa. Yace kin kara masa inkiya ke nan nace shine daidai dashi ai suna lafiya ko ya labarin gida koda yake muna waya dasu Binta ma nasan suna lafiya koda yake tace an ma mama rasuwa zariya ta tafi can tun jiya zata kwana uku a can. Yace kai haba bata ko fada muna ba wallahi wa ya rasu a can zariya din sai kuma yace kada in tsare ki a hanya don naga kamar bakin son hakan ke. Murmushi nayi nace idan hakan ya dauro yaya zanyi sai yace shigo mana in karasa dake idan ba damuwa nace lah ai ba wani nisa don na kusa karasawa ai. Sai dai don Allah ina zaka bi don ina son sauka a bakin, banki in tura kudi yace to shigo mana in sauke ki ai ke din kanwar mu ce na zagaya gefen ina fadin na gode. Mun dan fara tafiya wayar shi tayi tsuwa ya daga yaya akayi ne mijin buzuwa banji may yace ba don karan kira,an dake tashi a motar murya malam Ahmed sulaiman kano ne. Yace wallahi gani nan dawowa sai dai kuma uzuri ya tare ni din na hadu da yar garin mu a hanya na rage mata hanya zamu banki da ita. Wake nan ya tambaya a cikin wayan yace khadija wama surname din ki Adamu nace mai a takaice yace khadija a dabu kawar tafiyan ka na ranan. What Yusuf sai da ka kara nemo yarinyar nan don Allah yarinyar nan bata da kunya fa ganin Yusuf nata dariya yasa ni wafce wayan ina karawa a kunne na naji yana fadin wanan yarinyar matsalace wallahi sam bata ganin girman babba. Nace nakai matar kane rashin ganin girman dan adam kai har kana da bakin fadar haka yace baki da kunya ko nace aikai kana dashi kada ka kara kirana da mara kunya wallahi. Yusuf ne ya karbi wayan a hamnu na yana dariya yace kadai ji abinda tace kada ka kara kiran ta da mara kunya ehheh. Yusuf abin naka ya girmay sani na yanzu tunda har ka iya mika mata waya ta zage ni yace bata fa zage ka ba man ina jin yadda kukayi da ita sarai. Mun iso ya tsaya na fita ina mai godiya yace shiga ki fito ina nan ina jiran ki har ki gama kin ga akwai hadari a garin sosai komawa zai maki wuya kuma. Nagode nace dashi ina fita yace ara min wayan ki kafin ki dawo dan jimm nayi kamar ba zan bashi sai kuna mika mashi wayan na fice daga motar sai da na gama abinda nakeyi na tabbatar da kudin sun shiga na fito lokacin har an fara yayafi kadan kadan a gari yana zaune yana duban wayan shi na dawo na samay shi ina shiga yace har kin gama eh nace mai ina rufo kofar motar waya na ya miko min na karba ina fadin ka gama dubawa ne yace dama waazi neke dubawa a ciki murmushi na danyi kasan baki na. Lokacin aka fara ruwa mai yawa duk da ban ganin hanyan da kyau amma na gane ba hanyar da muka fito bane muka bi yanzu. Dan kallon shi nayi yace kada ki damu zan dauki mutumi ko ne ya gama mintin driver kuma wai yakai Nafisa Nasarawa bai dawo ba. Banji dadin jin hakan ba sai dai ba yadda ja iya kuma a wani ma, aikata muka shiga ya tsayar da motar da sauri ya fito ya shiga motar ni kuma na koma baya. Kamar ban cikin motar don banyi magana ba sai fada yakewa Yusuf wai ya dade baizo ya dauke shi ba yace kan wani aikin da kasa kanka can . Ya haba taimako ne fa nayi kasan ace a taimaki mata ai a duk sanda suke ga bukatan taimako cikin tsawa yace ya ishe ka hakana Yusuf enough ta fada da karfi yana dafe kan shi da hannun shi daya. Nan zan sauka nace a daidai lokacin da yake dafa kkan nashi da alama bai san dani a cikin motan ba ma sai a lokacin dan juyowa yayi yana kallo na da mamaki a fuskan shi ya sai kuma ya juya yana kallon Yusuf din. Na sake fadin a nan zan sauka nace fa nace ma Yusuf ya juyo yace acikin ruwan nan zaki sauka haka a ina zaki samu abin hawa nace kada ka damu ai zan samu idan na fita. Yace to bari in dan karasa dake inda zakiyi saurin samun abin hawa ya fadi shima fuska a dake da alama yaji haushin abinda yayi mashi a lokacin. Karasa da ita ka ajeta yace ba tare da ya kalli kowan mu ba yai magana dama ba sauke ta zanyi ba ai sai na kaita inda na dauko ta. Ba wanda ya sake magana a motan har bakin gidan ya tsaya da mota lokacin an dan rage ruwa sosai amma anadan yi kadan kadan yace ashe hajiya an mata rasuwa ne. Ina fita naji yana fada mai hakana na gode yaya Yusuf agai da gida da mutanen gidan Allah ya kara rufa asiri na fice daga cikin motan abina. Ban tsaya ba don ruwan sama bai bani lafiya idan ya buge ni sai dai ban tsira ina fita ruwan ya sake saukowa da karfi da gudu na karasa cikin . Sun kama hanya ya dubu Yusuf din yana fadin wata hajiya akaima rasuwa nace yace hajiya mama mana hajiya mama nawa kake nufi ita yanzu wanan yarinyar ke fada min . Shiru yayi bai sake magana ba sai zuwa can yace wata ce ma yarasu a zariya din kana son sani kake daure fuska haka tsuki yayi sai can yace barin kira hajiya din in ji. Har ya dauko wayan ya fara duba lanban mama din sai kuma ya dago kai yace kana da nomban wanan yarinyar kaba in kira ta. May zakayi da layin ta kuma yarinyar da bata da tarbiya yace malam idan zaka bani ka bani kawai ba dogon zance nake so ba kyale shi yayi kamar bada shi yake magana ba. Sai zuwa can yace ana son ai maka gata kana wani jiji dakai wanan jida kai din ba zai kaika ko ina ba a harzuke yace nomba nace kabani kada ka fada min wani magana da zai kara bata min rai bayan wanan. Har saida yakai shi hara ban gidan shi ya ajeshi zai fita ya miko mai wayan shi yana fadin ga nomban nan kamar ba zai karba ba sai kuma ya daure ya karbi wayan ya kwashe nomban. Ya mika mai wayan ya shige ko sai anjima baice dashi ba shiko murmushi yayi yadan bugi sitiyaein mota shi ya juya ya fice gidan. Nafisa buzuwa ce suke tafe da kawar ta nan cikin garin Abuja sun fito nasawa state ganin wani malamin su a can da tai ma mijin karya zasu duba wata aminiyar ta ne . Bai hanata zuwa duk inda take so shiyasa tale samun yin yadda take so a gidan don shi kwata kwata bai dauke ta da irin wanan halin ba na matan dake shige shige. A hankali suke magana yadda sani driver ba zai fance su ba shiko a idan yake tuki ya mayar da hankalin shi ga hannya ne amma kunnuwan shi yana gare su. Nafisa ke fadin kin san Allah wanan sakawa zanyi yai min aikin da ko uwar shi ba zai iya daga ido ya kalla ba balle wata mace don naga alaman wanan arnen yada aiki sosai. Don su malam kasan mu ko ka basu aiki irin wanan sai sun kawo maka Allah kusa kafin su duba maka kukan ka. Suwaiba kawar ta ya mutsa baki tace ke ma kikan so damun kanki nafisa mijin da ko a yanzu a hannun ki yake wanda kika sa ya kore uwar yayan shi kuma ka zauna lafiya may kuma yanzu zai wani daga maki hankali. Bai fa kallon mace sau biyu a yanzu hakan ba anan matsalan yake ba suwaiba wanan abokin nasa da suke kamar tagwayen sheri dan iska mara zuciya nayi kora da hali nayi na fili amma ya na lake kamar kaska dashi. Kina ganin ko baiyi niyar yi ba shi bai iya dauko ko mace ya kawo mai ke komai tsiyan su fa baki taba gane sirin su dashi dashi. To ai yanzu ba tashi zakiyi ba tunda shi kin riga da kin samay shi a hannu ko sai yadda keki so dashi yanzu akan wanan abokin nasa zaki koma ki san yadda kika raba su. Gaban Sani driver ne ya fadi har yana batun kauce hanya dama yana zargin gidan da yakai su din ga zargin shi ya zama gaskiya har ana batun raba ogan nasu da aminin shi. Wanda yasa in tayi nasaran yin hakan ta gama da ogon nasu ke nan gaba daya tunda shi kadai ne dama ya saura yana sashi a hanya yanzu. Muryan ta yaji ta daka mai tsawa ya kula da tukin da yake yi ya dubi hanya mana yace hajiya rami na kaucewa shi ya kawo hakan. Suwaiba tayi mata rada su bar maganan harsu sauka kada yaji abinda suke kullawa sai suka dauko wani sabon hira. Sai kuma tace malam sani ke nan dama ina son magana ta siri dakai sai dai maganace ta taimakon juna dani dakai. Yace hajiya wani taimako kike sona dashi tace siri ne kuma amana a tsakanin mu dakai amatsayi na matar ogan ka kuma wanda yasan wasu abubu nawa. Idan kuma kaga bazaka iya taimaka min ta wanan hanyan ba to zamu hada deal dakai in dinga biyan ka akan aikin ka. Dan juyowa yayi yadan kalle su zuciyar shi ya tabbatar mashi da cewa wani abu mai muhinmanci zata saka shi yai mata da ya shafe ogan nasa. A fili yace hajiya fadi bukatan ki a shirye nake da in aiwatar maki matukar bai fi karfin iyawa na ba murmushi tayi tace ai ba wani abu mai wuya bane zan saka ka yi. Ogan ka nake son ka sama ido don Allah duk wata mace da kaga yana hurda da ita a bayana har sun shaku a tsakanin su banda gaisu ka sanar dani ni kuma nayi maka alkawarin duk wata zan baka dubu biyar bayan wanda mai gida ke baka. Yai dan dariya yana shafar kanshi yace hajiya idon wanan ne kar kiji komai aran ki nayi maki alkawarin ko gaisawa da wata naga yayi wace bata gamshe ni ba zan fada maki. Suwaiba tace dakyau dan gari dama ai na fada maki babu abinda kudi bai bayar wa ke bude bakin jakkan ki ga aiki da cikawa kawai. Da sunan zuciyar Sani driver da basu furta komai a gaban shi ba don nasiha hajiya mama kullun suka je kaduna ya shiga gaida ita shine don Allah ga amanan yaro na baka Sani ko ba komai yanzu mun zama daya dakai tunda ana wuri daya. Duk da kasalan dake damu na a lokacin bai hanani tashi in girkawa kaina abinda zanci ba lokacin bayan na gama ne na fitar da kayan da nayi aiki na wanka na shiga bayi na watsa ruwa masu zafi don ruwan sama bai bani amana ajikina. Ina fitowa daga bayi ne mukai kicibis da zarah da ta shigo dakin nawa a lokacin wanda alama ya nuna yanzu ta dawo daga cikin gari sabada ledan da take dauke dashi a hannun ta. Nasan key din dakin ta tazo dauka tana saye da wasu kaya da ya matse mata jiki sosai kin dawo nace mata eh kin gani sai yanzu na dawo wallahi. Inda key din yake na nufa in dauko mata na mika mata leda daya ta aje min daga cikin ledejoji dake rike a hanun ta nace lah dakin dauka wallahi na fada maki ai ban son komai daga irin abinda kike dawowa dashi. Lumshe idon ta tayi cike da jin takaici na tace na sani amma wanan ba inda kike zato na samo shi ba sako ne da samu an kawo min daga gida naga idan na barshi ma a hannu na baci zai yi shiyasa nace bari kawai in mika maki. Ledan nabi da kallo a raina nace watau sakon da iyayyen ta suka aiko mata dashi bai da wani amfani a gare ta sai na mazan da take bi ke nan. Karban key din ta tayi ta fita dakin na bita da kallo tana saye da kayan da ya matse mata jiki sosai ga kitson kanta da ta sako su har kafadan ta. Tsuki nayi na shimfida anbin sallah na tayar da sallah na na idar na koma na jingina da katifa na ina jan casbi a hankali waya na dake gefe yayi kara a lokacin. Number ne ba suna na daga ina mamaki waye mai wanan special number yake kirana kuma kusan kiran zai katse na dauka. Da sallama a baki na sai naji shiru kara maimaita sallaman nayi wanan karon sai aka amsa min a gadarance kamar naso in sheda mai kiran amma na kasa canka. Shiru har lokacin na sake cewa hello naji ance ina jinki nace wai waye please ko wrong number aka kira ne yace ke kina magana da Abdulsamad Abdulrahim ne . Nace waye haka kuma bazaki sani ba don ba lallai ne ki sani din ba nace kai ta shafa wanan kuma banda lokacin irin ku haka kuke kiran mutane don bata masu lokaci kawai. Ke ban son rashin kuyan da kika iya ke har a wayan ma sai kin nunawa mutane halin ki ba wani abu yasa na kiraki yanzu sai don inji wayarasu hajiya ta tafi zariya. Au kace min miskilin mijin buzuwa ne nikan ina zan sani kaji ka da wani magana ni zaka tambaya wa hajiya ta rasa kuma ? A har zuke yace eh don a bakin ki mukaji ta tafi zariya shiyasa nake son jin wanda muka rasa din bawai na kiraki bane kimin rashin kunya. To ban sani ba kuma kada ka kara kiran layi na kaji na fada maka zan kashe nace wai ma a ina ka samu layina dan fitina ? Wanda kika ba ya bani layin ki mara kunyar yarinyar kawai zaki gane baki da wayau idan na kama ki don naga rashi kunya yana nema yakawo kaina. Kit na kashe wayan ban bari ya gama fadin abinda yake fadi ba don ba zan iya tsaya in saurare shi ba nace wanan wani iri fitina ne kuma? Ina ruwan shi dani da zai wani bugo min waya wai yana tambayana wa mahaifiyar shi ta rasa da ta tafi zariya gaisu dan rainin wayau shi ba danta bane baifini kusa da ita ba waini may hadina da wa yan nan mutanen ne haka da suke son su shiga min rayuwana ina zaune kallau. Shiko a ban garen shi ji yayi kamar ya samay ni ya fafala min mari ya sauke haushi yaya akayi ne na raina shi haka ne. Yaja tsuki ya fara laluben nomban mahaifiyar tashi dole ba don yaso ba yaji may yasa har abu na faruwa irin haka take nisan ta shi da ita duk da yasan fushin da hajiyan keyi dashi a kan Fati ne ba komai ba. Kamar bata dauka ta dauka tare da fadin sallamu alaikum ya karba mata a cikin ladabi sai ya fara gaida ita bayan gaisuwa ne yace cikin kwantar da murya hajiya naji ance anyi maki rasuwa a gida kin tafi ? Eh haka ne nayi rashi amma ni ya shafa ai rashin da nayi don jin ka baida wani amfani a gareni inda dai dangin ka na kauyen maradi ne da ka tafi ko tuntuni. Shiru yayi yana sauraren zafafan maganan da mahaifiyar shi take fada mai tace wai tunkuna ma wani dan karabanin ya fada ma nayi rashi a dangina har kaji duk da nasan ba kiran mutane yanzun kake yi ba buzuwan matar ka da dangin ta sun ishe ka. Hajiya kiyi hakkuri nima a wurin yariyar nan Yusuf ya jiyo muna shine nace ba a fada min ba tunda har zaki je zaria ki kwana biyu haka ba karamin rashi kika yi ba. Tace wace yarinya ke nan kake magana a kanta yace yarinyar da kika hadamu da ita kwanaki muka taho abuja sai dai yarinyar bata da kunya ban gane inda maganan ta ya dosa ba. Au khadija kake nufi ko wa yace ina ganin sunanta ke nan Yusuf ya hadu da ita take fada mai yaban layin ta na kirata tana karanta min shirmay . Tace Ladi ce matar kawun ka Allah ya karbi abinshi shine nazo ita khadijan kuma ta damu da nine shiyasa tasan damuwa na har taji. Yanzun kai bakaji kunya ba ace wai har khadija zata ji zance na kai bakaji ba haduwan ka da yarinyar gaba daya ya canza muna kai kana ko tuna makomar ka ga Allah. Bani ba ba mahaifinka ba duk kayi watsi da alamarin kowa kana ganin buzuwa da yan uwan ta sun isheka rayuwan duniya. Mu din dai da kake gudu din mune dai iyayyen naka har gobe zance guda ne abin nan da ka guje mu akan shi yana nan yana jiran ka . Sannan da kake kiran khadija mara kunya ita ma ka sa mata tsanar ne na babu gaira babu dalili saboda da tafi karfin matar son naka ko may . Zai yi magana ta kashe wayan ta ta kyale shi ranshi yaji ya baci sosai da maganan hajiya yasan akan Fati take wanan fushin haka dashi to shi may ye laifin shi a ciki. Hajiya suna gama waya binta ta kira tana tambayan ta ko sunyi waya da khadija tace mama ta kura tana tambaya na ke nace kin tafi zariya an maki rasuwa acan zaki kwana biyu. Tace oho yanzu yayan ku ya kira waya wai sin hadu da yusuf take fada mai a wurin ta suke jin an min rasuwa don baida kunya har khadija taji abu ya samay ni tana jajantawa amma shi bai ji ba. Sai kokarin son ya zagi yar mutane yake wai bata da kunya shi waya fishi rashin kunya yanzu shida ya nuna muna ba komai muke a gare shi ba. Sun gama da binta gulma ya ci binta sai ga kiranta ina shirin kwaciya ya shigo min. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABUBayan mun gama waya da ita naji raina ya baci sai a lokacin na gode ma Allah da ban goge number shi ba a wayana kira nayi har sau biyu bai daga ba sai na tura mashi sako masu zafi na kashe wayan. Don nasan zai gani da safe in ma kwanciya yayi a lokacin haka yasa na danji zafin da nake ji ya rage min da kyat barci ya dauke ni a ranan. Har na rufe ido sai nayi wayana yana kara na dauka a zatona shine yaga sakona ya kira wayan sai dai ba number daya kirani daya kira dashi bane. Nace ummhumm ina jin ka naji ance haka ake karba kiran wanda baka sani ba na sheda muryan Yusuf din nace yayana kaine a na dauka wani ne. Yace nice injin ruwa bai saki jin zazzabi ba dariya nayi nace ai na watsa ruwan zafi a jikina yace good dama na kiraki ne don mutumin ki ya karbi number ki a hannu na nasan zai iya kiranki kada ki biye ma halinshi don Allah don bansan abinda zai kiraki ya fada maki ba koda yake yace akan maganan hajiya mama zai kiraki yaji don Allah , , , Na katse shi da fadin ai ya kirani ko har munyi tsiyan shi ya dauka kowa nema yake a gare shi ko yaushe ni kuma na wanke shi tass. Da karfi naji yace haba don Allah nace wallahi na kwashe komai na fada mai har text din da na tura mai mai zafi yace amma baki kyauta ba wallahi. Nace saboda may zai mun hadi yace khadija kin san kuwa kece mukee son kizama weapon din mu wurin yakan buzuwa nan gaba. Don Allah ki dinga sausautar harshen ki gare shi nace wa ni ni ina ruwa da shi da zan zama muku makami a gare shi da buzuwan shi. Dariya yayi yace ke ko ke dashi khadija ke da komai da zaki yakar muna buzuwa don kin cancanci yin hakan. Ni din yayana yace kwarai kuwa kauna na sai dai idan mun hadu zan maki bayani yadda zaki gane nace to shike nan tunda haka ka fada yace bani na fada ba umurni nima aka bani kan hakan . Yace sai dai idan mun hadu din zan maki bayanin komai nace Allah ya kaimu ina saurarenka da haka muka yi sallama dashi ya barni da tulin tunane a zuciyana. Da safe zarah ce take buga min kofa jin bugun kofan na tashi na bude daki tana tsaye kofan dakin nawa ganin tana son shigowa na bata hanya ta shiga daga ciki. Tambaya na tayi ko da safe zan fita nace ai kemakin sani yanzu haka shiri nakeyi kada in makara take cewa dani zata fita amma wai za a kawo mata sako shine take son in karba. Nace zarah fitan kuma zakiyi yanzu tayi dan guntun tsaki tana fadin eh wani friend dina zaiyi tafiya nake son inje muyi sallama dashi. Zarah ba zaki wankan ki fada ki zauna ki abinda iyayyenn mu suka kawo mu yi ba wanan dabiar da kika dauko bai da amfani gare ki nan gaba. Ta dan yi murmushi ta nufi wurin da taga na aje plate din abin ci da tukunya tana bude bayan ta bude ta dago tana dariya tace an fada maki yadda bakin san wayen kai ba haka kowa yake yanzu da anganki kamar may wayayen kai . Nace in dai irin wanan wayen wane kada Allah ya nufe ni da yin shi ina neman tsarin Allah ga irin wanan dabian naku Allah kuma ya shirye ku ku gane gaskiya. Ta juya ta debi arish a plate ta zauna ta fara ci ni kuma ina ta shirina nace kiyi ki gama gada ki makarar dani anan don banson in makara. Tayi murmushi tana kai abinci a bakin ta sai da ta hade tace wanan halin naki na ina kika fito karatu ina zaki karatu sai ke khadija. Khady look at you me kika rasa ke kanki jarin kanki ne amma kin tsaya kina wahal da kanki haka har kina wani girki tunda safe kamar wata matar aure amma waike nacin karatu sai wahala kike haka. Wallahi da zaki yarda akwai wanda zan hada ki dashi cikin kwana biyu kiyi clean ke baki daukan misali a kwaina khady da haka nake ? Amma yanzu gani tunda hanya ya bude min mai na rasa na rayuwa atare da ni amma ke gaki da abin kawo kudi kina ta faman kumshe shi a jikin ki ta fada tana dariyan shakiyanci. Ni dai ina tsaye ina mata kallon mamaki da huduban shedan da take min har kuryan dakina ta dauka nasihan ta ya na shigana ne ganin yadda na tsaya ina kallon ta. Tace ina son ki fahimci wani abu tsarin rayuwa yanzu ya canza ki shigo kawai a dama dake yarinya. Nace cikin murmushi zarah baki fance ni batsarin rayuwa ta daban yake da naki ban sanya ma zuciyana kwadayi ko son jin dadi a ko wani irin yanayi ba don haka kada kiyi tsammanin guntun huduban ki zaiyi tasiri a raina . Ni da kika ganin nan ina da mutunci na kuma nasan ciwon kaina dana iyayyena kada kiyi tsammanin kananan kwarin da kike bi zasu iya rudana da wani abu. Shi jin dadi lokaci indan lokaci yayi sai inji amma ba ta hanyar wullakata kai yadda kukeyi din nan ba kema idan da zakiji sharata da kin watsar da wanan rayuwan ki rungumi abinda ya kawo ki Abuja. Su kansu mazan da kuke bi aida karatun suke amfana yanzu bance maki ban saurayi ko rayuwa ba sai dai in gajarce maki ni indan zanyi mai tsabta da sanin ciwon kai zanyi amma bana kwanan gida irin naku ba. Baki zarah ta tabe min tana dariya ta saba da nasihana kullun wanda ita a ganin ta ni har yanzu ban waye ba ban san ciwon kaina ba bansan ta kan duniya ba kuma. Nace keyi dariya amma ni idan zan faso gari ba irin wa yan nan kanana kwari masu gurbata rayuwa zan tsaya dububa ba sai wanda ya san kanshi da mutuncin kanshi. Ta mike bayan ta gama ci dama ina magana ina kallon agogona ne kada in makara tace ina son ki fahince ni a yanzu ba a samun irin wa yan nan mazan da kike hasashe kinga ko zaki shawa wuya wurin neman su. A naki ganin ke nan zarah amma muna nan dake zakice na fada maki watarana ta miko min key din ta nace kenan yauma till down zakiyi tace yo may za a fasa kuma. Ta fita na rufo kofana muka fito tare da ita a titi muka raba hanya tana neman lift ni kuma na nufi cikin makaranta ina mamakin wanan rayuwa da zarah ta daukan ma kanta. Itama yar minna ce kama na dalilin haduwan mu ke nan da ita don ko a minnan ba unguwa daya muke ba su suna zama a cancaga ne ni kuma muna tsakiyan gari. Kasancewar mu yan gari daya yasa muka zama kamar yan uwa da ita da farko halin ta mai kyaune kafin idon ta ya bude da bin mazan abuja. Sai lokacin muka raba hannu da ita amma hakan baisa mun daina kula junan mu ba kamar baya sai dai ban taba yarda naci abinda take samuwa ba daga wurin yawon banzanta ba. Tun abin na damun ta har yazo ya daina damun ta ta daina ba sai wanan da iyayyen ta suka kulla suka aiko mata yanzun tana ganin tafi karfin shi ita shine ta kawo min inyi amfani dashi. Tun asuba yake tayar da ita ta tashi tayi sallah amma tana kwance tana barcin ta har yagaji yatayar da ita da karfin tsiya ta zauna tana mustsukan ido alaman barcin bai isheta ba har lokacin yana ganin ta tashine yasa shi fita daga dakin azaton shi zata tashi tayi sallah. Ya fita zuwa dakin motsa jikin shi da yakeyi duk safe inda kuma yake aje wasu kayan amfanin shi jiya anan yabar wayan shi yana canji ya je ya kwanta yana tunanen rashin son ibadan da batayi. Ya gama komai na motsa jiki da yakanyi da safe ya wuce zuwa inda wayan shi yake jone ya dauko din ka idan shine sai takwas yake bude waya da safe. Budan wayan yasa sakon da suka taru mai shigowa ya gane su wanda farko budewa nawa ne ya shigo da farkon. Mamaki yayi don ba suna sai lamba ga dogon sako kuma da maishi ya turo mashi kamar kada ya karanta tunda baisan mai sakon ba sai kuma wata zuciya tace dashi karanta kaji mana abinda sakon ya kumsa kila mai amfani ne gare ka. Fara karanta sakon ne yaji ranshi ya baci don ya fahinci inda sakon ya fito don ganin farkon rubutun nawa kamar haka Mijin buzuwa a zaton ka zaka iya rabani da hajiya mamane ko ka zubar min da mutucina da take gani kayi kuskure wallahi kuma kayi karya don bakina da naka ban fada ma hajiya mama tana gida an mata rasuwa ba. Ga wanda yasan mutuncinta yasan darajan ta na fadawa shida ya tambaye ni ko ina da labarin su bakai da buzuwa wace bata da daraja da galihu tasa ka zubar da matan ka da yayan ka da kowa naka kana ganin tsohuwar buzuwa tana maka rudi da huduban shedan kullun. Kai bari ma kaji wallahi wanan buzuwar ta zubar ma da kima da komai naka a idon duniya tunda kiri kiri ta mai dakai mijin hajiya. Ga mutum har mutum amma baida ta cewa saboda mace macen kuma buzuwa wace bata san Allah how dear you kaida mace bata bari ka zauna dako matar sunnan ka har kake da bakin yi mun hadi a wurin mama, , , , Jikin shi har rawa yakeyi da yake karata text din kasa kai kashen rubutun daki ya nufa da sauri da zuman ya shiga yai wanka ya fita ya samu Yusuf shida yaja mashi rene da wullakanci wurin yar karamar yarinya harta iya turo mashi text din banza haka. Sai yayi magani na a garin sai yasa na raina kaina may nike dashi may nake takama dashi da zan iya yimai cin fuska haka ina aibanta shi shi da matar shi. Waya ya fada min maganan da sukayi da hajiyan su hajiyan ne zata fada min kowa komai dai may nene sai ya rena min wayo sai na gane banda wayo yau a garin nan duk inda na shige sai ya tononi a cikin garin nan yayi min wulkanci Sai dai yana shiga dakin su kuma sai bacin ran nashi ya karu ganin Nafisa kwance tana barcin ta hankali kwace rashi ne ya kara baci ya tuna abinda nace a text dina. Bai san lokacin da ya isa wurin ta yakai mata mugun maka a tsakar bayan ta ba ta mike firgigit tana fadin Samad may nayi maka ? Tsawa ya daka mata yace wanan abin zai hada ni dake ke sai yaushe ne zaki rike ibada a zuciyar ki ne yaja tsuki ya shige wanka. Da sauri ya watsa ya fito ranan ya fito bai wani dauki dogon lokaci ba ya shirya ya fita daga gidan koda ta fito ta samu baya gidan. Tun a mota ya kira Yusuf yana fadin kana inane yanzu? Gani gidana ya bashi amsa OK kajirani ganin zuwa yanzu gidan yace eh mamaki Yusuf yaji yana tunanen mai zai kawo Samad gidan shi wanan lokacin haka. Don ka idar shine sai takwas yake fitowa ko takwas da rabi ware hannu yayi alaman shi ya sani ya mike ya shiga wanka kada yai mashi girshi. Yana shiri ya sake bugo mai waya gashi kofa gidan shi ya fito ya karasa ya fito ya samay shi don ko driver bai fito dashi ba Yusuf din na gani haka ya rufo gidan nashi ya fito ya samay shi. Anan ya bude mai mota ya shiga yarufe sai ya dauki hanya batare da yasan inda zasu nufa ba sai yaga ya miki mashi wayan shi duban wayan yake da mamaki yake fadin na maye wanan kuma ? Ka duba mana cewa fuska a daure ya karbi wayan ya fara karantawa a hankali yana sake murmushi ya gaba yana mika mai wayan yace kai amma wanan yarinyar takai jaruma wallahi haduwan zai zama abin shaawa ga mai kallo. May ne kace yanzun kai baka ga abin jin haushi ba a nan yace ban gani ba sai ma wani abin da na hango na daban tsakanin ka da beauty din. Yau sai nanu namata ita ba kowa bane a garin nan sai na wullakanta ta a garin nan dariya yayi sosai yace da kaima kan ka wallahi da ka tozarta kan kuwa. Wai kaiko kaga yadda kukai balain dacewa da yarinyar nan kuwa wallahi ni abin naku burgeni yake yi idan kuna yi har wani dadi nake ji. May kake nufi ne wai yace abinda idona ya hango min mana a kai saidai fatan alheri amma zancen ka ci mata mutunci bai taso ba ko kaje ka tozartata duk ba wanan a tsakanin ku ko kamanta da hikimar hajiya na hada ka da wanan yarinyar ne ko kana nufin kai baka gane hakan ba. To bari kaji Khadija itace zata iya fitar dakai daga zargin da ake maka na cewa Nafisa ta gama dakai da cewan da ake saboda ita ka kasa zama da Fati. Akan wani dalili zata fitar dani ta yaya din zata fitar dani yace muje zuwa nan gaba zaka sani idan lokacin hakan yayi yanzo ina zamu ne kadauko ni tunda safe haka. Wurin ta zamu in gwada mata ita din ba kowa bace ya kwashe mai da dariya yace ta zama kowan ke nan tunda har zaka iya biye ma shirmay ta na mata. Bai kara magana ba sai juya kan motar yayi zuwa office din su ya shige bai tsaya jiran Yusuf din ba. Anan malam musa driver ya tsayar dashi yana fadin yana da magana dashi na siri da yake son suyi a tsakanin su yace da malam sani din wani abu ya faru ne yace eh to sai dai maganan nason siri gaskiya yace dashi babu damuwa kasa may ni a gida da yamma idan mun tashi. Ga haka suka bar zancen da malam sani din sai dai ya barshi da tunane a zuciyar shi ko akan may yake bukatan kebewa dashi bai sani ba ya san dai abune mai muhinmanci sosai. Shiko gogan acikin office maganan da sukayi da Yusuf ne yake ta mashi yawo arai wai zata zama mai garkuwa a kan matsalan shi da Fati da Nafisa ta yaya ma haka zai faru . Nan dai ya watsar da maganan ya ci gaba da aikin dake gaban shi sai dai yanayi yana tuna zancen a zuciyar shi. Kai tsaye da na fito kamar yadda na saba gidan da muke na nufa yau yawan ci basu da lectures sai karan gida ke tashi ko ina a cikin gida. Yunwa nake ji don ban tsaya nayi karin kwarai ba da safe sallah nayi sana fara hada tea na nasha sai da na dan huta a wurin na mike ina sauya kayan jikina. Na saka dan guntun rigan da nake zama a daki dashi gyaran dakin nayi na gyaro ko ina na dakin sai na dora girkin dare don shinkafa da miya nake son yi irin na yan makaranta. Bayan na gama miya na dora shinkafan na koma na zauna a bakin katifa ina tunane zarah ne ta fado min a rai yau in zan lissafa kwananta biyar bata dawo ba. Zarah tana daya daga cikin "ya"ya dake cin amanan iyayyen su don babu inda suka rageta don koba a fada ba zarah tafi gata don sati biyu bai shigewa iyayyen ta basu turo mata da sako ba. Amma duk ta watsar da wanan gatan nata tabi ra,ayin kwadan abin hannun samari wanda ya rufe mata ido a yanzu har yakai ga ta watsar da karatun ta. Ido na lumshe tare da girgiza kaina ina cewa ubangiji katsare mu ka karemu ya Allah kasa mufi karfin zuciyar mu don yanzu rayuwa abin tsorone . Sai gata washe gari ta dawo dakina ta nufa don karban key din ta koda ta shige ban sake mata fuska ba daga inda nake kwance ta tambayi key din ta na nuna mata da hannu kawai ta nufi wurin ta dauka. Harara na bita dashi tana ficewa daga dakin andan jima kadan sai gata ta dawo dakin daga ita sai wani dan guntun tawul da ta daura iya cinyan ta tana tambayana wai ban rage abinci ba in bata. Wani kallo nayi mata nace inda kika fito gantalin ki kwana da kwanaki baki kici abinci bane acan ? Tace kin san yanzu wata yayi nisa ba wani abin kirki ake samu ba sai maneji nace sai ki je gaba ki nema ni banyi abinci ba yau. Ta ce khady yaushe kika fara rowa haka ba halinki bane rowa nace ban dafa ba nace maki ashe karyan iskanci kike yi da zaki dawo kwana da kwanaki hannu empty. Ta dan tsaya jin ganin ban kulataba ina karatuna sai ta fice min daga dakin dagowa nayi nabita da kallon mai kama da harara har tafice daga dakin. Bayan ya gama saurare abinda malam sani ya gaya mashi jikin shi ne yayi sanyi karshe yayi mai godiya tare da jaddada mashi kan kada ya fada ma Nafisa komai ya dai saka ido ga alamarin ta kawai. Bayan fitan shi gidan nine na fado mashi a rai wayana ya kira mun gaisa dayake shi mai son wasa ne nan yajani da wasa wanda bai wuce hiran mijin buzuwa. Yace gobe dai weekend ne ba shiga aji ke nan nace eh sai dai ina son zan fita zuwa wurin wankin kai don ina son gyaran jiki gobe dai. Yace ashe shi gyaran ma sai anje wani guri yin shi dariya yaban don irin zolayar shi nace ana mace ba gyara ne yace kwarai kuwa har in ta san kanta. Karfe nawa zaki ya tambaya nace wuraren goma zan tafi nasan zuwa karfe sha biyu ko da rabi na gama yace da safe banda time da nazo na kaiki sai dai ki fada min sallin din da kike zuwa in duba ki idan na rarage abinda nake yi. Nace No kabarshi kawai ba wani nisa yake dashi da inda muke ba nagode yace aini nace ki fada min ko nace beauty hair drasses na fada mai layin da yake a saman babban titi. Munyi sallama ina mamikin halin shi da saurin sabo irin nashi na zauna na tsefe kaina a cikin daren nan don kada in makara in samu mutane a wurin. Washegari da safe na shirya na isa sallon din ba wasu mutane dayawa don haka nabi layi sai da akawanke min akai min drying din shi kafin su fara min kitso. Ranan nasha gyara sosai na jiki daidai zan fito sai ga wayan Yusuf shigo yana tambayana ina wurin ko wuce nace an kusa gamawa nan da minti talatin zanbar wurin . Nakashe wayan akaci gaba da min gyara sai yaba yawan gashina da tsayi suke yi nidai murmushi kawai nake masu ban wani dogon magana da kowa a wurin. Sun fito daga kubuwa duban fili da sukaje gani a hanyansu na komawa gida yaga Yusuf ya dauki hanya bai iya magana ba yana aiki a system din shi kan shi a duke yake. Sai dai yasan ba hanyan gida Yusuf ya nufa dasu ba aikin da yakeyi ya dauke mashi hankali a lokacin ganin ya tsaya a bakin wani gyaran jiki na mata yasa shi dago kai yana tambayan shi ina ne nan kuma ? Kafin ya bashi amsa yaji yana fadi a wayan shi fito gamu a kofa idan an gama maki nace gani tafe na fito tun fitowa na ya hango nice tafe kallon mamaki yake wa Yusuf din. Har na karaso bakin motar nasu sai a lokacin nasan tare suke dashi fadi yusuf ke yi da na karaso wai wanan haduwa haka fa kanwata . Kaike kara zuzuta yayi maganar kamar bashi ya fada ba yace ba dole ba in zuzuta kanwata yar gidan mama wanan ai kyasa ayi karo a hanya nidai murmushi kawai nayi mashi. Na fara gaida su yace shigo mu sauke ki mana ba hostel zaki koma ba nace a a nagode yayana ku tafi abinku kawai dakai dayane zan shiga amma dai ku tafi kawai. Yace au don wanan miin buzuwan da kika gani ai bashi ke jan motar ba ko shiga muje don ki kawai muka biyo nan fa. Jin haka yasa na bude motar na shiga batare da na sake wani magana ba shiko sai aikin shi yake yi kawai ana tafiya mun kai wurin wani babban shago yace don Allah ku bani minti biyu in dawo. Ya faka motar yafita sai mu biyu a cikin motar kowa da abinda yake yi a lokacin sai can naji yaja tsuki yana kallon shagon na dauka dani yake yi nace dakata malam bafa kai ka dauko ni ba da zaka ja min tsuki haka. Da mamaki ya dago kai yana kallo yace ke dani kike nace da wani nake haka kawai zaka kama jamin tsuki a mota da mamaki yake kallo na yace ke wata irin yarinya ce da bata da tarbiya. Kadai gyara maganan ka malam tarbiya ai ko makaho yasan akwaishi nan sai dai a lalaba a gani ai ba bace marasa tarbiya suke ba. Bai kai karshen magana ba cikin zafin nama da kunar zuciya ya juyo inda nake yace wa kike nufi baida tarbiya cikin muryan nan nashi mai dadin saurare da yake rowan ta. Tsoro naji ganin irin kallon da yake bina dashi mai kama da harara ko tsana sai nayi kasa da kaina na kasa furta komai don kwarjin da yai min a idona Ya nuno yatsan shi daidai saitin fuska na tare da tsure ni da idanuwan shi lumsarsu yana fadin ke in badan Yusuf da bai san ciwon kan shi ba har kucaka irin ki ta isa ta shiga min mota na a tare dani. Yace kallani nan ko a hanya nagan ki baki isheni kallo ba a cikin mata don banga abin gani a wurin irin ki ba cikin dakiya da dauriya nake kallan shi ina jin kalamin shi har cikin raina sai dai ina tara abinda zan mayar mashi ne a zuciya ta duk da naji tsoran yanayin shi. Yaci gaba da fadin idan baki hankali da ni ba watarana sai na balbala ki wallahi don ni mace bata kawo min raini nace dashi. Don Allah malam matsamin bakumayi mamaki jin haka don ba abin mamaki bane don ka fadi hakan tunda dama kai irin maza nan ne dake raina jinsin su sai kai ido ga mata ketere saboda zalama irin na rashin sanin ciwon kai. Don wanan matar taka abin kyama ga jamma a da kai ka mayar mutum har kake ganin tafi ko wace macen kasan nan dadin abin dai kaima macen kasan nan ta haife , , , , Fat naji yakai min bugu a baki don zafi sai da na dafe baki na ina dubawa ko jini yake min ban san lokacin da idona ya fara fitar da hawaye ba na yun kura zan fita daga motar yasa hannu ya danna lock mutar ta rufe kit yace kuma ki saurare ni. Duk kika sake ganina a mota kikayi gigin shigan shi sai ya jefar dake a waje mota ya take ki kin mutum in kashe ki in kashe bazan . Nace ni wallahi ba banzan bace sai dai in kaine yace bakin naki bai mutu bako yana kokarin kai hannun shi ya kamo baki na na noke kaina a kafana sai bai samu kama bakin nawa ba. A daidai lokacin Yusuf ya iso wurin da manyan ledoji a hannun shi yana bude motan zai sa ganin mu haka yasa shi ya sake murmushi. Ina jin shi nayi saurin dago kai nace mugu kawai azzalumi yace kai yaya haka may kai mata don Allah take kuka kuma ya waigo zai kara jamin baki na noke ina son fita a motan Yusuf ya tare ni yana fadin haba dai yaya zakaci zalun ta kuma haka ? May tayi maka haka wai kasa ta kuka ya juya yana cewa bakin nan mai rashin kunya na daka ido ya zaro yana cewa ka dake ta Abdul ? Kadan ma ke nan nayi mata ai fita nake son yi ba hanya don Yusuf dake wurin yayi rufe kofan ya zagaya ya shigo motar sai da muka fara tafiya yace ka bata hakkuri Abdul. Ina baya ina kuka naji ya fada mai hakan yace nace ka bata hakkuri yace wani zanba wanan yariyar hakuri ko wa yace bakai ka zalunce ta don may bazaka bata hakkuri ba ko kafin ka tafi da hakkin ta ne a kanka ? Baiyi magana ba sai aikin shi dayaci gaba dayi yace wai may ya hada kune haka da sauri nace zagina yayi na rama. Motar ya tsaya a kofa gidajen mu na fita da sauri ya biyo ni yana kirana ban tsaya ba wata yar gidan yaba kayan ta shigo min dasu suka tafi ban san yadda suka karata ba. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABUIna isa na fara bude kofana na lokacin yarinyar ta iso da kayan da Yusuf ya bata tana mika min kallon kayan nayi sai na karba ta karasa min da sauran a cikin daki na. Godiya nayi mata tace babu komai ai ana tare bayan na aje kayan na fada saman katifa na wasu hawaye masu zafi ne suke silalo min a fuska na. Idan na tunana da maganganun da ya fada min masu zafi duk da nima din nayi karfin halin ramawa a lokacin sai nake ganin ya kwaraini da yawa. Na dade a wurin ina neman hanyan da zan rama abinda yayi mun din don yaji zafin da naji ban kai ga samun mafita ba wayana yayi kara a lokacin. Yusuf ne ya kirani sai da ta kusa tsukewa na dauka na kara a kunne na ina sauraron shi yace har yanzu kina fushi ne yar mama. Daurewa nayi nace ai ban fushi dakai don bakai min komai ba yaya na yace dakyau ina son ki saurare ni dakyau magana nake so muyi dake yanzu. Ina jinka nace mai. Khadija don Allah ina son ki bani hankalin ki ki fahinci abinda zan fada maki yanzu naji na kara furtawa. Don Allah ina son in rokeki wata alfarma wani aiki zaki nake son ki min a kan aboki na amma aikin yana da wahala sosai sai dai indan kin daure ba wani wahala a cikin sa. To ina jinka Allah yasa zan iya kuma Allah yasa dai aikin bai fi karfina ba, murmushi yayi yana fadin bai fi karfin ki ba ma insha Allahu don zaki iya. Nace fada min inji aikin idan ba zai shafe karatuna ba da rayuwa na zan iya insha Allahu yace good girl dama na dade ina neman mace irin ki mai gaskiya da zan saka. Ba wani abu zan saki ba sai taimako rayuwan abakina Samad nake son in danka a hannun ki don kice a yanzu kadai nake da ita da zatayi min wanan kokari. Nace ni kuma yayana yace kwarai kuwa ke khadija don ko zaki iya idan munyi laakari da irin halin ki na san zaki iya shiyasa na zabo ki. Tun ranan da muka shiga dakin hajiya mama na fara ganin ki da kuma abinda yafaru dake da Nafisa matar shi kika tsaya min a rai. Ban kuma gaskanta hakan ba sai da naga kin iya biyu su a motar su zuwa nan Abuja kuma komai bai faru ba yasa na kara yarda da abinda nake shirin yi din . Sai gashi kuma yanzu abubuwa suna wakana a yadda nake son su tafi a tsakanin ku cikin hukuncin Allah komai yana tafiya daidai. Khadija ko kin san ba macen da ta isa ta tsaya kusa da Samad tun lokacin da ya auri Nafisa buzuwar matar shi kuwa. Nasan kin san matar shi Fati da akai masu auren gida har suka haifi yaya biyu shigowan buzuwa gidan ya sa suka rabu da ita badon basu son junan su ba. Khadija kin san abinda ya daure min kai nace a a yace yadda Yusuf ya aminta dake a lokaci daya duk da nasan ba abu bane mai wuya a wurin Allah idan ya tashi yin ikon sa akan abu. Don haka nake son ki taimaka muna ki sake jiki da shi tayadda zai aminta dake idan haka ya samu gare mu na tabbatar da sheri buzuwa yana gap da karyewa. Da sauri nace ba zan iya ba gaskiya ku nemi wata wanan miskilin mara mutunci ai buzuwar ne daidai dashi yace khadija zaki iya zaki iya komai. Kyau dai Allah ya baki shi ilimin addini da na boko duk kina dasu a wadace to may zai saki ce bazaki iya ba ai ko ba don niba ko don hajiya mama da fati da yaran ta zaki iya. Nace yanzu may kaka son in yi wai yace shina ke son in fada maki da farko dai idan ki bi labari na zaki gane Samad bai iya ssoyayya ba shine matsalaan farko da aka samu gare shi. Murmushi nayi nace bai iya soyayya ba ta yaya ya auri matan shi har suka zauna Fati har ta haihu dashi biyu shima din murmushi naji ya dan yi yace. Bamu tare ke nan kin manta na fada maki ita fadi hadin iyayyene auren su ita kuma buzuwa abu biyu muke zaton shine silar auren su na farko dai ta rude shi da kyaun ta na biyu kuma ta hanyar sihiri da sauri nace sihiri kuma bada ni ba gaskiya. Yace da zata iya maki komai da tayi tuntuni ai shine ya bani daman sakaki wanan aiki a yanzu. Nace a takaice dai kana son in bata lokaci na a kan shi abinda ya kawo ni in barshi inje taimakon wani wanin ma wanda bai san darajan mutane ba. Aikin da zaki muna ke nan dama ki koya mashi zama da mutane da sauran abubuwan da ya watsar a baya ki dawo muna dashi Abdulsamad din shi na baya. Babban magana ke nan yayana yace ba wani babba bane a matsayin ki na mace zaki amfani da daman ki taimaka muna ki tai maki hajiya dake cikin halin bakin ciki a kashi. Shiru nayi ina tunane ko badon Yusuf ba ko don hajiya da yaran Fati zan iya kasadan yin wanan gwajin da suke sona dashi yanzu. Nace to shike nan naji zan yi matukar hakan ba zai shafi mutunci na ba dai yayi saurin cewa idan nasan zai zubar maki da kiman ki ba zan saka ki ba ai. Nace amma fa in ya nemi keta min mutunci ba zan kyale shi ba zan dauki mataki da kaina yace wanan ba halin shi bane don nasan halin shi tare muka taso tun muna yara dashi. Nace Allah bamu sa,a yace amin na godd da kika fahince ni yanzu zan samu lokaci in shigo inji mai kike bukata don kin san dole sai kin koma ke ma babban yarinya sosai. Kada ka damu zanyi amfani da wanda nake dashi yace kin wuce wanan yanzu khadija zaki zama budurwan mayan garin abuja ne fa. Yace ina son ki fara daga yau nace yau din nan ina zanganshi yace zai bugo maki waya ba yana da layin ki ba nace eh zaki kaga ya kiraki kan abinda yayi maki. Amma sai dai please ki bishi a hankali yana da izza da saurin fushi da zuciya bai son yawan magana idan ba yaso ba amma banda wanan baida komai da zaki damu. Ni kuwa nasan haka nida ya fada ma magana yau sun ranshi sai dai zan jure kamar yadda kuke so inyi din. Ajiyan zuciya naji ya sauke yace ban san irun godiyan da zanma maki ba ga wanan haracin da kikai muna wanda nasan insha Allahu zai zamo maki alheri ke ma nan gaba. To Allah yasa hakan alheri ne a gare ni dai fatana in ga ya koma da iyalin shi normal sai naji ya sauke ajiyan zuciya yace final shine dama bukatan mu . Mukai sallama ya barni ina tunanen yadda abin namu zai kaya tsakanina da miskilin mijin buzuwa ta ina zamu fara nace anya ban daukar wa kaina abinda ba zan iya ba kuwa. Gashi kuma Yusuf yace sirine ne tsakani na dashi sai Allah sai ko nan gaba da zai fada ma hajiya mama shirin shi. A raina nace zan iya insha Allahu indai iyalin shi zasu dawo gare shi sai dai ban taba zaton abin zai zo a kaina haka ba amma ba komai wahala bata kissa ai. Nan dai nayi ta tunanen ta yadda zan fara deal din akan shi amma dai Yusuf yace shi zai fara aiwatar da komai kamar yadda yake yi da farko. Safiyan lahadi wanki nayi sai wanan bakuwar yarinyar da ta shigo min da kaya don dai han san ta a gidan ba tazo min hira dakina ina gugan kayan da suka bushe min. Nan take fada min ai ita yar jos ne amma tana zaune ne da yayanta a nan cikin gari ta dawo hostel ne don ta samu yin karatu da kyau naji dasin haduwa na da ita ko banza zan rage zaman kadaici ni kadai da nakeyi ni kadai. Waya na yai kara na daga Yusuf ne bayan mun gaisa yace fito gamu kofan hostel din ku dam naji gaba ya bada na kalli maryam dake gefe na nace ina zuwa ta mike ita tace zata je ta gyara daki don gobe akwai classes. Ba wani dogon kwalliya nayi na dan yafa gyale na na fito tun fitowa idon su yana kaina har na iso inda suke a cikin motar su. Na gaida Yusuf din yace ga abokina ogana baki gaida shi ba na dan juya wurin shi a yatsune nace oh ashe tare kuke ina wuni. Haushi da takaici ya kama shi ya rasa ma zai yi sai da Yusuf yace khadija na gaishe ka fa cikin yanayi da alama na ko in kula yace lafiya kawai ya kawar da kanshi gefe. A ranshi yace i hate dis girl wallahi Yusuf ya katse shi da cewa oga gata nan ta fito fa ya fada cikin tsigar tsokana ya juyo da sauri yace wa wurin na tazo dama. Yace bakai kace muzo kabata hakkuri ba abinda kai mata jiya kasa ta kuka ya damay ka da sauri na tare Yusuf da cewa ai nice zan bashi hakuri nida na bata mashi rai jiya. Don fadin gaskiya ni kuma nasan gaskiya na fada duk cikkaken namiji da yasan ciwon kanshi ba zai tsaya mace na juya shi macen ma kuma buzuwa wai. Yusuf dama ka kawo ni nan ne don ta kara ci min mutunci ko may haushi ya ishe shi yarasa may zai ce min wallahi na tsani wanan yarinyar ya fada a hasale . Cikin ko in kula nace i hate you too dama abinda yasa kuka zo ke nan daga ganin ka nasan ba yin kanka bane buzuwa ta hasala ka ka koma ma matar ka kawai ta asali ko mutuncin ka zai dawo ga idon jamma, a. Yusuf yace kai oga fitina khadija ko rigima nace bai son gaskiya ne gadai mutum har mutum amma bai kai ga cikan kamala ba har yanzu ga idon jamma a. Oh stop it gara ku fito fili kununa ma duniya soyayyan ku da wanan sallon soyayyan naku da kuke yi kullun u don't need to pretend garama ku fara tun yau. Wai Yusuf may kake nufi dani akan wanan yarinyar ne da kullun kake kawo ni wurin ta taci min mutunci hakane. Ni dramar kuce take burgeni wallahi don naga idan na kawo ka wurin khadija tana saka magana kana rage damuwa ko yaushe kuma tana ma tuni da abinda ka manta. Gyara zama yayi a motar ya kwantar da kai tare da harde hanaye shi wuri daya yana kallon bakin hostel din mu yadda mutane ke ta shiga da fita ciki. Nima kallon Yusuf nayi nace yayana wani wuri zaku ne yace muna dan yawata wane muka zo duba ki kin san ke amanan hajiyan mu ce gare mu yajuya wurin shi yana fadin ko ba haka ba aboki na ? Tsaki yaja ya kara kawar da kanshi gefe nace sai dai tsiyan abin indan yayi fushi fushin bai mashi kyau sai ma ya kara mai muni sosai. Murmushin dole ya sake yace kai Yusuf muje don Allah wanan na gane zata iya haukatani in banyi da gaske ba. Kaiko daukanta zamuyi mutafi da ita adan sawo mata wani abin mana kaga sai ta kara hucewa ko tunda gashi har ta baka hakkuri yanzu ai komai ya wuce kenan. Kinga ba sai kin fada ma hajiya mama dukan bakin ki da yayi ba jiya ai yanzu kun zama friends kuma ko fada ya kare ke khadija ba yayaki hakkuri don Allah. Da sauri ya juyo inda nake sai na dan durkusa nace ya Samad kayi hakkuri don Allah idan na maka laifi. Oh baki san ma kin min laifi ba ke nan Yusuf yace shigo mota sai mu karasa magana a hanya yamma nayi kwarai. Banki ba tunda nasan plain ne na shiga motar a hankali ya harba titi ina harara dan iska a inda nake zaune Yusuf ne ya shiga aiwatar da nashi shirin a lokacin cikin motar yana dan muna nasiha. Yace kar kuji komai indan nine take a deep breath and confess your love to each other wani irin dogon nunfashi yaja tare da lumshe idanuwan shi. Da sauri nace yayana love kuma a ina kataba jin anyiwa mutum dole haka akan abinda yaki jini yace don't say dat again just say yes to each other don kuna bukatan hakan. Khadija ina son ki rike min oga na tsakani da Allah ko babu soyayya ku zama aminan juna muna son ki gyara tsakanin shi da hajiyan mu ta fahince shi ta bar hushi dashi. Sai lokacin ya kallo Yusuf ya sauke wani ajiyan zuciya don ya zaci Yusuf yana son hakane don gyara tsakanin shi da mahaifiyar shi. Nace yaya zanyi in gyara mashi laifin dashi yayi da kan shi har kake tunanen nice zan gyara hakan yace yes idan hajiya taji kuna tare nasan zata ji dadin yin hakan da kuka kin ga zata fitar ma abokina da zargin da suke mashi na buzuwa bata bari ya rabi wata mace sai ita. Sai yanzu na gane nufin ka abokina ya danyi gyaran murya sai kuma yayi shiru can yace da farko dai na gane manufan ka yanzu Yusuf . Yace zamu shirya dake idan har zakiyi min wanan taimakon iyayyena su fahince ni a hankali nace idan ka shirya yin hakan a shirye nake in taimaka ma in har zaka koma masu da zuciya daya. Maganan ta dan soshi ranshi amma haka ya dake yace na gode a hankali ai lokacin gode min baiyi ba nace mashi. Tsayar da motar yayi a bakin wani babban sai da kayan sawa irin na mata da maza ga motoci birjit a wurin an paka su a haraban wurin. Bissimilah yace muna kallon shi yayi yace wa wai ni kake nufi kowa yace daku duka nake magana ai yace may zanyi a wanan gurin yace kaunar mu zamu ma sayayya mana. No kuje kawai yace yana gyara zaman shi a yadda yake nace da ka barshi ma ban bukatan komai a yanzu yace tunda nayi niyar yin haka barin in fita induba zaku iya jira a mota yana bude motar zai fita yake wannan magana. Da sauri nace dashi barin fito mu shiga tare yace No ki zauna abinki yanzu zan fito ba dadewa zanyi a ciki ba. Yana wuce na koma na zauna bayan na bishi da kallo wayana na dauko ina dubawa shiru motar babu mai maga a cikin mu sai can naji yaja guntun tsuki wai da bai harka da kananan mata sai manya masu aji ko su sai a waje idan yafita duk da ba wai yana yawan hurda dasu bane yanzun ga Yusuf yana son ya dauko mashi wani aiki ga wanan yar karamar yarinyar dako sa,an kannen shi batakai ba sosai. Nima tsakin naja ina gyara zama cikin tunanen da nakeyi nashi. Ga dai mutum har mutum kudi kwaliya kwarjini duk Allah ya bashi sai dai yawan miskilanci da girman kai da jan aji din yayi yawa kamar ba mace ce ke juta shi ba a gida. Ke ni kike wa tsuki ko kowa ya juyo tare da zuba min kyawawan idanuwan shi a kaina na ma mance kana cikin motar nan murmushi mai kama da takaici yayi yaci gaba da zuba min kyawawan idanuwan shi can ya koma ya lumshe su tare da komawa saman kujera ya zauna. Ya sake cewa kina aji nawa ne yanzu ba tare da ya juyo ya kalle ni ba shiru nayi ina game da wayana batare da na nuna mai dani yake magana ba. Dake nake magana ko bakiji bane nace wa ni ai na dauka da kurma nake a motar a hankali ya kada kanshi ta dan sake murmushi yace ke dai ba zaki bar wanan halin naki ba ke nan. Nace ba halina bane hakan a ra nayi don in kare kai na daga masu raina ma tallaka hankali ya fido ido waje yace haka kika dauke ni ke nan . Hakan na gani kamar kana tsoron talaka a kusa da kai sai dai ba abun mamaki bane don ko a gida haka naga kanayi masu wanan daure fuskan. Kin san nayi ma aboki na alkawarin ban kara fada dake yanzu don haka ki kama min bakin ki tunkan in hasala da wa yan nan maganganun naki. Kai ashe kasan girman alkawari haka ne nakoji dadin jin hakan saidai kamar yadda kai mashi alkawari ka cika nima ada hakana naiwa kaina alkawarin ba zan tsaya da wani namiji ba sai gashi a sanidin taimako ina son karya alkawarin da na dauka ma kaina. Yaja numfashi tare da cewa wanan deal ne a tsakanin na dan wani lokaci banga abinda zai sa ki dauke shi kamar serious ba. Nayi dariya tare da cewa wasa mai kamar wahala ba indan buzuwa ta sanda hakan akwai matsala babba ashe sai na kwashe da wanni irin dariya mai ban haushi dake wa yayi bai ce komai ba cikin kuluwa. Yusuf ya fito da manyan jakkuna a hannun shi yana kokarin bude motar ta kofar baya ya saka jin dariya yasa shi cewa abin ya fara tafiya ke nan dai. Ya dai kusa na bashi amsa a takaice kai a fasa wanan deal din nace a fasa gaskiya zai fi don wanan ba zai kai ko ina ba. Zai kai mana yace yana rufe kofan motan ya zagaya ya shiga kallon Samad dake dafe da kan shi yayi muka kama hanya a lokacin hadari ya hadu sosai a garin ruwa na iya zuba a ko wani lokaci. Mun iso Yusuf ya tsayar da motar yace khadija mun gode sai mun kara haduwa yanzun ba time hadari ya hade gari ta ko ina nace nagode kwarai. Ka kula min da mijin buzuwa don Allah na bude motar zan fita yace ga kayan ki nan ki kwasa duka naki ne godiya na sake mai karo na biyu na fice daga motar. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABUIna shiga ruwa na saukowa daga sama da karfi dama hadarin da ya gama haduwa a lokacin kiris yake jira ya fara zuban ruwa. Ruwa ake sosai a lokacin na kuma san basu kai gidajen su ba duk da ba zan iya cewa ga nisan gidajen su ba a lokacin. Na fara cire kayan jikina aka turo kofan dakin nawa da na saya da sauri na juya don ganin wanda ya shigo min a wanan lokacin haka. Maryam yace sabuwar kawar da nayi a cikin hostel din namu tana rike da wani warmer dain abinci na silver mai marika tashigo tana dauke da murmushi a fuskanta nima murmushin na mayar mata a lokacin nace cikin ruwan nan kika fito. Tana aje kulan tace tun dazun nake dakon dawowar ki ai sai yanzu na ga wuta a dakin ki na san kin dawo gami da yi min sannu da dawowa na amsa ta. Na karasa cire kayan na daura zani a jikina tace abinci na kawo muci don yanzu na samu yar uwa na huta zaman kadaici hakana murmushi nayi ina zama a saman katifan nace fitan nan nawa har kikai girki haka ? Tace dama akwai miyan a fridge sai shinkafa ne kawai na girka muna yanzu nayi mamakin jin har da fridge a dakin ta don ban taba shiga ba sai ita ce mai zuwa dakin nawa. Ido na ta kai ga ledan da na shigo dasu dakin yanzu na dauko na fara budewa kayan mata ne a ciki irin doganyen rigunan nan har kala biyar sai takalma da jakka biyu. Sai dayan ledan mai dauke da kayan drinks da su packed din sweet irin mai tsadan nan tace woow duk wanda yayi sayayan nan yasa kansa wanan rigunan duk letes ne fa don anty na business din da take yi ke nan wanan dawowan da tayi daga dubai naga ta dawo dasu har nace taban guda daga ciki tace sai dai in saya. Nace uhmm kyautar maya ne haka maryam wasu yan yan gari mu ne da suka zo yanzu muka fita tare suka saya min su. Maryam tayi dariya tace manya ko ba nawa sa ba nerbough don wanan wawan kyautar sai da wata a kasa kin san ko ba karamin kudi aka kashe wurin nan ba. Nace kuma kin ga ba wani abu a tsakanin mu sun dai ce ne mudan fita in rakasu wani wuri ni ban ma shiga shagon ba Yusuf kadai ya shiga sai gashi da wa yan nan kayan haka ya fito. Tace haka abin yake ai don masu kudi basu jin zafin fitar da kudin su, ga abinda suke so don wanan kyauta ai ta maya ne daganin su duniya na damawa dasu Allah. Nace sam ban san yayi min wanan mahaukacin sayayya ba da na dakatar dashi wallahi ni na dauka ko irin dan drink's din nane da sweet fa. Maryam tace may ye na damuwan kan ki tunda bake kikace su saya maki ba sai dai gaskiya kyauta yana nuna alama ga abinda ake so ne. Nace so kuma ai sun san ban da lokacin wani so a yanzu kawai dai raayin su ne yin hakan sai dai zan dakatar dashi ga yi min haka nan gaba. Abinci ta fara zuba muna muna hira na kwashe kayan na kawar gefe guda ina ce mata kinga yanzu sai dai mu canza tsari ba wai kullun kita dafawa kina kawo min muna ci ba haka. Dariya tayi tace kin manta da rana naki mukaci shiyasa nima na dafa muna yanzu muci ai ko hakan kuma laifi ne nerbough ? Muna ci muna hiran makaranta da ita har mun kusa gamawa wayana dake gefe yayi kara da sauri na mika hannu na dauko don kada ya tsunke. Daddyn mune akan layin na dauka da sauri ina hadiye abincin da ke a bakina yace may kike ci haka khadja ko dadi kuke ci a makarantar mu muna nan gida muna hadiyan shikafa da mai ya fada cikin zolaya . Nace daddy Allah ya nuna muna mun samu kuma kuji dadin da iyayye ke ji ga diyan su watarana indai zakuyi farin ciki da hakan. Yace ko yanzun ma mun gode maku don muna cin moriyan ku a haka yaushe yaushe kika turo muna da kudin hannun ki wai mu kara nayi fada ai da yar uwarki nace ke da kike makaranta kin fimu bukata a yanzu ai. Burin mu daya shine muga kin tsayar da miji da wuri kiyi koyi da yar uwar ki kema kiyi aure basai kin yi dogon karatun nan dakike so ba. Dariya nayi nace kai daddy aure yanzu kuma nida nake son in zama babban lauya kafin in aure amma tunda naga raayin ka ke nan ba damuwa . Daddy da izzinin Allah zan cika maku burin ku daddy na karasa fadi cikin sanyin murya daddy yace da sauri . Dear kada ki sa wanan a rai yanzu buri na fada maki kawai shi aure ai dan lokaci ne indan lokacin yayi ko da shiri ko ba shiri zakiyi ne ai nafison in ganku cikin farin ciki a koda yaushe bana son bacin ranku kada magana na ya kara maki zuciyar ki akan karatun ki. Ya kara da fadin Allah dai yayi maku albarka dake da yan uwanki don baku taba bata muna rai ba da halin ku. A hankali na goge hawayen da ya zubo min a idona nace mukai sallama dashi bayan ya gama kwatar min da hankali na. Maryam ido ta tsura min ina aje wayan tace dani ina son nima inga ina haka da iyayyena wallahi sai dai hakan bai samu ba a gare ni don na taso ne ba tare da iyayyena a wuri daya ba. Mahaifiyar mu sun rabu da babban tun muna kanana sai dai idan naje inkai masu ziyara dukkan su tunda riko na yadawo hannun yayata. Nace Allah sarki lalai dole kiji sha, awan hakan gaskiya don iri haka babu daddy ni kinga iyayyena sun fi son suga nayi aure ko yaushe maganan su ke nan a kaina. Sai dai ko yaushe auren nawa zai zo ban sani ba tunda ko sauriyi tsayayye ban kai ga tsayarwa ba a yanzu haka. Tace to ina ga dai yazo din ne tunda ga wanan yanzu da ya fito ya fara nuna maki son shi dariya nayi nace maryam ke nan baki ganewa ne ke. Bandai fada mata komai ba mukaci gaba da hiran mu sai goma ta koma dakin ta nima na gama abinda nakeyi na kwata. Har na kawanta naji wayana na verviration a gefena nasa hannu na dauko wayar nace salamu alaikum. Yar mama kina lafiya yaya ruwa , ? Na sauke lafiyayyen murmushi nace lafiya kalau yaya Yusuf yace kina kara fasa min kai fa da yayan nan da kike kirana dashi nace kai ka saya a kira ka da sunan. Nace yaya kuka isa gida kuma yace lafiya kalau sai yanzu na kai mutumin ki gida yanzu haka ina hanyan gidana ne na kiraki mu gaisa. Yace bayan mun rabu dazu mun dade muna maganan ki da mutumi na nasan zai kiraki yau din na shiya na kira ki in fada maki don naga ya yarda sosai da shawarana. Nace anya kuwa zan iya cika maka alkawarin da na dauka don mutumin naka akwai zuciya sosai wallahi ni kuma ban iya daukan haka don nice zan taimake shi ba shi zai taimake ni ba. Dariya yayi yace a yadds kuke yi din nan shakuwa zaizo ya shiga tsakanin ku sosai zakice na fada maki watarana bagashi yanzu ya fara saukowa ba. Idan ba ta haka na fito mashi ba da wuya yayarda mu aiwatar da komai yadda muke so amma ki daure don Allah mubi abin sannu ni dai buri na shine ki san yadda kikayi kika kara ma wanan buzuwar kadarin ta a gurin jamma,a. Abin ne da kamar wuya yaya na sai dai zan yi kokari inga nayi yadda kuke so din yace good girl Allah ya taimaka ya bada sa,a nace amin. Shine kuma ka yi min dawainiya haka mai yawa don Allah nan gaba kada ka kara min irin haka don hakan zai yi maida ni cikin wani yanayi daba shi nazo yi a gatin ba. Dariya yayi yace Khadija kin san dai sutura shine mutum yanzu don haka farawa akayi don ina son ki goge sosai ki fito a cikin classes ladies ta yadda zamuji dadin aiwatar da komai a cikin sauki nace to na gode sai dai a rage don Allah. Kada kiji komai mana lokacin kine yayi kawai ki kwantar da hankaki kici arzikin ki a saukake wanan ba komai ba kada ki damu da hakan don har motan shiga ba dadewan nan ba zaki samu in komai ya tafi daidai. Zanyi magana ya katse ni da cewa na iso gida zan shi sai dai indan mun kara waya don yanzu zamu rage haduwa sosai kada a zargi wani abu a gare ni. Mun gama wayan ina mamakin su kudi kamar na sata haka nikan ban cika amincewa da irin haka ba azo ba a daidaita ba shirin mu ya watse abarni cikin wahala daga baya. A hankali ya shigo gidan babban falon su ya samu su hidaya da sauran yan su zaune suna shan bakin shayin su na buzaye. Gaisuwa sukayi bai tsaya ta kansu ba ya shige ciki bai jin dadin yadda suke cika mashi gida a ko wani lokaci haka. Duk da wani lokaci abin yana taba mashi zuciya ganin yanzu babu wani nashi da yake zuwa wurin shi kamar lokacin da suke zaune kano da fati . Yan uwan shi na yawan ziyarar su maza da mata amma tunda abin ya juye haka sai dai kulun idan ya dawo gidan ace mai akwai bakin da suka zo daga kauyen maradi. Dakin ya nufa ya tura kofa a hankali dakin na nan a yarda ya barshi da safe ba a gyara shi ba in zai iya tunawa yau kwana uku ke nan bai samu lokacin da zai tsaya ya gyara dakin ba. Don cikin yan kwana kin nan suna zirga zirgan filin da suke son saya a kubuwa ga kuma wanan shirin da Yusuf yake son yi a kan shi. Rigar shi ta sama ya jefar a saman gado ya kara bin dakin da kallo ya ja tsuki ya nufi yanyar bathroom din shi wani zarni ne ya daki hancin shi da sauri ya fito ya nufi hanya wajen dakin. Dakin Nafisa ya shiga don yana kyautata zoton tana ciki tunda bai ganta falo ba kuma bai ganta a nan dakin shi ba. Yana shiga nan ma wani tsami ya tare shi mai kama da karni karni yabi dakin da kallo ga kaya a ko ina watse a dakin tana kwance saman godon dake tule da kayan da bai san ko na maynene ba. Nafisa na ganin shi tace ka dawo ashe yanzu nake tunanen ka fa a raina nace ko ina ka shiga tunda ka fita da safe baku dawo ba. Haushine ya kamashi yadda take kwance ta mike kafa sai kadasu take yi tana magana kamar wata basaraka da ita. Kallon da yake mata ne yasa ta tsargu yace Nafisa wai ke dadin may kike ji ga kazantar nan naki ne haka don Allah dubi dakin da mutun ke rayuwa wai a cikin sa. Kina mace kice ba zaki iya gyaran muhalin ki ba sai wasu sunyi maki wai ma ina masu aikin da kikace kin dauka ban ga wani abinda suke a yi a gidan nan ba. Tace Samad yan uwana ne fa ko kuma yanzu kana bakin ciki da zaman su ne a gidan ko suyi aiki ko kada suyi zasu dai zauna anan tare dani ne ko ? Nasan wanan munufakin kila yaka su hadiye a falo ya zuga kwanan nan sai nayi maganin shi wallahi ni banga dalili da zai sa yayi ta shigo min gida ba haka ba gaira ba dalili yana sa muna ido. Ke na fada maki duk abinda zakiyi idon ki ya fita ga Yusuf don idan kikace zakiyi kokarin raba ni dashi kan ki zakiyi wa kin dai san halina and kuma ki tashi kije ki pulloshing din rubish din da kikayi min a bandaki tunda ba dakin ki bane. May nayi kuma kewayawa fa kawai nayi a ciki na fito yace zaki tashi ko sai na bata maki rai yanzu ya fadi yana dan zare mata idon shi. Mikewa tayi da kyar tazo ta wuce shi zuwa dakin ya bita da harara ya mara mata baya yana sa kai warin bayin ya ji har cikin dakin da sauri yafita zuwa dakin hutun shi tare da rufo kofan da key don bai son damuwa. Anan ya cire kayan shi ya yi wanka ya fito sallah ya gabatar ya dade zaune a wurin yana tunanen halin Nafisa ga gida da ta cika mai da yan uwanta babu halin ya zauna a tsararen falon shi ya sha iska a ciki. Tsuki yaja ya mike don ya kwanta nan yaga wayan shi da ya jefar saman gadon daya shigo dakin kafin ya kewaya dauko wayan yayi yana duba lokacin maganan Yusuf ya fado mashi a rai. Da yake ce mashi kabi yarinyar nan a sanun har mu cin ma manufar mu a kan hajiya ba wai nace kaso ta bane dole a a wanan wani dama ne da muka samu zamuyi amfani dashi. Nomba na ya bida a wayan da ya rubuta ma tsoturburn girl ya danna kira sai ko kiran ya shiga tunanen ya fara yi idan na dauka may zai ce min sai yaji na dauki wayan da sallama a bakina. Queen yar matsala yaya kika shiga gida yaya kuma ruwa i hope bai taba ki ba dai ? Murmushi nayi sai da yaji shi cikin zuciyar shi nace au mijin buzuwa ne a layi lallai kana son aikin nan da zan maka ke nan ? Yace to yaya na iya tunda Yusuf yace ke ce maganin matsalata yanzu indai har zaki min hakan ai ya zama dole in koyi zama dake da halin ki . Nace ashe shiyasa na samu queen din yan matsala yace idan akwai abinda yafi queen din su kinci a baki wanan muka min. Murmushi na sake yi nace nace nako gode da wanan sunan da aka rada min sai dai ina ganin bada ni sunan ya dace ba yanzu ai. Da sauri yace dawa ya dace nace kaida buzuwar matarka mana fara yar dagwas mai gashi har baya sai dai kassh kuma gashin sai naga kamar bai samun gyaran da ya dace dashi balle har kaji dadin shakan shi dakyau. Ke kada fa kiga na kiraki ki nemi tozarta min matata don kin san tafi komai da kike takama don wanan banzan dalilin na Yusuf da yakawo bashi ne zai sa ki samu daman fada min maganan banza ba. Wanan kuma fadi kayi mijin buzuwa don yanzun haka ma nasan tunanen yar asaline ya hana ka shakat sai da ka kirani kaji yaya nake sai dai kana tsoron buzuwar ka nasan ma yanzu haka wani wuri ka samu ka labe kake wanan waya dani. Idiout stupied girl kawai ya fada ya ja tsuki ya kashe wayan yana huci wai may yarinyar nan take takama dashi ne wai zuciyar shi tace kyau ilimi tsabta da fadin gaskiya. Idon shi ya lumshe yana tunane sai kuma ya sake guntun murmshi a yadda yake rigingine a kwace taba kofan da Nafisa keyi yasa shi bude idon yana jin ta har ta soma bugun kofan bai tashi ya bude mata ba sai gyara kwanciyar shi yayi dakyau ya fara adduan barci haka har barcin ya dauke shi yana tunane. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABUZaman da maryam yana min dadi sosai don itama bata da wasa da karatun ta gashi musan mutuncin junar mu kamar mun dade da haduwa da ita. Ita ta tilasta min fara amfani da kayan da Yusuf ya saya min tace may ye amfanin ajesu da nakeyi gara dai a fara gani a jikina zai fi. Ban sake bi takan su Yusuf din ba na mayar da hankalina ga abinda ya kawo ni garin sosai sai dai muna waya da kowanin su har yanzu wanda wayana da Samad duk ya kira fada ne da zolayan junan mu har ai fada a kai ga kashe wayan. Munyi jerabawan karshen zango na farko inda muna gap da gamawa Yusuf ya kirani nake ce mai sati mai zuwa zan tafi minna don ba zan leka kaduna ba wanan hutun saboda hutun ba mai yawa bane . Nan yake ce min suna tafe gurina kafin in wuce gida don suma zasu shiga kaduna don Samad ya dade bai je gida yana kokari yaga ya shawo kan shi su tafi. Nace ka barni dashi in gwada in gani idan zamuyi sa, a da nawa dabaran yace ya gode muka kashe wayan suna zaune tare aiki suke a wani file. Yusuf yayi mamakin jin ya tambaye shi khadija yace tana nan lafiya kasan jerabawa suke yi kwanan nan wayan shi ne yai kara baiyi saurin dubawa sai da ya gama abinda yake ya dago wayan. Kallon Yusuf yayi da mamaki tare da fadin Yusuf yarinyar nan ko mutum ce jifa itace ke kirana yanzu muna maganan ta. Yusuf ya kalle shi yace mutum ce mana kamar kowa kaima kana ranta kamar yadda take a ranka ke nan . Ya dauka ciki daure fuska kafin in magana ya fara fadin lafiyan kirana ina aikina nace lafiyan ya kawo haka ai . Ya sake kiran suna na a zuce da karfi yace matsala na amsa mai da cewa may ye ne haka zaka fasa min kunne da kira haka kamar makaho. Kai na tsani wanan yarinya ya fada a hasale na amsa mai da nima haka wallahi cikin yanayin na bashi amsa. Nace dama abinda yasa na kiraka don in fada ma ya kamata kaje gida ka duba tsofin ka don gudun su da kakeyi ba shine mafita ba gare ka. Yace what da karfi don bai yi tsammanin jin wanan magana haka ba a baki na Duk wani da mai neman albarkan iyayyen shi yana tare da su a kullun suna saka mai albarka da fatan gamawa da duniya lafiya don samun haske a gare shi. Kai kana ganin kudi da girman kai da suke rudin ka zasu iya sama ma farin ciki haka ne a gare su, sunyi ciwo sun yi rashi amma bakai tunanen zuwa ka duba su ba har yau. Who dear you are da zaki fada min abinda zanyi akan iyayyena, nace ni bakowa bace sai mai neman albarka iyayyena don haka kai ma na tunar da kai akan hakan. Kuma kada ka manta da su Affan don sun fi kowa bukatan ka a wanan lokacin don nasan zaka iya zuwa masu hannu sake kai ba abin kunya bane a wurin ka. Don haka oga aje a duba su kada a shagala da yawa wataran sune masu duba mu you are stupid kece zaki tunatar dani komai kike nufi wai ke wacece wai waya baki wanan right din da zaki min wanan magana haka. Nace gani kamar kowa na tsoron fada maka gaskiya don suna ganin kana da kudi niko kudin ka ba damuna sukayi ba wallahi gaskiya komai dacin ta dole ne in fada ma mutum shi. Amma gani nayi buzuwan ka kamar kanta kawai ta sani sai yan uwanta ai don haka nima dan uwa na na sani a yanzu. Kit na kashe wayan ina dariyan keta shima Yusuf dake zaune yana jin yadda mukayi dashi sai murmushi yake yi yana huci yabi wayan da kallo. You see abinda nake fada maka kenan gashi yarinyar nan har ta hango tunda kaji ta fadi haka akwai abinda taji ya faru a gida may be. May yarinyar nan ta dauki kanta ne wai zanyi fa maganin ta a garin nan Yusuf da sauri Yusuf din yace kunfi kusa ai ni dan kallo ne a tsakanin ku sai dai ya kamata ka bincika idan ba wani taji bai da lafiya a gidan ba. Tsaki yaja yana rufe file din da suke aiki akai alaman rashi ya baci sosai ya dafe kai da hannun shi daya tunane ya shiga yi yaya akayi yayi sake rainin da bai taba shiga tsakanin shi da kowa ba har shiga tsakanin mu haka wai abinda nake mai zakace ko mu din cousin ne. Kan shi yana dafe da hannu shi daya Yusuf yace muci gaba mana yace kana iya tafiya yanzu makarasa next yanzu matsala ya shiga . Dariya yayi yana mikewa yace matsalan khadija ke nan ko hararan shi yayi da idanuwan shi da sukai mashi ja shidai ya fice bai yi magana ba. Ya dade zaune a gurin a karshe ya jawo wayan shi yana neman layin mommy don ita kadai ce zai tsaya yayi magana na fahinta da ita ya gane komay ke guda. Kira biyu ta dauki wayan da sallama a bakin ta ya amsa mata tare da fadin mommy kowa na lafiya ko kwana biyu ban kira waya ba. Tace lafiya kalau muke sai dai Alhaji ne jikin nasa ba dadi wallahi wanan matsalar tashi dai ta kwanaki ke damu shi kuma sai kuma Affan da suka kwanta asibiti amma dai yaji sauki sosai yanzu. Wanan yarinyar takai shu,uma wallahi mommu tace wace yarinyar ke nan kuma yace da sauri No magana mukeyi a nan bayan ya gama waya da mommy sai ya kira hajiya mama. Sun gaisa ta fara mai korafin rashin kula da kyautatawan da bai yi take mai fadan ga mahaifin shi nan ba lafiya yan uwan shi na kai da komo akan sa amma ace shi yayi biris dasu badon suraj da yazo ya kai shi asibiti ba may yake son mutane su fada a kan shi. Hakkuri ya fara bata yana fadin in Allah ya yarda jumma,an nan mai zuwa zai shigo ya tabayi jikin Affan sai bata bashi amsa ba. Bayan sun gama waya ya dade zaune a wurin kafin ya mike ya nufi hanyar fita office din ya rasa abinda ke yawan shagaltar dashi yanzu gamay da iyayyen shi haka. Zuciyar shi ne tayi mashi zafi don haka ya nufi gidan shi dan ya dan sarara batare da ya sanar da kowa ba ya fice a ma,aikatar nasu sai gida. Tun a kofa yake jin suruntun yana shiga Nafisa tana zaune a tsakiyan falon tana shan bakin shayi a dan karamin cup tana lumshe idanuwanta. Ganin shi a wanan lokacin tayi mamakin dawowan shi gida yanzu rigar da ya barta dashi na barci ne saye a jikin ta har wanan lokacin ga su hadiye na busa shisha duk falon ya gauraye ta ko ina kamar ba falon da ya narka ma makudan kudi ba haka. Batare da yabi ta kansu ba ya haye sama zuwa part din shi har ya kama hanyan da zai kaishi dakin shi sai kuma ya juys ya shige dakin hutun shi ya rufo kofan. Sai da ta gama shan attayen ta ta mike zuwa wurin mijin nata ba tare da damuwa da irin shigar dake jikin ta ba bata samay shi a dakin ba don haka tasan yana dayan dakin da yakan kebe kan shi wani lokaci. Can ta nufa duk da tasan ba lalle bane ta samu kofan a bude sai dai tayi mamakin da ta tura taji kofan a bude ta sa kai ta shiga yana kwance yayi rub da ciki a saman gado ta iso gare shi tana fadin. Samad yau lafiya ka dawo irin wanan lokacin tana kokarin hawa saman gadon ta zauna a kusa dashi juyowa yayi yana fuskantar ta wani irin karni da bashi kanta da jikin ta ke sakewa da kyat ya daure yace banjin dadi jikina ne tace oho ba sannu ba Allah sauwaka. Samad dama ina son in fada maka satin nan akwai bukin da zamu maradi sai kuma wayan nan kannen nawa maza da suka zo zasu koma gida. Gashi kuma ina son ka canza min mato don wanan naje dashi har sau biyu an sani dashi sai kuma su hadiye da nake son inyi wa sayayya kafin mu tafi dakuma, , , , Ke enough ya ishe ni don Allah duk wanan abin a cikin sati daya kike son inyishi ko kay wai may yasa ke baki da tunane ne wai ? Tsayawa tayi tana kallon shi galala tana mamaki yadda a dan lokaci yake son juya mata baya haka a lokaci guda tace Samad ni kake dakawa tsawa haka. Kallon ta yayi yace an daka maki ke baki da aiki sai na abaki dai a naki ai ma yan uwanki kaza ai masu kaza sam baki damu da na wa yan uwan ba da damuwar su. Tace amma kasan ina da yan uwa da ka aure ni ko yace wa kika fi yan uwa da bukatu ni nawa yan uwan basu son ai masu ne komay. Tace wanan kai ya shafa matsalar kace kuma ni dai nawa yan uwan na sani kuma dole kai masu don dani sula dagora. Mamaki da karfin halinta yaji yadda take fadin magana son ranta kai tsaye ta nuna mashi nata kawai ta sani shi yaji da nashi. Queen matsala kinyi gaskiya yace a ranshi ya ta tunar dani wani abu mai nauyi da na manta a rayuwana shiru yayi taci gaba da masifan ta akan shi bai iya furta komai ba a lokacin. Tashi yayi ya fada bathroom ya rufo kofan da karfi ruwa ya watsa a jikin shi yai wanka tare da yin alwala don yayi sallah la,asar don har lokaci ya dan gwauta da mintoci. Har ya fito tana zaune a wirin inda ya barta ya dauki room fresh ya fesa a dakin don bashin da dakin ya dauka ganin zai ta da sallah ya sa ta fita daga dakin ta barshi. Gyaran kai da jiki mukayi na zuwa gida don haka agajiye muka shigo hostel din mu maryam ta zauna dafa muna abinci ni wanka nashiga don zafi nake ji jikina ina ganin yayi min dauda. Tsab na fito nayi sallah a wirin na jawo ledan ice cream din da maryam ta sayo muna na fara sha a hankali maryam tace wallahi ji jake kamar kada ai hutun nan da za ayi. Da sauri na juyo ina ce mata saboda may maryam kika fadi haka tace ban son rabuwar mu wallahi yanzu ko ja koma gida banda wata abokiyar hira a kusa dani don anty na ba zama takeyi ba tana da yawan tafiye tafiye kullon don ita business woman ce . Nace ko dai ai koya nene kyayi kewan gida mana ni banki ba yanzun haka in bude ido in gani a cikin garin minna ma. Tace kin ji dadin ki wallahi khadija na yarda ba jin dadi bane farin ciki don ko dashi ne da bazan fadi haka ba farin ciki yana ga inda kake da sukunin aiwatar da komai. Kafin in magana wayana yayi kara na dauka kina ina nace maynene yace ki ban amsa kada ki min halin ku na yan African don Allah . Katambayi mutum ya mayar ma da tambaya shi kuma nace ina hostel mana yace ok kawai ya kashe wayan shi dip bin wayan nayi da kallo nace miskilin banza kawai. Maryam ta gama abinci wanda indomei da kwai ta dafa muna wanda yaji danyen attarudu mai yaji a ciki zubawa tayi a plate guda ta dauko muna lemon kwali a cikin fridge din ta wanda muke ajewa yanzu a ciki ida mun samu. Na fara cin abincin ke nan cibi biyu kawai nayi wayana yayi ringing na duba yaya Samad nagani a layin kamar kada in dauka dai na dauka kuma gani a kofan ku ya fada kawai. Kofan mu na maimaita da mamaki nace may kazo yi a nan kuma ban sani ba yace idan zaki fito ki fito sai ya kashe wayan kawai. Tsaki nayi na wurgar da wayan tare da fadin dan wahala kawai maryam dake zaune ta tsura min ido tana kallo na murmushi tayi tace. Uhm wani lucky guy din ne yazo haka ake ja mashi aji kuma abinda wasu ke nema ido rufe a zo gurin su anzo kike wanan masifa haka ? Nace sister kin faye bin kwakwafi wanan fa ba masoyi na bane zuwa kawai yayi ya bata min lokaci na ina zaune kalau. Don Allah ko may ya kawo shi kije ki saurare shi ba dadi mutum yazo wurin don ka ka wullakanta shi haka muje in zaba maki kayan da zaki saka in maki rakiya. Dole na mike muka tafi dakina ita da kanta ta zaba mi wani dogon riga mai ruwan ganye da dan karamin gyale shi sai da na shirya tsab a cikin rigan tabi jikina ta feshe da turararuka masu kamshi muka rufo kofan muka fito tare. Yana zaune a cikin motar shi riga da wandon shadace mai guntun hannu rigar ma iya ciya dinkin yake light green kayan su matukar karban jikin shi da dinkin . Wurin dirkekiyar motar shi da ke fake a kofan can dan nesa kadan damu muka nufa ko ganin maryam ya hana shi fada ban sani ba sai cewan da yayi. Ita ko maryam tunane take a ranta ina tasan fuskan nan nashi ne ya katse mu da cewa kin san ina waje zaki shanyani a wanan wurin naku mai kazantar tsiya haka ? Nayi dan dariya tare da cewa cikin wayance abinda yafa da nace ga kawata maryam tazo gaida kai don ma ita ta matsa min in fito yanzun haka. Anyway maryam ga yayan mu Abdulsamad Abdulrahim nan ku gaisa tace dama nace kamar nasan fuskan nan ai tace ina wuni yayan mu anzo lafiya yaya iyali. Yace lafiya kalau yaya karatu koda yake exam kukeyi yanzu ko yana wani kauda kai yana basarwa . Tace karatu Alhamdullahi mun kusa cin ma karshen shi da yardan Allah ai a huta gajiya dama nace barin zo mu gaisa ne kawai yace to na gode kwarai da alama kin fi kawar taki kirki sosai. Dariya tayi tace a a wallahi ai kirkin khadija na daban ne wallahi tana da kiki matuka shiyasa ma nake jin dadin zama da ita wallahi. Baki ya tabe ta juya ta tafi tana mashi a huta gajiya ta nufi hanyan shiga hostel din namu sai lokacin na sauke ajiyan zuciya bayan tafiyan ta. Katse ni yayi da fadin tsaye zaki min sai kace wanda tazo tadi da buduruwar shi haka bude kofan motar shi yayi na zagaya na shiga sai naji ya rufe motar. Shiru daga ni harshi ba wanda ya iya magana a lokacin sai ma gyara kwanciya yayi a motar bansan lokacin da nace dashi baka da lafiya ne Yaya Samad. Shiru yayi kamar baiji ni ba sai can yace may kika gani a tare da ni nace yau na ganka so weak ne ba miskilancin nan naka yasa na gane bakajin dadi ko baka cikin good mode. Wai ke aljana ce ko may dazun kin fada min magana akan ahalina ya zama gaskiya yanzu kuma waya fada maki banjin dadin jikina ? Nace yanayin ka ya nuna min haka sai ya dago da sauri ya na kallo na nima kallon shi nake yi sai dai ba zan iya jimirin kallon nashi ba a lokacin saboda kwarjin shi da ya cika min fuska a lokaci daya dukar da kaina nayi kasa ina wasa da yan tsun hannu na. Yau ina bakin naki ya shiga nace ko don Yusuf ne dama kike da bakin a gaban shi nace da sauri ko daya wallahi gani nayi yau kana bukatan kulawa don baka cikin hayacin ka sosai. Don jikina ya bani baka da lafiya sai naga ya koma ya kwanta kamar yadda yake da farko ya fadi a kasalance cewa kaina kamar zai rabe biyu nake jin shi khadija. Kasha magani na tambaye shi da sauri yace ban sha ba wani magani kake sha yace panadol extra nakan sha wani lokaci. Wayana na fara dannawa ina neman layin maryam ta dauka nace fito min da panadol extra din nan da goran ruwa don Allah yaya Samad bai jin dadin jikin shi tace to da sauri na kashe wayan. Motar shiru ba a dauki lokaci ba sai ga maryam ta iso da maganin ta kwankwasa glass din motar ya bude mata karba nayi ina mata godiya tace babu komai mana Allah ya bashi lafiya. Maida marfin motar nayi na rufe na fara kokarin bare mashi maganin tare da bude goran ruwan nace mai gashi ka sha. Ya dago kanshi da kyat ya kalleni ya kalli maganin da ruwan da nake mika mai sai naga ya bude min bakin shi alaman in bashi da kaina . Dan rankwafawa nayi ina saka mashi maganin a baki na kawo goran ruwan na bashi ya hadiye da kyat yana wani lumshe idonun shi yana bata fuska. Komawa yayi ya kwanta tare da fadin thanks nace Allah ya baka lafiya amin yace da kyat ni dai komawa nayi na zauna na zuba mai ido. Wasu irin jijiyoyi naga sun fito rada rada saman goshin nashi wanda ban taba kula ko yana dasu bane dama tsoro ne ya kamani kada wani abu yazo ya samay shi fa a nan wurina nawa ya samay ni kuma. Shiru daga ni har shi ba wanda yayi magana a cikin mu har mintina na shudewa a hakan suna batun zama awa daya muna nan a hakan dashi kamar mai barci. Abu daya ne yasa hankalina dan kwantawa ganin yana numfashin shi normal a lokacin yasa nayi shiru tare da zuba mashi ido kawai ina kallon ikon Allah. Wayan shi dake aje a motan ne ke ringing ganin anata kira bai dauka ba yasa na daga kiran don ba suna batare da na saurari mai magana ba nace mai wayan bai da lafiya please. Naji muryan mace tana fadin ke wacece da sauri ya dago ya kwace wayan a hannu na ya katse kiran yace akan may zaki daga min waya waya baki wanan damar da ikon daga min kira a wayana. Zanyi magana yace get out tunda ka samu lafiya yanzu zaka iya ci min mutunci sai dai ka sani ba zan ce ma komai a yanzu ba don yanayin da kake ciki na bukatan natsuwa. Get out i said na bude motar na fita ba tare da na juya na kalle shi ba naji ya tayar da motar ya jata da karfi yabar gurin nashige ciki abina. Dakina na shiga na wurgar da sauran maganin saman katifana na fara kokarin cire kaya a jikina sai ga maryam ta shigo tace ashe kin dawo. Eh ya tafi ya samu lafiya ai nace mata ina daura zanin a jikina na nike kayan na za saman jakkunan kayana dake gefe daya a dakin. Shiko tunda ya kama hanya yake jin wani bacin rai da bakin ciki a ranshi yana fadin wanan aljanan yarinyar sai ta kasheni wata rana. Yarinya yanzu ta sauke min bacin raina yanzu kuma ta kara sakani a wani anya ma mutnce kuwa dai , ? Yana shiga gidan a hargitse ya samay su duk kan su Nafisa ta haukace masu daga ita sai dan buje a jikin ta tana fadin yaushe samad ya fara cin amana na haka ? Yaushe samad ya canza ban sani ba nayi sakaci da yawa har na bari haka ya faru a yau da ban dauki mataki ba. Haka ya shigo ya samay ta tana wanan sambatun a cikin yan uwanta da suke ririke da ita kamar sabuwar mahaukaciya. Nan ya shigo baice da kowa kalaba cikin fushi ya shigo gidan don haka basu ga fuskan wani magana a gareshi ba. Tayo cikin shi da zagi tana fadin macuci mayaudari sai Allah ya isar min a gare ka har zaka dauki waya kabawa wata mace ta fada min wai baka da lafiya a wurin ta. Da karfi ya banbare hannun ta da ta rike mai wuyan rigar jikin shi ya fisge ya shige dakin shi a hasale. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABUMaryam kamar jirana take in gama debe kayan a jikina ina zama tace amma friend zurinfin cikin ki yayi maki yawa wallahi. Ashe wanan guy din da ake nema ruwa a jallo dan uwan ki ne ban sani ba saurin kallon Maryam nayi nace ruwa a jallo ake nemas may yayi. Tace tsadan ganin gare shi mana gashi dai matashi ne amma Allah ya kai shi ga babban matsayi nace wani matsayi ne gare shi wanda kike zuzutawa haka wai ? Kai haba friend zakice baki san koshi waye ba kina tare dashi haka mutumin nan fa na hango tsatsan son ki a kwayar idon shi. Nace baki hango gaskiya ba idon ki bai hango maki gaskiyan alamarin ba kuma koda kin hango ma bai taba zama gaskiyan magana. Mutumin da gidan shi yafi karfin shi a karskashin mulkin ki mace yake wanda baida mutucin duban yan uwan shi tunda na fara magana ta kafe ni da idanuwan ta. Shiru nayi don na farga na fara sakin layi dariya tayi tace min kin dakata kuma mana nace barni da abin haushi don Allah kwantawa nayi rigingine ina tune a raina sai kuma na bushe da dariya ni kadai. Kallo na tayi tana mamakin abinda nakewa dariya haka ni kadai nace yau akwai bura uba a gida Samad tace akan may kuma nace ke dai bari. Buzuwar matarshi ta bugo waya tana tambayan shi na dauki wayan nace mata gashi nan wuri na baida lafiya. Ido ta zaro waje tace kika amsa kiran matar tashi khadija nace kwarai kuwa ina dariya nace zata gane shayi ruwa ne maryam. Ba gani take ta mallake shi ba ba macen da ta isa tazo kusa da shi hatta uwar shi ta raba shi dasu duk yan uwa ganin su take muggaine bata yarda dasu ba. Kirikiri ta hana matar shi zama a dakin ta dole yanzu saida ta koma gida take zaune ba ruwan shi da yaran da ya haifa da cikin shi. Tace khadija kina nufin wanan guy din yana da iyali haka dama idan ka ganshi sai ka dauka ko auren farko baiyi ba a rayuwan shi. Nace wa mai iyali ne da kike ganin shi wurin nan auren gata ya samu ga iyayyen su shine kuma bai iya riko ba saboda buzuwar matar shi. Nace Wasa farin girki yanzu muka fara wasan da ita sai na manna mata karamin hauka a zuciyar ta tunda tace bata son hurdan shi da ko wace mace. Haduwa goma zamuyi dashi sako goma zan tura mata muje zuwa indai nice ko wace mace da dabaranta ake haihuwan ta sai dai na wata yafi na wata kissan. Khadija kin ko san kisan macen buzuwa macen buzuwa fa duk inda take shu,uma ce bata bari miji ya zauna da matar shi lafiya sai ita. Nace maryam kin san ko matan minna ko waye su ba buzuwa ba ko tsakiyan matan maradi za a kaini na shirya mata indai akwai ayar Allah. Zan bi dare in bi rana sai na nuna mata muma matan Nigeria akwai shu,umai cikin mu ai banda matsala tunda na san lagonta ta . Allah ya bamu saa tace nace amin sai na girgiza kai nace bawai da manufar yaso ni har cikin ranshi nake wanan abin ba yi dai nake in nuna mata boka da malam karya ne. Tace yanzu yaya kuka kare dashi nace korata yayi daga motar shi kai tsaye dariya ta kwashe dashi tace ai ba zaki kara ganin shi ba ko. Nace gobe ma yayi nesa ki gan shi nan ai ni abin har mamaki nake ji wallahi tace don dai kince buzuwa ce matar shi amma da sai in ce wani namiji zai samay ki ya bari ki kufce mashi khadija. Kyau Allah ya baki tsayi da gashi ga ilimi addini dana boko kin tara ranan da naji kina karatu wallahi har rudewa nayi na raya a raina da naje gida komawa zanyi makaranta ni ma na samu in sauke. Tun ina karama fa na sauke maryam yanzun haka ban bar karatu ba don ina nan ne bana zuwa amma a gida ban wasa da karatu ko kadan kinga yayata malama ce sosai wallahi. Tace ai naga alama tun haduwa na dake idan kuna waya da ita zata tana makaranta ko gata tana shiri fita makaranta may yafi wanan dadi ga mace. Nace kinga mu zama yakawo kakannin mu zama garin minna amma aslin mu yan wani gari ne da ake kira ka,oje tun ana hade da sokoto da Niger yanzun haka mu bamu san gida ba mu filani ne na asali wallahi. Mahaifiyar mu ce kwarin minna amma saboda zama muka juye muka zama mutanen minna baki sanin mu baki ne idan ba mun fada ma ba. Haba nature din ki yayi kama sosai da na fulani ashe ma ke ruwan su ne nace ada ke nan ina so zuwa garin mu sosai inga yan uwana wallahi. Don ance har yanzu yan uwan mu suna garin don daddy din mu shi yasan gari har yakan je lokacin da bai tara iyali haka ba. Tace ya kamata ku nemi gida su san ku fa nace muna da burin haka nida ya Amina ai sai dai kin san abin sai an shirya ne . Dakin shi ya nufa ya fara cire kayan shi zuciyar shi yana mai soya yana jin kamar ya ganin a gaban shi ya shake ni don haushi da takaicina da yake ji. Nafisa ce tazo dakin har lokacin a hasale take daidai ya fito daga wanka ta yi mai wani mugun kallo tace yau sai ka fada min gurin wace kaje har ta dauki wayan ka ta kirani dashi. Baiyi magana ba sai kokarin saka jallabiyan da yake yi a jikin shi ta karaso tana ce mai wata yar iska yar kasada ke son shiga rayuwan ka Samad ? Ido kawai ya tsura mata yana kallon ta batare da yayi mata magana ba ta sake maimaita tambayan shi samad ka fada min wa cece kaje wurin ta har ta dauki wayan ka ? Ta karaso tana rike mai kwalar dogon rigan da ya a jikin shi yanzu kama hannuwan nata yayi ya murde ya wurgata saman goda ya nufi inda turaren shi suke ya dauko yana fesawa jikin shi. Ta kara juyowa ta nufo shi a hasale tana cewa kunji kun gama iskancin ku shine ka dawo gidana kana min wankan tsarki anan. Da mamaki yake kallon ta ya bude baki da kyar yace Nafisa yau ni kike wa zargin aikata zina da wata kace tace dole in maka samad may ye hadin ka da wata mace , ? Yace dani mazanaci da akan ki zan fara tunda dashi kika gabatar min da soyayyan ki farkon haduwan mu dake. Haushin maganan shi taji sai ko ta haushi da duka da yakusa tana ture shi tsayawa yayi yana kallon ta da mamaki. Jayeta ya kara yi ya hakadata gefe ya fice daga dakin ta biyo shi tana zagi ta uwa ta uba ya shige dayan dakin ya kyale ta. Yana shiga wayan shi na kara ya dauka Yusuf ne yake son fada mashi ya gama tsara masu tafiyan da zasuyi kaduna. Yace sai dai abinda zamu saya wa yaran nake son mu dauko khadija ta zaba muna abinda ya dace dasu tunda mu ba zaben kayan yara muka iya ba. Yusuf ya ambaci sunan shi a kasalance Yusuf din ya amsa mai yace don Allah ka rabani da wanan yarinyar dake batun tarwatsa min gida da rayuwa na. Cikin mamaki Yusuf din yace tayi ma wani abune kuma ban sani ba yace may ne ma batai min ba yanzun haka in ka saurara zaka iya jiyo hargowan Nafisa akan khadija. Da sauri Yusuf din yace dashi kai haba sun hadu ne komai ko ta samu labarin khadija din ne yace basu hadu ba sai dai yau kaddara ya hadasu a wayana. Nan ya koro mai abinda ya faru yau din dariya sosai Yusuf ya kwashe dashi lokaci guda yace kai khadija akwai jan magana da rashin tsoro. Yace ni yau taja min masifa da fushin Nafisa a gidan nan ban son wanan bakin kishin na Nafisa wallahi idan ya tashi bataji bata gani imagine wai har ni Nafisa ke ma zargin zina yau. Intrested ashe yau tasan zaka iya kara aure ko wani lokaci ke nan wow i am impress da jin wanan labarin Allah yasa haka yasa ta fara gyara halin ta. Rikici kake son jawo min Yusuf da ka hada ni wanan aljanan yarinyar mai shegen rigima wai dole sai itace zatai min wanan aikin ne ? Kana son mu canza wata ce ya tambaya shi a cikin gatse yace No da sauri yace ta faye matsala ne wallahi. Yace da matsalan nata za a gyara komai kai dai ka kara hakuri don Allah yace wallahi yarinyar ta fara shiga raina amma kuma ta faye matsala ne ai. Yanzu yaya zan iya shawo kan Nafisa a gidan nan gaba daya ta birkice min yau kan kishin wace ma bata sani ba har da duka na fa takeyi. Duka kuma subbahanallahi kai kuma sai kai tsaye tana dukan ka ko mai yace to may zan mata Yusuf kit Yusuf din ya kashe waya alaman yaji haushin maganan abokin nashi. Dariya ya soma yi bayan ya kashe ma Samad waya yace komai na zuwa yadda nake so da alama samad ya fara son khadija. Wayana ya kira bayan mun gaisa yake tambayana ashe yau mutumin yazo gurin ki shi kadai nace eh dan matsalan yazo min wai bashi da lafiya. Sai bayan na taimaka mai da magani yaji sauki ya soma karanta min haukan shi wai na fita mai a motar shi tunbai balbalani ba. Dariya yayi yace may ya hada ku har haka nace bakin rigima na yasani daukar mai wayan matarshi da take neman shi ganin kamar barci yake wayan nata ruri nikuma sai na dauka. Dariya yayi sosai a lokacin yace aiko nasan yau suna can suna tafka fitina a tsakanin su kin ja mashi aiki yau Nace shi ta sha matsoracin namiji kawai wanan ma ko ga maza yan uwan shi nasan matsoracine wallahi dariya Yusuf yayi sosai. Yace to yanzu na kiraki ne don Allah gobe indan kina free zaki taimaka muna da sayen kayan yaran samad don Friday zamu shiga kaduna insha Allahu. Nace idan dashi ne gaskiya ba zan tafi ba yace saboda may khadija kefa kika kawo wanan idea din zaki ce kuma bazaki tafi ba. Ki daure ki karasa ladan ki don Allah ai ba don shi zakiyi ba yaran fa kika dauki alkawarin taimakawa saboda Allah shiru nayi yace may kikace nace a hankali naji sai dai idan ya wuce gobe ba zan samu fita ba don ina da exam talata kuma zan wuce gida. Yace nagode khadija Allah ya biyaki da alherin sa yadda kike muna Allah ne kadai zai saka miki sai mun hadu goben zamuyi magana Allah ya kai mu nace dashi. Na kwanta cike da tunane a raina wai dama da gaske akwai mazan da suke irin wanan rayuwan a gidajen su don dai ni nasan mahaifin mu zaki ne a gidan shi akan iyalin shi. Wai duk gidajen masu kudi haka yake ne rayuwan su sai mata ke juya su yadda suka ga dama idan ka gansu awaje sai kai masu kallon isa da izza amma a gidajen su sai ka raina su. Yaya matashi kamar Samad zai zauna mace tana juya shi haka yadda take so wai kuma yana sunan miji a gidan shi gashi da ilimi daya dace yayi amfani dashi ako ina ya kama amma mace ta na juya shi son ranta. Kwafa nayi nace wallahi gobe zasu ga tsiya don sayayya zanyi masu kamar na hauka inta gani ta haukace da tushe. Washe gari nace ma maryam ta shirya zamu fita da su yaya Samad zasu zo mu muyi wa iyalin shi sayayya tace tau da murnan ta. Mun shirya tsab don Yusuf ya bugo min waya suna kan hanya zuwa wani dan abu ne ya tsayar dasu yanzu. Sun iso wayan Yusuf ya shigo min gasu a kofan mu nace gamu tafe yace keda wa khadija nace da kawata maryam zata tayani zaben kayan ne sai kun fito yace min. Mun fito daga gidan kwanan namu na dalibai muka hango su can nesa kadan inda suka aje motar su muka karaso wurin . Motar Yusuf ya fito ya bude muna muka shiga ya rufe sai da muka zauna muka fara gaida su wanda nidai kusan Yusuf kawai na gayar maryam ne tace da Samad yaya jikin shi yace cikin daga hannu da sauki. Sai looacin ciwon kan da yazo dashi jiya ya fado mashi a rai don fitinan da suka kwana sunayi da Nafisa yasa ya manta da komai nashi. Kawar ki bata magana ne Yusuf ya kawar dashirun da motar yayi a lokacin maryam ne ta bashi amsa da fadin ai itace dai magana ya zama aiki a gare ta nikan ko aku ya ganeni ya kauce min wurin zuba. Ashe kuna da aiki shi yasa abin yazo maku daidai naji mamakin da kika iya zama da wanan mai zubin yan ruwan dariya ta danyi tana cewa ashe kaima kyaunta na ruda ka haka. Haka take ruda maza a cikin makarantar dama wajen makarantar amma kunsan may wai duk wanan bata ga may mata ba har yanzu ga kyau yana tafiya a banza a gurin maza. Tsuki yaja tare da juyowa ya dan watsa mata harara lokacin da take fadin ni wallahi ina son ganin lucky man din zai iya sace zuciyar wanan yar kwalisan yarinyar. Zaki ko sha zaman jira don maza basu son zuben mace irin wanan da ko ina tabi surar ta na rawa sun fi son mace mai natsuwa da kamala. Yusuf yace har kin sa yau na fahinci wani abu da kika kawo wanan maganan haka nayi real sign ba karamin kyau ki ga khadija ba da har na kasa fahintar abinda yasa abokina yake yawan rudewa idan ya hadu da khadija ashe kyawon tane yake yawan tsorata shi yana mata kallo mai kama da tsoro but still yanzu da yai maganan nan sai na gane kyauta ne yake yawan ruda shi. Da na dan shiga rudanin wanan abin amma yanzu maganan nan da kikayi yasani a hanya watau a takaice aboki na yana rudewa idan yaga khadija sai take mashi zubin yan ruwa idan ya kalle ta. Tayi saurin fadin ya gano sirin da Allah ya boye ne anan ai khadija matar manya ce wallahi duk namijin da yai saa ta kalleshi da manyan idanun nan nata yakan shiga rudu ne ya rasa inda yake ina ga shiya take tsoron fita wallahi. Don Allah malam idan kun gama kaja mota kakai mu inda zamu ko ka mayar damu inda ka dauko mu zaifi ya fada batare da ya juyo gare shi ba Yi hakkuri malam abinda na gani na fada yasin khadija ta hadu ba karya a gurin nan kai mai dani inda ka dauko ni ya fada a dake. Nidai nayi kamar badani suke yi ba kaina yana duke ina danna wayana dake hannu na muna charting da zarah. Yusuf yace karkai fushi dani abokina gaskiya muka fada anan take a deep breath and confess khadija ta fi matan da kake gani haduwa. Bude baki yayi ya zaro ido yana kallon yusuf da mamaki kalaman shi dayaji na bazata yasan Yusuf ne kadai duk duniya yake iya fahintar shi lokaci daya. Yusuf ya sake kallo shi ya dan lagabe kai tare da girgiza mashi kai yace dont give me that look just say yes to your mind she is realy beautiful as you see. Take ya daure fuskan shi tamau tankar bai taba dariya ba yace Yusuf kayi kuskuren furtan hakan a gare ni don kafi kowa sanin banda lokacin yin hakan . Nace kunyi babban kuskure Yusuf da kuke son kamanta da wanan mutum matsoraci ko kuna zaton sakewan da nayi daku kun dauke shi da wani manufane ? Ba so ko wani abu makamancin haka cikin zuciyana don ban taba daukan haka ba a tsakanina dakai sai mutunci da niyar taimakon ka a zuciyata don rayuwan ka na bukatan taimako da agaji ga wanda yasan shi. Tsakanina daku kuma sai dangantarkar irin na zumunci na an fito wuri daya da biye min da kukeyi da kyautatawa . Da ka sani da baka dauki haka ba da zafi don zuciyar ka ta baka ba daidai ba me yasa zakayi zaton soyayye zai yuyu a tsakanin mu don kana kyakyawa mai kudi maiji da ilimi da wayewa ko may ? To ni duk wanan nasaban naka baya burge ni don ni ina fatan samun miji ne wanda yasan kanshi yake iya mulkata ba in mulkeshi ba ko wata tana mulkanshi. Barin fada maka ban taba jin son ka wallahi a raina don halinka bai mun ba bai kuma taba burgeni ba tausayi ne da fatan alheri ka shirya da iyayyen ka takowani hali . Don halinka da dabiar ka yanayin rayuwan da ka shiga da komai naka yana bukatan gyara a yanzu. Ya isa yace da karfi ya fada cikin kuna rai, yayin da maryam tunda na fara magana take rufe min baki waina bar maganan . Idon shi yayi mai jawur hankalin shi yana neman barin jikin shi zuciyar shi yana son tarwatse mai yace ba laifin ki ba ne. Yaja wani irin huci ya furzar a bakin shi yace Yusuf ka juya mu sauke su inda ka dauko su don Allah. Bana son inkara ganin fuskan yarinyar nan na tsane ta wallahi bana son kara haduwa da ita a rayuwa na . Shiko Yusuf a ranshi ya gigice da fadan mu sosai yana rayawa yaushe ne zai samu cin ma manufar shi a kan mu yaushe zasu bar wanan halin may yasa Samad ke biye mata suna haka kamar wasu yara kanana. Ya zama mai dole ya shiri mu tun yanzu tun kan mu rabu a hakan ba wani ci gaba gashi ya fara ganin hasken alamarin tun ba a je ko ina ba. Ya zama dole ya gyara wanan abin tun anan don ba zai yarda abokin nashi yaci gaba da zama haka ba yanzu in ya bari muka watse a hakan abin bayi ba wallahi. Naji Yusuf din yace Khadija ba nufin abokina ke nan ba baki fahince shi bane tun farko kin san tun jiya fa yana da haushin ki a ranshi don haka don Allah bashi hakkuri ya huce dake haka please. Yadan juyo yana kashe min ido sai na gane manufarshi da sauri sai da na hade wani bakin ciki na iya furta to kayi hakkuri don Allah ban fahince ka bane na fada a sanyaye. Da kyau Khadija matar na tuba ko bata laifi komai rintsi ya juya gurin shi yace kayi tsamanin jin hakan daga bakin ta yanzu a yadda tahau din nan. Wani iri yaji yace a ranshi may yasa na kasa fahintar wanan yarinyar ne wai me yasa na fadi wanan maganganun masu zafi gareta yanzu bayan nasan gaskiya Yusuf suka fada. Halinta daban ne da na sauran matan dake bina suna ribibin in so su kai tsaye zata iya fada ma gaskiya batare da tsoron komai ba kuma ya amfane ka. A sanyaye yace Yusuf ban san may yasa take son bata min rai ko da yaushe muka hadu ba zan bata dama taci gaba da min yadda take so ko yaushe. Motar ta tsaya a bakin wani plaza babba ba wanda yayi magana Yusuf ne yace bissimila mun iso mu shiga mu fito tukun. Fita mukayi a motan har lokacin jikina a sanyaye nake jin shi don abinda ya faru a motan Yusuf ne yazo daidai inda nake yace khadija na gode da kika fahince ni ba komai nace dashi cikin yake. Muna shiga shi yana bayan mu yana tako a cikin izza da kamala maryam tazo daidai kunne na tace dan dakata mai ku jera mana. Hara na aika mata nace sai dai ya mutu idan sai na jera dashi din ya dai ci albarkacin Yusuf da kuma na iyayye wallahi. Ban garen kayan yara muka nufa inda maryam ta fara duba kayan ina tayata har lokacin ban sake ba nan muka shiga jidan ma yaran kayan sawa da sauran abubwan yara. Mu koma bangaren takalma da dasu sauran abin bukatan yara harda su tawul da sabule da su kulan zuwa school muka hado dashi a hankali na taka wurin kayan mata na zaba ma anty fati kusan kala goma masu kyau da tsada. Su dai ido kawai suka saka min har lokacin da muka gama Yusuf yace mu zabi abinda muke so ni wani jakka da takalma kawai na dauka maryam kuma ta dauki wani dogon riga da jakka. Munje gun biya muka da ja baya naga ya ciro katin shi na bakin ya basu suka debe kudin su suka miko mai mun shiga motar mun zauna. Yace kina ganin mun sai komai da zasu buta nace insha Allahu har maman su ma da sauri ya juyo yadan kalle ni kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa yusuf yaja motan muka tafi. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABUHutun sati uku kacal muka samu wanan karshen zangon don haka naji dadi sosai da bai kasance dogon hutu bane don zan samu zama a minna tare da iyayyena in yi hutu. Wanda rabo da in samu kasancewa dasu haka a wadace har na manta yanzun haka na fito daga zana jerabawan karshe na wanan zangon da mukayi da yazo min da rikicin haduwa da Abdulsamad da abokin shi Yusuf. Ba ranan zan tafi ba sai washe gari don haka maryam ta tsaya jirana don taso muje gidan yayar ta na nuna mata ban son zuwa can din. Komai na gama shiryawa a dakin sai kayan da zan saka ne da katifa ban samu daga wa sama ba don kwantawa da zanyi na yau kawai da safe in dage shi sama in tafi gida. Bayan mun rabu dasu yusuf ya kirani yana tanbaya na ya muka isa hostel din mu tare da kara yi min godiya . Bayan mun kashe wayan gidan Abdulsamad suka nufa sun kusa shiga gidan ne Abdulsamad din yace dashi idan sun tafi kada a sauke kaya da aka sayo a gidan shi abar kayan acikin mota kawai idan sun isa Yusuf yagane manufan shi na fadin haka. Sai dai bai ma abokin nashi magana ba gamay da abinda ya fahinta na son kada a sauke kayan dayace kada ayi har lokacin gidan ba dadi tsakanin su da Nafisa. Wanka ya fito yana goge ruwa akanshi ta shigo dakin har lokacin tana nan cikin fushinta da shi zuwa tayi tambayan shi kudin da tayi requesting wana zata yi tafiya zuwa gida. Tace Samad kwanaki na ta matsowa har yanzu bakai magana kan abinda na bukaci ka bani ba wanda zan je gida dashi indan zan tafi sai in wuce dashi. Yadda take magana bai sa ya daga kai ya kalle ta ba Samad dakai fa nake magana ya dan wuce ta zuwa bakin gado ya zauna . Ta juyo gareshi tace magana fa nakeyi maka kana ji kuma ta fadi a hasale sai lokacin ya dago yace kada ki kara yi min maganan nan. Don bashi ke gaba na ba gobe kaduna zan tafi in daba iyayye da iyali na wani irin gumzi tayi tayo kan shi tana fadin wallahi baka isa ba. Ba kuma inda zaka kaje na fada ma don baka fada min zancen tafiya ka ba don haka ban shirya ma tafiyan ka yanzu. Murmushi yayi yace kice ma mai shirya min tafiyan don kece zaki sallamay ke nan ko ? May kake nufi da wanan maganan haka ban ci na sani bane idan za kai tafiya yanzu koma ko da da kake fada min ni nake sa ka fada min . Yace shine kuskuren da na aikata a baya yanzun kuma a shirye nake da na gyara komai da ya faru ido ta zuba mai cikin firgici take. Ganin zata damay shi yasa ya fice ya bar mata dakin don da dakin yaso ya gyara kafin ya kwanta don ya kwana biyu ba samu tsayawa ya gyara ba. Don yanzu gyaran dakin kwanan nashi ya dawo kan shi saboda indan yan uwan nata sun mashi gyara sai abubuwan da dama suyi ta bacewa a dakin. Wanan yasa ya daina bari su shiga mai daki suyi mashi gyara sai shi ya ke gyaran dakin nashi da kanshi ya don yafi mai sauki idan bai gyara ba ita bata da lokacin gyaran . Haka kuma zata shigo ta kwanta a cikin dakin ba kunya ba tsoron Allah haka dai ake rayuwan a dunkule ba wani jin dadin irin na aure tsakanin mata da miji. Laptop din shi ya dauko ya na dubawa sai dai tunane ya hana shi yin wani aiki a ciki bakomai yake tunane ba sai irin maganan da nake fada mai, mai kama da shagube yana jin haushi na ashe gaskiya nake fada mashi. Yaushe rabon shi da yaran shi suzo kusa dashi su zauna a matsayin shi na mahaifin su suji dadi babu. Ya tanbatar da ya tafka babban kuskure da Allah zai iya kama shi da laifin da ba zai iya amsawa ba gobe kiyama. Khadija khadija ya furta a hankali kin taimake kin ceci rayuwana ta yadda ban taba zato ba wanan wace irin yarinya ce mai hikimà da basira. Ya dade a wurin zaune har ya kai kwance sai da wayan shi yayi ringing ya daga wani yaron shi na wurin aiki ke gaya mai an samu wasu filaye ns gwaunati a gwagwalada da wasu mutane ke son ci. Yace da yaron nashi ya bari sai next week za a duba case din idan Allah ya kaimu sun gama waya kiran Yusuf ya sake shigo mai inda yake fada mai gashi a kofan gidan shi sin dawo da motaci an gama duba su . Yace gaya nan fito mikewa yayi ya zura santala santalan kafan shi cikin wasu budaddun takalma ya sauko zuwa kasa inda ya samu falon cike da yan uwan Nafisa kamar suna shawara. Ganin yadda ya fito yasa ta dago kai tana kallon shi ya fito ya samu Yusuf din zaune a saman dan wani dakali yana jiran fitowan shi. Ya fito ya fara mai baiyanin komai basuyi aune ba sai ganin Nafisa sukayi a gaban su tana huci ba bata lokaci ta shiga dura ma Yusuf din zagi tana ai banta shi. Bai tanka ta ba sai faman kururuwa take masu a kai tana kiran da munafuki dan bakin ciki ko bai so sai ya gansu da Samad agidan shi. Dama tasan duk wani munafuncin da ga wurin shi yake fitowa daga shi har samad din sai ta dauki mataki a kansu. Amma dai karki manta bakece Allah ba ko don haka babu wani abin da zaki iya muna sai Allah don in da sabo ya saba da wanan halin na Nafisa. Sau da yawa idan sun kwaso rikici da mijin ta a kanshi take saukewa don tana ganin shine mai zuga shi sai taga ta kamo shi da kyau dan lokaci kadan kuma sai abin ya juye mata. Wanda take ganin Yusuf din ne ke mata zagon kasa a hakan sai dai bai nasaran rabata da Yusuf din da yake son yi ko yaushe. Da kyat yan uwanta suka samu takoma ciki bayan sun kare masu kallon banza suka shige da ita cikin gida tana ta haure hauren rashin mutunci. Washe gari tun da safe ya shirya Yusuf yazo zasu tafi kamar yadda ya saba motoci uku zasuyi tafiyan da shi sai dai wanan karon tafiyan ya canza masu sallo. Na farko su kadai ne ba tare da buzuwa ba na biyu kuma tare da a abin arzikin da bai saba tafiya dashi ba zasu dunfari gidan. Ana kara gyara kaya kamar daga sama sai ganin ta sukayi a wurin motacin tana ganin kayan ta shiga tonawa har ta gano abinda ke cikin buhuhunan da akayi siling din su din. Ranan sun ga masifa haka sukaja mota suka tafi ransu bace da halin da Nafisa ta nuna masu din sun isa a cikin lokaci gari bai je gidan ba sai da ya karasa gidan shi ya huta don sun iso kan shi yana mashi ciwo sosai saboda hayaniyar da baiso. Tunda Yusuf ya sauke shi yanufo gidan nasu da abinda suka zo inda sai gani motane keyi anata shiga da kaya a cikin gidan ana jibgeasu a kofan hajiya mama kamar yadda ya umurce shi da yi. Sun kasa boye mamakin su anty amarya ce ta fara tambaya anya wanan abin da Nafisa ko aka zo wanan karon dariya Yusuf yayi yace bada ita bace anty muka dai muka zo. Mommu tace abin kan da mamaki gaskiya Allah yasa babangida ya canza daga wanan karon dariya Yusuf yayi yace insha Allahu mommy kudai taya mu da addua. Ya shiga dakin hajiya mama don ya gai da ita ya samay ta da yan matan ta suna mamakin wanan sayyayan da suka gani haka wai daga gun Abdulsamad ya fito haka ? Ya shiga dakin sai da ya zube kasa ya fara gaida ita sai faman murmushi take yi har lokacin ta kasa boye mamakin ta bayan sun gama gaisawa dakin take tambayan shi wanan sauyin yanan Abdul din data gani. Yace hajiya adai taya mu da addua kusan kece sillar canzawan nan nashi lokacin fada maki komai baiyi ba amma nan gaba insha Allahu zan sanar dake komai so nake komai ya tafi haka yadda muke so dashi . Don yanzu insha Allahu akwai canji sosai wallahi nan dai suka dan taba hira yace Abdulsamad na tafe zamuyi bayananin komai idan ya shigo. Duk da zaman lafiyan da akeyi gidan bai hana a kebe gefe ba ana gulman wanan sabon yanayin da aka hango a gare shi. Sai dai kowa ya matsu yaga abinda ke cikin buhuhunan wanda ba wanda ya iya gane komau ye a cikin su su indan gaiyan aikin nasu ya shigo. Saida suka sauko sallah jumma a ya shiga gidan iyayyen nashi a falon Alhajin su ya fara shiga ya gaida shi da mashi yaya jiki ranan yaga sauyi sosai na sakin fuska a wurin mahaifin nashi wanda ya dade bai gani ba. Bayan sun gama da mahaifin nashi ne ya shiga ciki ya fara gaida ummi sai mommy sai anty amarya ya wuce dakin hajiya mama wanda dama kullun itace karshen shiga da yafito kuma sai ya bar gidan. Sun gaisa da ita acikin sakin fuska ya dubi Affan dake zaune gefenta yana cin abinci ya kira yaron saboda rashin sabon da basuyi ba dashi ya dago ya kalle shi kawai ya gaida shi. Sai baiji dadin yadda yaron yayi mashi ba shiru ya dan biyo dakin take tambayan shi iyali ya amsa da duk sina lafiya hajiya tace dole ita da yan uwanta zamu tambaye ka don sune yanzu iyalin naka. Babangida yanzu kana ganin abinda kakeyi kana aikata daidai a rayuwanka mutum ya watsar da iyalin shi ya rugumi wasu bare can. Shiru yayi ya dukar da kanshi tace kaima kanka fada kada ka mutu a cikin wanan halin kasan Allah na zai barka ba Yusuf ne yace ayi hakkuri hajiya komai zai zo daidai in Allah ya yarda adai tayamu da addua. Nan ya fara mata bayanin kayan da suka zo dashi inda ta fahinci komai yace saura kayan abinci muyi magana ko za a kawo zuwa yamma sai a raba yadda ya kamata. Yayi mamakin yadda yaji mahaifiyar tashi tana kwararo mashi addua yau da saka mashi albarka wanda ya dade baiji ba daga gare ta duk zuwan da yake yi da fada sukan kare ya fita rai a bace. Yau sai gashi sanadin yarinyar da yake gani mai matsala a gare shi yaja mai samun addua irin haka a gurin mahaifan shi bai fita gidan ba sai da yayi masu alheri yakuma mata alkawari zai je zaria yayi masu taaziyan rashin da akayi can. Taji dadin jin hakan sosai na ya fito ya barsu a cikin farin ciki ya koma gidan shi don yana bukatan hutu a lokacin bayan fitar shine hajiya ta kira su mommy tana masu bayani aka shiga bude kayan da ta nuna masu din. Kowa yayi mamakin ganin hakan don basu zaci haka ba yanzu a gare shi sai addua suke mashi da fatan gamawa lafiya kowa aka cire mai nasa cikin farin ciki da jin dadi. Tunda ya koma wake kwance a dakin shi na gidan ba abinda yake tunane sai irin yadda na fada mai magana mai amfani acikin gatse kuma yayi mai tasiri. Yani yace a ranshi lalai ya zama dole in san yadda zan gyara alamarina da yarinyar nan don ita din ba abin yar wa bace . Cikin dan lokacin kadan tayi min sanadin dawo min da farin ciki tsakani na da iyayyen har da yan uwa wanda wanan tunanen bai taba zuwa min ba ko wani ya tsayar dani ya fada min gaskiya yadda take fada min kai tsaye. Tayi namijin kokari wurin ganin ta tsaya ta fada min maganna irin haka kai tsaye bataji shakka ko nauyin fada min yadda kowa ke shayi na ba. Wayan shi aka kira ya daga Faiza ce take mai godiyan abinda aka kawo masu yace babu komai ta kashe kuma Lawisa yar wurin ummi ma ta kirashi tana mashi godiya haka suka dinga kiran shi sai da yagaji ya kashe wayan shi ranan. Wani irin farin ciki yake jin kanshi ciki mara misaltuwa da wanan kiran da yan uwan shi suke mai a lokacin don ba zai ce ga ranan da suka kirashi karshe ba. Ya zama dole gare shi ya san yadda ya gyara mu,amulan shi da duk wani dan uwa nashi da ya watsar da farko. Sai yaji yana sha, awan ya kira layin khadija a lokacin yayi mata godiya haka yasa ya jawo wayan shi ya kira layin ta. Ina fitowa cikin makaranta na samu guri na zauna ina jiran maryam tafito mu wuce cikin gidajen mu don an kara muna kwana daya yanzu. Kiran shine ya shigo min wanda tun bayan rabuwar mu ranan ban kara ji daga gare ba sai yanzun da ya kirani din na tuna dashi. A hasale na dauki wayan ba tare da nayi magana ba don na gane shine jin shiru ya danyi yawa banyan na dauki wayan sai nace A hasale nake fadin lafiya ka kirani ko ka kirane ka fada min ka tsane ni din da kake fada min ko yaushe ?. Murmushi naji yayi kasa kasa sai ya sake kiran suna full yace khadija a zuciye nace ina jinka ai yace ba wanan kiran nayi maki ba yanzu. Nace may ye ka kira malam ni kada ka bata min lokaci haushi ne ya ishe shi a lokacin yana rayawa a ranshi yaya zai yi dani ne wai ? Cikin sanyi murya yace min thanks khadija na gode kwarai da taimakon ki gare ni sai dai don Allah, , , , Dama abinda yasa ka kirani ke nan don ka samu wani sabon yaudara ka zageni kuma dashi na fahince ka don haka banda lokacin ka ni yanzu. Na fadi a cikin tsigar tsokana tare da saurin kashe wayan sai dai a zahiri jikina yayi sanyi da yadda naju yana maganan cikin wani yanayi. Shiko ina kashe wayan yabi wayan da kallo kamar nice wayar ya sauke wani irin ajiyan zuciya yana fadi a fili shi kadai a daki. Wanan yarinyar ni yaya zanyi da ita ne wai ta fahince ni yanzu ya girgiza kai yace kina da matsala khadija yarinya haka bata da kwaciyar hankalin fahinta. Why why khadija baki so na da kwanciyan hankali a tare dani yanzu ne mikewa yayi daga kwancen da yake ya nufi fridge ya dauko goran ruwa mai sanyi a ciki ya kwankwada tare da wurgi da goran ya fito falon shi. Mutane ya samu sunzo gaida shi inda ya bisu da alheri sai yamma lis ya samu suka rage nan ya nufi bathroom din shi don ya dan watsa ma jikin shi ruwa ko zai ji sanyi. Dan ruwan dumi ya hada saboda yanayin garin na kaduna ya shige jacuzzi ya dan dauki lokaci yana tunane kafin ya fito ya sa kaya a jikin shi ranan a maslcin uguwan su yayi sallah magariba tare da jamma, an unguwa da mahaifin shi aciki. Ba abinda yake tunane sai yadda zai samu mu shirya a tsakanin mu gashi dan lokaci kadan yarinyar ta shiga zuciyana ta samu wuri a ciki. Tunanin yadda zai shawo kaina amma ya kasa samun mafita har wanan lokacin shigowan suraj soja wurin shi yasa ya matan halin da yake ciki don sun dauki lokaci dashi suna fira kafin Yusuf ya shigo mai da abincin da mommy ta girka masu. A tare da Suraj da Yusuf din sukaci abincin suna hira a tsakanin su bayan fitan Suraj ne suka samu kebewa da Yusuf wanda tun bayan zuwan su basu samu zama a tare ba. Nan yake kara mai godiyan kokarin da yake mashi inda yake sanar dashi ya kira ni don yai min godiya amma naki fahintar shi Yusuf din yace ya sake kirana zan fahince a hankali. Ba laifi yace dashi sun dan dauki lokaci sukayi sallama akan da safe zai shigo su tafi zaria idan sun dawo yana son kuma ya dan je wurare masu muhinmanci a kaduna daya dade bai tafi ba. Yusuf na fita ya kira waya maryam ta dauka ta miko min bayan ta dana recieve na dauka da sallama na kara a kunne na. Bayan mun gaisa ne yake rokona da in karba wayan abokin shi inji may zai fada min dariya nayi tare da fadin abokin nan naka ne ai sai a solo baida mutunci. Yace kada kice haka Khadija baki fahince shi bane amma abokina mutumin kirki ne wallahi ki bashi dama ku fahinci juna yanzu zai bugo waya godiya yake son yi maki akan taimakon da kikai mashi na bashi shara kuma yabi yaji dadin shawaran ki shine zai maki godiya akai. Munyi sallama dashi ranan maryam tazo dakina wai a nan zata kwana saboda exam din da zatayi washegari yana da zafi ita kuma tana son tayi karatu a daren ranan. Muna tsaka ga karatu wayana yayi kara na daga tare da karawa a kunne na muryan shi naji yana tambayana har yanzu baki barci bane. Karatu mukeyi na bashi amsa yace OK dazun na kiraki in maki godiya kika kashe waya nace ina busy ne a lokacin. Khadija ya kira sunana amsawa nayi ciki ciki yace please ki bani dama in maki godiya akan abinda kikai min shiru nayi na kasa magana. Khadija kina jina nace ina jin ka mana sai naji tayi wani kasalalen murmushi yace in tambaye ke zaki ban amsa tsakani da Allah ? Nace sosai makuwa idan har na sani may zai sa in boye maka tunda ba rike min baki zakayi ba. Ajiyan zuciya naji ya sauke sai can yace may yasa kike son yawan bata min kina son ganin hasalana ni koda ban tashi hasala ba ? Kin tsane ni kin ki jini baki kaunar ki ganin a cikin farin ciki why khadija why kika zabi wanan rayuwan a tsakanin mu. Shiru nayi na kasa magana nauyin shi da kunyanshine suka kamani a lokaci daya na rasa may zance dashi don yadda yake magana bazakace shi din bane mai izza da jiji da kai. Nasan kin san bawai son soyayya ne a tsakanin mu ba amma kuma kika zabi yin haka a gare ni ki fada min may ke sakina tsana na haka da yawa. Dan murmushi nayi tare da fadin yaya Abdulsamad ke nan ni nasan babu dingo soyayya ma a tsakani mu tun farko sanan kuma ni ko in so ka ko da so ka ba abinda zai ragaka dashi duk dayane a wurin ka. Ni dama ba kai na tsana halin ka na tsana da matar ka da bata san mutucin yan uwanka ba har hali ku ya juye iri daya da ita. A yau in rayuka zai sauya kasan mutucin kan ka dana yan uwanka ka farga ka dawo yadda mahaifan ka suke son ganin ka da yan uwanka ka san darajan su da mutuncin su fiye da kowa. Amma ni may zai sa na tsane ka kana a matsayin yayana aiko don mama zan so ka zanyi muamula dakai kamar kowa. Don dama ba kinka nayi bani halin ka dai na tsana bani ba kowa ma zai so ya kulla halaka dakai ta yadda baka zata ba. Murmushin da naji yayi yasani shiru yace khadija idan nace maki ashiri nake da in caza yanzun zaki yarda koma in ce dake din na canza a sanadiya ki. Jin shi kawai nakeyi ta yaya ni zan iya canza mutum kamar Abdulsamad a lokaci daya haka. Muryan shi naji yana fadin kina mamaki abinda na fada ne yanzu yace yes ke khadija kin tunatar dani abinda na manta acikin abinda nake dauka shirmay kukeyi ke da Yusuf a lokacin. Nace ba abinda mukayi da har zai kawo sauyi gare ka haka da wuri sai dai idan dama Allah ya kaddara tamu din abin zai fito ma. Kuma ina mai farin ciki da jin haka idan ya kasance gaskiya ne maganar ka da sai nafi kowa farin cikin haka a duniya. Yace to ki fara farin ciki daga yau don ko kin sa iyayyena sun min abinda suka dade basu min ba a yau don haka khadija ban san ta yaya zan gode maki ba da tunatar dani da ki kayi ga abinda na manta hakki na ne yinsa a baya. Koda da wasa ko gatse kika fada min wanan magana to ki sani your words inspired me har nakai ga samun kalmar albarka a bakin iyayyena yau abinda na dade baji ba a gun su. Yau kin dawo min da farin cikin dana rasa da dadewa a tare dani kalman ki na ranan gare ni sun sa na dawo da natsuwana. Ya kuma fara dawo min da respect da power na ga idon mutane dana rasa a baya wa yanda ya kamata ace komai wuya komai dadi ina tare dasu. Ba zan iya kwantata maki dadin da naji ba yadda na kasance da yan uwana da abokai kai har ma da makwabta na ayau suna murna da zuwa gare su. Don haka yazama dole in gode maki please khadija kada kiki fada min gaskiya a duk lokacin da kika ga na kauce ma hanya. Murmushi nayi nace naji dadi kuma na tayaka murnan dawowa farin cikin ka gare ka don ko yau ranan kace ranan farin cikin ka. Ka kuma gode ma Allah da bai sa ranan ya kasance ranan nadamar ka bace ya fargar dakai da wuri haka. Allah ya kars shirya zukatan mu ni zan kashe karatu nakeyi ka tsayar dani don gobe zamu gama exam jibi gida zamu. Da sauri yace jibi wata rana nace talata inda Allah ya kaimu da safe zan tafi gida don yin hutu a can. Yace No kada ki tafi don Allah ranan ki jira in dawo akwai abinda nake son in shirya akan tafiyan ki nace Allah sarki dama ka hutar da kan ka don ni a shirye nake yanzun haka. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABUBayan gama wayan mu dashi jikina ne yayi sanyi sosai a kan maganganun da yayi sai naji wani iri ba dadi a raina yadda mutum kamar Abdulsamad yake magana da ni haka acikin mutuunci da girmamawa. Karatun da ban sake komawa gare shi ba ke nan cikin sanyin jiki da tunane barkatai barci ya dauke ni a wurin maryam dai batace dani kala ba a ranan. Washegari bayan munyi sallah asuba zaune nake saman sallaya na nakasa motsawa abubuwa da yawa ne suke min yawo azuciya na. Na dauko kura,ani na fara karatu don ka,idane duk safe sai nayi kafin in fita dakina sai dai idan ina cikin lalura a ranan. Wayana yayi kara ban kula in duba mai kirana ba har sai da nakai karshe sanan na mayar da hankali da wayan da ke neman agaji kuma mai kiran bai fasa kira ba. Yusuf ne ke kirana akai akai haka mamaki naji don bai taba kirana da safe irin haka ba ga kuma kiran dana gani yayi yawa. Yasa nace lafiya wanan kiran haka da safe haka na tambayi kaina kiran ne ya kara shigowa again da sauri na dauka don kada ya kara katsewa a lokacin tare da fadin yaya Yusuf lafiya dai. Naji yace ina kika shiga haka waya nata ringing baki daga ba nace ina zaune karatun kur,ani nake a lokacin yace da kyau yar mama da alama dai ke din babban malama ce hakan na dakyau wallahi. Tambaya shi nayi lafiya kira yau da safe haka yace ina fa lafiya yar mama ta ruda min ogana kuma abokina nima umurni aka bani akan lallai in kiraki in fada maki don Allah kada ki tafi yau ko gobe ki bari mu shigo abuja gobe. Katse shi nayi da fadin yaya Yusuf may zan mashi duk abinda nayi kona fada mai da ya faru wanan haka Allah ya kaddara a kan shi. Sai mu godema Allah da yasa yayi saurin ganewa yasa kuma halin ya dore a gare shi haka kada yayi nadaman mazuru don jiya yakirana wai yana min godiya. Ni abinda na fahinta shine rashin mai fada mashi gaskiya a tare dashi yadda ya dace yasa buzuwar matar shi ta samu galaba a kan shi haka sosai. Yanzun kuma na tunar dashi Alhamdullahi tunda ya fahinci gaskiya har yayi niyar gyarawa da kanshi so ni yar barni don Allah ban son matsala ko wani abinda zai jawo ma karatuna matsala. Dariya naji yayi yace duk mun san da hakan amma ki dan daga muna kafa kijira har mu dawo din please maryam ne ta wafce wayan a hannu na tana fadin insha Allahu zata jira ku dawo yace maryam mun gode da hakan. Bayan ta kashe wayan na kalle ta nace akan may zan tsaya jiran su maryam ki tuna fa na gama abinda ya shigo dani abuja satin nan iyayyena kuma sun san da haka mai zaisa na kara kwana. Wanan ba komai bane mai yuyuwa shima so yake ya saka maki da makan mancin abinda kikai mashi idan ya dawo. Maryam bayi don ya saka min saboda Allah nayi haka tace dole ne tunda yana ganin kin cece shi daga halaka abinda wanan shi bai taba lurar dashi ba. Don Allah kiyi hakkuri har su dawo din gobe ne fa kawai ba wasu kwana masu tsawo zaki kara ba hakan shiru nayi ban nata amasa ba sai dai zuciyana cike yake da tunanen dalilin da yasa yake son in tsaya sai sun dawo garin zan tafi. Khadija godiya ya kamata kiyi ga abinda kikayi ya zama alheri gare shi wurin Allah nace nayi maryam kuma na gode ma Allah da haka ya kasance ta sanadina. Amma maye dalilin shi na son ya tsayar dani wai sai ya dawo zan tafi tunda yasan bashi ke da ikona ba, tace dole akwai dalilin dayasa yace ki dan dakance su din yau da gobe ne fa kawai insha Allahu. San nan kuma nasan dai dalili daya ne kawai don kin cancanci hakan a gare shi yanzu amma mu bari din har yazo muji. Kila kuma dai sai kuma ta kama dariya a hasale nace don Allah dai ki bari karki bata min in ce na fasa tsayawan. Shiru tayi do ganin yanayina daya sauya tasan zan iya abinda na fada din ita kuma bazata so ace na wuce ban jirashi ba. Haka kawai naji kaina yana sarawa raina yamin mugin baci haka yasa na mike daga wurin na koma saman katifa na, na kwanta ina ci gaba da tunane a raina. Wayan aminiyar ta takira cikin tashin hankali take mata bayani tana kuka wai samad din ta yana son juya mata baya a lokaci daya . Don ma idon ta naga ala,amarin shi ne yasa tayi saurin ganewa da wuri ta kare da cewa na shiga uku madam tawa ta samay ne wallahi idan Samad ya fara neman mata ni yaya zanyi. Tace haba ki kwantar da hankalin ki tunda akwai mafita zamu iya kaishi wurin mai rafanne yasan yadda ya lankwasa muna shi ko uwar shi indai mace ce ya dinga jin ko ganin ta kamar jaba. Ke dai kada ki nuna mai kin fahince shi lankwasa shi zamu a cikin ruwan sanyi batare da wani hayaniya ba. Wa ni tun yaushe nagama buda mai wuta wai fa satin nan har kaduna ya shiga ba tare da sani ba kinga ke nan abubuwan sun lalace don samad bai taba shawaran zuwa gida batare dani nabashi shawaran ya tafi ba ko shi sai idan ina da abinyi acan. Don haka nayi mai kaca kaca kafin yatafi wai ma kin san may wanan zuwan don ki san komai ya fara lalacewa har sayayya yayi masu da zai tafi abinda ban taba gani ba tun zuwa na gidan nan. Madam tace matsalan ki ke nan Nafisa baki da kwanciyan hankali idan abu yazo maki abishi a sannu sai kinyi hargowan nan naki da kika saba ko yaushe. Don haka yanzu ki kwanta kamar komai bai faru ba yadda muka saba ta haka zamu fito mashi mu kara kaifin aikin mu a kansa don ba zamuyi sanyi muna kallo Samad ya kubuce muna ba don muna samu a wurin shi sosai. Don haka ki kwantar da hankalin ki zan shigo gidan naki sai mu tsara yadda zamu shawo kan ala,amarin tace da ita Madam hankalina baya kwanci don natsani in bude ido inga samad yana mu,amula koda na aiki ko na yan uwantaka da wata mace a duniyan nan musan man matan hausawa yan uwanshi. Kada ki damu madam tace da ita zanzo gobe sai muyi magana a tsanake amma fa sai kin kwantar da hankalin ki . Ajiyan zuciya ta sauke tana fadin zanyi kokari hakan suna gama waya ta sake kiran wata wai hajiya Auta da ke mata shige shige a kaduna. Itama bayani tayi mata na halinda take ciki tace kada ta damu gobe zata je mata zaria wurin malamin da take zuwa tayi mashi bayanin halinda take ciki. Daga nan kuma gida Niger ta kira tayi ma yar ta wace ke mata shige shige acan bayanin halin da take fuskanta daga Abdulsamad din yanzu tace kada ta damu za,a yi komai yadda ya dace. Sai lokacin hankalinta ya kwanta don tana ganin kamar har anyi aikin mako don ta yi believe da aikin bokaya da malamanta sosai. Shawaran da madam ta bata take so ta fara aiwatarwa indan ya dawo daga kadunan inda take sa ran dawowan shi yau din don tasan ba zai wuce kwana daya ba can tunda ba tare suka tafi ba. Nikan nace Abdulsamad da sauran mazan dake cikin irin halin nan sun shiga uku ga matan su ruwan sha surukule abinci ma haka wurin kwanciya ma hakane Allah ya tsare ya kare ya shirya zukantan mu. Baidawo ba ranan kamar yadda tayi tsamani abinda ya kara tayar mata da hankali ke nan ta kwana a cikin tashin hankali da damuwa. Yana gurfane a gaban hajiya mama yana mata sallama zasu tafi inda take zaune akan kujera falon ta . Akwai wani nauyi da kawaici dake tsakanin shi da mahaifiyar tashi tun farko kansancewar shi dan fari a gurin ta ba wani sakewa ko shakuwa mai yawa a tsakanin su tun farko don kawaici. Ya dubeta sanan ya sunkuyar da kanshi tare da fadin hajiya mu zamu koma ke nan ta dan dubeshi ta kawar da kai gefe tace. Allah ya kai lafiya mun gode da hindiman da akaimu Allah ya karams dukiya albarka cikin sauri suke hada baki da Yusuf wurin cewa amin hajiya mungode. Sai dai kuma rufe bakin su yayi daidai da cewan ta yaya zancen iyali ka kuma har yanzu bamuji shawaran da ka yanke a kai ba kai suka dukar kasa gaba dayan su don basu zaci hajiya zata kawo wanan zancen ba a yanzu. Taci gaba da fadin babangida kayiwa yarinyar nan adalci da diyan ka don ko sune ne jigon ka watarana kana ganin wanan abinda ka dauko na tallaban wata wace ko haihuwa bakuyi da ita ba zai haifa maka da mai ido gobe. Yaran nan fa girma suke yi yanzu idan har suka san abinda kake yi ma uwar su kana ganin abin ba zai shafe ruwan ka ba wataran. Yusuf ne ya kawar da shirun dakin bayan hajiya ta gama magana yace hajiya a dan bamu lokaci kadan don Allah akwai shirin da muke yi komai zai zama daidai bada dadewa ba da yardan Allah. Sai dai a taya mu da addua da rokon Allah wanda shi muke bukata gare ku yanzu amma nan gaba kowa zai dara in Allah ya yarda. Allah ya yarda tace dashi bata kara magana ba suka mike suna fadin zasu tafi ta bisu da addua wanda yasa zuciyar shi jin kamar an gafarta mashi a lokacin. Abinda ya dade bai samu ba daga gare ta idan yazo da fada sukan rabu a gidan rayuka sukan baci sosai. Tunda suka kama hanya ba wanda ya iya magana a cikin su kowa da abinda yake tunane aranshi saida sukai nisa Yusuf yace wanan abin yayi min dadi matuka. Yau hajiya ta rakamu da addua tare da fatan alheri a gare mu abinda ta dade batai muna fatan alheri da sakin fuskan da muka samu gareta ba irin yau. Murmushi yayi tare da kwantar da kan shi saman widow motar yana lumshe idon shi cikin jin wani irin yanayi a jikin shi. Har suka iso Abuja kamar bai cikin motar gida ya wuce dashi direct inda ya samu gidan kamar yadda ya barshi Nafisa ce da yan uwanta suke yadda suke so su kadai a gidan babu kowa nashi a ciki. Bayan sun gaisa ne ya haura zuwa sama dakin shi ya fara rage kayan jikin shi don ya dan watsa ruwa ya kwanta ya dauki lokaci a bayin kafin ya fito ya fara saka wasu kaya masu sauki a jikin shi don ya sha iska. Yana saka kayan Nafisa ta shigo dakin bako sallama tana cewa kun dawo ashe yadan juyo ya kalleta ya mayar da hankali ga abinda yake yi din. Ba laifi yau ta sa kaya masu dan kyau a jikin ta da alama kila tafita ne ko zata fita din don idan ba fita zatayi ba ita kwalliya bai damay ta ba haka take zama a gida ga kaya nan kamar ya kashe ta kuma bata kyauta wasan dadi. Cike da sallo ta karaso gare shi ta amshi dan tawul din da yake tsane jiki dashi tana goge mai kai tare da fadin kaje gida hankalin ka ya kwanta ke nan ? Bai mata magana ba haka kuma bai saki fuskan shi ba har lokacin tace nayi mamakin zuwan ka gida a wanan lokacin bayan ba haka muka saba zuwa ba. Yace banda daman zuwa ganin mahaifana sai mun tsara dake ko may ba haka nake nufi ba gani nayi ya kamata ace nasan da zuwan ka tun wuri ai. Sai da ya soma tafiya yace yanzu na canza sallon tafiya ne ba dole bane sai naje dake indan zan tafi don kema idan zaki gida ba binki nakeyi ba ai. Cikin yanayi mamaki tasha gaban shi tace may kake nufi da fadin ka canza tsarin ka yanzu yace komai ma don na fahinci baki kaunar yan uwana yanzu da ci gabana. Na fahinci sakin fuskan da nake maki ne ya jawo min abubuwa da dama daga gare ki na koma nine mata kece miji a yanzu gidan nan. Don zan tafi wurin iyayyena har kike tayar da jijiyoyin wuya wai jayi masu sayayya ke nawa nake baki idan tafiya gida ya kama ki. Kuka ta sa mashi wai yayi mata gori kan abinda yake mata ita da iyayyen ta kallon ta kawai yayi ya fara kakabe gadon shi inda yake son ya kwanta cikin kuna rai. Ta dawo bakin gadon bayan ya gama kakabewa ya kwanta ta zauna a bakin gadon tashi gaba tana kukan munafunci. Sai da kukan ya ishe ne ya juyo gare ta yana fadin kukan ya isheni hakana in zaki gyara ki gyara dan gaba tace haba Samad may kake nufi da maganan da ka fada min. Kana nufin ina hanaka yiwa yan uwanka alheri ke nan yace baki hanawa kikayi bakin ciki ga abinda zan dan kai masu a gaban kowa. Tace kowa su wa baidai Yusuf bane gurin da sauran drivobin ka yace su ba mutane bane komai tace to kayi hakkuri haka ba zai sake faruwa ba insha Allahu. Nasan ban kyauta raina ne ya baci a lokacin bayin kaina bane ka sani son kane ya rufe min zuciya na. Yadan dubeta yace don kina sona sai ki hanani yima iyayyena da iyalina alheri ko may kai min afuwa ba zan sake ba tana fitar da hawaye gwanin ban tausayi. Nace naji ya wuce kuma kada ki sake yi min haka don ranki zai baci dani idan kin sake ina son in kwanta in huta ne haka yasa ta mike ta fita jiki a sabule da ita. Mamaki take a zuciyar ta yau ita Samad ke da bakin fada mata haka da bakin shi babu shayi ko tsoron da yake gwada mata. Tace zaka san koni waye idan na kulleka a wuri daya a karkshin ikona ba yan uwanka ba har iyayyenka da iyalin ka sai abinda nace maka a kan su. Kwantawa yayi don ya huta amma ya kasa samun sukuni a lokacin saboda damuwa dayayi mashi yawa ga tunanen zuwa ya duba khadija ya damay shi ga kuma Nafisa da ta fita tana kuka yanzu a dakin. Mun gama exam na dawo hostel tun jiya da na shigo ba fita ko kofan gida ba ina jin ya gidan nata parkin suna fita daya bayan daya a gidan. Kwaciya na gyara ina jan tsoki haka kawai an tsayar dani don wani bukatan da ban sani ba an bata min lokaci na ga banza. Da yanzu ina gida don tun da yamman jiya naso wucewa tunda ba wanj mugun nisa ke ga Abuja zuwa minna ba ko goma na dare zan iya tafiya gida idan na so. Wayana yayi tsuwa ban yi saurin dagawa ba sai da na lalabo na dauka naga ya Aminace take kirana a lokacin . Dauka nayi ina mata sallama bayan mun gaisa da ita ne take tambaya na kama hanya karya nayi mata nace ban gama ba sai gobe zan gama sai in tafi tace Allah ya kaimu. Na tambaye ta ina su boy yaron ta tace sun shiga wurin mommy ta aike su can. Nace ke dai da mommy sai Allah anty tace suna da kirkine mutanen akwaisu da so jamma,a sosai wallahi. Dan murmushi nayi kawai tace ah ai na manta in fada maki mutumin ki fa yazo gida ya kawo wa iyayyen shi da matar shi alheri da yan uwa kowa yana ta mamakin sauyi da aka gani a gare shi. Nace ah haba dai don Allah tace wallahi baki ga irin alherin da ya kawo masu bane khadija nima da na shiga gidan mommy take nuna min . Nace shidai ya sani ai kila buzuwan matar shi ta barshi ya kawo masu ne tace bai ma zo da ita ba ai shika dai yazo wanan karon. Nace kila shiyasa ya samu kawo masu alheri tace waya sani khadija Allah dai ya kyau ni ba kishiya nake gudu ba irin wa yan nan matan dake juye kan miji a lokaci daya ka rasa gane kan mijinka ne abin tsoro ai. Nace da sauri No no ya Amina don Allah kada ki hada yaya da wanan mutumin don ba halin su daya ba ma tace saboda may shima ba namiji bane irin sa nace na fada maki ba daya suke ba ya Amina. Tace Allah ya sauwaka nace amin tare da kawar da zancen nace idan naje gida may zance ma daddy tace nima ai zanzo kafin ku koma school idan anty hauwa ta haifu. Don ina ganin tun last month ake sa ran haihuwan ta gata ta wuce lokacin ta nace ashe cikin ya tsufa haka ne muna gida zata haihu ke nan tace insha Allahu. Mun gama waya mun kashe na ci gaba da tunanen hiran mu da ya Amina din murmushi nayi nace baki san komai ba yar uwa. Zaki sha mamaki idan kin san nice mai shirya wanan plain din haka murmushi na dan sake nace ashe nima shu,umar kaina ne ban sani ba. Kiran Yusuf ne ya shigo min yana tambayan ina ina nace hostel a takaice yace akwai mutane ne nace akwai su amma kadan yace gashi nan zuwa yanzu sai kazo nace dashi ya kashe wayan. Maryam ta dawo daga wurin gyaran kai ta samay ni akwace take fadin ai na dauka barci kike yi nace na fara ya Amina ta tayar dani ga waya. Nan nake bata labari hiran ya Amina dani tayi dariya tana bude tukuyan abincin mu tace bata san ke ce mai director ba yanzu na zuciyar shi. Da sauri nace zuciyar shi fa kikace tace uhumm wai ke baki sani ba idan baso a tsakanin ku kina nufin zai ko kalle ki ne ma. Shiru nayi ban bata amsa ba sai da ta zauna nace wai ke da tunanen ki ke nan akai mu tace bani ba kowa ma saboda kun dace dashi. Nace baki ji ba ke nan don babu ta ida muka dace dashi wallahi ni ina ni ina wanan miskilin mara dariya da fara,a. Zaiyi dariya wata rana sai kinyi mamaki zakice nace maki watarana amma fa idan kinyi nasaran canza shi din don kan ki ne zaki taimaka ba wani ba. Nace a a gyara maganan ki dai maryam don ba gaskiya zuciyar ki take fada maki ba tayi murmushi ta soma cin abincin ta. Yusuf ya kirani yace fito gani a waje ban bata lokaci ba na mike saboda na matsu inji abinda yasa suka tsayar dani garin har wanan lokaci. Dan simple makeup nayi na fito a can nesa da mu na hango motar su a fake na karasa inda yake da sallama na gareshi. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABUA zoto na shika dai ne a cikin motar sai da na isa kusa ne naga sabanin haka ashe tare suke da dan baiwa yana zaune kamar kullun ya aza Laptop a cinyar shi yana dubawa. A sanyaye nake nace dasu sannu ku da zuwa yaya hanya yaya mutanen gida kun barsu lafiya ? Yusuf yace ke ce African ta gidi khadija tambaya haka a jere lokaci guda wani zamu fara amsa maki daga cikin wanda kika jero muna a lokaci daya ? Nace amsa daya ya wadata gareni wanda nake fatan alheri a cikin shi yace to duka amsan ki alheri ne don duk Alhamdullahi gaba daya kowa na lafiya kuma hanya lafiya. Murmushi nayi sai yace baki gaisa da oga na ba kuma aboki na dan satan kallon shi nayi nace ai bugu daya nayi maku gaba daya nashi gaisuwan daban ne kuma ? Yace oga ne fa khadija kema kin sani ai dole gaisuwan manya ya zama daban da na saura nace a wurin ka yake daban don kace shi din ogan ka ne amma ni a wuri na duk daya kuke gare ni. Eh to kya iya fadin haka yanzu amma dai nasan nan gaba bazaki fadi hakan ba dariya nayi nace saboda may kana ganin zanyi aiki a karkashin shi ne ko may , ? In wanan kake tunane may zai kai lawya aiki a FCDI kuma sai in dai bukatan haka yataso mu a bukace mu a wurin muyi aikin mu mu bar wurin. A a a ashe da babban lauya muke bamu sani ba haka nace cikin murmushi lawyer to be insha Allah ba ya juya gare shi yace kai kaji ashe da Barister muke bamu sani ba shike nan yanzu muyi abin mu ba kwabo muna da mai kare mu. Nace wa ni ai nice ma zan tsaya sai na kama masu cinye ma gwaunati kudin filayen ta in daure mutum inga tsiyan kwashe kudi ana tura ma yan Niger suna cinyewa dama yan Nigeria kuke ba sai in maku sausaci a kai. Sai lokacin ya dan sake murmushi yace ashe har kin fara hada evendece a kaina ban sani ba nace tun yaushe na fara hadawa zan tura babban kotun mu. Dariya sukayi sosai gaba dayan su yace dama karatun da kike yi ke nan ashe nace kwarai don kama manyan bariyin gwaunati ba. Yace ashe aiki ya ganki magana yake ba tare da ya dago kai ya kalle ni ba sai dakilan laptop da yake yi hankali kwance da gani abin ya zama mai jiki hakan. Yusuf yace wai kin san ban taba sanin abinda kike karantawa bs ke nan sai yanzu na dan natsu nace shi nake karantawa ai Allah ya bada saa yace nace amin nagode. Still bai dago kai ba yace wace zata kama ka kakewa addua haka kuma yace ai addua ya zama dole muyi mata shi fadi take yi kawai mutum ya taba kama kanshi da laifi ne. To wai ni fa kun barni a cikin duhu yakamata ace yanzu ina gida kun tsayar dani a nan aikin oga ne haka khadija bai son ki bar garin nan yanzu ne yasa ya tsayar dake. Kallon shi nayi sai faman aikin shi yake yi hankali a kwance bai dago ya kalle mu ba nace ni ai ba yar Niger bane da yake tarawa a gidan shi kamar almajirai. Dama titi yake bi yana ba mabukata alheri da zai fi samun lada ga Allah da wanan ciyar da mayaudaran dayake yi zai fi mai Alheri sosai. Rufe Laptop yayi tare da fadin wai ke maye matsalan ki da yan Niger ne cikin rashin sani nayi subul da baka nace kishi mana lokaci daya suka ce kishi nace wallahi. Murmushi naga yayi yana lumshe ido Yusuf ko sai kallo na yake yana dariya shi ya bude idon shi yace kishi yana jijiga kai nace na kasata ba . Sun zo suna kwashe muna dukiya suna raya kasan su da sunan aure nan ko barayi ne na zaune Yusuf yace a a kada ki gyara zancen kuma mana khadija yar mama. Nace a in ba kishin kasata ba kishin may zanyi kuma Yusuf yace gashi a gaban ki kishin dai kike yi amma kada ki gyara kice kuma wai kasan ki. Ikon Allah akan may zanyi kishin shi shi mijina ne ko wani nawa ba hadin kifi da kaska ai Yusuf yace waye kifin waye kasa yanzu. Yace itace kaskan mana nine kifin ba ita ta lake min ba kana gani kuwa ido na waro waje nace ni din yace Yes kamar zanyi magana sai kuma na kalle su tare da fadin sai anjiman ku. Ina juyawa da sauri Yusuf yake kirana ban tsaya ba ya fito daga motan ya sha gabana shiko yana ciki sai murmushi yake ba abinda ke mai yawo a rai sai kallaman kishin da nace. Ya samu na tsaya yace ke ko daga wasa zaki mai da abin wani magana nace ina nuna shi bakiji may ya fada min bane yanzu wai ina like mai. Yace ai wasa ne ko shima yasan baki like mai shiyasa ya juye maganan yace ke ce mai like mai yanzun bamu muka zo wuri ki ba wake nan kaskan a cikin mu ? Bude motar yayi ya fito yana mika tare da nufo inda muke tsaye yana fadin wai may kaskan nan take fadi ne haka ka tsaya wani bata magana can. Yusuf yace kin gani ba har ya kai ga fitowa a mota don ki yace ai ita ma ta fito don ni ko, kallon shi nayi na kauda kai na gefe daya. Ya karasa takowa zuwa inda nake yace wai yaushe ne zaki tafi in samu in huta da wanan matsalar taki. Nace nice yar matsalar yace gashi ko kina muns ko yanzu kai na girgiza kawai nace ba komai baka da laifi fito war maryam ya tsayar damu daga maganan . Ta fito tana gaishe tare da masu yaya hanya da mutanen gida yusuf yace suna gaida ku tace kuna nan da miss barister ne yace wallahi kuwa kauna a kwai rigima ai. Tace da kyat na shawo kan ta ta tsaya da yanzu tana gida baku samay ta ba Yusuf yace kin kyauta shi dai tunda ta fito bai mata magana ba ko gaisuwan da tayi bai karba ta ba sai ma daure fuska da ya kara yi yanzu. Yaushe ne zata wuce Yusuf ya tambayi maryam tace bataki ko yanzu wanan ta bar gari ba ta isa da dare da sauri shi yayi magana da fadin No bako a cikin daren nan ba kan gaskiya. Nace may ye a hanya da zaka ce ba da daren nan ba zan isa ko lafiya yace No sai gobe za a zo a kai ki har gida. Nace a a kada ku wahal da kan ku motar kasuwa nake shiga yanzun ma shi zan bi in Allah ya yarda bani kadai ba kowa dake wurin yayi mamakin maganan shi da yace. Ba zan yardan ba ki bi motar haya ke kadai idan wani abu yaje ya samay ki fa a hanya ki sani a wani hali don haka ki shirya gobe zan turo malam sani ya kaiki gida da safe. Ido gaba dayan mu muka tsura mashi da yake maganan kamar wani uba da yar shi ko miji da matar shi yadda ya hakikance yana fada a hasale dani. Zan yi magana Yusuf yace ya gama yanke hukunci akai Allah ya kai mu gobe din ai yau da gobe duk na Allah ne ko amma ki bi motar haya wani abu yaje ya samar mashi ke a hanya kuma ? Maryam ne tayi dariya nikan hararan shi nayi mai dani gida yace a dake Yusuf yace to bissimillah muje in sauke ka ko ya juya ya fara tafiya ba tare da yayi magana ba kuma. Sai Yusuf ne ya tsaya yana ce muna yar mama ni zan tafi ban sani ba ko zamu sake haduwa ga wanan ayi ma kanne tsara ba dashi ya mika ma maryam sai kuma ya sake ciro wasu yana miko min wai na karba. Kai na girgiza mai nace daka barshi don ni ina da kudin mota a hannu na tsaraba kuma ai kowa yasan makaran ta naje basu expecting din tsaraba a wuri na. Yace daga wanan time din sai ki fara masu tsaraba baki san tsaraba ko ga babba yana da muhinmanci ba ne mutuka kauna na. Dole ya mika min na karba tare da mashi godiya har dan Baiwa ya fara mashi horn a mota yace Allah sada mu da alherin sa nace amin yaya Yusuf ya juya ya tafi sai da suka shige muka koma ciki. Maryam bata shigo daki ba don haka ni kadai na shiga na adana kudin tare da cire rigar da nasaka a jikina. Can ta shigo ta hada muna abinda zamu ci ina kwance a wurin tunane ya addabe ni a raina har ta gama tace inzo muci don na idar da sallah a lokaci. Sai da muka zauna cin abincin ne muka fara hira da ita take tuna min maganan shi da yayi dazun tare da fadin guy din ya hadu wallahi Daure fuska nayi nace a naki ganin kike ganin haka amma ni mai zaisa in sawa raina abinda nasan ba mai yuyuwa bane gare ni ai ko a mafalki wallahi. Ko dai baki san ko shi waye bane yasa kike wanan magana haka shima dai Yusuf ai yanayi ne don wasa kawai amma ba gaskiya bane so kima daina wanan zancen don Allah. Wayana dake gefe ne yayi kara ban gani don wayan a silent take lokacin sai maryam ne ta gani take ce kamar kiran ki ake a waya fa sai nayi saurin juya don in duba. Tashi nayi na dauko wayan mai kiranane yaban mamaki tunda basu dade da barin wuri na ba, daukan wayan nayi na kara a kunne na da sallama yace fito gani waje. Da mamaki nabi wayan da kallo muryan shi naji yana fadin kin ji abinda nace nace eh maryam na kalla da ta tsareni da idanuwan ta nace a sanyaya wai shine a waje . Ta kwashe da wanin irin dariya bance da ita kala ba komai ba na zura rigana na fita zuwa jin may ya kawo shi kuma. Ina fita na hango motan shi dan nisa kadan damu na karasa wurin na samu ya fito da kafa daya a waje yana duba abu a cikin motar na iso wurin. Ina wuni ya dan juyo ya kalle ni yace zagaya ki shiga dan jin nayi bai zagaya ba kamar yadda ya umurce ni dayi ya sake dagowa bayan ya rufe cabinet din motar yana fadin baki ba ne dole na zagaya kamar yadda ya umurce ni din dayi. Bayan na shiga naga ya tayar da motar ya bar gurin down hostel din ya halba motan muka hau expresse ba wanda yayi magana a motan sai dai gaba na yana dan fadi don ban san ina muka nufa dashi ba. Mun dan yi nisa da gurin ya juyo ya kalle ni yana fadin maman ki ita kadai ne a gurin mahaifin ki ? Mamakin tambayan nashi nayi sai ban iya bashi amsa ba na kawar da kaina gefe yace ina magana kin kyale ni nace akan may zakai mun wanan tambayan haka. Yace don na isa na tambaya yasa na tambaye ki OK idan kana son sani sai kaje ka gani da idon ka ai. Kan nen ki nawane dariya tambayan ya bani sosai nace yau ni naga ikon Allah to kannen na biyar ne na bashi amsa tare da kawar da kaina. Ok kawai yace mukaci gaba da tafiya sai wani katon Plaza muka tsaya ya juyo yana fadin bissimillah fito mu shiga yace. Ban ki ba na fito muka shiga shagon sai faman gaida shi masu shagon keyi layin kayan sawa muka nufa yana gaba ina bayan shi. Abin ya ban mamaki yadda naga yana jidan kaya a wurin ya ban mamaki ya koma layin kayan yara sai lokacin ya juyo ya tambaye ni shekarun su nawa ne kallon shi nayi nace a kwai sha uku da sha daya sai takwas da shidda mutum biyu. Maza da mata ne ya kara tambaya nace maza uku mata biyu sai yaran yaya na biyu yan she kara takwas da shidda maza. Bayan mun gama wurin takalma muka nufa muka zaba sai layin zanuwa nan ya zaba da dama ya zaba sai ya duba kudi ya gani yake daukan mafi tsada a wurin. Ya sa yaron shagon ya tura yakai yace a samu trolley masu kyau a saka mai kayan a ciki muka bar shagon hanyar down hostel muka nufa sai lokacin hankalina ya kwanta. Bayan ya tsaya da motar nayi kokarin budewa naji ta a rufe gam na juyo na dan kalle shi naga shima ni yake kallo a lokacin sai na kawar da kaina gefe daga kallon shi. Ina son in maki godiya amma kin kasa tsaya ki bani daman yin hakan gare ki nace godiya akan may fa ? Au baki ma san abinda kikayi ba ke nan nace ban sani ba sai ka fada min iska ya dan furzu daga bakin shi yace OK you can go zamuyi waya idan kin isa ki gaida gida na gode kawai nace na fita. Banji yace dauki kayan ko wani abu ba nikan na shige abina ina fadin dan rainin wayo kawai dama sayayya zan rakashi shine yake min tambayan bazan a hanya. Har yasa gaba na faduwa ina zan kai wanan uban kayan danaga ya jida a shagon sai yanzu hankalina ya kwanta. Koda takwas na safe yayi mun gama shirya komai muna zaman jiran su sai na tafi maryam tace zata wuce itama takwas da wani abu ya bugo min yana fafin in fito da kayana ga mota a waje ana jirana. Fitowa nayi da kayan maryam ce mai karasa min su a wurin motar har aka gama na rufo kofana na saka key din a jakka ta mukai sallama tace za a zo yanzu a dauke ta ta buga waya gida itama. Driver ya bude min baya na shiga muka dauki hanyan minna shigan wuri zan ma minna wanan karon ba yadda na saba ba da dare nake shiga garin. Tunda muka kama hanya barci ya dauke don sanyin motar da lafiyar ta sai faman gudu driver ke shararawa dani ina barci na hankali kwance. Barci nayi sosai driver naji ya tsaya a wani gari na bude ido fita naga yayi zuwa gun masu sai da manja da doya a hanya ya saya aka loda mashi a motar muka kama hanya kuma. Tun ina duban waya sai na koma barci abina muryan driver ne ya tayar dani yana fadin hajiya wani unguwa zamu je na bude ido ina kallo har mun isa deport din mai zamu shiga cancaga . Nace a cikin gari kwagila road, zaka kaini yace ban san wurin ba don ni bakon garin ne nace OK mushiga sai in nuna maka. Miko min envelop yayi yace oga yace idan mun iso in baki wanan sako wai sai kin shiga gida ki bude nace OK Mun wuto ina mashi kwatance har kofan gidan mu motar ya tsaya duk da rana ne kowa na zirga zirgan gaban shi nai hana masu zama layin namu zama suna ganin motar ya tsaya kofan mu suka sako ido caa suga waye a motar yazo gidan mu. Driver ya fito ya bude min motar na fito can naji wani classmates dina na primary yana fadin yau Khadija ce a garin namu. Murmushi nayi mai nace Faisal mun samay ku lafiya ya karaso muna gaisawa dashi na shiga yace bari ya taimaka min da saka kaya a gida. Da sallama na shiga inda kanne na dake daki suka fito da gudu taro na suna ihu na rungumay su tsayawa nayi ina kallon kayan da su Fesal ke shigowa dashi gidan namu. Na kasa furta komai mama ma kallon kayan take da mamaki yaran suka fita sai gasu suna shigowa da ba adadi nace wai duk mu muka zo da wanan kayan haka wai ? Mama tace waya zo dashi in ba ke ba bagashi kin ga ana shigo dasu ba tare da kayan ki ko kina nufin baki san da su bane wai ? Wallahi mama ban sani ba sai yanzu nima nake ganin su anan kamar kowa yadda ya gansu mama ta katse nu da cewa motar wa kika shigo ne naji yara na fadin kin zo a mota mai kyau. Shiru nayi na dukar da kaina ba tare da magana ba har suka gama shigo da kayan mama tace ku dauki ruwa kusa a plate kukai ma mai motar kafin ya tafi. Yaran suka ruga da gudu suka dauki ruwan leda suka sa a plate suka fita dashi waje kamar yadda mama tace dasu ta wuce tabar ni tsaye a gurin. Dakina na nufa tare da dan hand bag dina dake rike a hannu na rai na babu dadi ko kadan a tare dani ina fadin yaya wanan mutumin zai min haka ya hadani fada da iyayyena su fara zargina. Anty khadija wai yace a fada maki zai wuce nace ya kice Allah ya kaishi lafiya nace a hasale yaron ya fita da gudu daga dakin zuwa fada mashi. Daddy ya shigo gida yana fadin ance baby na ta dawo sai kuma yaja ya tsaya yana kallon kayan da mamaki dake zube a tsakar gida. Mama tace kai nake jira dama kazo ka gani ko zata fada ma inda kaya ya fito haka don wai ita ma bata sani ba tace kuma su sukazo da kayan. A sanyayye na dago labule dakin na fito ina fadin daddy sannu da dawo wa mun samay ku lafiya ? Lafiya baby na sai dai wanan kayan kuma fa ina suka fito haka nace wallahi daddy ban san da su ba sai da muka iso na gansu. Kamar yaya bakin san dasu ba bake kika zo dasu ba sai nayi kasa da kaina ban yi magana ba kuma kayan yake bi da kallo tiryan tiryan yace ikon Allah. Shiga ciki ki huta zamuyi magana anji yanzu zan tafi inyi sallah ne ya wuce gurin da buta yake yana dauka ni kuma na sake labule na koma ciki jiki a sanyayye. Na fada saman gadon dakin duk da kuran da yake ciki don ba gyara ake ba a kai akai tunda ba kowa a cikin sa ina zaune kamal kanina ya dawo shiya fara shigo min da kaya yana min sannu da zuwa. A dadafe na amsa mai ina kallon akwatinan daya shigo min dasu akwatunan da muka sayo a daren jiya ne dashi inba idona ke min gizo ba. Watau kayan de na yan gidan mu ne kenan ba wasu ya saya wa ba mikewa nayi don in yo alwala ina shiga banda ki sai na samu ai period dina yazo min ba daman inyi sallah ke nan haka na fito jiki a sabule na aje butan. Sai mama ta aiko da abinci a kawo min ban kali abincin ba nace kaunata ta aje min a nan kawai ina jiran dawowan daddy daga wurin sallah. Envelop din da driver yaban na tuna dashi na dauko a cikin jakata na bude a hankali kudine a ciki sabbi ful din su anyi rubutu kamar haka a wrafer farko daddy sai na biyun mama. Na ukun ne bai rubuta komai ba na shiga uku nace tare da yin nadama da haduwa da shi karo na farko a rayuwana don ban san yadda daddy da mama zasu fahince ni ba. Nayi dana sanin tsaya jiran shi da yace inyi har na tsaya din sam ban kawo komai a raina ba irin haka don ban taba zaton hakan ba dayayi min. Muryan daddy daya shigo naji ana gaida shi yasa ni kaduwa bai min magana ba har yaci abincin shi ya fita haka na tashi na gyara dakin tsab na fita da na wankewa na wanke a ranan. Na dawo na sa kamshi a dakin tare da gyara komai a yadda nake bukatan shi a dakin na koma na zauna wayan maryam ne ya shigo tana tambayana yaya muka isa ? Nace wai kin san abinda mutumin nan yayi mun kuwa maryam nan dai na koro mata labarin abinda ya faru bayan isowar mu gida da driver. Tace ikon Allah sakayyan da yai maki ke nan ashe kai lallai mutumin nan yaci sunan sa dan Baiwa ne shi din. Nace ke maryam har kin samu bakin yabashi ko may may kike son in fada ma iyayyena yanzu don Allah wa zance yake gare ni da yai min wanan kyauta haka. Tace ki fada masu gaskiya taimakon shi kikayi ya saka maki da alheri haka nace ban sin su san ko shi waye tundai Ya Amina . Dariya tayi tace komai dadewa ai zata sani ne nace amma fa ba yanzu ba koda zata sani din don ban son ta fasara ni da wata manufa. Har dai dare banji daddy yayi min magana ba haka yasa na dan sake jiki naji shigowan daddy gidan sai na sha jini jikina a daki ban fito yadda na saba muyi hira ba dashi. Ina nan kwance wayana yayi kara na dauka kamar yadda na rubuta a sunan shi dan Baiwa shi ya baiyana a wayan. Kamar ba zan dauka ba dai na daga maimakon inyi magana sai na kama kuka nace may yasa zakai min haka don Allah ? May kake son in fada ma iyayyena yanzu a kan kayan nan yace daddy na gida nace yana nan yace dama shina ke son magana dashi na kira ki yanzu. Da sauri nace may zaka fada ma daddy din yace gaisawa nake son muyi dasu in masu bayanin kayan ba shike nan ba. Yasir na kira nace ya kaiwa daddy waya ana magana dashi ban san yadda sukayi ba a wayan har mama naji suna gaisawa da ita. Washegari da safe ban tashi da wuri ba don fashin sallah da nakeyi sai da naji motsin daddy ya dawo na fito don in gaida su har lokacin a cikin damuwa nake. Daddy yana zaune a cikin dan karamin falon mu ga abin karyawa a gaban shi mama tana gefen shi ta motsa mashi kunun da ta aje mai a gaban shi sai kamshi kosai ke tashi a falon. Daga kofa na tsuguna ina gaida su daddy yace a a baby na shigo mana daga ciki na tashi na karasa shigowa cikin falo har lokacin na kasa sakin jiki dasu kamar kullun. Daddy yace ya karatu nace daddy Alhamdullah yace babu matsalan komai ko nace daddy ba matsalan komai na fada tare da sunkuyar da kaina kasa. Ina kokarin mai da hawayen da ya ke shirin silalowa a idona nace daddy sai dai wanan mutumin da ya hado ni da kayan nan wallahi ban san ya sakasu a mota ba sai da muka zo nan taimakon shi nayi shine ya saka min da haka. Ido duk kan su suka tsura min da nake masu bayanin daddy yana kallona yana yaba hankalina don yasan ba zan boye masu komai dake faruwa ba. Saboda karya ba halina bane kai tsaye nake fadin gaskiya ga mutum yace dakata khadija kin mashi alheri kin shirya shi da iyayyen shi. Shi kuma yaji dadin hakan ya saka maki da alheri ko kamar yadda yace na gyada kai nace hakane daddy. Mama tace ina kika hadu dashi haka khadija nace mama a wurin da aka tura mu aiki ne na hadu dashi ya samu matsala da iyayyen shi da yan uwanshi. Shine na basu shawara ya nemi shiri da yan uwanshi da mahaifar shi ta hanyar aikata masu alheri daya jaraba hakan sai suka shirya dashi. Shine yazo yace zai saka min da alheri akan abinda nayi mashi tace khadija shine ya kashe maki wanan uban kudin daga taimako kawai irin haka ? Nace mama wallahi ni ban san haka zai min ba daga ta Hussai yace ma mama kin san ni ya kamata in dauki zafi akan maganan nan fiye da kowa. Amma sanin halin ya ta danayi yasa na yarda da bayanin mutumin nan tunda ya rantse min da bata roke shi ba kuma ba da wani manufa yayi mata haka ba. Yai min bayanin da hankalina ya sa na yarda dashi da ita sai dai yanzu ba yadda muka iya tunda kayan nan sun riga sun shigo gidan nan. Kiga ba komawa zasu yi ba tunda dai ba rokon shi tayi ba sai dai khadija a gaskiya nayi mamaki da wanan abin don ba karamin kudi ya kashe ba ga kayan abincin nan. Da sauri nace daddy ba kayan abinci bane kawai har da na sakawa da kudi sune a cikin wanan akwatin da ga gani jiya. Ido maman mu ta fitar waje tace khadija anya ba dan yankan kai bane kika hadu dashi kada fa watarana ya gama zolayar ki da abinduniya mu nemiki mu rasa. Dariya maganan ta yaso bani sai na dake nace mama ba dan yankar kai bane don nasan kowa nasa na kuma san matar shi. Share kawai duk wanan tunanen nayi shi a daren jiya har nafila sai da nayi akai banga wani abin cuta ba daga gare shi sai tarin alheri da na hango ga wanan alamarin. Shiyasa kika ga ban wani damu ba da hakan sai da ita din ta kula da kanta da mutuncin ta da irin tarbiyar da mukai mata zan sake yin yau na gani don ni kaina abin ya daure min kai sosai. Mikewa nayi na dauko kudin da kayan na turo zuwa dakin nan na fara fitarwa ina masu bayani yadda kayan suke nima mamakin yawan kayan nake yi a cikin macewa jiki. Daddy yace aje kayan zamuyi sai na nemi yar uwarki a waya naji shawaranta akai da yadda za ayi da kayan. Zan dage da rokon Allah don ina jiba jikina kamar akwai alheri ga haduwan khadija da wanan mutumin sai dai mu bar ma Allah sanin shi. Koda yakira ya Amina yayi mata bayanin abinda na dawo dashi wanan karon tare da fadin ta sake binkice na tsakani na da wanan mutumin don a gono gaskiyar maganan. Ta kira ni lokacin ina kwance mara na yana damu na da ciwo na dauki wayan ina gaida ita bata tsaya amsawa ba sai cewa tayi Deeda make faruwa ne daddy ya kirani yana fada min wani magana da safen nan. Shiru nayi sai da ta kara maimaita maganan ta nace cikin kuka wallahi ya Amina ba halina da kuka sani da na canza yanzu. Nima ban san da kayan nan ba sai da muka shigo garin nan na gani nan dai na koro mata bayanin komai don ba zan iya boye mata ba ita. Tace khadija kina nufin dama Abdulsamad ne ya yi maki wanan alherin ban sani ba khadija baki jin tsoron buzuwa ta san wanan labarin ta yi maki illar nace ya Amina yaya zanyi ni ban roke shi ba shiya bani. Tace dama khadija kece kika saka yayi wanan alherin da yayiwa iyayyen shi ashe dama duk kece sanadi ni ba komai nake ji wa ba sai buzuwan matar nan tashi wallahi. Takira daddy tayi mai bayanin komai yace shi zancen buzuwan matar shi bai damay su ba tunda ta sheda ba mugu bane. Nema ne idan naga zan iya sai in yi dashi wanan ba komai bane Allah yasan abinda ya hada a tsakanin mu ya kawo hakan sai dai mu saka ido a kan yar mu don har yanzu khadija yarinyar ce karama. Ya Amina tace gaskiya ne daddy zan shigo kafin ta koma dayardan Allah anan suka rufe maganan tare da taya ni addua ga wanan lamari tunda daddy yace abarwa Allah sanin shi a tsakanin mu. Maryam ta kirani nake mata bayanin abinda ya faru dani maimakon ta tayani jimamay sai naji tana min dariyan shakiyancin da ta saba min tace shike nan ya nuna maki wayon manya ya gabatar da kan shi ke nan gare su. Nace wai ke maryam don Allah may yasa kike irin haka ne sai a na maganan gaskiya sai ki dauko wani zance daban tace shike nan yanzu mubar zancen a haka dai. Nace zai fi sauki muka dauko maganan karatu bayan mun gama wayan ne barci ya dauke ni a wurin wanda nasan barcin da ban samu bane a daren jiya. Nan dai na kwashi barci na sosai a ranan sai wani lokaci na tashi don mama taki sake min fuska yasa ban son fita a tsakar gidan sam. Wayana yayi kara na dauka Dan Baiwa nagani a rubuce wani haushin shine ya kamani a raina nayi banza da wayan nashi bandaga ba har kiran ya katse. Ya sake kirana da kyat na iya daga wayan don har yanzu ina fama da ciwon mara dake cina jin murya na da yayi yasa shi saurin fadin. May ya samay ki baki da lafiya ne may ke damun ki ne khadija haka yadda naga ya rude ne nace banda lafiya ne . Tun yaushe nace tunda safe daddy na gida naji ya tambaya nace yana waje turo min da layin shi may zakayi da layin shi nace dashi. Ban number shi nace maki ya fada a dake nace ban san number shi OK zan kira a bani number yar ki in karba a gurin ta yace da sauri nace a a din Allah ni dai kada ka kirata naji sauki. Dole na bashi layin daddy din don naga yana niyar kashe wayan bayan na bashine ya kashe wayan bai fi minti goma ba sai ga daddy ya shigo gidan yana fadin ina khadijan take ne wai ashe bata da lafiya bamu sani ba. Sai da wanan yaron ya kirani yanzu yake fada min khadija bata da lafiya a kaita asibiti wai zai turo da kudi kamar shine ya haife ta. Mama tace ni tunda jiya da ta dawo na ganta kwance ban san may ke damun ta ba, har dakina daddy ya shigo ya samay ni kwance sai dai ba barci nake yi ba. Zama yayi saman tsohowar kujeran dake falon yana fuskanta na yaga yar raman da nayi yace baby na may ke damun ki ne yanzu wanan mutumin ya kirani wai baki da lafiya. Sai dai ban san ida ma yasamo lambata ba ya kira nace niyace in bashi na tura mai yanzu amma ban san kiranka zai yi bz ai daddy yace zai turo da kudi wai kije asibiti nace ya barshi bayan kudin da ya turo muna zai kara dawainiya kuma. Daddy yayi murmushi yace kin san may yace dani na girgiza kai cewa yayi wai dawainiyar ki yanzu akan shi yake. Nace daddy kada ka yarda da maganan shi wallahi ni ba komai a tsakanin mu yace naji sai dai yadda yake ya nuna min da fuskan gaskiya yazo maki don bai bar abin a tsakanin ku ba ku biyu ya sakomu mu iyayyen ki a ciki bai boye muna ba. Yanzun dai yace a tura mashi da account number da zai turo kudi kije asibiti nace daddy nifa ba komai a tsakanin sai mutunci kawai yace yaji. Sai ga daddy ya shigo zuwa sha biyu yana fadin ya turo dubu hamsin in tafi asibiti nace nasha magani naji sauki daddy dama ciwon mara ne kawai ke damu na. Yanzu yaya kike son ayi da kudin da ya turo maki kasa kasa da murya nace kayi amfani dashi kawai daddy. Sai yamma ya kira yana tambaya ko naje asibitin nace eh yace sun baki magani nace eh nasha har naji sauki sosai yace ashe period kike yi kike wanan raki haka ? Shiru nayi banyi magana ba yace duk wata haka yake maki nace ban sani ba yace kan ki ga Yusuf ku gaisa. Kunya naji sosai jin har da Yusuf yasan ina period yanzu muka gaisa yayi min yaya jiki nace da sauki yace ki sha magani kin ji sauki ko nace eh yayana . Sai shiru ya biyo nace Yusuf batare da fadin yayan da na saba kiran shi dashi ba yayi makin jin hakan daga bakina sai ya dake yace yaya akayi yar mama ? Nace kayiwa mutumin nan fada mijin buzuwa akan abinda yayi min bai kyauta min ba don may yake son saka iyayyena su zarge ni. Yace zargi kuma khadija akan may nace yanzu haka tunda na dawo mama sai fushi take yi dani akan abin da ya saka a motar da naje gida dashi. Saboda shi take fushi dake nace wallahi ni na rasa may zanyi akai suna ganin kamar ban kama kaina bane a Abuja ina hurda da mazan banza ne a can. Sai daddy ne kawai daya fahinci komai da taimakon ya Amina na samu ya dan sausauta min bai fishi dani muryan shi naji yana fadin why mama zata yi fushi dake akan dan abinda na tura masu. Mama bata yarda da tarbiyan da sukai maki bane ko may in haka ne kuwa zan shigo da kaina in mata magana da zata fahince ni ita ma. Ban saka ba haka ka hadani dasu dazun daga na fada ma banda lafiya ka fadawa daddy yazo yana yi min fada balle maman mu da ta hau dani. Ba matsalan ki bane nasan abinda zance da ita idan nazo nayi saurin fadin bansaka ba dai ka barni da ita zamu shirya wataran. Bayan na kashe wayan na mike na shiga wanka na fito na canza kaya jikina zuwa dogon riga nayi kyau sosai a cikin rigar lokacin yamma yayi sosai nace zan je gidan su hafsat kawata da tai aure ta haihu bani gari. Kallon da mamaki min ne yasani tsarguwa sai daga baya na fahinci rigar da na saka ajikina ne yasa take min wani kallo da bashi ba. Sai na dawo tace min batare da ta kalle ni ba na fita jiki a sanyayye zuwa gidan hafsa din dake bayan minna minicipla coucil. Hafsa kawa ta ce tare muka taso da ita kasancewar unguwar mu ba nisa da karatuna ya dawo minna na hadu da ita muna zuwa girl day dake a bayan old airport tare kusa da tsohon makarantar wtc na mata. Bayan mun gama ta samu wani guy ta aura dan kabilar Nufe dake tashen kudi a lokacin . Na fito gida a hankali nake takawa iskan marance yana kadawa inda nake ganin fuskokin wa yan da na sani muna gaisawa jefi jefi dasu a hanyan. Har na isa gidan na samay ta tana girkin abincin dare tana gani na ta tare ni da murna muka gaisa ta nufi falon su dani ina biye a bayan ta. Sai bayan na zauna ne ta dauko min baby ta har yaron ya fara wayo sosai ta miko min shi sai bina take da kallo wai na sauya gaba daya na zama wata big girl dake nace kai haba dai hafsat har dake cikin fadin haka. Tace wallahi gaba daya kin sauya ma sani na ne khadija nace yanayi ne kawai wallahi yazo a haka ba wani abu may ye sunan yaron na tambaye shi. Muna hira tana duba girkin da takeyi har ta karasa takawo min nace wallahi hafsat a koshe nazo gidan nan watarana zanci. Mikewa nayi saboda magariba daya kawo jiki sosai na bata asai ma yaro takalma ina shirin fitane mijin ta ya shigo gidan. Allah ya gani jini na bai hadu da mijin ta ba tun farko asali ma nice ya fara cewa yana so sanin shi da nayi dan duniya mai wayan yan mata da kyale kyali yasa ban bashi fuska ba. Naje hutu kaduna kafin in dawo na samu sun dinke da hafsa har sukai aure yanzun ma da ya shigo gidan ya samay ni sai da ya daga min gira ba tare da sanin hafsa ba. Harara na watsa mai na fice gidan tare da yi mata sallama nadan yi nisa naji muryan shi a baya na yana fadin khadija ji mana. Juyowa nayi fuska a daure ina kallon shi nace lafiya dai ko ya washe baki yace don Allah sorry to distub you kin boye fa da yawa ban san kin zo garin ba ai dana kawo maki gaisuwa. Dan murmushi nayi nace ba komai ai gashi mun gaisa yanzu dama boye nazo gani na ganshi har yayi wayo. Yace in ba laifi ki bani layin ki akwai maganan da zamuyi kin san dai yanzu ba da bane zaki iya fahinta na har yanzu ba kin fita raina bane. Auren hafsa Allah ya nufa sai munyi da ita amma ni ke ce choice dina tun farko hafsa dai ta shishige min har na aure ta. Dakata Adam kada ka kara taro na da irin wanan maganan ko da hafsat bata gidan ka kai ba choice dina bane ka sani ban hurda da maza irin ku da kafan su bai tsayo a guri daya ba. Ke kizo kici arziki kibar arziki kawai don yanzu arzikin bana yaci uban na da zan iya daukan lalurar ki da komai naki wallahi. Wani kallo na watsa mai na up and down nace a haka din kake tunanen zan iya cin amanar kawata aminiya ta nace Allah ya tsare ni da masu irin halinka. Na wuce na barshi tsaye a gurin yana bina da kallon zalama irin ta yan iskan maza yana sosa kan shi baida mu da mutanen dake wuce ba a saman titin. Na shigo gida ana kiran sallah magariba dakina na nufa sai da mama ta gama alwala ta kwada min kira na fito inyi sallah lokacin sallah yayi. Nace mama kin manta bana sallah ne ta ce oho ta shige dakin ta sai bayan sallah isha,i daddy ya dawo gidan suka zauna a dan falon mu har kanne na ciki suna kallon NTA dake labaran marance. Daddy ya duba bai ga na shigo ba yake tambayan ina nake mama tace ina dakina kafin yace wani abu wayan shi ne yayi kara ya dauka bayan sun gaisa ne yayi mai magana yana son magana da mama ne daddy yasa handfree din wayan yadda zai ji abinda yake fadi. Sun gaisa yace mama don Allah a dan sasauta ma khadija da takurawa tace na saka kuna zargin ta da aikata ba daidai ba ni kuma nasan idan har kun yarda da tarbiyan da kukai mata ba abinda zaisa ta canza daga baya kuma. Mama kiyi hakkuri khadija na nan a yadda kika santa alheri kuma yanzu na fara maku kuda ita muddin ina raye sai abinda yafi karfina ne bazan maku ba. Alherin yar ku gare ni ne ya jawo maku hakan ba ina nufin Khadija da wata manufa bane sai alheri don ta cancanci haka a gare ni so kuyi hakkuri a sake mata fuska babu komai sai alheri ga haduwana da khadija. Bayan sun gama waya da mama ya gama daure ni a gaban su da ban gane manufar maganan shi ba daddy ya kwala min kira daga falon. Da sauri na shigo dakin har lokacin shigan da na fita gidan hafsat ne a jikina ban cire ba na samay su a zaune falon. Gaidasu na fara yi tare da samun wuri na zauna mama tace khadija yaushe ne kika canza haka wai ? Nace cikin dago kai da mata kallon mamaki nace mama wanin abin nayi kuma again tace yanzu bamu da shakat a gidan nan dan abu kadan sai ki kai karan mu ga saurayin ki. Da sauri nace mama wane saurayina kuma danakai karan ku gare shi tace wanda kika jajibo a Abuja mana wanda ya fimu sanin zafin ki a yanzu. Mama ni ba saurayina bane wallahi ba wani abinda ya taba shiga tsakanin mu na soyayya har yau tace in babu yaya kika kai karana wurin shi wai na saki gaba a gidan nan tunda kika dawo. Kai kai innalillahi haka yace maku mama fada nayi mai fa akan abinda yayi min nace kina zargina ga abinda kika gani ya bari ban so. Daddy sai dariya yake muna ni da mama don yasan duk iya binciken shi bai gano wani abu da nake aikatawa a bayan su. Tun daga wanan ranan mama bata kara daure min fuska ba muka koma daidai a gidan kamar yadda muke a baya. Wayana gaba daya na kashe sai zan kira nake kunna wa don ban son wani abinda zai haifar min da matsala kuma tsakani na da iyayyena a gida. Ya rage saura kwana biyar mu koma makaranta sai ga kamal mai bi mun ya shigo da kaya wai ya Amina ta shigo gari. Da gudu na kwasa nayi waje ina masu sannu da zuwa tana sallaman driver da ya kawo ta gida na rungumay ta na sake ta naja hannun yaran na rungume su a jikina. Ciki muka shiga gaba dayan mu bayan ya Amina ta huta taci abinci tana zaune a falo na shigo da karamin dan ta a hannu na tace dada hutu ya kusa karewa dai nace wallahi ya Amina. Nakai zaune kusa da ita tace dama ina son in zo gida in samay ki kafin ki koma ne nace tau wani abin nayi ya Amina ? May ye ma baki yi ba khadija ina ke ina Abdulsamad mijin buzuwa fati da mijin ta ta barshi dole don wanan buzuwa ke yanzu kike kokarin jefe kan ki ciki. Kai ya Amina kuna bani mamaki wallahi wai ya fada maku muna soyayya dashi ne halan na san dai shi ba zai fada ba. In kuma don wanan abinda yayi ne kuke zaton muna tare ne da bakin shi ya fada ma daddy gaskiya ba sona yake ba. Haka kike tsamani ke ko azaton ki duk wanan alaman da yake gwada maki ba so bane hakan wani namiji zai samay ki yace bai so ki. Kin fi buzuwa durin na ya mace sai dai fari da gashi zata gwada maki ko farin ma ba wani can ba don ke ma ba baya ba. Sai yanzu nake gane maganan baban boy da yake cewa ke din matar manya ce watarana ina ganin kamar fadi dai yake yi. Abin mamaki ne yadda har Abdulsamad ya fada tarkon ki abinda ba wanda ya taba tsammani zai iya sai gashi lokaci guda har kin fara canza shi da naki sallon soyayyan. Mama da ta shigo dakin dauke da kwanon da ta tuka muna tawaska ta aje tana cewa ke ma dai kya fada idan anyi magana tace an matsa mata ba soyayya suke da shi ba ko takai karan guri shi. Shi ko ba kunya gare shi ba ya kira mutane yana rokon su akan a daina matsa mata don Allah ni daddy ku har mamaki yake bani yarda ya yarda da mutumin nan a lokaci daya. Da ban san halin shi ba sai ince ko don kudin shine yake son shi ya Amina tayi sauri cewa a a mama ba halin daddy bane haka da yana bin kudi da ba zan auri Abban su boy ba. Mama tace nasani ai shine abin ke ban mamaki yanzu ai tace yarda ne kawai wallahi in badon buzuwar matar shi ba ai Abdulsamad mijin aure ne ga ko wace mace ta samay shi. Nan ya Amina ta fara ba mama labarin shi da rayuwan su har karshe nace wai ku may yasa kuka damu da wata buzuwa can ne. Kowa tashi tafishe shi amma ni bata cikin tsarina ni dai kawai bai min bane ina zan jefa kaina ga family man mai iyali da yawa haka. Wanan duk ba matsala bane tunda yana da abin kula da koda mata nawa yayi niyar yi abin damuwa shine kishi da wanan buzuwan da bata da imani ko kadan. Balle idan taji ba barin shi zatayi ya aure ki ba kuna tana iya yima rayuwan ki illar yada taiwa fati ko sunan ta baya son ji yanzu. Allah bai bata iko a kaina nace ke don Allah rufawa mutane baki ana baki kina roko may kika taka da kike fadan haka nace mama Allah. ZAINAB IDRIS MAKAWA ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABUWashe gari muka shirya zuwa beji duba wani kakan mu dake zaune acan kanin mahaifin maman mu ni da ya Amina da yaran su. Bayan Nkwa bamu iya wani gaisuwan kirki ba sai habalu da sauran kananin kalma irin na gwarawa da muka rike a bakin mu. Tsohon yaji dadin ganin mu yana ta murna da zuwan mu gidan duba su anan muka wuni tare da su sai yamma muke son mu dawo mu biya maikunkele gidan iyayyen mama din. Tsohon bagwaren yana waje zaune da bakon shi muka fito zamu wuce muna masu sallama bakon nashi ne yayi yare sai naga tsoho yayi dariya tare da fadin yaki nan amarya na. Nazo na duka a gaban shi yace bako na ne ke son ganin ki sai na gaida dattijo ya mika min hannu alaman in bashi nawa hannun. Ban ki ba nayi kamar yadda yace min sai da ya kalli tafin hannu na da kyau yayi murmushi yace Allahu akabar akwai tarin alheri ga wanan hannun naki sosai zan ba kaka ku wani abu ya baki gobe ba mai wuya bane abin inda zaku tsaya na awa daya zan iya hada maki ko anan ma. Don tsari juyawa nayi na kalli ya Amina tace ai zamu iya tsayawa mu karba nan saman tabarman muka zauna ya bude jakkar shi ya ciro wani dan farin abu a wani kwanko yayi ta abinda zaiyi a abin sai ya miko min hannu na mika mashi nawa. Ya fara murza min abin a tsakiyar tafin hannu na har saida abin ya bace bat a hannu na ya dan dade rike da hannu na yana min tofi har kaina sai daya dafa yayi min yadda yayi a hannun ya sake ni dama tsamin jikin shi duk ya isheni sosai. Ya Amina ma tace aiwa yaranta da ita ba irin wanda yayi min yayi mata ba zamu tafi na bude jakka na fido dubu daya na bashi ya girgiza kai. Yace idan ina da dari biyu in bashi kawai yaci goro dashi na duba naga wani sabon dari biyo na dauko na bashi nayi mai godiya muka tafi. Muna cikin mota ya Amina tace na rasa may sa tun kina karama idan mun fita ke kawai mutane ke taimakawa wanan karo na biyu ke nan da haka ya faru dake. Nace su suka san abinda idon su ke gani a kaina wanda mu bamu gani hakan dariya tayi tace kila ya hango maki buzuwan ku ne . Kai ya Amina may yasa kuke fadar haka ne karfa maganan nan yakai kunnen su mommy da yan gidan su fa. Tace indan ya kama suji ai ji zasuyi khadija lokacin jin su ne baiyi ba kawai amma duk wanda yaji mamaki zai yi wallahi. Sai dare muka isa gida don mun bata lokaci a maikunkele wurin yan uwa da abokan aarziki ko da muka dawo wanka kawai nayi na samu wuri na kwanta abina. Da safe muka tashi da labarin haihuwan antyn mu Anty Hauwa dake aure a pilamigo easther wanka mukayi muka nufi gidan ta acan muka wuni sai four muka baro gidan ta. Koda muka dawo gida mama tana dora girkin dare sakwara zatai muna da miyan egushi tubewa nayi na fara taya mama aikin dakan sakwara don doyan ya dahu ko. Ya Amina data fito dakin ta tsaya tana kallon yadda nake dakan sakwaran ta kwashe da dariya tace ashe kin iya idan nace muyi sai kice bakya son ci. Sallaman da muka jiyo a kofan shigowa gidan mu ya hana ni bata amsa naci gaba da dakan sakwarana. Anty Amina ce ta dan leka raga mai sallaman sukai kicibis da Yusuf a tsaye yana gyara rigar shi da ya dan takure ga zaman mota. Kamar daga sama ta san shi a gidan su mommy shine dai bai santa ba tace cikin mamaki Yusuf kune tafe haka da yamman nan ? Yayi mamakin sanin shi da tayi haka shi bai santa ba sai dai ya gane muna da kama da ita sosai sai dai tsayin da nafita da kuma hasken fata don ni daddy na fadin gidan mu na debo sosai ina da zubin fulanin su na ka,aje ne. Ta juya tana fadin barin sanar da Khadija gata can yau sakwara take daka muna a gidan yayi dariya ta wuce ciki ina ganin ta shigo tana dariya ina rike da tabarya mama na duke tana saka wanda na daka a leda tace khadija ga ki da baki fa a kofan gida. Da sauri nace da ita su waye ya Amina tace wa kike tsamani zai zo maki yanzu banda su Yusuf da abokin shi nace kai haba dai ya Amina may zai kawo su nan in ba gulma ba. Tace to gulman ko ya kawo su gasu can a waje dai nace wai da gaske tace ina wasan haka dake ne dama tabarya na aje ina fadin yau na shiga uku. May suka zo yi yanzu kuma don Allah tace kyaji idan kin fita ai ni wallahi sai naci masu mutunci don may kuma zasu biyo ni har gida haka ? Harara mama ta watsa min tace idan zaki natsu ki natsu kije ki gan su falo ya Amina ta shiga ta fara gyara wurin inda zasu zauna ko kafin in fita na samay su da daddy suna gaisawa a waje na juyo na dawo ciki abina. Har ciki daddy ya shigo dasu ina labe a dakin mu ina kallon su sai da suka shiga sun dade ciki da daddy da ya Amina kafin ta fito ta kwala min kira ban fito ba ta samay ni a dakin tana dariya. Ya Amina may wanan mutumin ke nufi da nine wai for god sake may ya kawo su har gidan mu ne don bata min suna. Kallona tayi da mamaki tace zuwa gidan ku shine barnan suna khadija ai gara da suka zo zai fi hankali mama ya kwanta. Ni kan na shige su wallahi tace don Allah ki natsu kije ku gaisa sunce hanya ne ya biyo dasu nan suka ratso su gan mu. Ina shiga na samu har da abinci aka aje masuz sai hira Yusuf keyi da daddyn mu shiko sarkin miskilanci ido kawai ya zuba ma kofan shigowa falo. Da sallama nashiga tare da samun wuri gefe na zube gwaiwa na a kasa ina gaida su Yusuf ne ya amsa min shiko ido kawai ya zuba min kamar yadda na samay shi zaune. Daddy ya fita falon yana cewa dasu yana zuwa ya fita daga falon bayan fitan daddy ban daga a yadda nake na dago ina kallon su nace may ya kawo ku may kuka zo yi gidan mu ? Baiyi magana ba sai bude kula abincin yayi yana kallon sakwaran tare da fadin ke kika yi wanan abincin wai ? Yaya akayi suka san haka nake tambaya kaina a zuciyana Yusuf ma budan abincin yake yana faadin yar mama ashe kin iya girki ne haka ? Yayana may kuka zo yi nan yace gashi kinga munayi kawai dai mun yi marmarin cin girkin gidan ku ne mukazo muci dan harara na aika masu. Abdulsamad din ne yace kina ganin zaki iya kashe min waya don kada na kiraki da sauri nace ni ba kashe ma waya nayi ba. May yasa baki kuna wayan naki ya tambaya cikin kura min idanuwan shi dake ban tsoro yanzu nace wayar ce bata da lafiya. Baiyi magana ba ya fara cin abincin ba ko kunya hankali a kwace nace baku da kunya ne zaku ci a binci a gidan mu ku wai wasu irin mutane wai ? Ruwan abincin gidan ku zaki muna ya fada nace ni naci na gidan ku ne to yace wayasan iyaka wallahi ban taba shan ko ruwan gidan ku ba ni. Yusuf yace saboda may yar mama yana kai lomar sakwara a bakin shi kunya su nake ji ban iya shan ko ruwa a gidan don nauyi. Ashe ko kin cuci kan ki don ni dai a sani na gidan mu bako bai shiga ba a tare shi da abin sha ko na ci ba daddy ya kwala min kira daga cikin gida na mike na fita da sauri ya daga kai ya bini baya na da kallo. Saurin kawar da kanshi yayi yana cin abincin da yaji dasin dan danon shi har cikin ranshi ina fita naga baba da leda ya sawo drinks. Yace in kai wa baki a falo a tire na saka nakai na dire masu a gaban su nace gashi kun sa baba kashin kudi bai shirya ba. Murmushi magana na yadan yi sun ci abincin sosai suka wanke hannu na fita da kayan bayan sun gama ne suka ce inyi masu iso su gaida mama zasu tafi. Fita nayi na kira ya Amina ina fada masu abinda suka ce man ita ta fada ma mama zasu shigo su gaida da ta nan mama ta gyagyara suka a kofan daki aka shimfida masu tabarma suka zauna. Bayan fitar sune na samay su a waje har sun shiga mota ina isowa Yusuf ya miko min waya kallon wayan nayi ina tambayan shi ta may yace ogana yace a baki tunda naki ta lalace kiyi maneji da wanan kafin ki dawo Abuja a sai maki wani. Amma don Allah kada ki kara kashe muna waya mu kira bamu samay ki ba ran mu baya dadi rashin jin ki da bama yi a koda yaushe. Kai na girgiza tare da fadin kubar wayan ku ni wayata lafiya take kashewa nayi kawai don, , , Ban karasa ba naji yace don kada kiji muryan mu ko may khadija nace kawai abubuwa ne sukai min yawa a nan bata waya nakeyi ba. Yaushe zaki dawo school don hutu ya kara nake gani nace sai anyi sunar yayan mu data haihu zan dawo uffer week may zaki zauna yi har uffer week Abdulsamad ya tambaya. Ba a gida nake ba tare da iyayyena na bashi amsa da hakan yace ranan tuesday zan turo a dauke ki yana fadin haka ya rufo kofan motar Yusuf yayi min sallama tare da kara mika min wayan suka tafi. Azato sun tafi ne sai ga yara suna shigo da drinks da wasu abubuwa a kwali wai i ji su ina daki ina kallon wayan daya ba babban wayace mai tsada fara kwal da ita. Ya Amina ne ta shigo dakin tana kallo na tare da fadin wai shi baya gajiya da wanan daiwaniyar da yake haka ne kuma kin ce ba soyayya kuke dashi ba. Wayan da ya bani ne na miko mata ta karba tana fadin ta maye wanan kuma nace shiya bani do kawai nace tawa ta samu matsala ne yasa basu samu na . Abin nayi ne ashe yanzu a ka fara wasan da ba ansan maci tuwo ba sai miya ta kare nace ba wani wasan da aka fara indai nice da na koma zan kakabe shi in huta da zancen su gaba daya. Tace ai wanan da alama kin samu kaska baya kakabuwa wasan dadi don ko ya fiki dabara yanzu gashi ya gama daure ki a gurin daddy da mama ko. No way to exscape daga tarkon shi a kwai game da na sani kan nan gaba din ba karamin aiki kika banbaro muna ba yarinya. Kai ke ya Amina ke kekara ma abin wuta wallahi ni may zanyi da mijin da wata ke juyawa a gidan shi kina so in shiga nima in koma yar bi ce kamar fati ? Ke zaki tsayane ki zauna kamar ita a wirin shi ta kai zaune tana fadin da farko ina tsoron abinda ke shirin faruwa tsakanin ku da shi. Amma yanzu zuwa na gida da daddy ya wayar min dakai sai hankali na ya kwanta da zance nake ganin kece haske da zai yaye duhun da Abdulsamad din ya shiga. Ya Amina ki bar wanan magana kimun fatan alheri a rayuwana ba irin wanan fatan ba na shiga wurin da fitina ta nuna kan ta a fili. Khadija kin taba ji ko ganin Abdulsamad ya taba bata lokacin shi ga wata mace irin haka amma sai gashi a kanki abubuwa na ta shirin faruwa a tsakanin ku. Na tabbatar da su hajiya mama zasuyi fari ciki da jin wanan labarin don wata kila adduan su ne ya fada kan ki. Shiru nayi ina sauraren ta tace abu daya zuwa biyu ne na farko gaba dayan mu sai mu dage da addua gaba dayan mu na biyu kuma kiyi kokari ki cusa mashi so da kaunar ki ta yadda buzuwa ba zata iya mashi gibi ba. Har muka gama magana ta fita ban iya cewa komai ba ta barni ina cike da tunane a raina na yadda abubuwa ke zo min a haka. Sai dare sosai suka shiga Abuja inda Yusuf ya aje shi gida ya nufi nashi gidan da motar shi da ya bari gidan don tafiya da ba shiri sukayi. Ko da yashigo gidan shiru yaji kamar yau mutanen gidan nashi basu ciki bai tsaya falon ba ya haura sama inda dakunan kwanan su yake. Ga kaya nan ko ina a warwatse ko ina agidan anyi amfani dasu an kasa kawar dasu don tsabagen kiuya da lalaci har ya kai kofan dakin ya tura a hankali ya shiga. Baiyi mamakin ganin ta a yanayin da ya samay ta ba don duk kwanankin nan a yamutse take a gidan ba wani gyara ko kwaliya da take samun yi . Tana zaune saman gado gashin kanta a wawatse ba gyara ta dago ido ta kalle shi tare da kallon agogon bangon dake dakin tace Samad ina kafito a wanan lokacin. Aikena kikayi da kike tambayana ya bata amsa tare da wuce wa wurin wardrobe din shi yana rage kayan jikin shi. Samad neman mata kafara ko mai yace idan na nemay su ba namiji nake ba wallahi baka isa ba ta fadi da karfi ya juyo gare ta yace ban isa ba fa ki ka ce Nafisa. Tace baka isa ba wallahi may na rage ka dashi a wanda ban baka da har zaka lakanci neman mata a yanzu daga sama. Ya ciro wani dogon jallabiya baka yana fadin waya san iyaka Nafisa baki san komai ba banda son kan ki da kashin kudi abaki kuma baki godiya. Kudi dole ne ka bani don kasan sune buri na kuma akwaisu bathroom ya shiga ya barta ta ta fadin bakaken maganganu gare shi har ya fito bata fasa magana ba. Gadon ya duba yace duba don Allah wai a inda mutum zai kwanta ke nan ya fara kakabe shimfidar da wani dan karamin towel daya fito dashi daga ban dakin. Yace mace sai tarin kazanta na fada maki bani son wanan kazantar taki amma ke abin sai gaba yake yi gare ki. Ai kasan a haka nake kuma ka aure ni na dauka idan kin shigo cikin daula zaki canza ne ashe ni ban san abin a jinin ki yake ba. Kazantar ne a jina na yake Samad yace in ba ajiin ki yake ba za a ce duk yawan ku baku iya gyaran wuri tace samad wa kake so in sa aiki a cikin gidan nan. Kafa san daga kanne na sai yayyena anan sai kuma kawu naina da gwago na yace may yasa kika boye min hakan da farko kin fada min yan aiki ne kika samo min kuma biyan su nake duk wata. Sai yanzu zaki ce min wai yan uwan ki ne na jini baki iya saka su aiki a gidan nan kin zo gidan nan kin samu masu aiki kika ce baki yarda dasu ba. Na baki go ahead da zaki kawo wanda kika yarda su suyi mana aiki ashe ke yaudarana kikayi ki kwaso yan uwanki kika cika min gida dasu. Samad ta fada da karfi kawo yan uwana danayi a gidan shi ne kake kira da yaudara yace yaudara ne mana mutum da gidan shi ba dama ya shigo ya huta a ciki yaji dadin ranshi. Samad yau ni kake fada ma haka don ka gani da ciki kake kokarin ka wulakantani yanzu ko may babu zancen wullakanci sai maganar gaskiya. Haukace mai tayi ranan tana fadin bai isa ya rabata da yan uwanta ba don tare ya gansu ya kuma yarda ya aureta a hakan. Haka ya kwana da tarin bakin ciki babu kunya washe gari kuma sai gata ta neman sulhu dashi don dai kawai ya biya mata bukatan ta don bata iya hakkuri dashi duk yadda ranta ya baci dashi ga wasu kudi da take son karba a wurin shi masu yawa don ai mata aiki a kan shi. Bata samu ko daya ba ranan don asubanci yayi ya fita wirin aiki da wuri koda yaje gurin aikin bai iya aiwatar da komai ba. Yusuf ya shigo ya samay shi a haka yake tambayan shi wai may ke faruwa dashi ne bai tsaya boye mashi ba ya sanar dashi halin da yake ciki da nafisa a gidan shi. Da yan uwanta da suka cika maigida da sunan yan aiki ta kwaso yana biyan su a wata ashe ba haka abin yake ba. Kai inji Yusuf lamarin Nafisa akwai daure kai wallahi Abdul yace nima bashi ba kazantar nan ke damuna Yusuf. Ka san dai halina da kyakyami wallahi komai na gidan nan yanzu kazantar shi nake ji in ba ruwan gora ba ban iya cin komai a gida na . Yusuf yaya zanyi da wanan masifa dana dauko ma kaina nasan ina son nafisa sosai why da ba zata gyara halin ta ba may ye ban ma Nafisa a rayuwan ta. Kamar karta samu cikin nan yanzu abin ya karkare jagule mata mace ba wanka ba saka sutura a jiki idan anyi magana sai tace wai lalurar cikine haka take cikin ta. Au dama ta taba ciki ke nan naga auren budurwa mukai mata wani kallo ya jefe shi dashi yace Nenan yar waye idan bata taba haihuwa ba nima daga bayan nan na fahinci yar tace ashe. Yanzun haka zan kare ga yawon restaurant ina cin abinci a garin nan kamar wani mara galihu dani. Kai innalillahi abin nakune akwai daure kai wallahi saukin abin khadija zata dawo next week zaka dan samu sauki a awurin ta. Saukin may zan samu a gurin ta ya tambayi Yusuf a yanayin rashin fahintar maganan shi Yusuf yace koba komai tunda ta iya girki naga ai zata dan dinga maka idan tana da time. No ban san in jefa rayuwan yarinyar ga halaka ko kadan nafi son ayi komai a kaidance yace kana nufin auren ta zakayi. Shiru yayi ya dafe kanshi bai sake magana ba ya fahinci bai son maganan don haka ya kyale shi tare da canza topic. Yusuf na fita ya jawo wayan shi ya kira layina muna gida ya Hauwa mai jego ya kira wayana ina wanke kayan miya a kitchen aka kawo min wayan. Sai da ya kusa katsewa na dauka tare da sallama yace ina kika shiga kika bar waya na ruri haka nace ina kitchen ina girki wa ya hauwa da ta haihu. Kuna gidan ta ke nan ya tambaya nace eh may kike girka mata nace miyar shuwaka zanyi mata da tuwon shikafa. Ke wa ya koya maki girki haka ne wai nace girkin ma har sai an koya ma mutum yin shi idai kana mace ai zaka iya girki ko wani iri dole. Aranshi yace ga macen da ta san kanta ba sai kuma yace ke wace irin yarinyace da baki iya kiran mutane kiji ko sun sauka lafiya ? Na aiku tafiyan dare ne ko ni na saka ku yin tafiyan da kuyi din yace OK haka zaki ce ma nace haka din ne ma ai. Sai naji ya kashe wayan dariya nayi nace zaka kaji ai ka daina in yar da magoro in huta da kuda har dare muna gidan sai tara muka dawo gida a gajiye . Ban kara bi ta kanshi ba har akai bukin suna aka watse lafiya drinks din da suka kawo muna yayi muna rana do shi mukai amfani dashi wurin taron sunan. Mun fara shiri don tare da yaAmina zamuyi tafiyan kamar yadda na fada mata yace zai turo mota hakan ne ya faru sai ga mota zuwa sha biyun rana ya tsaya a kofan gidan mu. Nan muka fito mukayi haraman tafiya nasha nashi ha a wurin mama da daddy 6 kafin mu wuce muka dauki hanyar Abuja tare da ita don zata kwana a wurin mu. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU INA BUKATAN ADDUAN KU YAN UWA ALLAH YASA MU DACEAlhamdullahi mun sauka lafiya inda na samu maryam ta dawo ko saboda kwanakin da na kara ta rigani shigowa na samu har ta gyara min daki ko. Anan driver ya zube mu ya wuce abinshi ko ba a fada min ba nasan anty ta biyoni ne don taga yanayin zaman da nake a Abuja inda tazo da sunan kwana daya sai gashi ta share biyu kuma muna tare da ita ban je ko ina ba. Washe gari da safe na rakasu tasha suka shiga motar kaduna suka tafi bayan yan nasihohin da taimin na in kula da kaina in maida hankali ga abinda ya kawo ni. Muka rakata garage ta shiga motan kaduna wanda ta dauka ita kadai sai yaranta har kaduna mun dawo hotel a gajiye don haka na kwanta barci don nadan ji dama jikina. Tun da na kwanta ban tashi ba sai bayan sallah la,asar na tashi nayi wanka na tare da gabatar da sallolina ban dade ba maryam ta shigo tana fadin kin tashi ? Nace wallahi tace ga abinci nan ki cikin kula idan kin tashi ci ni na koshi sauran kayan bukin da ya rage na zauna ina ci nace abinci sai da dare. Ina zaune kamar daga sama zara ta shigo dakin nace mutumiyar ashe ke ma kin dawo ke nan tace dazu fa na gama tunanen ki. Zarah tayi dariya tace ai ni na riga ku dawowa tun wancan satin daya wuce na dawo school da sauri nace ai lokacin ba ai resuming ba. Ta wallahi gajiya nayi da zaman gidan shine nace hutumu ya kare aka shiryani na dawo school kaina jinjina nace Allah ya kyauta da halinki zarah tunda har kin san ki aikata haka. Dariya ta sake min tana fadin gidan ne babu dadi yanzu da na saba da ruyuwan independent din kaina . Sai da taci abinci a dakin ta koshi tana bani labarin tafiya sukayi da saurayin ta ta raka shi kano shiyasa ban ganta ba maryam baya ta bamu tana diban takardun da take hadawa har zarah tabar dakin. Sai lokacin ta juyo take ce min irin wa yan nan bai kamata mutum yana hurda dasu ba ai kada su bata ma mutum suna a banza. Nace yaya zanyi mun fito gari guda da ita bazan iya kyale ta ba ai kin ji dai ina bata shawara ko zata daina halin nan da tasawa kanta. Allah ya kyauta tace muka canza hiran kada muci namanta bamu sake fita ba har gari ya waye muka shiga school. Wanan karon Nafisa bata yar da ba dakanta ta shirya tafiya zuwa kaduna bayan ta dawo Niger don an bata labarin wani sabon malami a Kusfa. Abdulsamad bai hanata zuwa ba don tace kaduna zata leka don ta kwana biyu da zuwa shiri sosai yayi mata don zuwa kadunan a ganin shi ai gida zata. Ranan da ta isa kaduna bata samu zuwa ko ina ba sai washegari suka tafi ita da Auta yar take ga su Abdul din sai dai halin kwadai irin nata zata iyayin komai akan kudi. Haka yasa suka kule sosai da Nafisa har aminci ya shiga tsakanin su tana mata shige shige dama Auta irin yan duniyan matan nan ne tunda ta fito gidan mijin ta bata sake aure ba tana zaman rayuwa kawai a gida. Su biyu sukai tafiyan sai driver daya kaisu bayan sun gama yi ma malamin bayanin komai ne malamin yayi dariya yace kamar yadda take zargi gaskiyan maganan ke nan ya fada tarkon son wata yarinya a yanzu sai dai abin bai wani yi nisa sosai ba. Idan kuma bata bi alamarin a hankali ba zafin kishin da take nunawa ne zai sa komai ya iya faruwa da ita. Hakalin ta ya tashi sosai wanan ne mutum na biyu daya fada mata haka malamin yace alamarin yarinyar yana da karfi sosai. Don asiri baya kamata kai tsaye da zaran zamcen yakai ga iyayyen shi komai zai iya faruwa a tsakanin su a yadda bata zata ba. Don haka sai kin natsu aiki zamuyi maki wanda zaki kama mijin ki a hannun ki indan shi ya kamu yadda muke so komai zai iya zo maki da sauki. Amma koda zakici nasara akan hakan sai kin bi a sannu don yarinyar tafiki komai da kike tunanen kina dashi abune wanda sai an aiwatar dashi a sannu saboda mijin ki yana mata mugun son da bai san yana mata ba. Nashiga uku tace malam tafini komai fa kace yace kwarai da gaske don gata nan a gaban mu kina gani ta shige maki gaba ko a wurin shi. Kuka ta fara tana fadin don Allah malam kai min rai ka taimake ni ko nawane zan iya baka indai zaka min aikin da za a raba su hayatan hayatan ya ji bai kaunar ta ko kadan. Gaba daya yanzu na daina gane kan shi ada komai yana min kai tsaye yanzu sai yaja min rai yake min abu da na dauka ko cikin dake gare ni ne yasa yake min hakan. Yace magana dai guda ce ga yarinyar nan kina gani taurarin ta na da matukar haske sosai duk abinda ta sama gaba takan cin ma nasara a kan shi lokaci daya. Yana nuna masu zanen da yayi a kasa wanda su basu fahintar abinda ya zana sai dai bayanin da yake masu wanda ke matukar tayar wa Nafisa da hankali. Yace saukin abin daya ne yarinyar mijin ki baya gabanta don wani dalili nata amma shi yana kokarin cusa kanshi ko yaushe a wurin ta ne. Tace da karfi shi samad din malam yace kwarai kuwa muddin muka ce zamuyi aiki na gagawa komai zai iya faruwa na fada maki. Idan baki yarda ba zaki iya zuwa gurin wani kiji nasan duk wanda zai fada maki tsakani da Allah ba zai fada maki sabanin abinda na fada maki ba. Tana share hawayen dake zubo mata take fadin malam yanzu may ye abin yi don ko yanzu da dabara na samu nazo nan din. Wanan ba wani matsala bane aiki zamuyi mashi wanda hankalin shi zai fita a kan wata mace baki daya sai mu cus mashi kaunar ki ke kadai. Ta gyara zama tana fadin in hakan zai samu malam shi nafi bukatan ai min a kan shi a raba shi da ko wace yar iska ce kison tayi min kutse a gidana. Ya zayyana masu aikin da zai masu din ta yarda ta amince zata biya makam din abinda ya bukata a wurin ta suka biya shi ba tare da taji komai ba sukai mashi sallama. Tun a mota take zazaga balai tana zaginshi da iyayyen shi Auta tana kara zugata da fadin wanan wata irin yarinyar ce da za a ce ta fiki komai har kyau ke nan malam yake nufi ko may. Don banda kyau babu wani abu da Nafisa ke kadagi dashi don ba arabi ba boko haka take dip dinta bakauya kuma. Koda ta dawo kaduna bata biya gidan su Abdul din ba bata mayi tunanen shiga gurin su ba don daukan su take a makiyan ta dama balle yanzu da sunan su ya fito ga zancen. Kwanata uku a kaduna bayan Auta ta koma ta koma ta karbo abinda zasuyi amfani dashi idan ta koma sauran sai ya hada yace zai kira Auta ta karban mata don sai ya nemi abin hadi. Haka ta shirya sai da zata wuce ne ta dan shiga tsatsaye ta gaida su hajiyan shi da sauran mutanen gidan ta juya suka tafi. Almarina kuwa tunda na dawo sau daya muka hadu dashi koshi a tsatsaye don ina sauri zan tafi class karatu don muna da test din da zamuyi washe gari. Yazo min da provition mai yawa kamar ba gobe har sai danace kayan suyi min yawa yace naci da kawayena. Sun tafi abisa alkawrin zamuyi waya amma har wani lokaci bai kirani ba Yusuf ma haka bai kira ba nikan haka yafi min nono fari. Don dama neman mafita nake dashi kuma na samu yanzu sun sarara min ranan muna hira da maryam take tambaya na su. Nace banji komai daga gare su ba na nuna mata ni basu gabana yanzu abinda ya kawo ni nakeyi. Tace kai amna abin mamaki ne khadija ace sun share ki haka ba labarin komai daga wurin su ko yusuf ai ya kamata ace ya kira musan halin da suke ciki. Ke kuma baki neme su ba halarci baice haka ba fa khadija shiru nayi mata don mu kawar da zancen su da ta dauko min ina zaune kalau. Sai bayan da na kwanta sai kuma maganan ya damay ni a rai gaskiya maryam ta fada min ya kamata ka kula mai kula ka koba komai zai san ka damu dashi ai. Ranan da kyat na samu nayi barci da tunanen su a raina sai dai ni ba zan iya kiran shi ba sai dai dan dama dama Yusuf din. Washe gari haka na tashi da jin bakin rai a zuciyata sai dai kawai na danne abin a raina don na kudurta a raina ba zan taba kiranshi ba indai nice zakira inji ko lafiya suke. Tunda dama ba wani soyayya ko wani abu ke tsakanin mu haka ba mai karfi kawai dai ya gaji danine shima ya hutar da kan shi. Na share kawai kada maryam ta fahince ni na shirya muka nufi cikin school don daukan lectures na watsar da maganan su a raina kada in sa wa kaina damuwa a banza. Alamarin gidan shi kuwa yanzu tun dawowan Nafisa daga kaduna sallon zaman su ya sauya don yana dan samun kulan daya kamata daga gareta duk da ba wani dadin yake ji ga hakan ba don baya samun sakewa har yanzu a gidan shi yadda yake so. Shima Abdulsamad din ina a ranshi yakan so ya kirani yaji lafiyata sai dai yanzu duk lokacin shi na aiki ne dana Nafisa a haka har yayi tafiya tare suka ketara da nafisa zuwa wanan tafiyan. Satin su biyu suka dawo Nigeria koda suka dawo abuja bai samu kafan kiran na ba don Nafisa ta mamaye komai a lokacin. Yau suna tare da Yusuf a office din shi Yusuf ma wanda yayi tafiya yake tambayan shi labarina ya yamutsa fuska yana fadin wallahi banda labarin ta itama bata neme ni ba. Yusuf yace haba kai ma kasan bazata nemay ka ai, amma hakan bai mun dadi ba wallahi dakace baka kirata ba waya ya dauko daga Aljihun shi ya fara neman layina a lokacin. Ban shiga school ba ranan don na tashi da ciwon mara ina kwance a dakin mu ko karyawa ban yi ba har lokacin don haka ina cikin barci mai nauyi daya dauke ni naji kira a wayana. Da kyat na lalubo wayan dake gefe na ina jan tsakin wanda ya tayar dani a wanan lokacin dana dan samu sa,ida na samu barci ya dauke ni. Koda na dauko har kiran ya katse sunan Yusuf na gani akan wayan ban kai ga tunane ba wani kiran ya sake shigowa again. Tunane nake a raina may kuma zai fada min yanzu mutanen da suka shareni kusan wata daya ke nan yanzu kuma zai kirani yace min may ? Kamar in share shi kiran ya katse sai dai na danna recieve inji abinda zai fada min a lokacin na amsa da sallama cikin muryan barci da yanayin ciwo a tare dani. Naji yace subbahanallahi khadija baki da lafiya ne may ya samay ki naji muryan ki a haka ? Da sauri ya dago kai yana kallon Yusuf dake magana a waya yaji yace ayya sorry sannu ko kin je asibiti ne nace nasha magani ai ba sai naje asibiti ba. Idon shi har lokacin yana akan Yusuf din yace may ke damun ta ne naji Yusuf din na fada mai wai banda lafiya ne a kwance nake ma. Taje asibiti Yusuf yace tace ba sai taje asibiti ba wai karban wayan yayi daga hannun Yusuf din naji muryan shi yana fadin ki shirya yanzu gani nan zuwa nakai ki asibiti ya fada kai tsaye. Nace naji sauki ba sai kazo ba na kashe wayan wayan ya kalla tare da mikewa tsaye yana rufe file din dake gaban shi ya fara tafiya. Yisuf dake zaune ya mike juyowa yayi yana fadin ka zauna ka karasa aikin barin je na ganta in dawo Yusuf yace amma kana ganin zata saurare ka idan kaje kai kadai. Wani kallo yayiwa Yusuf din kamar zaiyi magana sai kuma ya juya ya fita Yusuf ta girgiza kai yana murmushi halin abikin nashi na bashi mamaki ace mutum haka da girman kai. Nikan ina kashe wayan naja tsuki nace mayaudari kawai naja filo na gyara kwanciya na barcin da ban koma ba kenan idona a rufe nake tunane nace yanzu na tabbatar da karkashin mace yake. Wata kila matan shi tasamu labari ne ta hana shi kula kowa yanzu ya dawo zai yaudare ni kuma ya bata min lokacina a banza. Dama ban sa zancen ko kadan a raina ba balle ya damay ni in ma junin shi iya yaudaran mata ne ya bata masu lokaci Allah ba zai bashi saa ba anan naja tsuki na gyara kwanciyana. Na samu barci ya fara dauka na naji wayan shi ya shigo min na duba na bar wayan nata ruri har ya katse kira uku yai min ban daga ba . Ranshi ne ya baci sosai yana shirin juyawa sai ga maryam kamar daga sama ta dawo don hankalin ta bai kwanta a yadda ta barni ta dawo ta dubani. Sai ganin shi tayi yana shirin juyawa da sauri ta karsa wurin shi tana gaidashi tare da fadin wallahi tana ciki bata da lafiya ne tun jiya nima yanzu na dawo in dubatane. Yace shi yakawo ni yazu asibiti nake son zuwa da ita a ranta tace boye min khadija ke nan rayi ashe suna waya dashi shine take boye min. Taji yace nakira wayan ta taki ta ga bayan yanzu Yusuf ya gama waya da ita ta fada mai bata da lafiya tace barin shiga in fito maka da ita nasan fushi take daku. Fushi ya tambaya da mamaki dariya tayi tace ina zuwa don Allah ta wuce ya bita da kallo har tabace yana mamakin kalamin ta wai fushi take da ku fushi akan may ? Tana shiga dakina ta nufa ta samay ni a kwance zama tayi a gefe na tana min sannu tare da fadin ga mutumin ki nan a bakin get yana jiran ki wai kuje asibiti yanzu. Wani kallo mai kama da harara na watsa mata nace rabu da mayaudari nine zai kai asibiti akan may zai zo min a yanzu da bana son ganin shi. Haba khadija kin san uzurin da ya tsayar dasu basu nemay ki ba tunda har yanzu ya iya zuwa da jin baki da lafiya ai ya kamata ki saurare shi. Haba maryam abinda kika sani ne nafi jin dadin zaman da nake yanzu babu takuran kowa a kaina akan may kuma kike son in kara fadawa tarkon mayaudari irin wanan mutumin da matar shi tafi karfin shi kuma. Kada kice haka khadija ko ba komai ya nuna kulawan shi a kan ki yanzu ina laifin wanda ya nuna maka haka a lokacin da kake cikin halin ciwo. Don Allah ki tashi ki daure badon ni ba sai don Allah ki tafi ki ganshi ko ba komai zakiji abinda ya tsayar dasu kwanaki mai tsawo haka baki ji su ba. Allah da kika hadani dashi ne zai sa in tafi badon wani abu ba can nasa, don ina son inyi nisa da shuumancin su yanzu tace daure kiwa Allah da kika ce zato kike yanzu kila ma ba matar shi bace ta hana ya kulaki. Kalaman ta yayi tasiri sosai a raina koba komai ina son jin abinda ya hana injisu kwana biyu don ban sin jawa kaina wulakanci ko kadan. Ita ta taimaka min na shirya atamfa na daura don yanayin da nake ciki tare muka fito zuwa ida yake zaune a motar shi. Yana yi yana kallon agogon hannunshi can ya ga fitowan mu tare da maryam ina tafiya da kyat yanayin ina jin jikin nawa sosai. Har muka karaso bai dauke idon shi a kan mu ba yi hakkuri mun barka kana jira wallahi barci na samu tanayi yanzu na tayar da ita. Bai yi magana ba sai kallona yayi yana fadin shiga mota mu tafi nace basai naje asibiti ba na sha magani naji sauki ina magana da kyat cikin daure fuska. Shiga muje nace maki da sauri maryam ta riko min hannu ta nufi gefen mai zaman banza tana bude min motar tare da fadin sai kun dawo Allah ya sauwaka. Sai da na zauna da kyau ya tayar da motan muka hau dogon titin da zai kaimu cikin gari sai da mukai nisa kaina da duke na dafe goshina da hannu na daya naji yace. May damun ki ne haka ban bashi amsa ba sai gyara zama da nayi ina cije baki don dan motsawan da nayi maran yana min ciwo yanzu. May damun ki ya sake maimaitawa shiru nayi can nadan sauke nufashi nace da kyar banda lafiya ne kawai tare da dan dafe mara na. Au ko abin ne yazo maki na manta yanzu kike cikin time din period din ki ko hararan shi nayi tare da kawar da kai ina cewa a raina kaji min mutum da bin didigi haka ? Kwana nawa yakeyi halan sake dago kai nayi na kalle shi kamar bashi yake maganan ba nayi saurin kawar da kaina daga kallon shi. Yace bakiji bane kwana nawa kike dauka kina period din nace ya fada tare da dan kallo na nace ban sani ba kada ka wuce hurumin da ba naka ba mana na fada ina kwantar da kaina. Murmushi yayi yace haka kike ce ko nace na fada din ni banga dalilin tambayana haka ba kai ba likita ba wani sai nayi shiru. Yace go ahead you say your words out, shiru nayi tare da kawar da kaina gareshi gaba daya ya sake fadin you free to say komai zaki iya fada don ance fushi kike damu. Da sauri na jiyo ina kallon shi nace fushi fa akan may zanyi fushi daku in ba ina son sama kaina nauyin da bai hauni ba ? Murmushi yayi da sai ka saurara zakaji shi yace kwana biyu bamu kasan ne daga ni har Yusuf na fita da madam dina ne mun tafi check up ciki ke bata matsala. Don Allah malam ni ban tambaye ka ba in zaku iya ma ku tare a can ba damuwa na bane wanan ciki kuma Allah ya bata lafiya ya sauketa lafiya amma mi ya hadani da tafiyan ku kuma. Kwana yasha muka shiga wani clinic inda yasa na fito muka shiga guri ya sama min na zauna ya nufi gurin tankan kati ba mu dade ba duk da mun samu mutane a gurin yace in taso mushiga gurin likita. Mun shi likitan yare ne don turanci suke dashi sun gaisa naji likita na cewa kayi sabin aure ne ashe yace mashi eh yace madam ta kwana biyu bata shigo ciki ya zaunu ko yace eh a gadarance yake ma mashi magana yace ina son ka duba min ita tana fama da mesturalpain ne. Yace ayya sorry madam yakamata ace ya rage maki ciwo yanzu da kiyi aure ya kamata ace kin rage jinshi haka indan zakiyi period don agana kawai matsalan hakan. Nauyi kunya ya rufe ni a wurin na kasa daga kaina shima wayan shi yake dakila baibi ta kan likitan ba sai da likitan ya fara tambayana ina mashi bayanin ya dago yana kallo na. Tashi nayi zuwa inda likitan yace in kwanta ya dan dadana cikin nawa na dan sake kara daidai kasan mara na daya tausa da dan karfi yace in tashi ya dawo ya zauna yana rubutu a wani farin takarda ya mika mai lokacin na dawo na zauna dakyat dafe da marana dake min tsananin ciwo sosai. Bayan ya mika mai yayi mai bayanin anemi wanan maganin in sha zasuyi min allura kuma zan samu sauki da yardan Allah ya mika mai hannu tare da fada mai inda zamu kai takardan a duba ni. Sai da muka gama komai muka fito yana min sannu muka dauki hanya wani shago ya tsaya yace min yana zuwa ya shiga ciki yadan jima sai gashi ya fito yaron shagon na binshi a baya dauke da wasu manyan ledoji biyu a hannun shi. Ya saka bayan motar ya shiga muka tafi bayan ya mikawa yaron kudi yana mashi godiya kaina na duke yace sannu likita yace zaki samu sauki dan anjima kadan amma zaki barci sosai ki ci wani abu don kince baki karya ba. Bana jin shi do murdan da mara na keyi ina dan cije baki ina jijiga kafa na da matse hannaye na duk yadda na so in daure na kasa sai da na yi ya gani a bakin down hostel din mu ya tsaya da motar shi. Zaki kara kawar ki ta taimaka maki ne ko in taimaka maki ki fita duk da ciwon da nake ji sai dana harare shi na bude motan na fita ko godiya ban mashi ba. Ina fita yace turo min kawar ki ta daukan maki magani kai na iya dagawa na shige ciki na samu maryam na girki a dakina din bata da kiuyar girki ita tana gani na tace har kun dawo kaina gyada mata na fada saman katifa nace yana kiranki a waje. A saka hijab da sauri ta fita daga dakin zuwa wurin shi bata jima ba ta dawo dauke da ledojin nan da ya sayo tace yana maki sannu wai sai kunyi waya yace kici wani abu kafin ki kwanta. Itace ta zauna ta bude ledan kayan ciyeciye ne a cikin dana sha tarkace dai gasu nan sai dayan ledan dake dauke da pad din mata always kamar mai bude shago dashi ban san ranan da zai kare ba. Abinci ta debo min na dan ci kadan na kwanta sai barci mai nauyi ya dauke ni a gurin ban kara sanin inda nake ba kuma. Yana fita ya daga wayan shi six miscall ya gani na Nafisa da sauri ya danna wayan ya kirata yana fadin sorry ina wani abune yasa banga kiran ki ba. Tace Samad ina kaje wacece akace mi an ganku tare a asibitin doctor Bisi yanzu waka kai asibiti wata macs ce aka gan ku tare tare ta fada cikin tashin hankali. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU Bai iya bata amsa ba sai kokatin wuceta da yake yi ya karasa cikin dakin rigar shi ta riko ta baya da mamaki ya juyo yana kallon ta. Shi da magana take mai wuya ina shi ina tsayawa fada irin haka da mace sau da yawa nafisa takan tunkare shi da irin wanan fita tana kokarin kama mai kaya ko ta sha mai kwala sai dai bai biye mata sai dai ya shige ya kyale ta tayi ta masifanta har ta gaji. Inda ita kuma a nata ban garen take ganin tafi karfin shi ne, dan bai da yadda zaiyi da ita dole ya zauna da ita take gani yau da ta cakuma rigar shi ta baya tana kokarin kaimai duka ya juyo da sauri yana fadin Nafisa ki na da hankali kuwa ? Cikin shi tayi tana banda hankali sai ka fada min wacce aka ganka da ita a asibiti dazun hannu yasa ya banbare hannun ta da karfi ya jefar da ita gefen kujera. Zafin kishi sosai ya rufe mata ido nan ta fara ja mai Allah ya isa ya ci amanan ta ya cuce ta sai taga bayan ko wacece ke son mata katsalandan a rayuwan ta. Yan uwanta suna tsaye cirko cirko suna kallon ikon Allah sai yare ne ke tashi suna magana rai a bace suna nuna goyon bayan yar uwan su. Harara ya watsa masu sai suka fara sulalewa daga falon kowa yana barin gurin don yanayin kallon da yayi masu din . Sama ya hau a hankali inda yake tafiya yana jin sautin kukan Nafisa yana isa inda yake. Tsaye yake yana balle bottom din rigar shi a hankali sai dai zuciyar shi cike yake da mamakin waya gan shi ya fada ma Nafisa cewa ya ganshi tare da wata mace a asibitin doctor Bisi.Doctor Bisi ne ya fada a ranshi sai kuma yace No it can't be doctor bisi is a man he can do such full to me. Beside, ma nine na hadasu da doctor bisi din anan don bata san kowa ba a Abuja sai zuwan da yayi da ita ne tasan kan garin. Bayan wucewan mijin nata ciki ne ta watsa ma yan matan uku da suga rage a falon harara tace a cikin yaren su na buzaye. Simi simi suka mike suka bar gurin itama mikewa tayi ta bishi ciki su karasa a can sai dai ta samay shi har ya shiga wanka ko. Zama tayi a bakin gadon cike da masifa tana jiran fitowan shi daga wanka su aza a inda suka tsaya. Zancen malaman ta ne ya fado mata a rai da kyat ta yaki zuciyar ta ta dan sasauta zafin da take ji nashi koda ya fito anan ya samay ta zaune cikin masifa bai kula ta ba ya fara gyaran jikin shi kamar yadda ya saba yi idan ya fito daga wanka. Kallo daya yayi mata fuska a daure ya kawar da kan shi gare ta ta mike ta tako gare shi tace samad ka daina ganin laifina. Ni kadai ce macen da ta dace kai a duniya da ina da iko ko macen kudi ba zan bari ta sauka a akan ka ba balle macen mutum. Ta hade wani miyaun fitina da yazo mata a makoshi tare da fadin nasha alwashin duk macen da tayi gigin shiga gonar ka sai naga bayan ta a duniyan nan. Kallonta yake da mamakin abinda ta fada yaga kuma gaskiyar maganan nata har cikin kwayan idon ta da gaskiya take maganan. Kuma ko wacece wanan macen sai na tono ta a garin nan na nuna mata ruwa ba sa, an kwando bane. Juyawa tayi ta fita daga dakin a fusace bayan taja wani uban tsuki tare da rufo kofan da karfi, binta yayi da kallo bayan ta fita ya girgiza kan shi ya tabe bakin shi gami da daga kafadan shi yace mahaukaciyar banza kawai. Karasa shirin shi yayi ya fara gyara gadon shi don yana bukatan ya huta don ya gaji yau sosai ga maganan Nafisa da ke ci mashi rai kishi kamar wace bata da hankali. Gadon ya hau ya kwanta bayan ya gama gyara yana sauke ajiyan zuciya a hankali may Nafisa take nufi da kalamin ta na sai taga bayan khadija. Yasan zata iya abinda ta fada mashi a yanzu karfa ya ja ma yarinyar mutane matsala a rayuwan ta don bai san abinda Nafisa zata aikata mata ba. Tunane yayi kada ya sare Nafisa ta samu daman da zats yi mai abinda taga dama a rayuwan shi don haka zuciyar shi ta bashi shawaran gwada Sa,an shi akan khadija ko zai yi nasara akai. Bai koma ta kanta ba yadda ya saba binta yana bata hakkuri har sai yaga ta hakkura yake samun saida a ranshi wanan karon sai yaji ba zai iya tunkaranta ya bata hakuri ba akan kuskuren da take tuhumar shi da aikawa ba. Kamar yadda Nafisa itama a dakin ta take zaune abin duniya duk ya damay ta ji take tankar tayi hauka don bacin rai wai yau samad din tane yakai wata mace asibiti ba ita ba. Wai wacece wanan da samad har ya iya tunkara da sunan so may take dashi may take tunkaho dashi a duniya wanda ake cewa tafi ta komai. Zubur ta mike ta fara zagaya dakin duk da dan cikin ta dake mata motsi a lokacin bai sa ta damu ta tuna da yadda take kaunar cikin nan ba. Kishi ne zalla a rayuwan ta kawai so take tasan wacece wanan yarinyar don tasan ta inda zata iya fito mata da shirin ta. Tana yi nata kallon lokaci don tasan dole yazo gare ta idan ta yi mai irin wanan boren nata sai dai a yan watanin nan tana ganin abubuwa suna son sauya mata sallo ga aikin ta. Shiko Abdul a dakin shi yana kwance barci yaki zuwa mai a lokacin tunane kala kala yayi shi a wurin Yusuf ya kirashi yana tambayan shi ko yaji yaya jikin nawa don ya kira wayana yana a kashe. Yace ban kirata ba don likita yace zatayi barci sosai a idan maganin ya fara mata aiki a jiki wata kila ta samu barci ne ta kashe wayan. Nan yake labarta mashi yadda suka kwashe da Nafisa da ya dawo gida hankalin Yusuf ya tashi yace sai nake zaton doctor ne ya fada mata tunda kace baku hadu da kowa ba a gurin. Yace idan shine ya fada mata kuwa yayi kuskure don cikin shi tayi don zan can za wani likita ke nan yanzu. Yusuf yace baka tunanen kada Nafisa ta gano a inda khadija take tayi mata wani abin yace haka ma ba zai faru ba zanyi tunane mafita akan hakan. Sukai sallama bayan sun gama tataunawa ga maganan ya kashe wayan yana gyara kwanciyar shi a hankali. Bai dade da gama wayan ba yaji an turo kofan an shigo dakin yasan ita ce don ita kadai ce mai shigo mashi daki. Ta karo gaban gadon ciki da mamakin ganin shi a kwance da tayi cikin rashin damuwa da ita har ta iso a gadon ta zauna tana fadin nasan ba barci kakeyi ba. Ya dago ido ya dan kalle ta yace banyi barci ba kuma hutu nake so a yanzu ta gyara zama tana kallon shi tace samad cikin sanyayar murya. Wai may na rage ka dashi a duniya may ye wanda ban maka har kake kokarin hadani da wata mace a duniya bayan kasan irin son da nake maka ba na wasa bane. Ta kamo hannun shi tana fadin gaba daya ka canza min a yan watannin nan ko dan ka gani da ciki ne ka dauko yimin hakan. Ka hana mu kwanciyar hankali gaba daya a gidan nan sai faman takura min kake yi ko yaushe. Sai ga hawayen da yaki zubu mata a daki yazubo mata a lokacin tace ko wacece sai na kashe ta a garin nan idan na gane ta. Cike da jin haushinta yace ashe ko ke ma za a kashe ki ke nan kinga matsalar ki ko meyasa ne har kullun ke baki tunane a rayuwan ki sai bakin kishi . Ni ina kokarin ganin ko yaushe inga lafiyan ki ke ko sai wani banzan kishi ke a gaban ki ban tsamaci haka daga gare ki ba na dauka kece mutum ta farko da zata shedi rayuwana a idon jamma,a. Yarinyace na kadai ta zan dawo gida in dubaki dole na dauke ta na kai asibiti doctor Bisi ya dubata ashe yariyar bata da lafiya shine ya taimaka mata. A rashin wayo na Nafisa sai cewa tayi ashe wanan likitan munafuki ne shine ta kirani yana fada min wai yaga ka kawo amaryan ka asibitin shi yanzu. Kawai may yake nufi don ya hada mu fada yayi min wanan maganan ko may yace da yake ke baki da tunane sai ki biyewa zancen shi ko ? Ace kulun mutum ba zai saka ma zuciyar shi salama ba koda yaushe sai bakin kishi ke baki hangen nesa akan ki fa duk yan uwana suke fushi dani. Hakan bai maki dadi ba sai kin tayar min da hankali kuuma har na tunzura na aikata abinda ban tashi yi ba. Tace da sauri don Allah samad kayi hakuri sherin shedan ne wallahi dana doctor Bisi sai da ta san yadda ta bashi hakkuri har ya hakura suka koma dai dai suka sulhunta kan su. Bai fita ba sai washegari bayan ya gama abinda yakeyi ya fice a gidan kiran Auta tayi ta fada mata ta koma kusfa ta fada ma malamin ta ya duba mata idan akwai matsala. Sai da ya duba wasu file ya dan huta tare da kiran layina maryam ce ta dauki wayan tana fada mashi ina bandaki amma naji sauki. Bai kai ga magana ba tace gani nan ma na fito tana mika min wayan tayi tana fadin yaya Abdulsamad ne a layin. Karba nayi tare da kara wayan a kunne nace hello cikin murya kasa kasa yace yaya jikin naki nace da sauki baki je class ba ke nan nace sai anjima zan shiga. Kin karya ko nace yanzu zan karya dai to idan kin karya kisha maganin ki zan shigo idan na rage aiki zuwa yamma in dubaki. Nagode na tsunci kaina da fadi Allah ya sauwaka ya fadi yana kashe wayan maryam tana gefe tana sauraren mu bayan ya kashe wayan na zauna saman katifa tare da kaiwa kwance. Tashi kisha tea din kada yayi sanyi gashinan na hada maki yamutsa fuska nayi nace miko min in sha bakinane bana jin dadin shi har yanzu. Daure dai kisha ko kadan ne sai kisha maganin ki gashi ta mike tana dauko min ledan maganin dake aje a gafen kayana. Tea din nasha tare da hade magani na koma na dan kwanta wayan daddy ne ya sake shigo min yana tambaya na ko lafiya jiya tanemi wayana yaji ta a kashe. Daddy iam sick yace may ke damun ki khadija murmushi nayi nace naji sauki ai period time dinane yake damu na amma kin je asibiti yace ? Naje daddy wanan mutumin ya kaini asibiti jiya yace good zan buga inyi mashi godiya don kwana biyu bai kirani ba yace nace bai kasan ne daddy ya kara da Allah ya sawaka ki kula da kanki ki abinda kika je yi khadija insha Allahu daddy na gode ka gaida mama. Madam ranan a gidan Nafisa ta wuni sun kule a dakinta suna jiran kiran Auta daga zaria suji abinda malam zai fada masu. Madam ta kawar da shirun da cewa wai shi wanan mijin naki wani irin mutum ne da baijin magani haka sai anyi kamar an samu kanshi sai abu ya zo daga baya ya can baki daya. Tace shike damu na madam dubi irin kudin da nake zubawa akan bawan Allah nan sai naga nasara daga baya sai komai ya lalace. Komai zan iya yi akan Samad din in dsi zan samu ya kawar da ido akan ko wace mace a dunuyan nan. Madam tace idan shiya kawar da idon shi a kan mata su matan kina tsamani zasu kawar da ido su ne akan shi dole suma dole da tasu shirin da suke don suga sun kamo shi. Don shegen kyau da daukan hankalina da wanan mijin naki ga abinda mata keso a tare dashi kudi da kyawo da hali. Hankalin Nafisa ne ya tashi sosai da maganan madam tace wallahi da ina da hali da boye shi zan dinga yi a gida. Dariya madam tayi tace idan kika boye shi kuce may ke da yan uwan ki Nafisa karki matanta shine hannu da kafar ku kaf zurian ku. Yanzun dai zan tafi Ondo ance akwai wani boka acan may aiki kamar yanka yuka wata kawatace ta gano hakan. Nikan ina can na dan samu karfin jikina shiryawa nayi zan leka cikin makaranta don kada a wuce ni da karatu da nazo yi. Daddy ya kira Abdul yana mashi godiyan kaini asibitin dayayi yace ba komai insha Allahu zai kula dani kamar yadda zai kula da kaunar shi. Bayan ya gama abinda yake ya kira Yusuf don su leka wurina kafin yaje gida Yusuf din yabar abinda yakeyi yazo suka tafi. Sun samu na dawo ke nan ya kirani a waya na fito na samay su a waje lokacin da na karaso wurin su na samu suna magana suna kallon laptop din dake a saman kafan Abdul din nasan wani abu suke duba a ciki. Karasowana suka bar abinda sukeyi din tare da maida hankalin su a gareni Yusuf ke fadin lalai jiki yayi sauki kauna na sai dai har kin dan fada kadan wallahi. Murmushi nayi na dan jingina jikina ga motar su nace naji sauki sosai yusuf yace barin in dan je can inga shagon yan makaranta indawo ina son duba wani abu a gurin. Nasan yayi haka ne don ya bamu wuri mu gana dashi wuce wanshi yace dan gyara zama yana fadin abin ya daina zuba ke nan ko ? Harara na aika mai tare da fadin ban sani ba sai ka fito ka duba ai tunda kana son sani ne sai yau naga dariyan shi yace kin dai ji abinda likita ya fada saukin abin ai. Banji ba kuma bana son naji tunda ba kai ke da lalurar ba au yanzu tunda kinji sauki kina da bakin magana ashe jiya fa nan kike ta murdemurde ina tausaya maki. Kawar da kainayi gefe guda ban bashi amsa ba na share shi yace na tambaye ki jiya ciwo ya hana ki ban amsa na. Nace may ka tambaye ni jiya din yace kwana nawa kike dauka kina off shiru nayi tare da bashi ba a raina ina fadin wai shi baisan ina matukar jin kunyanshi bane da yasan abin dake damu na. Gashi kuma ya tsare ni da tambaya irin haka da zai sani jin kunya da nauyin shi ai wanan kamar kamar yar iska ya dauke ni. Niko gidan mu in badon ciwon mara ba har zanyi in gama basu sani ba ji nayi yace may nene abin jin kuya kibani amsa na kawai don ya kama ne in sani. Nace don Allah yaya Abdul ka daina wanan zancen naji yace na daina tunda baki son zancen yanzu. Badai kina shan maganin ki ba akai akai nace ina sha na gode daddy ma ya bugo waya nake fada mai ka kaini asibiti yace zai kiraka yayi ma godiya. Yace ya kirani ai dazun sai danace mai kaina nayiwa aiki ba sai ya godd min ba nace ka fada ma daddy hakan ? Yes ya dace ne in fada mai don lokaci yayi da zai fahinci hakan daga inda Yusuf yake tsaye yake kallon mu yana jin farin ciki a ranshi. Hikimar yin haka da yayi ke nan a gusa daga wurin don mu samu daman sakewa da junan mu don idan yana wurin komai bazai wakana ba a tsakani karshe ma muna iya yin abinda muka saba fada ke nan. Ka samu zuwa duban su Affan kuwa na kawar da zancen da wanan tambayan murmushi yayi yace ban samu komawa ba sai dai na fara shirin komawa. Sai dai wanan karon ban san wani shiri kikai ma tafiyan nawa ba idan zan koma nace dama idan zaka nike shirya maka tafiyan. Yanzu shirin ya dawo kan ki don haka kece mai shirya komai ta wanan bangaren ya kamata ace na fara maki albashi a wanan bangaren don kin ci hakan a gare ni . So ki fara shirya min nan da two weeks zan tafi ina jira inji shirin da kai ma tafiyan nawa da abubuwan da zan yi a can. Yusuf ne ya iso gurin yana fadin mu tafi ko kada lokaci ya kure maka anan tunda munga lafiyan kaunar tawa sauki ya samu. Har kagama duba shagon nace mai yace ko dai in koma ne kada in takura maku kuna hiran ku na jin dadi zan katse ku kai haba yayana wani hira kuma a haka ? Ni dai daukar shi ku tafi kada yar buzaye tace ina shigewa mijin ta yanzu Abdul yace kina tsoron ta ke nan ? Nayi saurin fadin tsoro fa tsoron mace yar uwana kuma macen ma kuma buzuwa da kyau kauna ta haka nake son naji mace jaruma wallahi. Kai kaji ya juya wurin Abdul din yana fuskantar shi tare da fadin na fada ma kauna ta jaruma ce ba irin ka ba mai tsoron buzaye yan haure. Idan bata tsoro ai sai mu gani a kasa ba cika baki a nan ba nace ko agaban ta wallahi zan cika baki idan ya kama in cika akan may zanji tsoronta ne wai ? Mace ce fa yar uwata kowa sai ya gwada sa an shi yayi mai fishe shi duk abinda take takama dashi wallahi ni khadija ina dashi fari kyau da tsayi kagako ba zanji wani shakkata ba. Irin kallon da yake jifana dashi daga cikin motar yasa nayi shiru dole don kallone da ke dauke da fassara irin mai nuna feeling ga mutum din nan. Mun gama shan matan juna suka ja motar su suka tafi ni kuma na koma ciki tare da tunanen da yawa a raina na canjin yanayin da na hango a kwayar idon shi. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABUKamar yadda yace nice mai tsara mashi tafiyan haka yasani a gaba dole sai dana tsara mashi zuwa gidan da zai yi da abinda zai kai gida. Da farko na dauka zolayane sai da naga abin nasa da gaske ne na tsaya na tsara da taimakon maryam nayi komai. Wanan karon bai sai kayan tsaraba ba kudi muka tsara zai bayar idan yaje sai abincin da zai sai ma iyayyen shi don rage ma mahaifin shi nauyi. Da yamma lis suka isa kaduna don haka ya wuce gidan shi bai shigo wurin su hajiya ba sai da safe bayan ya karya ya shiga gaida su. Sai da yagama gaida abokan zaman hajiya suka wuce nata part din dake daga can ciki yana fuskantar part din mommy. Sai dai tsakanin su akwai dan filin tsakar gida da shuke shuken filawoyi a gurin da wani babban icen ambrale dake basu innuwa a gidan. A kofa su kai sallama ta amsa masu daga ciki suka shigo ko ina na falon tsab yake sai kamshin turen wuta dake tashi a falon. Tana zaune tare da kannen shi Binta da zainab su uku a falon gaida shi kannen nasa keyi ya amsa masu a tsatsaye tare da zama saman center capet din falon shi da Yusuf. Gaida hajiyan sula farayi a cikin ladabi inda hajiyan ke nuna farin ciki da ganin su tare da fara,a a fuskanta. Tana man kamar yadda take a cikin gyaran ta ko yaushe atamphar super ne ja a jikin ta babu wani alamar tsufa ko girma a tare da ita hutu da jin dadin da mijin su ke basu ya kama ta. Cike da kula take amsa masu tare da tambayan da Nafisa suka zo ne Yusuf yace su kadai suka zo don Nafisa cikin ta ya fara girma yanzu. Tace cikin mamaki ciki ke ga Nafisan bamu sani ba mu tana kallon su cike da kulawa Yusuf yace wallahi hajiya ai cikin ma yanzu zai kai wata shida ko bakwai. Ikon Allah to Allah ya raba lafiya ashe da baka fada yanzu ba da sai dai muji haihuwa kawai. Yace ba akai ga haka ba ai hajiya zakuji ne don dai ba a tare ne Affan ne ya shigo falon bai mai da hankali shi wurin su ba sai fada ma hajiyan dayayi a jiki yana fadin wai yaji ciwo a waje. Tace baka ga Abban ku bane Affan daba gaida su ba yaron ya dan kara lafewa a jikin kakan nashi Yusuf yace malam Affan kuna lafiya ina daddy yake ? Hajiya ke fadin maza ka gaida Abban ka da baban ku daga jikin kakan yace ina wuni bazakaje kusa dasu ka gaida su ba in ji Binta dake dagawa daga inda take zaune zainab ko sai charting take a wayan ta. A dadare yaron ya isa gurin su yana kara gaida su Yusuf ya jawo yaron a jikinshi yana tambayan shi dan uwan shi yace yana gurin mommy su. Hajiya tace ai shi wanan dan lake ne tunda uwar tabar gidan ga ta koma gidan su kullun yana can like da ita. Da sauri Yusuf din yace hajiya Fati ta koma gida ne kuma tace to mu rike ta ne nan tunda abin yaki ci yaki karewa haka. Ai gara dai ta koma gida ko hankalinta zai kwanta a can anan taki ta sake sai rama da takeyi kullun Abdul ya mika hannu yana tambayan yaron labarin makaranta. Yayin da Yusuf da hajiya ke magana akan komawan fati din gidan su yace zamu lekata kagin mu koma abin ne sai an hada da hakkuri. Don Fati taki tayi hakkuri da yanayin Nafisa amma ai ita ta zabi ta zauna nan kaduna cewan ta hankalin ta yafi kwanciya da nan din. Wayan zainab dake gefe ne yayi kara ta dauka tana fadin Khadija Adamu wallahi nayi fushi dake ai tana mikewa ta shige dakin su. May wanan yarinyar ta bugo ta fada ma zainab yanzu ko dai komai da sanin su take aiwatar wa yace a zuciyar shi sai ga khadijan ta fito tana hajiya ga khadija na son gaida ke. Ta amshi wayan da faraa a fuskan ta muka fara gaiswa da ita ba wani dogon magana bane gaida ita kawai nayi tana sa min albarka. Ta mikama zainab wayan ta ta sake shigewa ciki shiru falon yayi sai hajiyan ne ke fadin yar albarka yariyar na da hankali sosai wallahi. Ta juya tana fadin yarinyar nan da nasa ku rage ma hanya wani lokaci da zaku koma abujane Yusuf yace oh khadija tana da kirki sosao wallahi. Ai nikan dan leka ta wani lokaci mu gaisa idan na samu lokaci tace ka kyauta haka ake son mutum ya zaba ma kanshi abu na gari. Yace hajiya babu komai a tsakanin na da ita wani dai ma yake raayin ta yanzu haka don yabawa da hankalin ta da yayi har lokacin hira yake da dan shi dabai sake jiki dashi ba. Ya dago kai yana fadin hajiya ko Abba ya fito yanzu mu gaisa dashi kafin ya fita tayi murmushi tace ai yanzu Alhaji ya rage fita kasuwa don yanayin girma da kuma jikin shi yana gida koda yaushe. Binta ta kwala wa kira tazo ta kira mata mommy a dakin ta don tai masu iso gurin Alhajin mommy ta shigo tare da Binta dataje kiran ta hajiya ke fadin dan ki zaki wa iso gurin Alhaji wai. Mommy tana murmushi tace kai hajiya sai kace wani bako a gidan Alhajin yana nan falo ya fito yanzu ma na baro wirin sa ta juya ta fita zuwa fada ma Alhajin zuwan su. Sai lokacin ya dubi hajiya yace wanan karon ban riko komai ba yana sa hannu a cikin aljihun shi yace ga dai kudi a kasa fa aba su mommy dubu daridari sai yaran nan a raba masu dari biyu ke kuma ki dauki sauran ya zube kudin a gefen mahaifiyar sai kuma abinci da anjima za a shigo dashi. Ta kasa boye farin cikin ta nan ta shiga saka mai albarka mommy ne ta dawo dakin tana fada masu su shiga yana jiran su har mommy ta juya hajiya tace . Mommu yara da alama adduan mu ya fara kana dan ki yanzu ga kudi ya kawo a raba ga kuma kayan abinci a tafe. Komawa mommy tayi dakin tana fadin kai madallah Allah mun gode maka da dan mu ya fara dawowa gare mu. Haka ake so wallahi amma da babangida kamar wanda baida kowa a duniya da gatan ka zaka bari shedan yana rudin ka. Ga dan uwaka nan Suraj sai shine ke bamu talafi bawai don bamu dashi ba don nemawa kansa albarkan mahaifa kawai don Allah aci gaba da kula da hakkin mahaifa dana. A da ya tsani mommy sosai don yana ganin nuna mashi kulawan da take kamar duk a munafunci ne sai yanzu yake fahintar halinta ne kawai a hakan ga yaran gida musanman na hajiyan su da takan nuna nata ne. Ita mommy Allah bai bata haihuwa da yawa a gidan ba daga Sadiq danta na fari sai salma kuma ba wasu manya bane sosai yanzu ma suke a secondary. Yace mommy in sha Allahu za a gyara kwanan nan ma zaki tafi abuja wurin mu don Nafisa ta kusa haihuwa ke nake son kije tare da iya na zaria ku zauna a gidan. Ba mommy ba har hajiya sai da tayi mamakin jin wai yau Abdul ne da kansa ke fadin wani nasa yaje gidan shi ya zauna don matar shi da zata haihu. Kirikiri a baya tace bai yarda kowa nasa yaje gidan shi ba don suna zuwa suna tayar kashi da hankali a gidan shi haka Nafisa ta fada mai a baya. Hajiyan su ce tace yar ikon naka tasan da haka kuwa yace haba hajiya sai ta san da hakan mahaifana da yan uwana zasu zo gidana. Idan na gama shiri zan aiko a dauke su yanzu idan na shiga gurin Abba zan sanar dashi bukatan hakan don ba zan so ta haihu babu wani dan uwana a kusa ba. Allah ya kaimu mommy tace da murnan ta fita daga dakin cikin farin cikin canjin da suka gani gareshi. Wayan shine yayi kara ya mike yana amsawa ya bar Yusuf a gurin hajiyan Yusuf yace hajiya muna bukatar adduan ki kamar kulun yanzu haka akwai yarinyar da Abdul ya fara so ina ganin zata iya zama da Nafisa. Duk wanan shiri nane don ba mace matsoraciya bane zata iya gwabzawa da halin nafisa ba don haka a tayamu da addua akan zancen in lokaci yayi nasan zakifi kowa farin ciki da zancen. Hajiya tace ashe ba batun mayar da Fati kuke yi ba ku wani tashin hankalin kuke shiri daukowa yace hajiya wanan shi kadai ne nake ganin mafita ga alamarin. Tace to shike nan addua dama kulun munayi Allah yasa hakan shine saukin abin amma dai wanan yarinyar ta cuta muna da yawa a rayuwan mu. Babu komai hajiya komai ya kusa zuwa karshe insha Allahu Allah yasa tace ya mike tana mashi godiya ya fita ya samu Abdul din a waje suka wuce wurin alhajin shi. Da sallama suka shiga dakin na Abba yana zaune saman kujera yana duba wayan shi ya dago kai yana amsa sallama tare da kallon su ta cikin farin glass din shi idon na medical. Kasa suka zube suna mika gaisuwa ga Abban girma da kuma ciwo ya ramar da Abban don mutum ne mai jiki a da yanzu ko girma da ciwo yasa duk ya zube. Sun gaisa sosai sabanin da da in yazo gaida Abban yake amsa mai a dadafe ba wani saki a fuskan shi. Ya aje wayan tare da mayar da hankalin shi gare su magana yake irin na dattako yana tambayan su yaya aiki da iyali suka amsa da lafiya kalau Abba Alhamdullahi. Kallon da yake masu ne yasa suka san da magana a bakin Abba din jikin Abdul yayi sanyi yana tunane a ran shi may kuma yayiwa Abba din yake mashi kallon tuhuma a yanzu. Yasan dai ba wuce maganar yar aminin shi ba da yake ganin yayi mata ba daidai ba shi dai Fati taja mashi kiyayya a gun mahaifan shi yanzu komai yake masu baya fari a gare su. Gyara zama yayi yana kallon Abba din don jin abinda zai fada masu Abba yace Yusuf zan iya cewa yanzu Alhamdullahi a yadda naga abokin ka yana waiwayan mu akai akai. Ko ba a fada ba alama ya nuna cewa yanzu ya fara samun kwanciyar hankali a tare dashi shidai Abdulsamad ya zuba ido yaji karasan magana shi. Abba yace ya na dade ina jiran wanan ranan tun ban mutu ba ranan da zaka gano gaskiya ka dawo a cikin hankalin ka irin haka. Wanda nasan ba yin kan ka bane don ba haka muka tarbiyarta da kai ba da farko don haka nake son ka kara natsu ka tsayar da ibadan ka duk wani abinda zakayi kada ka manta da yawan addua a tare da kai don shine jagoran rayuwa ko ba haka ba ya tambaye su. Lokaci guda suke kada ma Abban kai tare da fafin hakane Abba , murmushi Abban yayi masu yace to yanzu saura maganan iyalin ka zan so inga ka hada kan iyalin ka a wuri daya. Kamar yadda ka taso ka gani a gidan nan kasan hakan shine cikar kamalan ko wani magidanci aga yana ba ko wace mace hakkin ta daidai gwargwado. Suka ce hakane Abba, Abban ya dan tsura masu ido yayin da kanun su yake a kasa suna sauraren shi Abban yace kai kuma Yusuf na dawo gare ka mai kake jira har yanzu baka maye gurin matar ka da ta rasu ba shikenan kana nufin ba zaka sake aure ba a rayuwan ka ko may. Yusuf din ya dago da sauri yana fafin ba haka bane Abba zan sake insha Allahu da zaran an gama na Abdulsamad dake tafe. Au Abdul din aure zai karane kuma Abba ya tambaya sai Yusuf yayi kasa da kai yana fadin insha Allahu Abba basu gama daidaitawa bane da yarinyar shi yasa bamu gabatar maku ba tukun. To madalla ka nuna ka gado gida ke nan to yaya maganan Fati kuma fa may ake ciki game da alamarin ta ? Abba insha Allah zata koma daki ta ba da dadewan nan ba akwai abinda muke tsarawa a kai ne yanzu to Allah ya bada sa a sukace amin ya kara da fadin a kula da hakkin akai dai. Insha Allahu suka fadi suna mikewa ta ciro kudin da ya ware na Abba ya nufe shi yana aje mai a gefen kujeran da yake zaune a sama. Suna fita dakin Abba suka sallami mutanen gidan suka fice a gidan Abdul yace Yusuf yaya zakai min haka kace wa Abba wai aure zan kara kwanan nan ? Idan ba haka na fada mai ba kana ganin iya abinda zai fada muna ke nan a yadda yake kallon mu din nan shine kawai mafita ai kai kasan ba auren zaka kara yanzu. Bai yi magana ba ya bi bayan shi yana murmushi don yasan ya kulu dashi sosai da yamma motar kaya ya tsaya a kofan gidan Yusuf yasa akai ta shiga da kayan cikin gida. Kowa na gidan sai farin ciki duk da zaman kishi dole na ciki na ciki a ransu ganin sauyin da yayi hakan bai hana a kebe gefe ai gulma ba tsakanin ummi da anty Amarya. Nafisa da madam murnan tafiyan shi kaduna a satin sukayi don dama kafan zuwa ondo take nema don Abdulsamad ya hanata tafiya yanzu ko ina. Tafiya sukayi sosai tun suna na dadin rai har ta fara galabaita ga tafiya don dan karan nisan da garin ke da tsakanin shi da Abuja. Bata dauka nisan shi yakai haka ba sai da suka fara hanya duk wanan bakar wahalan bai sa ta janye kudirinta na zuwa wurin wanan bokan dataji ana yabon aikin sa ba. Ko da suka isa ondo da safe wani motar suka kara bi zuwa kauyen da bokan bayaeraben yake zaune sun isa a wahalce don har amai da zazzabi sai da tayi a hanya. Sun isa dajin mai kama da gari da baifi yan gidaje a kirga ba sai da suka huta kafin su samu ganin bokan don ranan suke son su koma Akure su shiga motan dare su koma abuja. Bayan ta gama fadin abinda take son yai mata nan boka ya fara surukule shi ya dago yana kallon ta na dan lokaci. Sai duk suka tsargu da irin kallon da yake masu wanda ke nuna akwai magana kai ya girgiza sanan yace aikin ta akwai dan wahala a cikin sa. Don yanzu haka mijin ta yana tare da wata yarinya sai dai bai hango soyayya tsakanin su ba amma akwai aure har da haihuwa a ciki. Kirjin ta ta doka tana fadin ta shiga uku ita samad zaiwa kishiya wacece zai aura har su haihu ? Sam ta mace da Fati ma mallakin mijin ta ne har da diya shi boka Allah bai bashi ikon tsafin shi ya hasko ni ba nan tasa ai mata aikin da za a raba tsakanin shi da ko wacece . Akuma fitar da ranshi ga ko wace mace a rayuwan shi sai ita kadai ya kara yin saddabarun shi na bokayen da suka gwane da tsafi yace ya ga wata mace sai dai baiga gaban ta sai bayan ta kamar tana son shiga rayuwar mijin ta amma dai bari ya mata aiki akan wace ta baiyana in yaso daga baya aikin da zaiyi zai gusar da waccan matar da yaga bayanta din. Tace tana son koda kashewa ne a kashe mata wace aka gani ko a haukatata gaba daya kowa ya huta. Yace an gama sai dai aikin ta na da tsada sosai tace kada yaji komai indai aikin zaiyi kyau nan ya shiga hada mata irin nashi surukulle da bayanun yadda zatai amfani dashi ba tare da kuskure ba. Yace ba mijin ta ba wata mace da zai duba a duniya muddin tayi abinda ya fada mata daidai suka kama hanya komawa gida bayan ta cika shi da kudi. Sam bata san Abdul kwana biyu zaiyi a kaduna ba lokacin da Abdul ya iso gida ya neme ta sai cewa sukayi ta tafi unguwane. Har ya shiga ya huta ya dan kwanta bata dawo ba ran shi ne ya baci sosai da ita yaji yana son fita don haka ya shirya ya fito dan yasan kafin ya dawo ta dawo gida a lokacin. Sai dai abinda ke bashi mamaki baifi ganin motocin shi duka dayayi ba a gidan yana tambayan kan shi da wace mota nafisa ta fita ? Yana fita batare da sanin inda zai tafi ba har ya yanke shawaran zuwa wurin Yusuf sai ya fasa don ya san yanzu shima hutawa yake a gidan shi kada yaje ya damay shi. Sai kawai ya yanke shawaran ya leka khadija don ya kwana biyu da ganin ta hanyar hostel din mu ya dauka sai da ya iso ya kira waya gashi abakin hostel. Nace da yamman nan yace na koma ne nace gani fitowa yaja iska ya kashe wayan na fito ina tako dadaya wanda ni ban san inayi ba ma. Na karaso wurin motar cikin yar murya na nace dashi sannu da zuwa baki maraba da zuwa na bane ko may ? Murmushi nayi tare da fadin naga baka fita a wanan lokacin ne kawai har ina da lokacin fitane na daban da ban sani ba yace shigo mota mana. Ina shiga sai kawai ya tayar da motar nace da sauri sata na zakayi ko may ? Bai bani amsa ba yaci gaba da kallon titi may zan sata anan, nace mutum, dariya yayi yace kan nan naki kuwa zaiyi kudi sosai nace ai kafin ka sai da nawa ka fara sayar da na buzuwar ka ita bakuwar haure, Kuff naji yake ma bakina dan bugu da sauri na dafe bakin nace saboda buzuwa ka dukar min baki ? Yace ban san hadinki da wanan buzuwar ba nace halinta halinta bai mun bane don tana da ji da kai da son wullakanta mutane. Ita abi kyama ba a kyamace ta ba sai itace zata kyamace mutane matar tawa ce abin kyama khadija ? Ba ita duk buzaye abin kyama ne gare mu yan Nigeria sai iri kune dake mai dasu mutane kawai baku kyaman su don su din ba abin yarda bane mazan su da matan su. Sai mutum ya yarda dasu daga baya su zo su yaudare shi yaudara a wurin su ba abin kunya bane don su din basu da kunya ko kadan. Shiru yayi yana tunane a ran shi bai bani amsan magana na ba nace kuma gasu da son raba mutum da yan uwan shi su cika gida da nasu yan uwan. Ga kazatar tsiya da son mamaye komai ya koma nasu su kadai koda kuwa sun samu wasu mata ne a gidan shiru nayi don na dauka bai saurare na a lokacin. Sai naji yace uhmm go on yaya kikai shiru ba labari kike bani ba nace au na dauka baka sauraro na ai gasu da dan banzan bin malamai da bokaye basu yarda da kowa ba sai kan su suna iya yiwa yan uwan su yankar baya su zauna da mijin yar uwar su. Zasu iya ketarowa da auren su suzo su auri wani anan alhalin duna da mazan da suka baro a gida sai lokaci lokaci suke lekasu. Kai bazaye muggan mutane ne sosai wallahi duk wayon ka zasu san yadda suka juya ka indai na miji ne ji nayi ya tsayar da motar da karfi yace bari inyi sallah please sai kici gaba da bani labarin ki. Fita yayi a motar ya nufi wani gu sai yanzu na duba naga ashe massalaci ne a wurin shiga yayi a ciki na mayar da kaina akan sit din motar ina kallon mutanen da ke gurin. Ya dan jima a ciki ya fito ya shiga motar ya kama hanya mun dan taba tafiya ba tare da nasan ida zamu nufa ba. Yace bissimila cigaba da labarin ki nace labarin yai ma dadi ke nan kwarai kuwa ina jin dadin labarin sosai nace toba zan kara fada ba. Don may ko don kar naji halin buzaye nace ba wanda baka sani ba a cikin wanan kai da ke da ita a gida may ya rage da baka sani ba. Ina ga saura bani kuddi baba ko a yaye ka kafa ka wayi gari ka samu ta ketara kasan su da dukiyar ka. Yace da taci rabon ta ashe idan ta iya ketara kasa da dukiyana duka eh tunda a banza kake samun kudin yace haka kike zato ashe ? Ni ba ragon namiji bane ko da yaushe ina tsaye da kafana wurin neman na kaina zaune a office din nace mai. Au haka kike dauka na ni ko a gidana nake ina neman na kai na nace gun buzuwa ke nan kai ya girgiza min. Koda yake dama abinda kuke nema a wurin su na daban ne da sauri ya juyo yace may muke nema a gun su nayi shiru tare da kawar da kai gefe. Fada min may muke name muka aure su nace su mana tunda irin su ne ku din jara, , , , shiru nayi karasa mana ina jin ki. Hannu yakai yana kamo min baki nayi saurin rike hannun nashi a karo na farko dana taba taba jikin shi da sauri na sake hannun nashi. Na kawar da kai na gefe hannun nashi ya duba a hankali sai naga ya sauke murmushi a fuskan shi yace how lucky you're ? Ke ce mace ta uku da na taba hada jiki da ita a duniya nace nima ina regreting din hakan da nayi wallahi. Shiru mukayi yaci gaba da tuki wani guri ya shiga da motar mai yawan ginene gine da sasa da yawa yace kin san wanan gurin tsoro ne ya kama ni dana kalli gurin sai na dauka ko hotel ne. Kai na girgiza alaman tsoro ya kamani sai naji yace nan ne ma,aikatar mu wanda daga MD din mu sai ni a gurin. Da sauri na kalle shi yace ko kina bukatan shiga kiga gurin da sauri na girgiza kaina nace a,a don Allah ka mayar dani hostel inda ka dauko ni. Ai bamu gama ba don baki ban amsata ba da sauri nace tamay yace irin mu da kika fara fadi baki karasa ba nace maganar yawuce ai. Yace a gunki ya wuce ni a wurina bai wuce ba sai naji karasan maganan ki ko mu kwana a nan da sauri na dago ina kallon shi don Allah dai kayi hakkuri ka mayar dani inda ka dauko. Maimakon yayi abinda na nace sai naga ya gyara set din motar ya kwantar dashi tare da sa hannayen shi yayi matashi dashi yakai kwance. Muna wurin shiru ba wanda yai magana a cikin mu sai tsukin da nake ja can yace a kasalance kada ki kara jamin tsuki a mota yanzu na fitar dake na wuce. Kayi hakkuri don Allah ka maidani hostel ina da exam next tomorrow ban son in fadi wani mutum ne ya dun faro inda muke yana haska toci a hannun shi. Ni dake zaune nake iya ganin mitumin dake tafe nace ga wani nan yana zuwa gurin nan fa bai damu da abinda nace ba yana kwance abinshi yadda yake. Har mutumin ya karaso ko ya sheda motar shine sai naga ya dan tsaya daga nesa damu yana fadin barka da dare yallabai an wuni lafiya cikin harshen turanci. Ya dago yana amsa mashi da lafiya kawai sai mutumin ya juya ya koma ciki ban san na firgice ba sai bayan wucewan mutumin yace lafiya kika shige min a jiki haka ? Ko kina son jin abinda buzuwa ke ji ne ajikina ta leke min da sauri nayi kokarin jaye jikina dana dan manna da nashi sai naji ya riko ni. Ta yadda har muke iyajin saukar numfashin junan mu a lokacin ka sake ni don Allah wai may kake nufi da nine haka wai ? Fada min amsan tambayana mubar aurin nan kada masu gadin nan su dauke ni dan iska nace sake ni in fada ma to yace sai kin fada jin irin rikon da yaimin yana kara manna ni a jikin shi nace jarabbabu irin su mana. Sake ni yayi ya daga bai ce komai ba ya tayar da motar muka bar gurin sai da naga mun hau titin da zai sada mu da hostel din mu hankalina ya kwanta dashi. Don yadda a lokaci daya naga canjin yanayi a gare shi ya firgitani ainun sai da muka dauki hanyar hostel din yace ki shirya shiga cikin jarababbun mutane daga yanzu. Ban iya magana ba bukata na shine inga kafata a kasa yanzu a wani shago ya tsaya ya shiga har ya dan dade sai gashi ya fito ina hangen shi tun daga nesa na raya a raina Allah yayi halitan namiji a nan . Baya ya bude aka saka mai kayan a ciki ya sallami yaron ya shiga muka tafi bakin hostel din mu ya tsaya bai bude motar ba niko a kage nake da in fita daga motar. Yace zan yi tafiya may yuyuwa baza mu hadu ba sai idan na dawo Allah ya tsare hanya nace dashi tare da kallon shi ya bude min motar. Kina level nawa yanzu a karatun ki nace two a takaice yace yayi nisa da yawa gaskiya nace ai ni ke yi ba wani ba ban ga amfanin karatun ba a guna amma ai naga su Binta da zainab sunayi suma ? Wanan matsalar su ne ni nawa matsalar na sani bata wani ba su ya shafa wanan bani ba amma kai mugu ne ko ? Zaki iya ba kan ki amsa idan kin so ko wani kalar nake ya bude min motar tare da miko min ledojin dake bayan motar ina karba na fice ina fadin mugu kawai da karfi. Girgiza kan shi yayi ya tayar da motar ya tafi sai da ya fara tafiyane tunanen Nafisa ya zo mashi a rai yana tunanen ko ina taje dazun ya dawo bai samay ta a gida ba. Ya iso gidan ya shiga a falo ya samu su Hadiye zaine suna hira suna ciye ciye gaishe suke da dawowa yace Nafisa ta dawo sukace bata dawo ba ya shige ya barsu a gurin zaune. Ya shiga ran shi a bace ya dubi lokaci yaga tara da wani abu na dare goma saura kadan wanka ya shiga yana tunanen Nafisa a ranshi har ya fito ya kwanta shiru ba Nafisa. Ni na fado mashi a rai jarababu irin ku murmushi ya danyi yana rufe idon shi kamshin turen oud dina yake tunowa daya shaka. Ya lumshe idon shi tare da gyara kwanciyar shi yana lumshe ido yaji dadin kasancewa mu a tare yau hiran da nake mai na buzaye ne ya dawo mashi a rai. Ba abinda na raga daga halin da yasan Nafisa dashi zai iya cewa kila wani ya fada min kadan daga cikin halinta daya fahinta. Sai dai abinda ya tuno inda nace suna barin mazan su a gida su zo duniya su auri wani mijin na daban sunayi suna zuwa ziyarar mazan nasu. May wanan maganan yake nufi kodai shiyasa Nafisa take yawan ziyaran gida akai akai bai sani ba da sauri ya kawar da wanan zancen kada zargi abinda bashi ba yashiga zuciyar shi. To wai ma ina Nafisa taje ne uban may tafitayi da tun safe har wanan lokacin bai ta dawo ba yaja tsuki yace zan gwada ma Nafisa matsayin ta na mace a gidan nan. Goma, sha daya shabiyu saura ya mike zubur hankali a tashe ya mike yana zura riga a jikin shi ya sauko zuwa kasa komai na falon a kashe yake . Su hadiye sun shige dakunan kwanan su kayan da sukaci abinci gurin babu kowa a wurin tsuki yaja ya fita waje ya nufi gurin maigadi yana tambayan shi ko yaushe nafisa tafita a gidan. Maigadi yace rabon shi da ita tun shekarajiya da kawar ta tazo suka fita komawa yayi ciki yana tunanen tun shekaran jiya da kenan Nafisa dama bata gidan tun lokacin da shima yayi tafiya ko may ? Kamar zai tayar dasu hadiye ya tambaye su sai kuma ya fasa ya koma ya kwanta suna barin mazan su a gida su je wani guri su kara aure suna yi suna ziyarar su. Abinda ya fado mashi a rai ke nan karfe daya agogon da ya kalla ya nuna mai da sauri ya mike zaune biyu saura na dare yaji ana buga gidan maigadi ya bude kofa motar ta shigo sai ganin nafisa yayi ta fito daga motar ta dan tsaya suna magana da ta cikin motan. Ta shigo gidan a gajiye take kafafuwan ta har sun dan kunbura saboda zaman motan da tayi mai tsawo dakin su hadiye ta fara zuwa. Ta samu suna barcin su hankali kwance ta ta da ita a cikin magagin barci tace kin dawo da yare tace na dawo bata gane komai a guta ba ta juya zata shige tace Alhaji ma ya dawo dazu da safe. Dam taji gaban ta ya fadi da sauri ta fita zuwa dakinta ta kayan sihirin da ta dawo take kokari boyewa a wardrobe din ta sai taga an kuna wutan dakin ta. A fusace ta juyo sai ganin Abdulsamad tayi tsaye yana kallon ta da sauri ta kara gare shi sai yayi saurin juyawa ya fice daga dakin . Boye kayan ta karasa yi ta rufa mai baya ta murda kofan dakin a rufe taji shi gam ta juya zuwa dakin ta ciki da fargaba da tsoro a ranta. Washe gari ta samay alokacin ya gama shiri zai fita yana daura agogo a hannun shi yana gani ta ya daure fuska tankar bai taba dariya ba a rayuwan shi. Rudewa tayi tama rasa may ta fada mashi can dai tace Samad kayi hakkuri na san ban kyauta ba na fita ba da sani ka ba. Jakar laptop din shi ya dauka zai wuce ta zube kasa gaban shi tana fadi ka yafe min gurin buki naje shine naka wanan lokacin ban dawo ba. Nasan nayi laifi fita in dade baka nan amma kayi hakkuri haka ba zai sake faruwa ba insha Allahu. Yace don gani saunar na miji ki fita gida na kwana da kwanaki yanzu kizo kice inyi hakkuri haka kai tsaye bayan kin gama yawon gantalin ki a can. Kin kwaso kafan ki kin dawo min gida ki koma inda kika fito zai fi maki sauki na baki minti awa daya ki fice a gidan nan da kowa naki. Samad kayi hakkuri ka yafe min ba zan sake ba yace rufa min baki munafuka wace bata san ciwon kan ta da darajan aure. Ya sure jakkar shi ya fice a dakin da kyat ta iya mikewa tsaye daidai lokacin ya dawo yana fadin fita min daga daki zan rufe abina ne . Ta bishi da kallon mamaki a kofan tana tsaye ya rufo dakin shi karo na farko a gidan abin ya mata zafi saidai cikin ranta tana fadin yi abin ka a hannu na zaka dawo kwanan nan. Ya fice ta bishi da kallo tare da juyawa ta wuce zuwa dakin ta tana mai jin haushin shi. Kutayani da addua yan uwa ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABUTunda ya je office ya kasa aiwata komai a office din ga Yusuf bai shigo ba har lokacin ranshi ke kara baci idan ya tuna da kalaman nan daya dana fada shi yafi bata mashi rai ko yaushe. Shigowan Yusuf office din tun daga nesa ya karanta zuciyar abokin nashi ya karaso gaban tebur din shi yana fadin wani abu ya faru ne na ganka haka. Tsuki yaja tare da juya kujeran da yake zaune sama yace may ye ma bai faru ba Yusuf wai kasan matar nan bata gida tun ranan da muka tafi kaduna. Ba ita ta dawo ba sai karfe biyu da wani abu ta shigo gida jiya da sauri Yusuf yace ina taje haka ko da sanin ka ta tafi yace idan na sani abin zai damay ni haka ne ? Kai wai may yasa wasu matan samun wuri ke sa su wuce limit din su ne na mata akan may mace mai ciki zatayi irin wanan tafiya haka ba tare da sanin mijin ta ba. Bata tsoron wani abu yaje ya samay ta a can yace ma Yusuf ni ba wanan ne damuwa na ba damuwa na shine ina taje ? Jiya jiyan nan Khadija taban wani mugun labari wai buzaye sukan baro mazan su na gado su shigo nan suyi auren bugi don kudi ni wanan abin shi abinda ya tsaya min a rai na. Ita Khadija ta fada ma hakana sosai kuwa jiya muna tare da ita tana zayano min halin buzaye sai naga babu abinda ta rage daga cikin halin Nafisa har ma da wasu da ban sani ba takara min haske akai. Lalai Khadija jarumar gaske ce tunda har ta tsaya ta iya fahintar dakai wanan abin yace ka san hauka irin nata ita bata dauka maganan ai zaiyi tasiri a raina ba haka. Yanzu fa har na fara zargin yawan tafiyan Nafisa kasan su akai akai da takeyi tunda gashi har yakai ta fara satan tafiya haka. Da fa shi yayi yace kada ka zargeta da wanan don ta fadi haka ba lallai ne haka ya zamo gaskiya ba akan Nafisa din sai dai idan wasu sun su suna yin hakan bance a a ba don son kudin su yayi yawa. Kai ina bazan yar da ba Yusuf ko na yarda da komai ba zan yarda da wanan gantalin da Nafisa ta dauko yi ba dole ne in dauki mataki a kai. Tunda ta fara haka maganin abin kawai ya kamata kayi don tana ganin ita kadai ke gare ka yasa take abinda taga dama a gidan. Yanzu zabi biyu shine nake ganin mafita a gare ka na farko walau Fati ta dawo ko nabiyu ka kara aure don ganin da takeyi ita kadai ce yasa take wa yan nan abubuwa haka. Ido ta kura wa Yusuf dake magana sai da yayi shiru yace Fati ita ta kasa zama saboda rashin hakkurin ta. Kai ya girgiza mashi yace ka daina fadin Fati bata da hakkuri halin Nafisa dai ya kori Fati gidan ka wanda a lokacin baka ganin haka kai. Zaka iya bata wani daman a yanzu ko abin zai gyaru a tsakanin ku amma fa sai ka jajirce wa hakan kafin komai ya zama dai dai don Nafisa shuumace ta kwarai. Ba zata taba bari kuyi zaman lafiya da Fati kawai a gidan ka dole sai da wace mace a tsakani mai kwato mata nata hakkin idan kun cuta mata. Bai iya magana ba sai jawo file din gaban shi yayi ya fara aiki ba tare da ya san abinda yake yi ba. Fita yayi ya bar mashi office don yasan halin tunda yayi haka ba amsan maganan shi zai samu ba a lokacin. Ya kai wani lokaci yana aikin da zuciyar shi raki sakewa don haka ya rufe files din ya mike tare da nufar hanyar fita office din. Gida ya nufa kai tsaye lokacin sha biyu da wani abu na rana tun daga kofa yake jin tashin sautin wakan yan yaren su cikin harshen buzaci ya karade gidan. Bai ko kali gefen da suke zaune ba ya hau sama ya shige dakin shi tare da rufo kofan da karfi zuwa yanzu sun fara isan shi a gida. Mutane haka ba kimsi ko kadan sai bakin ci da ihu yau ma don samun wuri kidan suka sake mai haka a gida anya ma suna wani cikaken ibada kuwa tunanen da yake kenan Nafisa ta turo kofan dakin ta shigo. Sau daya ya kalle ta ya kawar da kanshi gare ta ta karaso kusa dashi da shi ra tsaya cikin murya da maida hankali gare shi tace lafiya yau kadawo a wanan lokacin haka ? Kallon ta yayi ya kawar da kan shi gefe daya ta sake cewa magana fa nake maka wai may ke damun ka ne haka ? Ya dago ido ya sake kallon ta da idanun shi da sukayi jawur yace ban son damuwa a wanan lokacin tace haba mai gida ai wanda duk ya ganka a wanan lokacin yasan akwai damuwa a tare da kai. Matsalar ki ce ta isheni Nafisa in ma ina da damuwa bai wuce halin ki ba tace halina na kamar yaya wani abin nayi maka ko may ? Au baki ma san abin da kikai min ba ke nan kike nufi tace don kawai na fita na dade shine zai zama matsala haka ? Fita nayi kuma gani na dawo lafiya sai may da zaka dauki wanan a babban matsala kuma ko nace ka barni in fita na san ba barina zakayi ba inje inyi lalurar gabana. Ina kika je har kwana biyu baki gidan nan tayi shiru tana tunanen karyan da zata yi mashi ya yarda da ita a lokacin. Ya sake tambayan ta sai tace na tafi bukin kawata ce da ta haihu a jos don ko na fada ma ba zaka yarda in tafi ba. Duban ta yayi cike da zargin ta sannan yace wata kawa kike da ita haka a jos da ban santa ba har zaki iya zuwa ki kwana biyu a bukin ta ? Ta dan zaro idanu tace dole ne sai ka san kawaye na duka wai yace da kyau Nafisa wanan halin da kika dauko a yanzu sam ba zan dauke su ba . Tunda har kika iya tafiya na kwanaki don kawai bukin wata kawa taki buki nawa akayi a gidan mu sau nawa kika taba zuwa? Sam yanzu zuciya ta ta soma zargin ki da aikata wani abu akaina da ba daidai ba sakamakin hurda da matan barikin da kike a yanzu. Zargina ka fara ne Samad akan may ba zan rage ki ba halayen ki gaba daya yanzu sun gundureni baki zama gida ba yar aiki ba ba wata yar kasuwa ba amma ke kenan kulun yawo fita. Gaba daya kin shiga rayuwana kin hana min farin ciki kin hana mata na ta zauna dakinta ke kuma ba kula nake samu a gurin ki ba. Au matar ka kace kace dama matar ka kake son ta dawo kawai kake wanan kamay kamay haka idan zata dawo zaki hana ne ko may ? , Ta dube shi a hasale to ta dawo din mu gani mana sai may yadda ta dawo haka zata koma da kafan ta. Yace haka kika ce tace na fada sai may ? Baya ya bata batare da ya kara juyawa kanta ba ta tsaya tana ta jidali wai ai dama ta sani zuwa kadunan da yakeyi yanzu saboda fati yake zuwa da yaran shi. Mamaki yayi sosai da ta iya karfin halin furta hakan lallai yasan ya cuci Fati da yawa ita da tazo daga baya ta iya fadan haka ? Ina ga Fatin da zaman gidan ya gagare ta da yaranta dole suka bar mata gidan har diyan shi ita ko tana zaune yan uwan ta da yarta a cikin salama. Lalai ya tabka babban kuskure a rayuwan shi dole kowa nashi ya tsane shi yanzu don sam shi bai taba hango wanan abin ba sai yanzu da taimakon Yusuf da khadija suka ganar dashi gaskiyar hakan. Ido ya rufe kamar yana barci don bai son hayaniya ko kadan gashi ya jawowa kanshi yar hayaniya a rayuwan shi bai taba nadamar auren nafisa ba sai wanan karo. Mikewa yayi ya shiga ban daki ya dauro alwala yazo ya tayar da sallah azahar ya gama ya dade zaune a gurin anan wayan Yusuf ya shigo mai yana tambayan shi yana ina ne ? Yace gida sai ya kashe wayan yasan damuwa ce taimai yawa yasa ya koma gida yasan ko a gidan ba wani sauki zai samu ba, don ko yasan Nafisa ba zata kyale shi ba. Sai dayayi sallah karfe hudu ya fito daga gidan kai tsaye ya yanke shawaran zuwa guri na don irin shammatan junan da mukeyi yana sashi nishadi a ranshi haka yasa ya nufi inda nake. Bai faye son zuwa wurina tare da Yusuf ba yanzu don idan sunje tare hiran kan koma tsakani na da Yusuf ne don bai iya sake jiki yayi komai a gaban Yusuf di yanda ya samu dama a zuwan karshe. Ya iso bakin hostel din sai da ya kare ma gurin kallon yadda mutane suke ta faman shige da fice ya daga waya ya kirani kamar kullun gani kofan hostel din ku yace ya kashe wayan. Muna zaune girki na gama muna muna ci kiran shi ya shigo min kalon maryam nayi nace wai may wanan mutumin ke nufi ne maryam jiya fa ce min yayi zai yi tafiya ba zamu sake haduwa sai ya dawo yanzun kuma may zo nema nan ? Dariya tayi tace ke mana don Allah tashi kije kada ki bata mai lokaci dan hararan ta nayi nace na kirashi ne ? Sai da na tsaya shirya nasa wasu material a jikina din kin buje da riga akai min wani zuwa kaduna da nayi maron colour dinkin yadan matse min jiki kadan don dan jikin dana kara yanzu. Sun kama min jiki tam sai kitson da mukayi satin nan na ghana wiving ya kara fito min da fuskana shar ga matsiyacin kamshin dake tashi a jikina wanda ke tafiya da imanin wanda ya shaka. Tun daga nisa ya zuba min ido yana karewa shiga na kallo har na karaso inda yake kofan motar ya bude min wai nashiga. Naki nace cikin girgiza mashi kaina yace common shigo don Allah mu tafi rakiya zaki min wani guri da sauri nace a hakan zan tafi wani gu. Ko banza kuma ba zan shiga motar ka ba again agogon hannun shi ya duba yace cikin dakewa kina bata min lokaci ki shiga mutafi. Tunda muka fara tafiya ba wanda yai magana a motar sai shi dake tuki a hankali cikin wani irin yana yi yana yi yana wani furzo iska daga bskin shi lokaci lokaci. Sai can ya juyo inda nake yace zakici wani abune kaina yana a waya na da sauri na dago kai nace wani sai kuma ja girgiza mashi kai nace ni a koshe nake. Ok rakani inci wani abu tun safe banci abinci ba da sauri na zaro ido nace azumi kayi ne ? Dashi nayi ma da zai fi min sauki yace ba tare da ya dube ni ba na mayar da kaina ga titi ina kallo sai kuma can kamar an tsunkule nace matar ka tayi tafiya ne ? Bai bani amsa ba sai karya kan motar shi da yayi zuwa wani restaurant din abinci mai kyau gurin da daukan ido ya parke a wurin . Mun shiga naga tsarin wurin yana da kyau sosai da alama yasan wurin da kyau don wani ke bebben wuri naga yana nufa a cikin wurin. Min zauna masu aiki gurin suka zo suna tambayan shi mai za a kawo muna ne yace ferfesu kawai zai sha bayan an mika mai dan takarda ya duba. Koda aka kawo mai bai wani sha da yawa ba naka ya aje cibin yana goge bakin shi tare da fadin tashi muje kawai nikan mike wa nayi nabi bayan shi. Sai da ya biya su kudin su muka fice muka bar gurin ina mamaki a raina nace yaya mutum kamar shi baici komai ba sai a wurin cin abinci zaici kuma bai tsaya yaci wani abin kirki ba. Kasa hakkuri nayi nace amma wanan ba girman ka bane cin abinci a waje alhali kana da iya li kuma a gari. Kamar bai jini ba yana tukin shi sai dai ban san ida muka nufa ba can naji yace dani yaya kike son inyi khadija in banci abinci a waje ba ? Kamar yaya kuma kana da mata a gida zaka ce haka yaya Abdul yace sunana Abdulsamad ko ke ma zaki bata min suna ne ? Yi hakkuri bani na kashe karen ba ratayan buzu ba zai zama nawa ba in bai zama naki ba wace ki dauki karen ? Naci yau kana da magana ke nan yace da yawa khadija iam not in good mood at all. Ayyah sorry Allah ya sauwa koma maye yayi maka mafita a kan shi yace amin na gode da adduan ki gare ni yaci gaba da tuki. Matsala a gun aiki ne ya taso maka yace matsala a gida na yake subbahanallahi nace dashi tare da dan kallon fuskan shi. Yace khadija dole in ci abinci a waje ko in zauna da yunwa ko zaki taimaka ki dinga bani abinci in dinga zuwa wurin ki ina ci idan na taso office. Kai don Allah ka daina zolaya abincin yan makaranta ne zakaci wanan ai sai mu da yazama muna dole muci shi. Badai ke kina ci ba nace sosai kuwa yace to ni mai zai hana inci tunda ke kika iyaci sai dai idan rowa zaki min kuma beside ke kika ce na daina cin abincin waje. Nace matar da ran ta da lafiyan ta zaka wai ni na dinga dafa ma abinci kamar wata wacce ka aje da zaman banza. Bai kara magana ba sai horn da yayi a bakin wani gida aka bude mai muka shiga dayan motar da suke zuwa wuri na da farko ne na gani a gidan. Maigidan na ciki ya tambayi mai gadi ya na gaishe shi bai amsa ba ya jefa mai tambayan shi sai maigadin yace yana nan bai dade da shigowa gidan ba. Fita yayi daga motan ya zagayo ya bude bangare da nake zaune jin ya tambayi mai gidan yasa banji wani tsoron shiga gidan ba. Sanyin A C ne ya tari fuskana da kamshin air freshner da falon ya dauka falon ya tsaru komai akwai a ciki ga wasu manyan kujeru da aka kawata falon dasu. Yana waya koda muke shiga gidan yana fadin kafito gamu a falon gidan ka yace a wayan baifi second ba naji ana bude kofan daga cikin gidan sai ganin Yusuf ya fito yana saye da kayan shan iska irin ta maza wando dogo tare da yar riga armless a jikin shi. Yana gani na ya bude baki da mamaki yace kace yau ina da babban bakuwa a gidana ina kafito da yar mama da yamman nan haka ? Ya nuna mun kujera da hannu yace bissimillah zauna mana khadija bamu hadu ba sai yau nace ina wuni ya amsa da lafiya kalau ya kike ? Ina nan lafiya yace Alhamdullahi yau sai gaki a gida na kwatsam na gan ki ba tsammani nace wallahi ga wanda ya dauko ni nan bai fada min ida zamu zo ba yace dai wani guri zan raka shi. Yayi maki wayan manya kenan don ya baki mamaki dan hararan gefen da yake nayi mikewa Yusuf yayi yana fadin barin kawo maku abinsha sai dai kiyi hakkuri kin san gidan gwauro kika zo. Da sauri na dago kai ina kallon shi da mamaki nace baka da aure ne dama yace eh baki sani bane yar mama ? Ashe mutumin bai fada maki komai game da ni ba yace ma Yusuf din an fada ma kowa irin ka ne mai zuba a lokaci guda. Yusuf yana dariya ya wuce inda fridge din shi yake ya dauko drink a ciki tare da kofuna ya kawo gaban mu ya aje nidai ido nake binsu dashi kawai. Ya aje tare da zama yana fadin bissimillah kusha lemon shi yasha nin ban sha ba gani nake kamar plain ne suke shirya min in fada ciki. Yayi yayi dani don insha nace wallahi na gode mai zai sa ka damu haka idan bata sha ba yace mai kasan bakuwa tace ita dole in damu idan tazo gida na bataci wani abu ba. Daukan cup nayi na tsiyayya kadan na dan kurba na aje cup din ina fadin na gode shima tunda ya kurba sau biyu ya koma ya jingina da kujera tare da dafe kanshi da hannun shi . Yaya dai Abdulsamad lafiya ko dan tsuki yaja tare da kara dafe kan nashi fuskan shi ya nuna alamun bacin rai da damuwa. Juyawa yayi guri na yana fadin may ke faruwa ne khadija nace nima haka naganshi wallahi ko maganan da nayi mai ne yasa shi bacin rai ban sani ba ? Ni kuma gaskiya na fada mai ba girman shi bane cin abinci a waje ban san ranshi zai baci da kalamina ba na fada mai haka. Dariya ya dan yi tare da fadin see you akan dan wanan maganan zan bata raina ai gaskiya kika fada bai dace ba nima na san da hakan. Watau khadija mutumin naki yana da matsala ne a gidan shi wallahi wana abin ya dade yana damun mu muma. Ace mutum kamar wanan ba abinda ya nema ya rasa a duniya amma cin abincin gidan shi ya gagare shi sai na waje ? Shiru nayi ina kallon shi yace ya zama dole mu samu mafita akan wanan matsala kada abin yazo yai yawa na yaushe kuma ? Ko sau daya aka ganka a waje kana magidanci kana cin abincin sayarwa ai girma ya fadi ko a wurin mutane sai dai a gyara don gaba. Yarinya kamar tsuhuwa wurin iya tsara magana haka ashe shiya take karatun lauya ya fada a ranshi. Khadija ni na rasa samun mafita ka wanan matsalar wallahi don ko nafisa ba gyarawa zatayi ba tunda in ita batayi ba bata bari kuma ya dauko yar aiki irin namu na nan wace ta iya saidai yan uwan ta zasuyi. Wanan kuma shi ya daukar mata don shi yaga zai iya zama a haka don may ba zai dawo da matar shi hala tsoron ta yake yi ? Sai lokacin ya cire hannun shi da ke saman kanshi yace tsoro tsoron wa nace ka alamu nan sun nuna kuwa buzuwa ta shiga gaban ka. Ke fa baki da kunya din kikan wuce limit din ki nayi saurin fadin wurin fadin gaskiya ba haka nan Ya Amina na ke fada min wai banda tsoron fadin magana ga kowa. Ni kuma naga idan gaskiya tazo a fadeta komai dacin ta kuwa dayake baki da kunya ba zaki iya fadin maganan da wani bai iya fadi ai . Ciki ciki nace a nan zaka zare idanu agida ko a zare maka idanu matsorancin banza kawai. Ban yi aune ba na gan shi a gaba na waye matsoraci yace cikin zare min idanu Yusuf nace ni gaskiya na fada ai Yusuf ne yace daga fadin gaskiya sai leifi ? Laifin ka ne mana kaima ka sani ai in ba tsoro ba ka dauki mataki mana a kan haka mugani nace aishi na gani walla, , , Hannu shi yake ya kamo bakina yana fafin wanan wanan baki sai nayi maganin shi wataran zai shiga hankalin shi. Don Allah ka bari bana son namiji yana taba min jiki wallahi kin dauke ni dan iska ke nan ashe nace bai da kyau yin haka ka sani. Yusuf yana dariya yace ina zuwa ya barmu a gurin zama yayi a kusa dani yana fadin bari ma yau in nuna maki dan iskan nake. Tsoro ne ya kamani yadda ya zauna a kusa dani din nace may ye haka malam ? Malama iskancin nake son nuna maki kalan tawa ki gani ya rankwafo inda fuskana yake har muna iya jin hucin numfashin juna a lokacin. Cikin sanyi murya nace ka dai san hakan bai dace ba a addinance ai kin san ban san addini ba ni yace wanan ba gaskiya bane don gidan ku kaf hazifai ne kuna karatun addini tun kuna kanana . Sai naga ya maida kanshi saman kujera yana zaune kamar yadda yake bai daga kusa dani ba yace khadija ina cikin matsala wallahi ina son in gyagyara wasu abubuwan da suka baci min a yanzu. But i don't know how to make things easy ? Tausayi ya bani nace ka yawai ta addua da sadaka ga dukan al,umurorin ka sai kaga Allah ya kawo maka mafita a ciki. Sai ya mike daga hannun kujeran yana fadi n muje in mayar dake yamma ya fara yanzu saurin mike wa nayi ya kira yusuf a waya yana fadin mun tafi. Yafito da sauri tare da fadin har kun gama hiran ta masoyana zaku tafi kai haba yayana firan masoya kuma a haka ? Har ya fara tafiya shi muka mara mai baya yusuf ya bani hakkuri akan bai bani komai ba gashi na kawo mai ziyara. Ba koma nace muka kama hanya na tsaye sai da yaga wucewar mune ya sauke murmushi tare da fadin ikon Allah komai yana da sanadin shi. Wanan karamar yarinya kuma Allah ya jefo a rayuwan Abdulsamad mutumin da magana da mace a wurin shi aiki ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABUYau take son ta gwada abubuwan da aikin boka dan Ondo wanda ya ja mata kunne da gujewa aikata kuskure tace zata tsare in sha Allahu. Ya shigo bai jima da dawowa ba ya fada wanka Nafisa ta shigo dakon kai tsaye tasamu yana ban dakin gurin wanka nan ta zauna a bakin gadon cike da jiran mijin nata. Ya fito daga ban dakin ta taso ta karbi duk wani abinda yake ma jikin shi tana mai gama daga goge jiki da shafan mai da saka turare da sauran su. Shidai ido kawai ya saka ma ta yaga iya gudunta don zuwa yanzu ya fara gano shirin ta sam bai yarda da wanan abinda take mashi ba . Ya gane sai tana son abu take mashi ladabin shegu a lokacin yake miji da zaran ta samu abinda take so shike nan ta koma ma halinta na I don't care da ta saba dashi. Zama yayi a bakin gado yana jiran yaji ta inda zata bullo mashi ta dan yi dariya tare da karasowa wurin shi ta zauna itama. Sai bayan ta zauna ne tace samad a ranshi yace nasan da wanan kan tace wai yaushe ne zamu tafi shopping ga ciki ya fara girma haka ? Yayi mata kyar da ido sai kuma ya sake guntun murmushi a fuskan shi yace ban san da wanan maganan ba ai. Ita ko tayine don tana ganin shi ne zai fi saka shi farin ciki har ta samu ta sake da ita ta aiwatar da nufinta gare shi sai kuma taji sabanin hakan a bakin shi. Sai ta dan tsuke fuska tare da fadin gaskiya ya kamata ace ka shirya wa tafiyan mu zuwa yanzu don kada nazo nayi nauyi da yawa kace ba zan fita ba. Abdulsamad ya tsura mata ido yana mamakin rigimar Nafisa yanzu bata aje kanta a kusa ba shi kayan bany ko a nan gida Nageria za a samau su ai. Ya cikin daure fuska kin fi kowa sani komai nake so zan iya odan shi a dan kan kanin lokaci ya iso gare ni ballanta na babu dan da aka haifa a gidan nan da na fita waje na sayo mashi kaya. Ranta ne taji ya baci don may zaya danganta sauran diyan shi da abinda ke cikin ta a yanzu da ta san tafi karfin kowa ma nashi. Shikan gado ya hau yana gyara kwanciyan shi don yasan ba tayin abinci zai samu a gurinta ba duk dako yana son saka wani a bakin shi yanzu. Nafisa kuma bataji dadin haka ba don tana gani idan ta kyale shi bazata samu yadda take son komai ya tafi ba har ya sadu da ita don ta riga ta shafa maganin da boka ya bata tayi amfani dashi. Tabo shi tayi tana kwantawa a jikin shi da sauri ya juyo gareta yana fadin barni banda lokacin aiwatar da wani abu yau a tsakanin mu. Tace aiko tunda ni ina da bukatan ka tare dani dole zaka daure ka biya min bukatana haka nan yasan ta da son ya kusance ta akai akai wanda a baya yakan biye mata. Kara kwanto mashi tayi ya kara daga ta ajikin shi karo na biyu yace ki barni please na fada maki ina bukatan kasancewa ni kadai ne duk iya nacin ta dole ta barshi tafita kamar zatayi hauka take jin kanta a lokacin. Ta jefeshi da harara ya karkace kai yana mamakin tace ba laifin ka bane tunda kai kana fita waje yanzu kana samun inda ke sauke nauyin ka acan. Sheri zaki min yau kuma Nafisa tace amma kasan baka kyauta mi ba nima idan kai min haka yau don ina bukace dakai a yanzu yace ki hakkuri nace yau ba zaki samu ba ya gyara kwanciya yana fadin hakan. A yadda ta rude sai ta bashi tausayi amma bai iya aiwatar da komai a yadda yake jin gabanshi yana faduwa mai. Jin fitan ta a fusace bayan ta gama mashi mita ta fice daga dakin ya girgiza kanshi ya gyara kwanciyan shi sai barci acikin barcin ne yayi mafalkin mara dadi da Nafisa wanda ya tayar mashi da hankali. Tunda ya falka bai koma barci ba tunanen mafalkin da yayi ne ya tsaya mashi a rai mikewa yayi ya dauro alwala ya gabatar da sallah tare da samun sauki alamura a gare shi kamar yadda mahaifan shi ke koyar dashi ko wani lokaci. Washe gari ta tashi gaban ta yana fitar da wani irin kaikayi dake damun ta sam bata kawo cewa aikin boka da ta sakane ya jawo mata hakan ba. Tunda ya watsa ruwa ya fito yana shiri zuciyar shi cike da tunanen abubuwan da suke faruwa dashi ya yanzu din. Sai da ya biya dakin ta ya dubata kamar yadda yayi mafalkin a haka ya samay ta tana ta faman da soshe soshe don kaikayin dake damun ta. Yace may ke damuwan ki haka ne kike wanan soshe soshen haka cikin bacin rai tace dama ai haka kake so dani tunda na bukace ka kashere ni. Banga dalilin da zaka daukoni karabo ni da kasata ba kazo yanzu kana nuna min gazawanka a kaina inda take shiga banan take fita baya ya ciki da irin kalaman da take fada mai. Hannu ya daga mata tare da fadin ya isheki haka na kada kine me ki fada min maganan banza an fada maki ni banda abinyi ne sai na kwanciya da mace kullun , ? Kallon shi take da mamaki don bata dauka zai fada mata wanan magana haka ba yace kinje kinyi biye biyen ki kin dauko wa kanki cuta kiike son aza min. Kuka ta saka mai tan , aza mai kururuwa bai kulata ba ya fice daga gidan kai tsaye kukan ta ne ya jawo hankalin yan uwanta gare ta suka shigo dakin. Har yaje office bai iya tsinana komai ba da yamma koda ya dawo ya samay ta a hargitse ya dawo har ya dade ta bishi dakin shi ta samu ya fito wanka yana daure da dan karamin tawul a jikin shi. Tunda ta shigo mai daki ya dago ido ya kalleta ya kawar da kan shi gefe daya yaci gaba da abinda yake yi din tazo gaban shi tace. Allah kuwa sai ka fada min abinda yasa ka tsiro yimin wullakanci haka ko dan kaga ina dauke da ciki ne a jikina yanzu yasa har kake guda na. Ya jefeta da wani muggun harara har sai da taji tsoro ta dan ja bays kadan yace look Nafisa idan dan dai kina son mu zauna lafiya dake sai kin aje kanki a matsayin da na dauko ki a gidan nan na mata. Macen kwarai itace wace ta san damuwar mijin ta da cin shi da shan shi da gyara mai makwacin sa da sauran su. Amma duk ke baki san yin wanan ba sai dai kici arziki ki wadatar da yan uwan ki ba tare dani kin dubi nawa da komai daya shafe ni ba. Don haka kodai ki gyara halin ki ko kuma in karo wata a gidan nan ku zauna tare wacce zata dinga kyautata min. Ya na kaiwa nan yaja dogon tsukiy ya dauki key din motar shi ya fice dakin ya barta tsaye tana kurma ihun bakin ciki. Wanan halin da Nafisa keyi wani lokaci kamar zautata sai daga baya kuma idan ta samu abinda take wa haukan ta dawo ta gyagije kamar ba ita ba. Iyanzu ya fahince ta idan tana bukatan abu bai mata shi ba babu sauran zaman lafiya a gidan tsakanin ta dashi shiyasa da zaran ta bijiro da bukatatun ta yake saurin biya mata akan lokacin. Wanda ita kuma take ganin aikin bokayen tane da mahaukacin son da yake mata yasa yake biya mata bukatanta a haukace kamar ba gobe. Wanda tayi believing da baka da malamai ta ne aikin su yake ci a gareshi da kuma kyau da zati wanda take gani dashi take rudan shi ba zai taba samun mace kamar ta a cikin matan hausawan Nigeria ba sai dai kalan matan mu na nan. Burin mazan Nigeria ne su malki mace mai kyau koda bata da hali na gari adai ce matar shi ta gwada wa tsara ne a gari. Bata san Nigeria akwai wanan akwai kuma la,akari da ilimi tare da wayen mace da tarbiya ga mazan da suka san kan su. Yau ma kamar jiya tashigo mai tana bukatan su kasance tare amma fir yaki amincewa ya biya mata bukatan ta kamar jiya haka ta wahala da wanan dan banzan kaikayin na gaba da tadamay ta. Yanzu kan ya gama sakankancewa a ranshi mafalkin shi gaskiya ne inda ya ganta dauke da wani mugun abu tana goga ma gabanta. Washe gari har ya shirya bata tashi ba daga barci tana ramuwar barcin da bata samu tayi ba a daren shiya tsaya ya tayar da ita cike da tsanar halin ta na rashin son yin ibada. Idonta da sauran magagin barci bai gama watsakewa ba tace har ka shirya fita ke nan yace idan ma ban fita ba wani abin zaki min ne tunda ba abin kari zaki hada min ba. Cikin bacin rai ga maganan shi tace ba muyi wanan alkawarin da kai ba na cewa nice zan dafa ma abincin da zakaci na dauko masu dafa ma kace basu iya ba don haka banda matsala ga wanan. Yace yana daukan jakar Laptop din shi tare da sabawa a kafadan shi Nafisa zakiyi nadaman wanan maganan da kike fada min don ya zama dole idan baki canza ba in dauko wace zata bani kulawan da nake so a gidana. Maganan shi Ya bata mamaki kwarai don bata zaton zai iya fadin wanan magana a gabanta ba kai tsaye sai gashi yau yana fada mata da bakin shi wai zai dauko mai kula dashi a gidan. Wai ina kudin da take narkawa malaman ta yake shiga ne haka gashi ta dalilin bin bokaye da malamai dasa gaba yanzu ta daina kai kudin da suke kaiwa gida duk wata ana amfani dashi. Ya bata mamaki kwarai ta samu ta danne zuciyar ta don ta san yanzu akwai sauyi a tare dashi ta dago ta kalleshi yana shirin fita daga dakin. Fuskan shi a daure yake har lokacin gabata ne ya kara faduwa sosai dole sai ta hada da kissa da kisisinan mata yanzu. Tace kayi hakkuri don naga yanzu magana kadan sai ka dauki zafi dani haka yace ai kece zan bawa hakkuri keda ban san na dauko ki kawai ne gidana don ki ji dadi ba. Ta sada kai kasa tace ba laifina bane ka sani don ba girki zan iya yi yadda kake so ba bai sake yin magana ba yaci gaba da shirin shi bayan ya gama ne ya dago ya kalle ta yana fadin ki tashi ki sallah don lokaci ya gama kure maki ko. Ya fice daga dakin bayan ya gama fadin haka bishin shi tayi da kallo har ya bacd ma ganin ta sai lokacin ta saukar da ajiyan zuciya. Tace lalai da sake ya zama dole ta canza halin ta idan ba haka ba wankin hula zai iya kai ta dare wanan wani irin mutum ne da magani bai saurin kamashi. Shin shi ba kamar sauran mazaje yake bane da take jin mata na hiran yadda suke samun kan maza je nasu suke juyasu ne ? Yazama dole duk wani abu da zatayi taga ta samu ya sauko kamar yadda malam yace ta bi komai a sannu kada alamarin ya juye mata gashi ko taga abubuwa na shirin juyewa da ita. Wai shin ko da gaskiya ne asiri baya kama mutum idan mace nada ciki ko ta haihu dole ne ta jirkinta har ta haihu ta bishi a yadda yake so ta nuna mashi ta kwanta yanzu. Alaadan shine idan ya fita office zai mata kira uku ko sama da haka amma sai take ganin sabanin haka yanzu tun yana mata kira daya har yakai yau ya bai kirata ba ki daya. Haka yasa ta fara zargin dama dalili yake nema da ita ai sunsha yin fiye da haka dashi amma bai sa ya daina kulata ba sai wanan kawai zai dauka da zafi haka. Har tayi wanka ta fito falo wurin yan uwanta da ta samu suna shayen shayin su bata daina tunanen halin da take ciki da mijin ta ba. Gaida ita suka farayi ciki harshen buzaci tana karba masu da kyat yanayin ta ya nuna ba ta cikin dadin rai. Yar dattijuwa daga cikin su ne tace yau ba zaki fita bake nan ta amsa tare da yamutse fuska tana fadin ba inda zanje yau suko sunfi sin tana fita a gidan don sun fi sake jiki suyi yadda ransu ke so idan bata gidan. Matar tace yanzu ya kamata ace kin fara natsuwa guri daya saboda cikin ki da ya fara girma don kina bukatan hutu. Ta dan lumshe ido tare da jan tsoki ta dafe kan ta tace wani irin hutu Yanyala, ni da abubuwa suke son rikewa a gidan nan yanzu. A lokaci daya suka zaro ido tare da mayar da hankalinsu gare ta suna sauraren ta tace ya zama dole dukkan ku ku gyara a gidan nan. Yace mun bata mashi gida bamu gyara ba ai mai girkin da na dauko ku da sunan masu aiki a gidan saboda haka nake son kowa ta dan fara aikin ta. Yanyala ta fidda idanuwa waje tana mamaki tace garin yaya har kika bari haka ya faru a tsakanin ku tace wallahi ke ma shedace ina iya kokarina don ganin haka bai faru ba amma hakan bai samu a gare ni. Yanyala tace gaskiya ya kamata ki fara tura kaya gida tun yanzu ko za a watse dai kin riga da kin debi rabin ki ko ke. Dama bazan Nigeria ai basu da tabbas ba kowane ke kamuwa yadda ake so ba don haka muke daukan su kamar wurin cin kasuwa a gare mu. Don ko da kasuwa zata watse dan koli yakasa ya kwashe rabon shi nan dai sukai ta shawaran abinda zasu yi akan sauyin da ta ke gani ga mijin nata yanzu. Idan da sabo na saba izuwa yanzu haka kawai zai zo ya dauke ni a mota sai dai mu zagaya gari ya dawo dani ya aje ya wuce makaranta. Yau ma da yai kwana biyu bai zo inda nake ba komai na tafiya a guri na normal sai dai zan iya cewa haduwa na dasu ya bude min wani sabon babi na rayuwane. Duk da nake yarinya kuma mace ban yarda na fara hurda dasu ba sai da na karanci rayuwan su nagane zama dasu ba yana nufin jefa ni a gurbataciyar rayuwa bane. Yauma ina daki kwance ni kadai ina nazarin wani littafi don sabon da nayi da yawan karatu sai dai ance sabo turken wawa ne don har na dan fara shiga damuwan rashin ji daga gare shi kwana biyu. Waya na da yai ringing na juya ina kallon mai kirana a lokacin ganin sunan shi a screen din wayan yasa na dan sake murmushi sai da naja mai aji na dauki wayan. Da sallama na fara magana ya amsa min yace kina hostel ko kina cikin makaranta ne nace ina hostel yanzu fito ina waje yace ya kashe wayan shi. Na shirya cikin wani dogon riga mai dan hannu shara shara riga yana dan matse kadan daga saman shi kasan shi a bude. Kai tsaye daga inda yake zaune a motar yana sana,an shi na hango shi cikin motar ya mayar da hankalin shi sosai ga abinda yake yi. Tun da ya dago kai ya hangoni tafe ya daina abinda yake yi ya tsura min idanuwan shi masu kashe min jiki da zuciya haka ya sake min su tankar wanda ya samu tv har na iso gare shi. Daga waje na gaida shi kamar wanda baiji ni ba yayi sai bude min motar yayi da alaman in shiga kai na daga na kalle shi carab muka hada ido dashi. Nan nace dashi karatu nake fa yallabai ka kirani yanzu yace shiga mu tafi na sani ai. Tambayan shi nayi da ina zamu tafi tare da kashe shi da idanuwana dasu ke rikitashi idan ya kalla. Sayar dake zanyi yace murmushi nayi nace ai dako kayi babban kamu yau galleliyar yarinya kamata ba karamin kudi zaka samu ba ko. Nace yanzu ya kamata ace kana wurin aiki ka ko gida kana hutawa dan murmushi ya sauke tare da fadin. Bazan iya zama gida ba ne yanzu. To ka koma office yanzu mana tunda lokacin aiki bai kare ba don nima karatu nake yi yace don Allah ki shigo mu tafi kona fito na daukeki in sa a mota. Nayi saurin nuna kaina nace ka dauke ni sai kace wata yar tsana ko matar ka can da zaka dauke ni. Don Allah shigo mu tafi kin sa mutane suna kallon mu na dan juya naga wasu yan mata dake gefen mu sun kura muna ido. Dole na bude motar na shiga ya tayar da motar muka bar gurin sai da mukai nisa ne naji yace may yasa duka mata wani lokaci halin ku daya ne wai ? Na bata fuska tare da dan kallon shi nace haba mijin buzuwa da alama yau baka cikin dadin rai kake hango matsalan gidan ka ga kowa. Kada ka danganta abinda ya hada ka da matar ka dani don bai shafeni ba ko kadan yanzu ma banga abinda nayi da zaka fadi haka ba. Yace nima ban san dalili kawai dai ina hango hakane gun ko wace mace kamar halinku duk dayane wani lokaci. Nace baka canka da kyau ba malam ai kaji ance mata suna suka tara . Ya kalle ni ya girgiza kai yace bazan iya tabbatar da haka ba sai na gwada don naga biyu halin su daya basu damu da damuwan mutum ba kansu kawai suka sani da son abinduniya. Wow i am impress dama haka ka dauki mata a ranka ashe ? Yes sai dai ban sani ba ko kamar yadda kika fada inke din ta daban ce don na dan ga alama haka. Shiru mukayi duka a motar sai can yace cikin langabar da kai please khadija kiyi hakkuri ki fahince ni don yanzu bani da zabi sai wanan tunanen. But sai dai ban san may yasa ba nake yawan son in kasance a tare dake muna irin wanan tafiya tare da shammatan junar mu. What na fada cikin mamaki da rashin fahintar maganan shi tare da fadin me ye maanar hakan a gare ka may yasa sai nice zaka ji dadin fada dani ranka yai maka dadi. Don haka kaje ka dauko ni a lokacin da nake a tsakiyan karatuna don kawai son fitina kace wai kana son muyi ta shammatan juna kana jin dadi. Murmushi yayi yana fadin bazaki gane ba ne khadija hakane kawai farin ciki na a yanzu a take na daure fuska tare da fadin maidani inda ka dauko ni don Allah. Haba mana khadija may kike fadi haka ke nan baki bukatan ganin farin ciki na ne komay yanzu fa kika gama fadin mata suna suka tara da bakin nan naki. Nace da ban dauka farin ciki kaka samu daga yin haka da nake maka ba ai na dauka bacin rai nake sakaka. Hummm yace sai ya juyo ya kalle ni yace to indai ina da wani matsayi a gare ki yanzu dai ki zauna mu tafi. Ba yadda na iya haka na koma na zauna tare da kawar da kaina gefe daya yace yanzu na fara sanin ashe suna kuka tara. Tunda gashi na roki alfarma a gurin ki kin yi min abu biyu ke nan na fahinta a gare ki yanzu zaman mu tare da ke. Nace wanan bata min lokaci na kawai kake son yi a banza bayan kasan ina da abinyi a gaba na yanzu. May yasa zan so bata maki lokacin ki haka bayan nafi kowa sanin amfanin abinda kike yi yanzu. Yanzun dai mubar wanan magana may kadauko ni yi a yanzu ne don Allah na tambaye shi tare da kura mai ido ina son jin amsa na. Wanan lokacin da wanan yanayin yafi min ko wani lokaci jin dadi a rayuwa na yanzu matukar ina tare da ke khadija. Kece mace ta farko da nafi jin natsuwa idan ina tare da ita khadija ya juyo ya kalle ni tare da fadin kin san may yasa nace haka ? Kai na girgiza mai cikin sanyin jiki alaman ban sani ba sai ya fada dai zan sani daga gare shi. Yayi murmushi ya kalleni yace kin san yadda zakisa zuciyar mutum ya sake ba tare da an rabu cikin bacin rai ba khadija. Ina jin dadin hakan da kike min ke ta daban ce da sauran matan zan iya yarda a yanzu saboda wasu dalili da na kafa akan ki. Wani dalili ne haka na tambaya da sauri tare da kallon shi yace baki taba rokona wani abuba khadija alhali nasan kina da bukatan abubuwa da dama tunda kin san ina da halin shi. Na nuna kaina nace ni in rokeka kuma akan may zan roke ka bayan nasan rabo ne idan rabona ya ratsa a kan ka zaka bani ko ban roka ba. Good girl tafiya zatai dadi a tare dake kuwa tunda kin san haka she nayi saurin fadin ashe kai marowaci ne ke nan ga mata ? Ya dan lumshe ido yace ko daya wallahi na dai fi son inyi abinda ba sai an roke ni bane sai dai ina haduwa da matan da basu da hakkuri ne khadija. Ban san lokacin da baki na ya bude ba nace kana nufin har da anty Fati haka take yaushe ma ta samu gurin roko a wurin ka kai ? Ya na tukin shi hankali kwance ya murmusa yace kin ga yanzu ma kin fada da bakin ki yaushe na kula ta balle ta samu tambaya na ? Haka kowa ke gani khadija shiyasa manya sukace tsakanin miji da mata sai Allah wanan abin na bar wa kaina sani kawai. Daga ya mayar da kanshi ga titi yana ta tuki a hankali tare da shakan isakan dake kadawa a lokacin may hade da kamshi kasa wanda ke nuna dama na son sauka a lokacin. Ba wani guri mukaje ba sai yawata garin da mukayi kawai ya dawo dani hostel ya aje ba tare da na tsaya ba na shige kai tsaye yaja motar shi ya tafi. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABUMommy wayayir mace mai haba haba da jamma irin matan nan ne masu fara,a a fuskan su kuma ita har cikin zuciyar ta haka take da kowa sai dai bata daukan raini. Abin ta bai rufe mata ido ba tana da ilimi na boko wadattace don duk matan na Abban su Abdulsamad suna da ilimin su ya aure su in ka debe ummi wace iyakarta secondary kadai tayi har hajiya mama mahaifiyar Abdulsamad a gidan shi ta hada karatun ta na NCE wanda dama koyarwa take koda ya aure ta. Ita anty amarya ma da aikin ta ya auro ta wanda yanzu ta daina duk ya hana matan nasa aiki ya tsaya ga bukatun su kuma. Mommy ne zaune tare da Abban yana karyawa hajiya mama wadda yaranta ke kira da hajiyan mu ko hajiya mama ta shigo falon. Akan maganan tafiyan mommy da Abdul din ya bugo yana mata tuni a daren jiya don sun fara tatauna maganan sai Abban bai bada goyon baya akan haka ba. Yanzu shine ta shigo ayita akaare idan zai yarda shigowan mama yayi daidai da shigowan hajiya ummi da anty Amarya data kira kaffinta shigo. Sun sami wurin sun zauna tare da fuskantar shi yasa yasan da magana sukazo mai ummi ce ta fara maganan amma sai anty amarya ta dan saka larin kishi a ciki tace ni naga ai ba sai taje ba ya mayar da matar shi mana zaifi sauki. Ummi da wanan kkaron bata goyi bayan maganan anty amaryan ba tace a a Sadiya tunda har kika ji wanan yaron ya bukaci hakan ai sai mu gode ma Allah da har wanan tunanen yazo mashi a rai. Ko ba komai ya kamata ace sanin halin ita Nafisa ya kamata wani daga cikin mu yaje ya zauna kamar yadda ya bukata din don ace mai daki shiyasan ida ruwa ke yoyo a dakin. Nidai kunsan ba lafiya ke gareni ba ba zan iya zuwa ba ita dai suwaiba din ya dace ta tafi don ita dai zainab din ya dace taje ta zauna dasu ta saka ido tunda da iyan bawa zasuyi tafiyan. Murmushi Abban yayi yace ke nan dai kun gama magana kuna goyon bayan dan ku ko ummi tace ba hakana bane Alhaji. Ganin dai dacewan hakan mukayi yasa muka goya baya ga maganan shi da kan shi babangidan ya fara tuntubana da wanan zancen da yazo na bashi goyon baya akan haka. Sai anty amarya ta kalle ta ta rausaya da kanta gefe daya bata kara magana ba har lokacin da Abba ya gama ja ma mommy kunne akan zaman da zatayi a gidan dan nasu. Suka bar mommy dashi a falon kowa ya kama gaban shi tun wanan ranan mommy ta fara shirin tafiya Abuja gidan Abdulsamad wanda suke kira da babangida kasancewa sunan mahaifin maigidan su ke gare shi. Abdulsamad bai fada ma Nafisa zuwan mommy ba gidan sai cin karen su ba babbaka suke ita da yan uwanta a gidan banza ta fadi masu kasa gasasa dama haka aladansu yake yar su ta auri mai arziki dangi su kwaso a taru aci arzikin ta. Mommy bata boye ma Anty Fati zancen tafiyan ta ba inda ta kirata ta fada mata da bakin ta tare da cewa zatayi iya kokarin ta taga ta shirya tsakanin ta da mijin ta kafin ta bar Abuja din. Allah ya kiyaye hanya Fati tai mata tare da cewa mommy amma fa sai kin hada da hakkuri don kun san Nafisa bata kaunar taga kowa ya rabi yaya Abdulsamad. Abinda yakai ni shi zanyi idan tayi ba daidai ba dole ne in fada mata gaskiya koda kuwa bata so dariya tayi don sanin halin Nafisa da tayi kamar yunwar cikin ta. Tsaye yake tsakar falon inda yake umartan masu aikin da ya shigo dasu da su gyara part din Fati yana masu kwatance yadda yake son gyaran. Nafisa da ke barci a dakin ta Yanyala ta shiga mata da maganar cewa may ke faruwa ne taga ana gyaran dayan part din da tace na uwar gidan ta ne. Kamar ba cikine a jikin ta ba ta diro saman gadon ta fito inda masu aikin su nan ta hausu da fada wayasa su aiki a gidan ta ba a fada mata ba. Daga bayan ta ya bata amsa yana saukowa daga sama yace nine nan maigidan na basu aiki suyi in biya su wani irin kallo mai kama da kai asuwa ta aika mashi. Bai tsaya kulata ba sai kokarin shiga dakin da yake yi tasha gaban shi da sauri ta tsare shi may kake nufi ne samad da wanan gyaran da akeyi ? Yace abinda kika gani Nafisa shi nake nufi don gida nawa ne ba naki ba kamar yadda kika fadi yanzu. Nan hankalin ta ya tashi sai ta fara surutu ita may yake nufi da ita da zai mata haka yace don yaga zata haihu zai dawo da fati da yaranta gidan shi. Tace nasan dama kule kulen da ake shiryama ke nan kake yawan zuwa kaduna akai akai yanzu dama ba so na yan uwanka keyi dani ba . Shi dai bai mata magana ba don mazan dake gidan suna aiki ya fita batunta basu raba hali a gaban su ba. Hankali tashe ta kira madam tana fada mata abinda ke faruwa madam tace kika sani ko watace zai dauko ya saka a dakin ba Fati ba ? Nan hankalin ta ya kara tashi sosai tace Nafisa dam wanan tunanen baizo min ba sai da kika tunatar dani haka yanzu. Madam tace to zauna nan kina fada akan fati wata tazo ta shige dakin kina gani saboda sakaci irin naki in zaki mike ki mike tun yaushe muka gama da wata fati can. Wacce hudi daya mukai mata muka fitar da ita a gidan har diyan ta sai tarihin su yanzu har kike tunanen ita zai mayar dakin ta. Ke kasar ku fa zaki koma aiki kaifi sai Niger nan kusa kafin ma mu dawo aiki ya kankama ko mu huta da ko wacece ma ke son muna kutse haka cikin ruwan sanyi. Nafisa tace madam kin san ba zuwan ba kuma ba kudin nake jiwa ba don zan iya saida da duk wani kaddara da nake da akan wanan aikin tunda yanzu na rasa gane kan shi. Matsala daya ne shine mutumin nawa yanzu kin san matsi yake min tun wanan tafiyan da mukayi ondo ya kara burge min a gidan nan baya sake min har yanzu ga kuma lalurar cikin nan dake jikina yanzu. Madam tace ke dai kawai tawa ki nemi kudi in ma bai barki ba sai ni inje maki manene amfanin zaman mu tare da ba zan iya maki komai ba. Ai kawai ki daina damun kan ki mu za a gwadawa hanyar boka ko malam kuma ko latsandan ne gaba da lahira indai ana zuwa zamuje shi. Sai lokacin Nafisa tayi ajiyan zuciya taji dadi a ranta tana ganin aduniya bata da kamar su madam dake tsaye a kan ta yanzu. Tace uwar dakina Allah dai yaja muna nisan kwana tare ni nasan banda kamar ki a duniyan nan yanzu. Da wanan shawaran hankalin Nafisa ya kwanta nan ta shiga buga waya gida Niger ko an samu wani bakon boka ko malami mai tashe a kasan. Sai da ya ga komai ya kankama yadda yake so ya bar gidan bayan ya sallami mutanen da sukai mashi aiki duk da yawan samari yan uwan Nafisa a gidan ba wanda zaiyi bugun gaba dashi yayi mashi aiki alhalin biyansu yake duk wata dasunan aiki suke mai a gida. Bayan kwana biyu su mommy sun gama shirin su tsab ya tura Yusuf ya dauko su zuwa garin Abujan mommy a gutin hajiya mama ta bar yaran ta tazo ita kadai sai iyan Bawa da suka zo tare da wata yar mai masu shara budurwa don taimaka masu da wani abin. Mommy sunyi waya da Ya Amina tana sallaman ta tace zata gidan Abdulsamad wanda matar shi watan haihuwan ta ya kama zasu dan kwana biyu acan . Ya Amina sai sulbul da baka tayi tace mommy ashe zaku hadu da Khadija na ke nan mummy tace banda abinki khadija dake makaranta ina zan ganta ni ? Sai dai idan sawa zanyi a dauko min ita ko akaini in gano maki lafiyan ta idan na samu lokaci dariya kawai ta Amina tayi don ta san gidan su Abdulsamad basu san komai ba a tsakanin mu dashi. Tafiyan rana sukayi don haka sai da yamma lis suka shigo garin Abuja din direct gidan shi suka nufa yana gida a lokacin don yana dakon zuwan su. Nafisa wace ke falo tana shan iska ga yan uwanta a kewaye da ita kowa na shaanin gaban shi sai sallaman su mommy da su iyan bawa suka ji . Gaban tane ya fadi da ganin su mommy din gidan don bata taba zaton zuwan su ba don a wautan Nafisa ta gama da kowa nashi yanzu babu mai marmarin zuwa inda yake. Zuwan su mommy ba karamin faduwan gaba yasa ta ba sai take ganin ai zancen auren da take zato ko dawowan Fati gidan gaskiya ne. Shiya fito daga daki bayan sunyi waya da Yusuf ya sheda mai sun iso ya fito da yar fara, a a fuskan shi yayin da ko kallo su mommy basu ishi Nafisa da yan uwanta dake falon ba . Shi da kanshiyayi masu iso dakin da zasu sauka din bayan dun gaisa sun mashi yaya gida ya fito tare da Yusuf da ya shigo da kayan su ciki da taimakon wani saurayi. Falon ya dawo inda suka samu Nafisa da yan uwanta sun juye harshe cikin yaren su na buzanci suna maganan zuwan su. Fuska a daure ya kalle ta yace Nafisa baki san mommy bane da gwago na iyan bawa da baki tare su da zuwa ba ? Tace a yatsune na san su mana ba matar mahaifin ka bane ita yace OK cikin wani irin kallo har ya fara tafiya sai ya juyo yace tunda kin san ta kin san kuma matar mahaifina ne baki iya taron su ba nima haka ban son in fita yanzu in dawo in samu wa yan nan yan uwan naki a gidan nan yanzu. Yana fadar haka ya juya ya fara tafiya tace wallahi baka isa ba don zuwan su zakace yan uwana su bar maka gidan ka yanzu yace zaki san na isa idan yan sanda dun shigo sun fitar min dasu. Idan akwai abin da yan Niger sukaki jini shine dan kakin Nigeria don basu yi masu da wasa idan sun farmake su. Nan Yanyala ta fara magana tace haba Allaji ai bin baikai can ba daga dan wanan magana har zaikai ka kira muna polizawa kawai dai jira muke su huta mu mika masu gaisuwan mu. Ya fice zuwa nemo ma su mommy abinda zasu ci a gidan don yasan ba zasu iya taba cin abincin da suka dafa ba. Bai dauki lokaci ba ya dawo dauke da ledoji iri na restaurant dauke abinci dasu ruwa a ciki ya bayar aka shigo masu dashi har dakin. Mommy ta idar da sallah sai ga yaron shi isyaka yana shigo da kayan ciki tare da gaba tar masu da abincin. Sunka ce har da dawai niya zuwa sayo abinci kuma nan dai iyan bawa ta kasa hakkuri tace zainabu may kika fahinta ga wanan zaman ? Murmushi mommy tayi tace ke dai iyan bawa ai ayi shani kawai wai ancuci na kauye wanan matar bata da hali ko kadan. Kin dai fara ganin makasudin zuwan mu garin nan ke nan don fitar shi kunyan abokan shi nasan halin matar nan tashi dakilace na gani a fada. Ba zamu sakar mata fuskan da zata kawo muna raini ko wulakanci ba don nasan tun zuwan mu batayi farin ciki da ganin mu ba. Sunci abinci sun huta sai ga Nafisa ta shigo tayi wanka ta saka sutura a jikin ta yan uwan ta suna mara mata baya suka shigo dakin. A falo suka samay su nan ta ja ta tsaya bata zauna ba tana fadin kunzo lafiya ya hanya da mutanen gida ? Mommy tace lafiya duk suna gaida ku yaya nauyi Allah ya rabaku lafiya tace amin sauran suka shiga gaida su da yi masu ya hanya suka fice daga dakin ba wanda ya zauna. Shiko bayan ya mika sakon wuri na ya nufa kamar yadda ya saba zuwa man koda ya kirani muna tare da maryam da zarah a dakina kiranshi ya shigo min. Mutumin ki ne halan yazo maryam take tambayana nace cikin tabe baki shine ai kin san bai tashi zuwa min sai wanan lokaci. Maryam tace ai kuna daidai dashi in kin isa ki fadi a gaban shi yana da amsan baki indai wanan yaya in love din kine. Kai maryam kina da wuyan sha,ani wallahi na fada maki ba soyayya a tsakani na dashi sai amin taka kawai na damuwa. Zarah ta dago kai tace min wani guy kuke magana muje in gani idan ya min in saka shi a layi mu shiga sha,ani dashi. Zarah wai ke baki jin kunyan fadin fitsrane haka tace in banda abinki wake ta wani wasa da so yanzu khadija bari kiyi wasa da daman ki yanzu yan jami,an nan suyi maki wuf dashi. Idan banda abinki an fada maki kowane yan matan jamia ke iya wuf dashi kai daya zarah wanan ya wuce sanin ki wallahi. Dariya tayi tace muje inga guy din nan dai da kuke wani zuzutawa haka dai murmushi nayi kawai don ba zan so a ganni da ita ba. Duk da ba wani shiga na yi ba amma suna ta yaba kyau da nayi wai na hadu zarah na fadin ashe zaki zama yar hannu haka khadija. Tare muka fito dasu sun zo su gaida shi tunda muka tunkare shi zarah ta tsunke da ganin motar da yazo da ita tana fadin tun ban ga guy din ba wallahi nasan zai hadu ko don motar nan da nagani how lucky you are da kika iya canko wanan zukeken guy haka. Mun iso yana ta faman ansa call a wayan shi sai da zarah ta kare mai kallo ta dago bayan ya gama wayan suna gaida shi bai wani sake fuska ba ya amsa gaisuwan. Tare da kawar da kanshi gefe daya zarah tace dama na sani sai irin wanan guy din khadija wanan jan ajin naki yayi yawa wallahi har ta gama ta wuce bai yi magana ba suna shiga maryam ta nufi dakin ta. Maganar shi ta farko bayan wucewar su shine ina kika samo wanan kawar kuma ? Nace a inda ka gan mu yanzu yace No ba girman ki bane da mutuncin ki yawo da irin wayan nan nace kawatace fa tare mukazo karatu daga gida. Na fada maki bana son in kara ganin ki tare da ita please na juyo ina kallon shi ido cikin ido nace tana da aibu ne komay ? Au ke baki ga aibu ta ba wanan bata da kamun kai ba girman ki bane yawo da ita nace ka taba ganin mu a tare ne ko yanzu ma daurowa tayi ka gan mu da ita. Har ya bude baki zaiyi magana sai kuma yayi shiru nima shirun nayi ba wanda yayi magana daga cikin mu. Can naji yace idan na fada maki wani abu zaki yarda dani ? Zaki yarda gaskiya nake fadi. Murmushi nayi nace idan maganar ta kama gaskiya mai zai hana nayarda tunda nasan gaskiya ka fada. Kin yarda dani khadija ? Nace na yarda dakai mana yaya Abdul fati da mijin buzuwa ina fadi ina mashi dariyan shakiyanci cikin gatse. Shima murmishin ya dan yi wanda sai wanda ya sanshi zai iya fahintar hakan daga gare shi yace kin san kamun kan ki yasa muke tare da ke har wanan lokacin. Kasan ni ne da zaka wani ce ina da kamun kai bayan iyakar mu dan wanan haduwan da muke yi. Na tsinci muryan shi yana fadin niko na sanki khadija you are classic baby da na taba haduwa da ita a rayuwana. Katse shi nayi da fadin may ke faruwa daksi haka ne wai ke irin wanan magana yanzu a kai na ko last zuwa da kayi haka ka dinga min wanan maganganun. Ya girgiza min kai tare da fadin ba komai cikin lumshe idanuwa shi sai kuma ya bude su ya sani gaba yana kallo na. Shirun motar na kawar da fadin yau ba fita ke nan yace ina kike son muje nace inda ka saba zuwa mana mu zaga gari kawai kana barnan man motar ka. Haka kika dauki fitan namu dama nace hakane mana tunda ba wani guri muke zuwa ba. Ke ce baki fahinci muhinmancin fitar namu ba kila amma ni yana da ma,ana masu yawa a gare ni matuka khadija. Don kasan cewan mu a tare you have change me now na fahinci su abubuwa da dama da ban taba fuskantar su ba a baya. Maganan gaskiya yau kin dawo min da farin ciki rayuwana har iyayyena sun zo gida da sunan kwana biyu a wuri na. Da sauri nace cikin murna wai da gaske kake yi yace kwarai kuwa deeda don yanzu haka mommy da gwagona iyan bawa na gida maganan nan da muke yi dake. Taya kike ganin bazan maki godiya a wanan kangin da nake ganin kin fitar dani wanda a da nake dauka da shirmay irin naki na yara kike yi. Sun kuyar da kai nayi kasa ina tunane hankalina yayi nisa bani jin abinda yake fadi tsoro na daya ne kada mommy tasan ina tare dashi ta fasara haduwan mu a wata manufa. Ban sauri maganan shi ba na katse shi da fadin zan roke don Allah kada ka bari mommy tasan kana zuwa inda nake don bansan da wani ido zan kallesu ba har hajiyan ka. Ya lura da irin rudewan da na shiga sai dai baice min komai ba ganin bai yi magana ba yasa nace please yaya Abdulsamad ka boye wanan a matsayin siri a tsakanin mu don Allah. Kallo na yayi ya sauke murmushi yace saboda may kike son kada su san ina tare dake nace dashi wayyo Allah kana son su dauke ni yar cin amana ne ko may ? Cikin sanyi murya nace kasan su ba zasu gane mutunci ke tsakanin mu ba sai su dauka muna tare da wani manufan da bashi ba. Hakan kuma yana nufi na ci amanan su ke nan gama yadda suke son Fatin ka a gidan yanzu kuma sai su gan mu tare yaya kake ganin zasu dauki abin. Kai tsaye yace zasufi kowa farin cikin da hakan na sani tunda sun san ki sun san halin ki zasu yi farin ciki da hakan. Daga yau magana ya kare ba sauran wani abu a tsakanin mu tunda bukatar mu ya biya ka shirya tsakanin ka da yan uwan ka. Mamaki magana na ya bashi yace juyo yana kallo na sai can yace ai deal namu bai kare ba tukun ko kin manta baki karasa aikin ki ba akan fati ? Na amsa da fafin kwarai bamu kai nan ba cikin takaici nace wana kuma yanzu ya rage gare ka sai kasan yadda ka shirya da matarka. Ba wani sauran magana yanzu a tsakanin mu kuma na fada cikin tsiwa ya juyo da kyau ya kalle ni yace don mommy tazo duk kike fadan wanan magana ko may. No ba don tazo ba in ma don tazo din ne haka ne bana son su dauki abinda wani fassarane kawai. Ya zura min idon sa yana kallin yadda duk na rude yace a ranshi ashe karyan rashi kunya nakeyi a da gashi yanzu daga jin mommy tazo duk na bi na birkice lokaci daya. Motar tayi tsit kowa da abinda yake tunane a ran shi sai da ya shafa kan shi naji yace relax deeda wace dake mommy zata san da wanan maganan dake tsakani mu wai ? Wata zuciyane ta bashi shawaran ya min wayau kawai don yadda na rikece din nan daga jin mommy tazo zai iya sa komai ya faru idan ya biye min. Kawar da zancen yayi da fadin zuwa nayi ki ban shawara yaya zan yi da Nafisa don batai farin ciki da zuwan nasu ba yanzu haka. Da sauri na dago kai na kalle shi da idona da suka sauya kala nace baka fada mata zancen zuwan su bane dama , ? Kai ya girgiza min yace ban fada mata zasu zo ba tunda ba itace ta aje ni ba yan uwan ta dake zuwa ai ba fada min take yi ba itama. Kada kaga laifinta a yanzu don kai kai sake har haka ya kasance tun farko saboda tsoron ta da kake nuna kanayi da farko. Ba tsoran ta nake yi ba deeda kaunane kawai na tsakanin miji da mata wanda ita ta dauka tsoron tane yasa nake mata hakan. Sai yanzun kasan da wanan yana iya faruwa ka manta a lokacin da take saka abu kana mata shi koda kuwa baka son abin ? Ya gyara zama yana fadin shine babban kuskure dana tabka a farko wanda nake nadaman yi shi a yanzu haka. Duk abinda zakayi ko zatayi kada ka bari rainin matarka yakai ga iyayyen ka don ko zaka iya canza mata amma ba zamu iya canza iyayye ba. Wai ke wake koya maki wanan hikimar haka nr ya tambaya cikin son in bashi amsa nace baka son maganan ke nan. Yace No idan ban so ai ba zan fada maki zuciyana na ba a yanzu don da zuwan su abinda tayi masu yaci min rai sosai ba zan boye maki ba don yanzu ke ce abokiyar shawarata shiyasa nazo maki da zancen. Yaya zanyi khadija ina son in fita daga cikin dana shiga a bayane gida na yanzu bana son su mommy su fahinci sakaci na a gida na. Nace na yaushe kuma saidai kada a kara muma makwabta ku mun sanni balle su mommy dake gidan tare ku. Ina son mata na khadija shiyasa har haka ya faru da ni kallon shi nake cikin mamakin kalamin shi na wai yana son matan shi da yace. Shin shi wani iriin mutum ne wai nace nafisa dai kake so amma baka son fati kowa ma yasan da hakan ? Haka kuke tunane ya fadi cikin zafin zuciya amma ita ai tasan ina sonta halin ta ne kawai baizo daya da nawa ba shine matsalan mu. Kalon shi nake sororo kamar na samu tv da alama yarasa yaya zaiyi da damywar shi ne ya tsinci kanshi cikin fada min sirin zuciyar a matsayi shi na mutum mai shekaru kamar shi. Tausayi ya bani don na fuskanci bayan Yusuf da suke tare baida wani wanda zai fada ma zuciyan shi ya fahince shi shiyasa yazo gare ni. Nace wallahi rayuwan ka na cikin hadari ya kamata ka koma ga Allah kayi abinda Allah yace shine kawai mafita a gare ka. Lokaci ya duba yace zai tafi lokacin sallah ya gabato zai dawo gobe tunda ba school mu karasa tataunawa mukai sallama ya tafi ya barni cike da tausayi shi. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU2️⃣4️⃣Gidan ya nufa kai tsaye tare da sayayyan da yayiwa bakin shi na abubuwan bukatun su ya nufi part din fati dashi. Babu kowa a falon sai yake mamaki yau ina mutanen gidan su shiga haka duk da basu ciki hakan bai hana falon nashi jin tashin yanayin da jikin su ke dashi ba a falon. Hakana har ya isa gurin su mommy zuciyar shi cike da tambaya da tunane ya samay su a zaune suna hira yarinyar da suka zo da ita tana cin abinci. Sai da ya aje kayan a gaban mommy ya zauna lokacin ya fara gaida su suna kara mashi yaya sula samay su yace mummy lafiya sai hamdala. Nan dai ya zauna dasu suka dan taba hira har wani lokaci sai ga Nafisa ta biyu shi har dakin dags kofa ta tsaya ta kira sunan shi. Bayan ya amsa kamar ba zai tashi ba sai kuma ya mike ya tafi sude su mommy kala basu ce ba suna kallon ikon Allah kawai. Ya fito ya samay ta zaune falo tana ganin shi ta mike da kyat ta fara fadin muje sama ina da magana dakai ne ta juya ta fara tafiya yana biye da ita a bayan shi. Ko da suka hau sama bai tsaya bin ta nata ba don har ta juyo da nufin tayi mai abinda ta kulla a ranta sai hango shi tayi yana bude kofan dakin shi kai tsaye. Ido ta bishi dashi tana fadin samad maganar nakira ka muyi zaka shige kuma yace baki san dakina bane ko a kan hanya kike son maganan da ni ? Sai lokacin ta dan juya ta dubu wurin da suke tsaye din sai kuma tayi shiru don ita bata ga komai a nan ba don sunyi magana ai gidan su ne. Dakin ta samay shi tsaye yana rage kaya a jikin shi ta fado dakin babu ko sallama ya dan juyo ta kalle ta ya kawar da kanshi gefe yaci gaba da abinda yake yi. Bayan shi ta tsaya tana kama baya tare da fadin Samad wai may wanan mutane suka zo yi ne a gidan nan ? Yaushe zasu koma don ban son sa ido da takura a gida na sai da ya gama cire kayan ya rage daga shi sai boxes a jikin shi yace cikin duban ta ina fatan wa yan nan mutanen da nace su bar min gida na yau sun bari ? Tsaye tayi sororo tans kallon shi ta shige ban daki ya barta a wuri tsaye tana mamakin yau wai itace samad ke ba amsa haka daidai da nata tambayan. Da dane da yanzu ya fara matairaice mata yana bata hakkuri akan zuwan su mommy din itako tana cika tana batsewa tare da kafa mashi sharudda dole ya bi ya juye mata makudden kudi yana lalashin ta. Yanzu ko da yake kokarin kwato kanshi daga sherin ta sai take ganin wasu ne suke kokarin bata mata aikin ta ta baya. Tunda ya shiga bayin taja kafanta ta zuwa bakin gadon dakin ta zauna tare da tin tagumi don ta fahinci ba maganar da zatai sanyi bane dashi sai da yanzu cikas din ta shine cikin da ke jikin ta don bai bari tayi yadda take so sam. Da mamaki samun ta wurin yake kallon ta da ya fito daga ban dakin don yayi zaton tuni ta tafi dakin ta ta kwanta sai ganin ta yayi zaune cikin damuwa. Samad wai may kake nufi danine yanzu da ke tsiro da wasu halaiya na daban da ban san ka da su ba a da don may zakace sai na sallami yan uwa na gidan nan ? Yace saboda ba gidan yar uwasu bace su bari idan kin kaiga naki gidan sai su kwaso gaba dayan su su dawo inda kike ba dai nan gida na ba. Da bakin ka kake fada min haka Samad yaushe ka tashi ga samad din da na sani mai so na da tausayina da son duk wani abinda nake so a rayuwa na. Da ke nan Nafisa a lokacin da ban fahinci koke wacece ba amma yanzu da na fahinta yasa kike ganin sauyi daga gare ni haka . Ban taba yarda da halin ki ba sai yau Nafisa da har mahaifa na zasu zo gida na ki tsare ni kina tambaya na wai yaushe ne zasu koma ? Alhalin ke ga yan uwan ki nan a gidan sun hana ni shakat dani da gida na ba daman in huta in samu natsuwa a ciki ga dan banzan kazanta da kuka bata min gida dashi ya koma wani iri. Samad mune kazamai dani da yan uwana kake nufi ko may yanzu ne kasan da kazantan mu din ko may yace da na dauka idan idon ki ya bude zaki daina Nafisa ashe abin ba haka yake ba a gun ki. Komai ai zaka iya fada a kaina tunda kaga yanzu banda moriya a gareka yadda kake so a da, da kake yawan naci a kaina da banda komai. Wanan ne tunanen ki ashe kike min yadda kikaga dama bakin ce in dauki matakin da zan dauka ki gani ba ranan to matakin ne yanzu na fara daukar wa kaina. Su mommy kuma da kika gani nan sun zo gidan nan ke nan harsai kin haihu kinyi arbain zasu koma gida. Ido ta zaro waje tace ina zasu zauna din yace a inda kika gan su and bari kiji idan naji wani rashin mutunci ya fito daga gare ki zan baki mamaki sosai a gidan nan. Mamaki ne ko rudewa ya kamata a wanan daren na Abdulsamad wanda take gani karfin haline irin nashi daya iya fada mata wanan magana haka babu ko dar a idon shi. Bai kara kulata ba ya shiga gyaran jikin shi ya barta zaune a gurin cike da mamakin shi fita yayi ya duba ko an rufe gidan ya samu ko ba a rufe ba shi da kansa yaja kofa ya rufe yasa mashi key. Washegari mommy da wanan yarinyar da suka zo mai suna Aisha bayan sunyi sallah basu kara kwantawa ba suka fito falon gidan suka gyara tas ta saka turaren wuta dana tsunke a ko ina na gidan. Take gidan ya dauki kamshi da sanyin Ac kitchen suka koma sai da gaban mommy ya fadi ganin yadda kitchen din yake kamar ba mata ke amfani dashi ba. Nan kuma suka shiga aiki a kitchen din gyara can gyara nan take kitchen din ya koma na macen da tasan kan ta girki suka dora na abinda zasu ci a gidan. Sai da suka kusa gamawa ne matan dake gidan jin kamshin girki yasa suka fara fitowa daga dakunan kwanan su daya bayan daya. Suna lekawa kitchen din suna masu ina kwana don tsaron mutuncin su ga maigidan. Bayan sun gama girki mommy ta zuba masu nasu taba Aisha nasu ta shige masu dashi ciki tabar saura da mutanen dake gidan zasu ci. Yanyala ce ta shiga dakin Nafisa take kwarmata mata abinda ke faruwa a gidan da fushi Nafisa ta sauko kasa zuwa kitchen din don taga abinda ke wakana mata a gida. Komai na gidan neat yake yau ya samu gyaran da ya dace daga bakin su ta shiga kitchen din taga yadda suka gyara komai suka jera shi a inda ya dace. Fita tayi zuwa sama ta samu Abdulsamad ya gama shirin fita tsab ta fado dakin da fushi tana fadin ban san may kuke nufi ba kaida wa yanda kake fadi wai iyayyen ka ne ? Ya juyo yana fafin kamar ya fa tace don may zasu zo min gida suna min abinda suka ga dama a ciki suna matsayin baki a gare ni. May sukai maki ya tambaya cikin bata lokacin shi yana sauraren amsa daga bakin ta tace a hasale yanzu ya dace ace sun shiga kitchen sunyi abinda suke so haka ? Sai da ya dubeta dakyau yace kada ki manta gidan dan su suka zo suna da ikon yin komai da suke so a gidan nan. Dansu ko dan ta da sauri ya kalleta yace may kike nufi da wanan maganan naki tace dashi gani nayi itama arziki tazo ci kawai a gidan nan do ba itace ta haife ka ba. Au dama wanan ne tunanen ki ke nan dama raba daya biyu a gida to bari kiji mommy tankar hajiya mu take gare ni don matar mahaifina ne ita ma kamar hajiyan mu don haka nake daukan su daya. Yanzu ke baki jin kunya baki tashi kin tare su da abin karyawa ba sun tashi sunyiwa kansu har kike fadan akan haka don baki da kunya ? Tace ba zan yarda da wanan wuce wurin ba irin nata dama na dade da sanin halin ta tun shigowa na cikin ku do haka kayi saurin taka mata burki a hakan. You're very stupid ya fada da karfi sai data razana yace kada ki fara kice zaki saka masu ido a gidan nan ko bayan fitana ne don zan saba maki sosai kuwa. Fita yayi daga dakin ya barta cike da mamaki tana ganin wankin hula zai kai ta dare wai itace samad din ta keyi wa abubuwa haka yanzu. Lalai duniya na shirin juya mata baya idan batayi da gaske ba tin yanzu dakin ta ta koma ta jawo wayan ta cikin tashin hankali take fada wa madam abinda ke faru da ita. Sai da ta gama sauraron ta tace Nafisa sai kin hada da hakkuri fa yanzu don ni a gani na akwai ida aiki ki ya samu matsala ko kuma don cikin dake jikin ki ne asiri ya daina kama mijin ki yanzu. Ina cikin wani hali walahi haka na nufin yan uwan samad zasu dawo gare shi suyi yadda suke so gidan nan ke nan wanda ba zan taba yarda ba sai dai duk abinda zai faru sai dai ta faru. Madam tace Nafisa kibi sannu fa ba kullun ne ya zama dole mutum yayi nasara ga abinda yake so ba kowa kika gani sai yanayi yana hadawa da hakkuri da kuma kissa bawai ga magani kawai muka dogara ba. Madam ni abin ne yazo min a bazata wallahi tace yanzun dai ki kwantar da hankalin ki mubi komai a sannu. Tace na ji amma duk da haka zan nuna masu gidana suka zo ba zan bari suyi min abu gaba gadi ba haka tace kiyi a sannu dai na fada maki. Shiko yana fita tun a falo ya fara ganin sauyin da gidan nashi ya samu da zuwan su mommy din ga gida ya koma neat a lokaci daya a falo ya hango su hadiye suna kuskus a cikin yare suna ganin shi suka shiga gaida shi. Fuska a daure take amsa masu ya wuce part din su mommy din wanda anan fati da take zaune da yaran ta ganin haka yasa ya tuna da abubuwa da dama na rayuwan su a baya a gidan. Kagin zuwa yanzu da komai ya hargitse mashi haka wanda kan shi yanzu ya dorawa laifin kasancewar haka kamar yadda na fada mai. Ya samu su mommy sun yi wanka suna karyawa a cikin tsanaki ya shigo da sallama ya gaidasu tare da masu ya gajiyan hanya. Mommy tace gajiya ai yabi lafiya don mun zama yan gari yanzu ko yace mommy duk ku kukai wanan gyaran haka a gidan nan ? Tace ba dole ba babangida gida ya koma kamar ba mata a cikin sa kasan mu mun saba mijin mu baya son ganin kazanta ko kadan. Iya bawa tace mai ni ina mamaki gida da mata haka ace bai samun gyaran da yadace mace ta yi a gidan ta wanan matar taka akwai bakin son jiki ne da ita. Ciki ai bai hana ka gyara muhalin ka sai dai dama idan gyaran bai damay ka ba can amma yaushe ne mace kirki zata bar gidan ta haka ? Mommy tace ga abin kari can a kitchen idan ta fito sai ta raba maku ka karya kafin ka fita yace mommy zuba min zanci anan gurin ku don bata fito ba ko ina sauri ne. Anan ya zauna ya karya tare dasu yana mai jin dadi a ranshi yaushe rabon da ya karya a gidan shi haka cikin dadin rai. Bayan ya gama yayi masu sallama tare da tambayan ko akwai wani abinda suke bukata a gidan ya sayo masu idan ya fita. Mommy tace sai kayan kitchen din da taga sun soma lalacewa saboda rashin amfani dasu da ba a yi akai akai yanzu dole a sayo wasu yaje matar shi tai mashi lissafi don gudun su shiga mata hakkin ta. Bai koma takan Nafisa ba ya fice gidan inda ya samu Sani driver yana jiran shi a waje suka dauki hanyar zuwa office din su. Barci nake a dakina tun dawowana class wayan shi ne ya tayar dani daga barcin da nakeyi nayi mamakin kirana a wanan lokacin da yayi. Bayan na karba mun gaisa ne yake tambayana idan maryam tana nan don Allah zai aiko Sani driver shi mu taimaka mu sayo mai abin girki a gidan shi. Da sauri nace mai kaga malam bafa zaman ka nake a garin nan ba da zaka dora min nauyi irin haka a kaina ina matar ka kaje ka tura ta ta sayo ma mana . Don Allah kiyi hakkuri ku taimaka min for today only naji nace na kalli maryam dake barci nace yanzu yau friady muna hutawan mu ya dauko wahala ya dora muna kuma. Ban sake komawa barci ba motsina ya tayar da maryam nan nake fada mata abinda ya bukata da mu tace to may ye a hakan khadija ? Ai taimako ne kin san matar shi ba wani wayewan kaine da ita ba kuma kin san gata da ciki baki yanzu nace wanan ai ba excuse bane. Son dorawa mutane wahala kawai yake yi don kada a zauna lafiya muna zaune kalau zai dauko wahalan gidan shi ya dora muna. Kin san may khadija nace aa cikin kada kaina tace walahi sai nake ganin wanan Abduldin yana bukatan taimako a rayuwan shi. Bai samu macen da ta dace da irin halin shi bane har yanzu yasa komai yanzu yake bukatan taimakon ki ban san yaya zaiyi ba ranan da zaku rabu dashi tunda kince ba soyayya bane a tsakanin ku. Nace ai ke kin fi kowa sanin hakan shiya san yadda zaiyi don ni bashi ne a gabana ba karatuna ne ya damay ni inga na kammala Allah yaban sa,a in samu aiki da wuri. Duk da haka khadija akwai matsala ranan rabuwan ku kan inda ran mu zamu sha kallo nace in babu sai abaku labari ai. Tace labarin taimako ya juye ya zama soyayya haushi maganan ta yabani ban samu bata amsa ba naso ta biye min kada muje ko ina ya karata can da halin shi shiya sani. Karfe uku bayan an fito sallah jumma,a sai ga malam sani driver yazo daukan mu nan yaban kudin yace wai zamuyi waya dashi. Muna hanya ya bugo min yana fada min duk wani abinda muka sani ana amfani dashi a fannin girki har nama da kaji da sauran su mu sayo mommy ne ke bukata a gidan. Kai dama duk wanan abin ba a saya a gidan ka may kuke ci a gidan silly girl ya fada ya kashe wayan shi naja tsuki. Mun shiga kasuwa maryam tayi kaca kaca da kudin komai mun hada sai yamma lis muka baro cikin kasuwan inda ya fara sauke mu a hostel ya wuce bayan hilux din su acike muka bashi sauran kudin shi ya kai mashi canji. Wanka nayi tea kawai nasha da nai sallah muka samu wuri muka kwanta don gajiyan da muka debo a kasuwan bamai taimaka wa wani a cikin mu duk a aikin sa kai da mukayi. Barci yana batun dauka na wayan shi ya shigo min jin murya na yasa yace har kin fara barci ne ko may ? Nace ba dole ba yau an samu wahalan da ba namu ba lada ba zunubi sai tarin gajiya khadija ke wace irin yarinya ne wai da ba tsoron fadin magana a bakin ki ? Yanzu dai ba wanan ba don may kuka ba sani ragowan kudin da ya rage yakawo min kuma ya fada min komai baku sayo wa kan ku ba ku. Saboda ba hakkin mu bane yasa muka bashi yakai ma kudin ka don Allah barni na huta malam gara da kai kana da madafa. Murmushi naji yayi yace ina dashi tunda ina da matar da zan runguma inji sanyi ke ko sai dai ki kama filon ki ko ? Kaidai ka sani nace mai sai da safe yace ba zaki tsaya nayi maku godiya ba zaki kashe min waya ?nace ai ba don ka gode muna muka taimaka maka ba na kashe wayan gaba daya. A gidan shi ya iso da kayan akai ta shiga dasu ciki shi kanshi yayi mamakin yawan kayan da muka sayo din ya kira Nafisa kafin ta sauko ya kira mommy da kanshi kan tazo idan akwai abinda babu sai a sayo gobe. Nafisa na zuwa mommy tana fitowa tare dashi yake tambayan ta ta duba ta gani ranta a bace tace komai yayi sai mommy tace komai an sayo sayayya haka kamar na mace. Nafisa da ta juya zata tafine ta juyo da sauri ta kara kura ma kayan ido tana kallo kayan da bata kalla ba da farko saboda idon ta ya rufe da masifa a lokacin. Maganan mommy ne ya tsaya mata a rai da tace sayayya kamar mace tayi komai an saya yadda ya kamata ta kira hadiye da yanyala wai su kawar da kayan wurin tana daure fuska gata mai gida. A daki ta samay shi zaune lokacin muna waya tace gurin ka nazo ya aje wayan da na kashe yana kallon ta ta samu guri ta zauna da kyat. Tausayi ta yaji ya dirka mai a zuciya tace may kake nufi da baka shawarce ni ba ka sayo wanan kayan haka sai da kasayo abinka zaka kirani. Yace saboda baki damu da asaya din bane yasa na sa a sayo min tace wace yar iska ce ta sayo ma cikin kura mashi ido da son jin amsa daga gare shi. Wanan ba matsalsn ki ba ne ke dai kiji da kanki ya fada mata yana kokarin mikewa tsaye samad mai kake nufi dani ne wai ? Da akayi may kuma yanzu tace ban fa gane inda ka dosa ba gaskiya da irin wanan halin naka yace saboda baki son gaskiya ne yasa na canza nima. Kana nufi nice mai laifi yanzu aike ma kin sani idan kina son mu shirya dake to ki canzs ke ma yaushe rabon da na karya a gida na in ba yau ba da mommy tazo. Dama nasan abinda ya kawo su ke nan ai hadin fada a tsakanin mu in bashi ba may zai sa su kwaso kafan su suzo nan wai sai na haihu. Yace saboda ina dan su kuma ni na bukaci haka a gare su tunda ke baki san komai ba sai bakin yawo da lalaci kawai da kashin kudi. Nice mai kashin kudi murushi yai mata yace ko yanzu ma nasan amsan kudin ne ya kawo ki ai ba wani abu ba tunda baki damu da damuwa na ba. Kaine dai ai naga kamar kana gudana yanzu nan dai suka shirya ranan ace tsakani miji da mata sai Allah suka manta da komai a ransu. Washe gari mommy ta sake hada masu break fast mai rai da lafiya tasa Aisha ta gyara dining din aka jera kkmai a yadda ya dace ta aikawa su hadiye da nasu. Tare suka sauko suka karya a tare sai hadiyan abincin take ba kunya ko wani nauyi a tare da ita bayan sun gama ya fita zuwa wurin aiki. Sai lokacin Nafisa ta kalle gefen dakin da su mommy ke ciki ta kira hadiya ta rufe mata kofan kitchen da store din gidan gaba daya. Da rana mommy ta turo Aisha ta gyara mata kitchen din sai ta samu gurin a rufe ta koma ta fada ma mommy. Mamaki ne ya kama mommy ta kira hajiya mama tana fada mata abinda Nafisa tayi masu ita kuma mama ta kirashi inda take shiga ba nan take fita ba tace maza ya dawo dasu gida tunda yasan gidan shu ba a hannun shi yake ba ya dauke su. Hakkuri ya fara bata yace zai dauki mata hakan tace ya yake son yi idan Abban su ya samu wanan baki labarin dama abinda yake ma gudu ke nan ya hana su zuwa tu farko. Hakkuri ya dinga bata har ta saurara mai tace tana jiran taji matakin da ya dauka a gidan idan ba haka ba zata fada ma Abban su abinda ke faruwa kada yaji a gurin wasu. Yusuf yana zaune yana sauraren su yana kashe waya ya dago idon shi da suka kade sukai ja yace wai may Nafisa take nufi da nine ? Guri ta samu take wanan abin mana Yusuf ya bashi amsa yace in bashi ba rashin mutuncin nata har yakai ga su mommy kuma yanzu. Mommy ne zata rufewa dakin girki bata girka ta basu ba basu damu ba suna yi kowa kuma yaci har zata rufe kada suci su kwana da yunwa komay ? Tasan yadda Abba yake ji da iyalin shi kana zaton da ba mommy bace in anty amarya ce Abban zata kira da kan shi ta fada mai kasan ko yau ba zata kwana gidan ka ba. Wallahi idan zaka kara aure ka kara shine kawai mafita ga wanan shu,umar mace da ka dauko wai mata bazata taba ganin darajan ka ba idan ba ta bude ido tagan ka da wata mace ba a gidan. Idan tana zama ta zauna in bata zama kuma ta kara gaba dama ba akirata ba kutse ne da sa kai irin su ta kallamay kada dadin baki da komai ta aure ka. Kai yace tare da bugun tabur din gaban shi ya mike cikin fushi Yusuf yace ina zaka kuma yanzu ? Gida yace cikin wani irin murya kamar mau zazzabi shima mikewa yayi ya bishi a baya tare suka fita daga office din shiya jasu don Abdul din bai da karfin haka a yanzu. Suna tafiya yana dafe da kanshi ba tare da ya kalle shi ba Yusuf din yace ba irin ku masu sanyin hali ne ya kamata ya auri irin Nafisa ba. Sun fi daidai da irisu wa yanda zasu caja junan su a zauna lafiya amma ai dama ita haka suke so su samu wanda suke juyawa son ran su. Yanzu ai ta fara koya min iya magana ita da wanan yar matsalan khadijan din nasan idan an auna ni za a samu VP dina ya hau wallahi Yusuf damay Nafisa take son inji ne wai ? ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU[25/10, 7:29 am] +227 98 36 59 34: Suna shiga gidan su Nafisa ne zaune a falo da yan uwanta sai wata bukuwa da tazo mata a lokacin wace bai san ko wacece ba. Sun fara gaida shi sai dai ita bata dago kai ta dube su ba ganin su tare da Yusuf da taki jini da tayi don a cewan ta Yusuf ne ke kulla mashi duk wani shawara a gamay da ita. Shima Yusuf din bai tsaya ta kan su ba ya wuce dakin da su mommy suka sauka dauke da ledan take away da suka sayo masu a hanya. Nafisa may ne hujjan ki na rufe kitchen da kikayi yau tace saboda gida nane yasa na rufe don ina da ikon yin hakan ko ? Idan abinci yayi saurin karewa wa zaka tambaya yadda akayi dashi ai naga da kawo abincin sai da ka kirani ai in gani ko ba haka na bane ? Nafisa lalai wuyan ki ya yi kauri a gidan nan har da zaki iya rufe ma iyayyena wuri kada su dafa abinda zasu ci ko suyi amfani dashi. Amma ba laifin ki bane laifina ne da na sakar maki wan har kike ganin kin isa kike son wuce gona da iri a gidan nan da rayuwa na. Baki dafa kin basu ba sun dafa ma kansu kuma kinyi bakin ciki da haka da suke yi ko kin mata nan din gidan dasu ne halal malal suna da iko da komai yadda suke su. Ai ban sani ba sai yanzu da ka fada a gaban kowa nasan yan uwanka sun fini muhinmanci a gare ka yace da may kike daukan kanki ne. Tace ai sai su fito mu zuba dasu a gidan bansan ka kawo su nan bane don su kara dani tsawa ya daka mata cikin kiran sunan ta da karfi. Mikewa tayi da kyat itama tana fadin ban san sun isa da kai ba sai naga muna raba kwana a gidan nan dasu. Haka kike ce tace an fada din yace bada su zan raba maki kwana ba amma ki sani zan kawo wace ta dace in raba maku kwana gidan nan wace zakuyi daidai da fitsaran ki. Su wa yan nan iyayye nane yanzu na kawo amma mai zuwa in raba maku kwana tana tafe kwanan nan. Madam ne dake zaune ta mike tana fadin Nafisa kina da hankali kuwa kin san may kike shirin aikata ma kan ki yanzu ? Ta figi jakkanta dake aje gefen kujeran da ta zauna tana fadin ni na tafi tunda baki da wayo yace bata san bata da wayo ba yanzu ne zata sani. Waya ya ciro daga aljihun shi ya fara fadin hello inspector kana jina wasu froriners nake son kazo ka kwashe a gida na yanzu don Allah. Jin haka duk suka mike tsaye don da a zaune suke gefen guda sun zuba masu ido suna sauraren su madam ce ta fara bashi hakkuri da fadin. Assha Alhaji ai a bin bai kai haka ba basai ka kira hukuma a cikin zancen iyalin ka ba anan akayi sai a sasanta shi a nan Nafisa kin yi kuskure ki bashi hakkuri ke kuma. Bani taiwa laifi ba su da ta bari da yunwa tun safe ne za ta ba hakkuri tace ni ban masu komai ba balle in basu hakkuri. Yace da kyau mommy da suke daki da Yusuf suka ji hayaniya yai yawa a gidan yasa suka fito daga dakin gaba dayan su. Sun fito daidai lokacin da take fadin batai masu laifi ba bazata basu hakkuri ba mommy tace Nafisa kinyi kuskuren ki ba mijin ki hakkuri mu namu mai sauki ne. Don shi muka zo gidan nan kuma da bakin shi yasa muzo ba wai haka kawai muka kwaso kafan mu zuwa nan ba tunda mun san baki son wani nashi ya rabe shi yasa kowa ya sallama maki shi yanzu. Shigowan inspector din da wasu polisawa uku ne ya ruda Nafisa da da ta dauki abin da burgan maza yake mata sun gaisa ya nuna su Yanyala da su hadiye yace gasu nan . Yar uwar su na aure suka zo suka tare min a gida ban san dalilin su nayin haka ba sai ku tambaye su hankalin kowa a falon ya tashi ya juya gurin su mommy ya fara basu hakkuri. Mommy tace mu bakai muna komai ba don wurin ka mukazo dama ba wurin wani ba macen police din ne ta fara ingiza keyan su hadiye gaba. Samad kayi hakkuri don Allah ba sai ka wulakanta min yan uwa ba don ni suka zo gidan nan sai ka hada dani duka kace a kwashe mu. Bissimila yace idan haka yafi maki yan uwa na daine dole na a yanzu gidan nan na kuma gwada maki haka kina iya binsu ga hanya nan a bude ya juya gurin police din yace ku tafi dasu duka. Samad ni zakai wa haka ni zaka fada a kwashe mu a tafi damu babu ko nauyin haka a bakin ka kake fada. Ke uwata ce ko may ko ajeni kika yi a gidan mara mutunci kawai ya juya zai fara tafiya da sauri tasha gaban shi tana fadin kuskure ne nasan nayi ba daidai ba don Allah kayi hakkuri. Madam tace tun farko da haka kikayi da abin baikai haka ba ya nuna su mommy yace su zaki ba hakkuri bani ba ai. Mommy kiyi hakkuri kisa baki a maganan nan don Allah mommy tace naji zan bashi hakkuri amma haka ya zama ishara a gare ki gaba. Nan Abdul din ya dage sai idan ta basu hakkuri zai jaye maganan tace cikin dukawa mommy kuyi hakkuri nayi kuskure don Allah. Iyan bawa tace amma ke kan anyi mutumiyar banza a nan yanzu baki ji kunya ba don Allah ga yan uwan ki ko ina a gidan baki bakin ciki da cin su ba sai mu da mukazo zama daku na dan lokaci. Dan mune fa mai dukiyan da kike kadagi dashi din har kike ganin kowa ba kowa bane a gurin shi sai ke da yan uwan ki keda iko komai dashi. Nan suka kaita fada mata abinda suke so a cikin nasiha tace ayi hakkuri zata gyara yusuf ne ya sallami yan sanda suka wuce. Ranan dai anyi ta ba dadi a gidan tayi nadama tayi bakin ciki abinda Abdulsamad din yayi mata a gaban kowa ya nuna bata da wani power a gare shi yanzu ga madam ma tayi fushi da ita ta tafi tana fadin ta bashe su a idon duniya. Ta kula wanan ta kwance wancan haka na ta wuni da sake sake a ranta a kan sai ta rama abinda yayi mata akan su mommy din da suka zo gidan don ganin bayan ta. Ita sam bata dauka don dan su da taimakon ta suka zo ba har yanzu don idon ta ya rufe da son bata kaunar taga wani wanda ba nata ba ya rabe shi saboda tsananin kishi da take dashi irin na buzaye. Ta kira madam ta bata hakkuri har suka shirya take anan kuma suka fara sabon shirin da zasu aiwatar a kan kowa ma daga bangaren shi. Shiko a bangare shi ranan daki ya shige bai son yawan hayaniya da kowa don haka ya ke be kan shi a daki ba abinda yake sai tunanen hanyar da zai samu mafita ga alamarin Nafisa. Saboda yasan ba canza halin ta zatayi ba kwanto kawai tayi a yanzu tana nazarin ta idan zata biyo mashi ne. Allah ya gani yana son ya kara aure kamar yadda Yusuf yasha fada mai shine kawai mafita gare shi akan Nafisa to amma wa zai aure din da zasuyi daidai da Nafisa a zauna lafiya. Khadija ina khadija karama ne sosai ga Nafisa da halinta ba zai dauko yar mutane ya jefa a matsala ba ya cuta mata don yanzu yana jin yarinyar a wani bangare na rayuwan shi . Don haka ba zai cuta mata ba ta wanan hanya na hada aure a tsakanin su wani abu yazo ya samu yar mutane a hannun shi. Ga mahaifin ta ko yaushe sukai waya yana mashi godiya akan kyautatawan da yake ba yarsu wace kamar kauna take a gareshi. To amma kuma ga shakuwan da sukayi taya zai iya rabuwa da khadija a yanzu nan tunanen irin rayuwan da suke yi da khadija din ya fado mashi a rai abinda ya sa shi dan murmushi ke nan kadan ya gyara kwaciya yana lumshe idanuwan shi. Wayan shi ne ya yi tsuwa alaman kira na shigo mai ya dan juya ya daga wayan Queen of matsala ya gani da sauri ya daga kiran nawa. Tambayan shi nayi lafiya kake kuwa yau ? May kika gani ya bani amsa dashi sai na rasa abinda zan fada mashi karya na samu kaina da yi nace kawai dai sai nake tunanen hakan . Fada min kewa na kikayi ko may kika kirani a cikin wanan daren haka baki san ina da mata bane ni Family man ne idan kika hadani fada da mata na fa ? Wayan na kashe ina ci gaba da tunanen mafalkin da nayi dashi a yanzu daga dan barci ya dauke ni sai wanan mafalkin yazo min gaba daya na saka waya na a off na gyara kwanciya cike da zullumi ina tunanen mafalkin. Can dai barci ya dauke ni na manta da zancen mafalkin koda na tashi naci gaba da alamura na shima kuma bai kira ba don haka na kara share shi. Nafisa ko hankalinta bai kwanta ba gida Niger ta kira mai mata aike a can da kukan ta wiwi matar tace may ke faruwa Nafisa ko sakin ki mijin ki yayi ? Tace bai sake ni ba serah sai dai gaba daya ya canza min yanzu nan dai ta koro mata bayanin abinda ke faruwa cikin kuka. Serah tace share hawayen ki Nafy murde dan iska zamuyi ya koma sai yadda kika ce a gidan ki bai isa ba wallahi yanzu dai ki daure kibi yan iska yan da suke so daga yau zan shiga in fita zaki gannin nan da kwana uku kedai turo min da kudi kiga aiki da cikawa. Tace serah har kin kwantar min da hankali na wallahi don yanzu ni damuwa na bai wuce cikin nan dake jikina ba don cewa ake wai idan mace nada ciki ko jinin haihuwa wai komai nata baici. Serah ta katse ta da fadin da ke nan wanan zancen yanzu may ye kudi baiyi Nafy ina nan shigowa nan da kwana uku kada kiji komai. Bayan sun gama wayan ta zauna ta zabga ta gumi ta rasa ta ina zata fara da shi zata fara ko da iyayyen ko wanan mugun abokin nasa da ta tsana. Zaman gidan yanzu haka ake yin shi ba ruwan wani da wani sai gaisuwa a tsakanin su dasu mommy kowa na harkan gaban shi. Shiko yana tsananin basu mommy girma da kulawan da ya dace a gidan wanda hakan keyi wa Nafisa ciwo matuka ta rasa yadda zatayi dasu a gidan. Kunci cikin zuciyar ta ba a maganan shi har yakai bata iya boyewa hakan yasa ma ta daina yawan saukowa kasa inda zata gan su ko wani abinda sukeyi shiko sam bai kula da halin da ta jefa kanta a ciki ba yanzu. Kamar yadda serah tayi alkawari haka ya faru tazo da kule kule da sihiri kala kala tun a ranan suka fara aiwatar da komai kamar yadda suke so ya tafi. Nafisa sai gani take har aiki ya fara ci saboda yarda da tayi da maganin don irin labarin da Serah ta bata yadda ta shiga kungurumin dajin kasan su wurin samo mata wanan asirin mai amfani da ci da sauri ga wanda akaiwa. Haka kawai yake ji kwana biyu yana jin haushin kowa a gidan inbanda Nafisa da yanzu yake jin wani irin so da kaunar ta yana shigan shi. Mommy dake da kaifin basira ta fahinci abubuwa suna sauyawa a gidan don haka ta fara tuntubar Iyan bawa akan abinda da ta fara hangowa ga dan nasu don tun zuwan Serah mommy tasha jinin jikin ta da ita don tsarin ta da zubin ta yafi kama dana yan duniya ta irin mutanen su. Batai kasa a gwiwa ba ta sanar da mahaifiyar shi hasashen ta amma tace kada ta bari kowa ya fahinci abinda ta fada mata ta dai taimaka mashi da addua. Hajiya mama tayiwa mommy godiya bayan sun gama tataunawa akan zancen sukai wa juna sallama aka aje wayan. Sosai hankalin hajiya mama ya tashi da maganan mommy haka yasa ta kira yayan ta da suke uwa daya uba daya a zaria tana neman shawaran shi. Yace ta bari zai ga wani malamin shi a nan cikin garin zaria da zancen don rayuwar Abdulsamad da wanan matar tashi yana bukatan addua sosai. Haka suka bar zancen akan zai kira ta taji duk yadda sukayi da malamin nashi idan ya dawo daga wurin shi. Ban san mun shaku da shi ba sai wanan karon ga jerabawa ya na gaba to muna ga zancen zuci dake damuna haka ya dan sani rama kadan. Karshe nabawa kaina shawaran abinda ka fisheni na watsar da komai na rugumi karatu na gadangadan ina yi tare da share zancen su gaba daya a raina. Ranan muna zaune da Maryam a dakin ta tsifar kaina na ke da ya kitso ya tsufa min zan je in wanke kai na wayana yayi tsuwa na duba Yusuf ne a kan layin. Nayi mamaki kwarai da ganin kiran shi a wanan lokacin na dauka da sallama tare da gaida shi ya amsa yana fadin kanwa ta ina kika shige haka ? Kai yaya Yusuf ina nan inda nafi karfi mana na bashi amsa yace ko dai mutumin nawa ya boye muna ke ne ban sani ba ? Wa ke nan kake magana nima na tambayeshi yace abokina mana kuma ogana a wurin aiki nace wai mijin buzuwa kake magana ? Dariya ya kyalkyale dashi yace kai khadija baki da dama wallahi har yanzu dai mijin buzuwa aiko zaku kwasa dashi idan ya jiki. Nace ina ruwa na dashi balle balle ya jini . Yace ke ko keda ruwa dashi khadija yar mama amma dai baki da kirki Abdul din ne zaki ce yau ina ruwan ki dashi da bakin ki kike fadin haka . Tsuki naja na tabe baki kamar yana gani na a lokacin nace ni na fita batun shi yanzu banda lokacin shi. Yace subbahanallahi may yai zafi haka ne a tsakanin ku kuma keda mutumin naki khadija ? Mutumi na ko naka yaya na kai nifa ko wancan lokacin da nake kula shi albarkacin ku ya samu a gare ni har na biye mashi amma ba don shi ba. Kai haba yar mama bai dace ki fadi haka ba tsakanin ki dashi yanzu ai kunyi nisa sosai bai kamata aji wanan maganan ba a bakin ki. Taimako fa kikace zakiyi sai da abu ya kusa kai karshe zaki ce ba ruwan ki dashi yanzu ai ko kece mai ruwa har da tsaki akan shi yanzu. Mu dai bar wanan zancen nace dashi da sauri yace akan may zamu bari idan na tambaye ki zaki fada min gaskiya ? Nace akan may ke nan yace akan mutumin naki mana nace idan na sani may zai sa na boye maka kuma ? Yace Yaushe rabon da yazo gurin ki ko kuyi waya dashi when last kukayi koda waya ne please kada ki boye min komai just feel free with me khadija? Dan jin nayi sai can nace gaskiya mun kwana biyu dashi don ba zan iya tuna zuwan shi gurina ba na karshe ko wayan shi a yanzu. Yace abinda nake son ji ke nan daga bakin ki sai dai zan ari bakin aboki na inci mashi albasa Abdulsamad yayi tafiya two weeks ago amma dai yanzu ya dawo. Sai dai ko a yanzu da bukata nazo maki a kan shi don gaba daya khadija ba zan boye maki ba Abdulsamad ya canza ga komai cikin yan kwana kin nan. Gashi matar shi na shirin haihuwa watan ta ya tsaya tun last month sai dai har yanzu bata haihu ba yana gida ko wani lokaci tunda ya dawo like da ita. Katse shi nayi da fadin ni may ye nawa a cikin zancen nan kuma can su karata shi da ita tunda shi ba tsayayyen namiji bane ko yaushe. Namiji ne mana khadija ai shiyasa na kiraki don ki sheda mai cikin wanan wasan da kuke yi don ya farga ga abinda yake yi din. Ni tsoro na shine kada su mommy daya dauko gidan shi su fahinci susucewar shi a kan wanan shuumar matar tashi sugane gazawan shi a gaban kowa. Shiya sani mana tunda shi ke ji a jikin shi ba wani ba yayi saurin fadin a a khadija ba haka zamu yi ba daurewa zakiyi mu fitar dashi daga wanan kangin don Allah. Ni haba yaya Yusuf ni may zan mai kuma shiya sani don Allah khadija dakata ki saurare ni don Allah nace ina jin ka ai. Zaki iya hakkuri ki daure ki kirashi a waya ki fada mai magana daya wanda zai shi ya natsu ya dawo cikin hankalin shi yanzu don ke ce kawai mafitar da nake dashi bayan Allah. Ni kuma why sai nice mafita akan haka yace saboda ban taba ganin wani ko wata dake fada mai magana yadda kike fada ba azauna lafiya kuma yai amfani da abin da kika da mai a zauna lafiya. Dan jin nayi ina tunane yace kada ki karaya khadija don nasan zaki iya ki taimaka muna please wanan taimako ne indan kin yarda. Yaya Yusuf wanan ya zama na karshe da zan ma wani alfarma akan wanan mutumin don gaskiya baida niyar canza halin shi nake gani . Khadija ba laifin shi bane shu,umar mace ya hadu da ita take juya shi yadda take so nace har da halin shi a haka. Kin yarda zaki taimaka muna ke nan nace naji zan gwada don Allah don kai amma da ba haka ba babu abinda zai kara damuna da rayuwan shi. Nagode kwarai da hakan da zaki min don wanan ne kadai hope din da nake dashi yanzu akan wanan matar tashi. Ina aje wayan maryam dake zaune ta kura min ido tana sauraren maganan da muke yi din tace kai wasu maza suna haduwa da shu,uman mata wallahi. Koda yake ba abin mamaki bane ga wanda yasan mazajen da ke auren irin yan yaren buzaye zai san mazan ne a kasa matan suna sama. Sai abinda sukace komai su mamaye na miji yazama nasu su raba shi kuma da kowa nasa sai su da yan uwan su zasu dinga bushasha da shi da dukiyan shi. Sai dai kima sam basu son auren mazan yaren su don irin bakar wahalan da suke sha wurin su amma namu mazajen su ke kwadayin matan buzaye saboda bakar jaraban da suka iya. Yanzu dai kira shi muji yadda zaku kwashe a tsakanin ku don nasan akwai drama nace ni wanan daure ni suke son yi maryam. Ban san may yasa suke cewa wai sai nice zan iya masu haka ba bayan yana da kanne mata da yan uwa da zasu iya. Su iya may khadija ai abin sai da hikima ke fa ba yar uwan su bace kin ga yadda kuke moved dashi kamar saurayi da budurwa ne. Ke komai zaki iya fada mashi a zauna lafiya wani dan uwa idan yafa da sai inda karfin shi ya kare ke ko sai ki fada mai a wasa bai dauki abin da zafi ba. Wayan ta na karba ta hanyan yi mata karya wayana ba kudi a ciki tace ai bai san layi na ba don haka ba lale bane ya dauki kiran . Bari dai mu gwada mu gani idan bai dauka kiran har ya kusa karewa ya daga tare da fadin hello nace dole zama da yan haure ya kowa ma wani akidar banza. Wake magana please ya tambaya nace wata buzuwa ce ko kana son kari su zama biyu a gidan ka murmushi yayi yace khadija nace ba ita bace. Kina zaton muryan ki nan zai bace min ne nace marya na yana kama da na buzaye ne ? Yace ai kamar ma ta baci baki ganin zubin ku daya dasu sai dai yaren da baki ji nasu kai malam ni kiran ka nayi naji ko mommy ta koma ne? Don nasan ba lale bane buzuwan gidan ka ta barsu su dade a gidan yace idan kina son sani kije gidan ki duba mana. Ban tashi ba ne da zanje yace ya kike nace ina nan yarda ka sanin a baya ke ba a maganar girma da arziki dake ne ? Nace banson don ba gaisuwa na kira ka muyi ba ko tambayana yaya ni yace ai kogi ba ki dadi ba ko nace . Wani kogin ke nan dai wani ko wani ruwa ne ya shige shi in ba nasa bane amansa yake yi don haka ba gaisuwan ka nake nema ba. Yace becareful nace a nan ko sai kaga mutum har mutum amma a gidan shi sai ka rena mai wayo idan kaga abinda yake yi. Ta yaya bakin haure har zasu shigo su samu mutum a gidan shi in ba samun wuri ba suce sai abinda suke so zasu mai ni wallahi na dade da raina aya don tsakuwar ta. Yau hausa kike ji ke nan nace daurowa ne hakan adai ji tsoron Allah kada mutum ya zauna mace ta mayar dashi saniyar tatsan ta . Ba mai ci sai ita da yan uwan ta kadai yace kina son wani abu ke nan nayi saurin fadin haram wallahi adai ci lafiya. Ga yan ketare nan suna taya ka ci idan ka wawuro su kuma sai su cafke ranan na zuwa da zan maka irin ku kotu masu ba bakin haure makafa suyi yadda suke so da dukiyar kasan mu. Yace magana kike ji ke nan dai nace ba wani magana sai fadin gaskiyan da na saba kulun idan naga anyi ba daidai ba. Ya Abdul ace mutum baiwa kansa adalci kulun sai abinda mace ta dora shi a kai yake bi yace wai may kike nufine don na rasa gane ida maganar ki ya doso har yanzu. Mafalki nayi naga ka susuce kazama bawan mata sai goyon su kake yi a bayan ka ka manta da kowa na naka sai masu jajayen kunne kasa a gaba. Murmushi yayi yace ki fito fili kice kin yi kewa na kawai kin tsaya kina dora wa wani laifi kuma ko na kulata ba mata na na kula ba na kula matar wani ne ? Mata wai mata matar namu duka dai inji manya mata kan tana kaduna ka barota can wanan ai ta bugi ne . Khadija you are very stupid matar nawa kike aiban tawa a gaba na nace ko a idon ka sai na fada don gaskiya ake fadi. Namiji kamar mace baida say a gidan shi sai na mace macen ma abin kyamatar mu gaskiya ka gyara halin ka sai anjima nayi saurin kashe wayan batare da najira amsan da zai fada min ba. Wanan yarinyar ta ci uban rainin wayo wallahi yace Yusuf da ke zaune gefen shi yana murmushi yace khadija ce halan ? Wa kasan zai min wanan idan ba ita ba ban san mayeatsalar ta da Nafisa ba ko da yake su mata haka suke dama ko Nafisan da tasan da zancen khadijan Allah kadai yasan iya boren da zatai min. Kana zuwa gurin ta ke nan har yanzu ya danja tsuki yana fadin wallahi na dade ban ganta ba tunkan naje Lesvegan rabo da na ji daga gare ta. Yusuf yace ai gashi yau ta kiraka ita yace ta kirani taci min mutunci ba sai nayi maganin yarinyar nan wallahi ta raina ni da yawa I don't know why take min abinda taga dama haka ? Kun fi kusa ai bani shiga tsakanin ku yanzu ai wani kallo yaiwa Yusuf din yace tunda ka gama hadawa ba ai ka fadi haka yanzu ? Au ni ma hada ke nan ashe wa ya manna min wanan chewing gun din idan ba kai ba ina zaune kalau abina. Amma ai tayi muna rana ba kadan ba kasan da hakan dai ? Tsuki yaja yace ban san ya nakoma ba wallahi yar karamar yarinya ta shige min na kasa yin komai akan hakan ? Kun dai shige ma junan ku yanzun ne kuma kake neman maraba da ita ko why zaka so ka rabu da khadija bayan kasan tana da amfani a gare ka ? Amfani fa kace Yusuf yana kallon shi da idon shi da ya kafa mashi sai da Yusuf ya rausaya kai yace kafini sanin haka malam. Kada ka bari shedan ya rudeka kaiwa kan ka hasara zukekiyar yarinya kamar khadija may kake fadi ne wai Yusuf ? Kiran kawun shine ya katse masu magana da mamaki a fuskan shi ya furta kawu habu yau lafiya kawu ya kirani haka ? Ya dauka suka fara gaisawa da kawun nashi wan mahaifiyar shi cikin kunya da nauyin kawun nashi yake amsa mai gaisuwan. Don ya manta yaushe rabon shi daya kira shi ya gaida shi a matsayin shi na wan mahaifiyar shi da take ji dashi a cikin yan uwanta. Bayan sun gama gaisawa ne kawun nasa yace dama na kiraka ne idan da hali ina son ka shigo kaduna a cikin wanan satin . Da mamaki ya tambayi kawun nasa yace kawu lafiya ko yace a, a lafiya kalau sai alheri akwai abinda nake son kayi ne idan kazo amma fa idan ba takura. Haba kawu ba komai in sha Allahu satin nan zan shigo ranan jumma, a asabar zan karaso zaria in gan ka kawun nashi yace nagode Allah yayi maku albarka ya kara tsare muna ku. Ya amsa da amin kawu na gode ya aje wayan yana mamakin maganan da kawun nashi ke dashi akan shi Yusuf dake gefen shi ne ya tambaye shi ko lafiya. Yana mai da kan shi bayan kujeran da yake zaune sama yake fadin wallahi ban san abinda yasa yake nema na ba a yanzu. Zamu tafi karshen satin nan don haka sai ka shirya muna tafiyan yadda ya kama sai dai ban so tafiya yanzu ba a yadda Nafisa take haka haihuwa yau ko gobe. Zamu iya zuwa muyi kwana daya idan hakane sai mu juyo idan ka gama ganawa da kawun. Yace hakan za ayi Allah ya kaimu lafiya gaba daya har ya manta da zancen wata khadija ko don mantuwan da yake fama dashi a yanzu. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU [25/10, 7:29 am] +227 98 36 59 34: Tunda mukai waya da Ya Amina tace min bata da lafiya sosai sai naji hankalina bai kwanta min ba ina bukatan zuwa kaduna weekend in dubata. Kwatsam aka wayi gari inace wa maryam kaduna zan tafi yau in duba jikin Ya Amina da bata da lafiya tace shine baki fada min zaki tafi ba muje tare . Nace kada ki damu watarana mu tafi tunda muna tare ai har bakin titi ta rako ni na shiga mota ta koma ita. Da wuri na isa don sammakon da nayi na samu jikin nata da sauki sosai na fahinci ciki ne ta samu ashe yana bata matsala dama haka take ciki da wahala ita. Gidan da bai samun gyara saboda laulayin da takeyi yasa gidan yayi datti da yawa sai da nayi wa gidan tas na yi wanka na kwanta don in huta. Tunda ya fara shiri Nafisa take tsaye a kansa tana fada dashi akan may zaiyi tafiya yanzu bayan yasan halin da take ciki zata iya haihuwa ko yau ko gobe. Ya dago yana ce mata tafiyan ya kama shi ne dole don haka na fada maki gobe zan dawo insha Allahu may nene kuma na fada yanzu. Tace yanzun dai baka damu dani bane ban san may kake yawan zuwa yi gida ba akai akai haka ? Au ke da kike zuwa gida wani abu kike zuwa yi a can tace zaka hada kaina da kaine nifa kasan ba nan iyayyena suke ba ya zama dole in rika duba su a kai akai. Da kyat ya samu ta barshi zai tafi koshi don yace aikin shine zai sa ya tafi yasa Nafisan ta daga mai kafa. Da suka isa kaduna zaria suka wuce kai tsaye don ganawa da kawun nashi dake neman shi ida sukai saa sun samu kawon a gida wanda ya nuna jin dadin shi da amsa mai kiran da yake mai din. Bayan gaisuwa sun natsu ne kasun ke fadin ba wani abune yasa na kiraka ba sai yar wata magana da ta taso daga mahaifiyar ka a gamay da kai. Zama ya gyara don ya saurari may mahaufiyar nashi hajiya mama tazo ma kawun nashi dashi duk sunyi tsit suna sauraron kawun. Yace tazo nan ta samay hankali a tashe take fada min abinda ke faruwa dakai na rayuwa musanman da kai da iyalin ka. Dama yasan maganan ba zai wuce wanan ba ai yace cikin karfin hali kawu wani abin tace nayi kuma yanzu ? Yace eh to tace bata ce ba kasan dai tsakanin da da mahaifi akwai wani kulawa da damuwa na musanman shiyasa tazo min akai ya kamata a taimaka ma da addua da wani taimako. Shine na kwantar mata da hankali nace zan yi wani abu akai don kasan naka sai naka a yadda naga damuwa a tare da mahaifiyar taka. Yasa bayan mun rabu naje wurin wanj malami tsohone aminin mahaifin mu tun yana raye nakai mashi wanan matsalar taka. To Alhamdullahi ya karbi maganan namu sosai da muhinmanci ida ya ce in bashi sati hudu zaiyi istihara sai a san abinda za a yi bayan satin hudun dana koma sai yace dani yana bukatsn ganin ka sai kazo da kanka zakuyi magana dashi. Wanan ne yasa na kiraka don kazo ku samu ganawa dashi kaji may zai fada maka sai musan mafita ga zancen. Zama Abdulsamad din ya gyara acikin ranshi yana fafin ikon Allah ita kuma mama tanan ta bullo min kuma yanzu bayan tasan ban son irin abubuwan nan tun farko. Amma a fili cewa yayi to kawu ba matsala amma dai sai dai ina fata aikin shi ba na kaucewa Allah bane dai ? Murmushi kawun nashi yayi yace haram haram kana ganin munyi kama da masu kaucewa alamarin Allah ne ya kamata ka shedi mahaifiyar ka kasan halin ta. Yanzu haka ma bata san komai ba tukun a wanan zance nafi son muyi magana ta maza da maza kafin ta samu labarin komai. Yace hakan na dakyau kawu don nima ban isa can gurin su ba tukun nan muka fara zuwa yanzu sai mun koma zan isa gidan. Tashi sukayi zuwa gidan tsoho malam illu don su gana dashi sun samu yana ganawa da wani babban mutum don haka suka zau a motar su suna jiran fitowan mutumin. Bayan mutumin ya fito ne kawun nashi ya ce su taso su shiga daga ciki suka fito daga motar zuwa ciki amma sai Yusuf yace zai jira shi a waje. Ya juyo yana fadin haba haba Yusuf ya zakace haka kuma mushiga don Allah zai fi akwai abin da baka sani bane nawa. Kawun yace mu shiga mana ai ba komai bane wanan mushiga daga ciki kawai mugan shi. Cikin suka shiga tsohon yana kishingide saman farin buzu irin na dabbobi da malaman da ke zama a sama. Yana ganin su ya dan dago daga kwanciyan manya da yayi nan suka zube don girmamawa suka fara gaida tsohon yace salihu kune tafe yanzu ? Yace eh baba yaron da kace yazo ne dan wurin ita kanwar tawa hafsat yazo yau daga can abuja inda yake aiki don amsa kiran da kai mashi din. Tsohon ya daga kai yana kallon su Abdul din yana jijiga kai yace Allahu Akbar yanzu wanan jikan mahaifi ku ne Allah ya jikan malam shaibu suka amsa da amin . Ya dauko wani tasbaha ya rike a hannun shi ya dan murza ya mikawa Abdul din baya ya ce shine wanan din ko kawu salihu yace shine baba. Yace canki daya a nan yana mika mashi tasbahan dake a hannun shi Abdulsamad din ya mika ya zabi dayan dan tasbahan tsohon ta girgiza kai yana murmushi. Ya dago kai yace Abdul yake ko yace eh Abdulsamad yake sunnan kakan shi yaci na wurin mahaifin shi yace to kamar yadda na fada ma zanyi istihara akan jikan nawa Allah ya bani iko nayi. Sai dai naga abubuwa da dama da suke faruwa da jikan nawa wanda da farko zan iya cewa akwai sakaci aciki alamarin jikan nawa. Abdulsamad yaya akayi kabar gida haka kana dan musulmai jikan malamai kamar mu kabar abubuwa suka cabe haka a lokaci daya gare ka. Zama Abdul din ya gyara yana sauraron shi maganar da ta fara zuwa bakin tsohon shi ne na fitar da yayi zuwa kasan waje satin da ya wuce zuwa wasan da suke yi acan na milloners in world. Zufa ne ya tartso mashi a goshi yadda tsohon ke bashi labarin abinda ya faru acan har ya fadi a wasan ya dai san babu wanda yasan wanan abin don ko Yusuf baida labarin abinda ya faru can sai ga wanan tsohon na bashi labari tiryan tiryan. Bayan ya kare mai wanan bayanin ya dago ya kalli Abdul din wanda kanshi ke kasa yana tunane yace sai kuma maganan da ya shafi iyalin ka yanzu. Malam ya danyi shiru na wani lokaci ya sunkuyar da kan shi kasa kamar mai nazarin wani abu yana kada kafan shi jefe jefi yace. Yace gaskiya nayi istihara a kan ka sai dai abinda zan fada ma ba lale bane ka yarda zaka iya zuwa wurin wani yai maka ko kai kayi da kan ka don zaka iya istihara ba abu bane mai wuya idan mutum yasa kansa yi. Yusuf ne yace malam ba matsala ai zaka iya muna bayanin abinda ke nan yanzu don musan abinda ke nan. Malam yayi baiyananen murmushi ya na gyara zama yace bani hankalin ka nan ka saurare ni da sauri suka dago suna sauraren bayanin shi. Yace abinda nagani a satin farko shine kana tsare a karshin wata mace fara doguwa sai kayi kamar zaka kubce daga sherin ta sai ta sake sabon shiri a kan ka ta kara daure ka. Sai dai dana sake yi naga wata yarinya fara itama a cikin rayuwan ka ban sani ba ko kasan da ita ko baka sani ba tana nan dai yar matashiya ce haka da ita. Sai dai ina ganin itace kamar warakan matsalan ka watarana amma dai ban sani ba Allah masani. Sai wanda nayi a karshen nan ya nuna min cewa zaka kara aure wanda haduwan ka da yarinya alheri ne sosai sai dai akwai matsala daga wurin wanan matar taka . Zaka kara aure nan bada dadewa ba zai zams maka alheri dan yarinyar mai biyaya gare ka ta kawo karshen komai a gare ka don arzikin ku yazo daya da ita sosai. Duk zauren akai shiru ana sauraren tsohon sai Abdulsamad wanda ke shatan zufa daga goshi shi. Malam yaci gaba da fadin sai kayi da gaske ka zama namiji zaka samu mafita don yanzun haka matar da zaka aure ban debe tsamanin ba ayau ko gobe zaku iya haduwa da ita. Yace wanan ke nan bansan abinda yasa yaran yanzu kuke sakaci da ibada ba bayan kuna da sanin da Allah ya baku wanda idan mutum ya rike yanayin sa ba wani shedanin da zai iya tunkarasa. Ya dauko wani abu yace amshi rika nan ya mika hannu da sauri yana karban abinda yake miko mashi din yace yau nake son kayi amfani da wanan abin idan ka isa gida. Zaka shaye shi duka sai ka rage kadan ka wanke fuska da hannayen ka kamar dai yadda kake alwala zakayi dashi sai ka kwanta insha Allahu zaka kubta daga sherin su da yardan Allah. Yace har in kayi yadda nace kayi da yardan Allah ba wani sihirin da zai shige ka koda kuwa sun hada da jinnu da sauran su don kamar ka dafe wani kafa na jikin ka ne da wanan tsarin Allah ya tsare ya kare yace dasu. Yusuf ne ya ce da tsohon malam batun yarinyar da kace fa tana nan kusa tsohon yayi murmushi yace gaskiya tana nan kusa damu a yadda nagani yanzu. Kuma ina sa ran haduwan ku ko yau ko gobe idan Allah ya kaimu sai dai mu bar ma Allah sanin shi. Gaban Abdulsamad din ne ya fadi a ranshi yana tunanen don yana tunane wacece wanan yarinyar da zai hadu da ita yaji har yana so ta. Godiya sukai ma malamin suka kawo kudi suka bashi kai ya kada masu yace ba wanan a tsakanin mu aikai jika nane bazan karbi ko kwandala a gare ka ba. Sukai mashi godiya suka mike zasu tafi sai tsohon yace akwai tafiyan da zai taso maja gashi na gani a gabana kayi kokari kayi wanan tafiyan don zaka samu alheri mai yawa a cikin shi. Ya kara godiya suka fita sai da suka sauke kawu salihu suka kama hanyar kaduna a lokacin yamma yayi sosai. Ba mai magana a cikin su kowa da abinda zuciyar shi ke saka mashi a lokacin don shi da farko bai yarda wai nafisa tana mashi sihiri bane. Ya dauka so ne kawai yake mata na tsakani da Allah mutane ke ganin wai sihirce shi tayi baida ta cewa akan ta sai abinda taga dama takeyi. Amma yanzu sai gashi dan tsohon nan ya jefo zancen ta a cikin maganan shi shi bawai ya yarda bane to amma kuma abinda ya daure mashi kai shine zancen tafiyan da yayi tsohon ya sani. Zai gwada abinda yace don ba a kin ta maya koma maye zai gwada maganin ya gani zai kuma bi a hankali yaga maganan tsohon ko gaskiya ne. Muryan Yusuf ne yaji yana fadin wallahi na dauka khadija ce tsohon nan ya gani a tasbahan shi ashe ma watace. Sai dai wallahi naso ka auri khadija ashe abin ba haka bane muna namu Allah na nasa ne. A tunanen ka ke nan kai ni ban kawo komai ba har yanzu don ba wata mace a gaba na yanzun haka abinda ya damay ni ya damay ni. Koda suka isa dare yayi don haka suka bari sai da safe idan zasu wuce su shiga su gaisa da su hajiya mama. Barci nake bayan na gama mata komai sai na koma in huta can cikin barcin naji muryan Y Amina a kaina tana fadin khadija don Allah tashi ki shiga gidan su mommy ki karbo min lemun tsami. Na dago idona cike da barci nace haba ya Amina nifa ban son shiga gidan nan har in koma tunda ba dadewa zanyi ba. Khadija magani zan hada dashi don Allah daure ki shiga ki karbo min dole na daure na mike ta fita daga dakin ta koma falo ta zauna. Na fito sai take cewa dani wurin hajiya mama zaki karbo min don mommy bata nan tana Abuja gidan Abdulsamad takai wata can an dauka matar shi zata haihu a lokacin suka tafi gashi har yanzu bata haihu ba. A raina nace ai nafiki sani na fita ina ce mata sai na dawo a gidan sunyi mamakin ganina don basu san da zuwa na ba . Sai da nabi kowa na gidan na gaida su na nufi dakin hajiya mama nan falon ta na samay ta na zube kasa ina gaida ita take cewa hadija yaushe a garin ? Nace jiya da safe na shigo nazo duba Ya Amina ce da jiki tace ayyah ai amina taji jiki wallahi haka take cikin ta ita. Nayi murmushi nace tace in karbo mata lemun tsami a gurin ki ne tace to barin in tashi in duba maki ko akwai saura. Sallaman su ne ya katse muna magana ta amsawa tare da fadin yaushe kuka shigo garin nan kuma ba labari don da gani anan kuka kwana. Hajiya jiya muka shigo munje zaria ne gurin kawu salihu sai dare yai muna a can kafin mu dawo cikin fadada murmushi tace toh daga wurin yaya din kuke ashe. Wuri suka samu suka zauna suka fara gaisawa dasu kaina na duke a kasa na somay da gani du sai bayan sun gama gaisawa ne hajiya ta tuno dani tace Aff. Kinga khadija na manta dake wallahi zuwan wa yan nan na bazata da sukai muna da sauri suka kallo ni kowan su na mamakin ganina a dakin mahaifiyar tasu. Mikewa tayi tana fadin khadija ga yayan ku nan wanda ya taba rage maki hanya kwanaki ashe suna hanya suma da kin sani ai dasu kika biyo koda yake kin ce ke shigan safe kikayi. Ina wuni nace dasu cikin jin kunya ban ko saurari amsar su ba na kawar da kaina gefe ina wasa da yan yatsun hannu na. Fita tayi zuwa wurin fridge din ta dake waje fitan ta naji muryan Yusuf yana fadin khadija yaushe kika zo garin nan ne ? Nace don Allah malam ban saku ba ku bari in rabu lafiya da hajiya don kunyar ta nake ji sosai na fada ma wanan aljanna ce wallahi. Inba ba wanda ya saba dashi ba ba zai dauka shi yayi maganan ba alokacin ban basu amsa ba don na hango hajiya tafe da bakar leda a hannun ta. Miko min tayi tana zama tana fadin ki gaida min ita da jiki in na samu lokaci zan kara shigowa in duba ta. Nace to mama an gode na mike da sauri ina barin dakin naji tace yaushe ne zaki koma Abuja ke. Nace gobe zan koma mama tace ku yaushe ne zaku koma tana tambayan su suka amsa mata da yau insha Allahu. Ai na dauka sai goben zaku tafi sai ku rage mata hanya nidai na wuce na barsu nan ina sauri in fice gabana na faduwa da ganin su. Har nayi nisa naji muryan Yusuf a bayana yana fadin yar gidan mama gani fa na biyo bayan ki. Tsayawa nayi ina jiran karasowan shi inda nake ya iso yana fadin surprise to see you dama ashe kema zaki shigo kaduna baki fada muna ba ? Yaya tace bata da lafiya nazo duba ta yace gaskiya naji dadi da na ganki nan nace namay fa baka san ina zuwa nan bane dama ? Yace na sani amma banyi tunanen zuwan ki nan a wanan lokacin bane sai abin ya ban mamaki matuka. Nace zai shige sai mun hadu idan mun koma yace shike nan amma da wata mota kika zo ne nace motar haya mana ina wucewa nake bashi amsa. Naba da baya naji yana fadin zamu biyo mu gaida yayar tamu nace basai kun zo ba an gode na shige gidan ya tsaya yana kallon gidan da na shiga. Abdul ya fito ya samay shi waje yake fadin dama kasan zata zo garin nan ne ita ma ko ta san da zuwan mu ne ta biyo mu. Murmushi yayi mai yace haka dai Allah ya tsara abinsa nima yanzu na ganta wallahi. Ina shiga nace dana sani wallahi da ban shiga gidan nan ba yanzu wallahi ina mika mata ledan nake maganan tace saboda may? Nace wai fa mutanen nan nagani a gida da sauri tace suwa nace su Yusuf da Abdulsamad mana tayi murmushi ta fara bude ledan tace a haka da yawa aiko na gode. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU Ido Ya Amina ta bini dashi kaawai na shige daki iya yanzu haushin su su duka nake ji shiru shiru basu zo ba yasa na saki jiki na koma normal life dina a gidan. Kwana hudu nayi a kaduna na juya na dawo Abuja ban tsaya na sallami kowa ba don dama banda gidan su mommy ban shiga ko ina ba . Tafiyan marance nayi don ban da kaya a tare dani ba zansha wahalan zuwa hostel ba daga inda na sauka. Maryam ta tare ni da murna tana fadin wallahi har hankalina ya tashi da naga yau ma har dare baki dawo ba nace na tsaya ne inga yadda jikin nata ya kara sauki. Ban mata hiran haduwan mu dasu ba itama din bata tambaye ni ba don batayi tsamanin zamu hadu dasu ba a can. Suna gaisawa da Abba shine Nafisa ta kira shi tana fadin bata jin dadin jikin ta yau tun da ta tashi yace subbahanallahi yanzu zamu taso. Sun iso sun samu taje asibiti ance haihuwa da sauran lokaci suka dawo gida duk wanan abin su mommy dake gidan basu san wainar da ake toyawa ba a gidan. Don dama sai taga dama take gaida su da kwana bayan nan zasu wuni basu ganta ba a gidan. Ga A,A sun ga sauyi a gare shi sosai tun bayan zuwan wanan matar a gidan komai da yake masu na kulawa ya rage a yanzu wani lokaci har fita yake bai gasa dasu ba. Ya dawo duk da yadda yake ji ya rage jin shi yau direct gurin su mommy ya fara zuwa ya gaisa dasu sukai mai sannu da zuwa tare da tambayan shi mutanen gida. Ya amsa da suna lafiya suna gaida su ya fito ya nufi part din su kwance ya samu Nafisa tana barci ya dan dade a tsaye kanta yana dubata ya juya zai fita ta falka. Shima juyowa yayi yana fadin kin tashi tare da zama a kusa da ita yana tambayan ta jikin ta tana wani yamutse fuska take fadin da sauki. Taje asibiti an dubata ance ba haihuwa bane da sauran lokaci Allah ya sauwaka yayi mata ya mike zai fita tace samad yanzu ya dace katafi kai zaman ka ka kyale ni. Haba Nafisa jiyane fa nayi tafiyan nan kwana daya nayi a can kawai shine kike fadin na tafi na kyale ki haka ? Nasan wurin wanan yar iskan matar taka fati kaje ka fake ga wai aiki ne zai kai ka can barin fada maka wallahi baka isa kace zaka wullakantani ba ka dawo da Fati a gidan ba. Kallon mamaki yake mata yace idan baki yarda Fati ta dawo ba ai zaki yarda wata ta shigo gidan nan ta zauna ko ya fadi a hasale. Ke baki damuwa da abinda ke gaban ki sai bakin kishi kawai dake cin ki haka har zaki ce wai saboda fati naje kaduna. Idan ma naje gurin ta ai ba laifi bane don fati matanane kowa yasan ina da hakki a kansu yana fadin haka ya juya ya fice daga dakin. Bin shi tayi da kallo mamakin shine ya rufe lokaci guda a lokaci daya ya juye mata haka har yana da corrage din bude baki yana fada mata magana son ranshi. Amma sai ta basar da zance da fadin kila gajiya ne a tare dashi ita kuma ta tare shi da zancen Fati da bai kaunan ayi mashi. Washe gari na idar da sallah ina zaune wayan Binta Abdulrahim kaunan Abdul samad ya shigo ga wayana. Na daga in fadin B,A ya kike tace wallahi khadija Adamu baki da kirki yanzu kizo kd ko neman mutane bakya yi in ba mama da ra fada muna yanzu muna maganan ki ba wai kin zo kin shigo har gida mu baki ne may mu ba Dariya nayi nace Binta Abdulrahim ke nan ni da na shigo gidan ko amsan abu kuma ban dade ba wanan miskilin yayan naku mai jin kai ya shigo na fita. Ashe kwana biyu kika yi kawai nace hudu dai don jiya na dawo Abuja da dare tace baki da kirki naji nace da ita. Zamu shigo Abuja idan matar yayan mu ta haihu zan nemay ki ai idan mun shigo kin san mommy na garin gurin shi ai. Nace Ya Amina ta fada min da nazo kd ai tace kin san yanzu mun dan fara samun kan shi yana dan kula mutane sai dai ba can ba. Nace da san nu zai kula ku ai watarana tace ai shi nace ma hajiyan mu da ta tayar da hankali kin san shegiyar matace buzuwan nan. Don su mommy sun je gidan kawai sai ta kule kitchen wai ba zasuyi mata girki a gida ba ki san muguwa wai da yunwa zata hore su kuma ? Don kawai su bar mata gida tunda bata kaunar ta bude ido taga yan uwan shi sun rabe shi ko kadan nace wanan yayan naku kamar soko yake ai mutum ya zauna haka mace tana juya shi. Khadija kin fa san buzayen nan yadda suke wurin mallake maza ai ke da gani kin san ba banza tabar shi ba idan munzo dai ai zamu sha kallo don nasan sai an kwasa da ita. Nace idan haka ne may zai kawo ku kuma ba sai ku zauna gida abinku ba tunda ba dole bane sai anzo din tace kindan haihuwar ta ke nan na farko a gidan shekara shidda da aure sai yanzu ta samu ciki dashi ana ta cin duniya. Wani abu da ban sani bane na ji ya tsaya min arai nace ku kuka sani ni dai idan kin samu lokaci don Allah ki shiga ki duba min jikin yar uwata don in san halin da take ciki. Tace insha Allahu zan shiga in duba maki ita nace halan ina Z,A take ko ta fita ne tace gata zaune tana jin mu wai fushi take da ke . Dariya nayi nace su zainab manya fushi akan may idan batai hankali ba sai na hada ta da buzuwa matar yayan ku ta latsa min ita da kyau. Tace ai kawar ki ce gaku kuma zaune a gari guda waya sani ma ko kun kulane da ita dariya ne ya kamani sai naji wayan ya mutu nasan kudin ta sun kare ne. Ita Binta bata jin ta kiraka ta dade kuna hira har sai kudin ta sun kare zata kyale mutum sai kuma tunanen buzuwa ya fado min a rai . Tsuki naja ina fadin lalle wanan takai shu,uma nan nake ba maryam labari muka zauna nan muka rage mata zunubin ta wurin cin naman ta. Bayan kwana hudu da dawo wan shi cikin dare ana ruwan sama sosai na kuda ya taso ma Nafisa gadan gadan da kyat ta iya saukowa falo hayaniyar su ne ya tayar da su mommy inda mijin duk ya rude saboda bai taba ganin mace tana labour haka ba sai wanan karon don anty fati haihuwan da tayi duk a gida take haihuwan ta bai nan. Ganin ga haihuwa yazo mata gadan gadan bata ko iya daga kafa yasa mommu tazo da sauri gurin tana fadin ta duka anan shiko duk ya rude sai fafin yake mommy ku kamata mu kaita mota muje asibiti. Tace bata iya tafiya Iyan bawa ne tace don Allah mazan su fice su barsu zasu kamata zuwa waje su Yanyala ko komai sun kasa iya sai yare suke sun rude . Da taimakon Iyan bawa da mommy ta samu ta haifi yarta a gurin kukan yarinyar da ya karade falon ya dawo da hankali wa yanda ke waje suna jiran a fito da ita. Sai da suka gama komai ne suka ce a shigo daga ciki mommy ta kamata zuwa sama dakin ta ta zaunar da ita a ciki tace tayi wanka sai suje asibiti a dubata. Shine ya shigo dakin yana gaida ita da yima mommy sannu da fama iyan bawa kuma tayiwa yar wanka bayan an yake ci bi. Ta fito wanka ya kara dawowa dubata tana zaune ta dubar yar ta da tasha kayan sanyi a jikin ta tana barci don ruwan zafin da iyan bawa ta gasa ta dashi . Da murmushi dauke a fuskan shi yake fadin baki kwanta kin huta ba har anyi sallah fa tace yanzu dai zan kwanta. Yace ki dan kwanta idan mommy ta dan huta gari yayi haske sai muje asibiti a duba ku tace ai ko bamuje da mommy ba ga Yanyala nan sai mu tafi da ita. Mommy dai zamu da ita itada tasan kan komai yanyala mai ta sani yanzu ai kinga ranan dauko su danayi suzo su zauna damu ko ? Tace ko basu zo ba ai haihuwa dai zanyi yau balle ni kadai na sha wahala na ai ba da wani ba yace yanzu zaki fadi haka amma da kike son taimako ai sunan ta kike kira ta taimaka maki. Fuska ta daure da alaman bata son magana ya mike yana fadin yanzu dai sai ki huta kafin gari ya kara wayewa mu tafi ya fice daga dakin. Ranta ne taji ya baci bata so su sa mata hannu ga alamarin ta ba sai gashi haihuwan ma a hannu su mommy tayi shi taja tsuki tana jin haushin yan uwan ta da suka kasa taimaka mata a wanan lokacin. Taja dogon tsuki tana kwanciya tare da tsurawa yar baby ta idanu tana son gano inda tayi kama da uban ta sai dai don kankantan yarinyar bata gane komai ba a gare ta illa yawan kaman da yarinyar keyi da ita na zubin buzaye. Shiko yana shiga ya fara kiran yan uwa da abokan arziki yana fada masu karuwan da ya samu . A ban gare na Binta ce ta fara kirana tana sheda min zancen haihuwan wanda yayi masu daidai don a karshen sati ta haihu don haka zasu samu daman shigowa wurin suna. Bayan mun gama waya da ita ne na shiga tunane a raina maryam na shigowa nake fada mata zancen haihuwan matar A,A din addua tayi ga yarinyar sai cewa tayi saura muje barka ko ? Da sauri nace wa ai ni nan da kika ganin ba abu kadan zai kaini gidan nan ba sai ya kama dole balle idan bai kira ya fada min ba ko barka ba zan mai ba, . Dariya ta dinga yi wai ko ina kishine zai sa ba zan tafi ba nace yanzu idan nace zan tafi gidan shi ke ba zaki min fada ba maryam. In dai ya samu nayi masa a waya ya gode a watse taro lafiya dai indai wanan yar barikin mata nashi ne in ba a watse da tsiya ba da yan uwan shi. Nan nake bata labarin da binta ta bani na hana ma su mommy dafa abinci a gidan da sauri tace abincin da muka sayo masu ke nan fa khadija ? Nace wa ya sanar mata mara mutuncin mata kawai wai kamar mommy zataiwa rashin mutunci irin haka saboda ta samu guri a wurin shi. Dariyan mumuke maryam take yi nace wanan dariyan fa haka kamar wace taga an cuci wani ? Ganin bata da niyar dainawa ne yasa nayi banza da ita har tayi ta gaji ita kadai sai bayan kwana biyu ne Yusuf ya kirani yana fada min wai an masu haihuwa. Nace nako taya ku murna Allah ya raya yasa dadin musulmi ne aka samu yace amin sai dai baki tambaye ni ko wa ya haihu ba koda yake bazaki rasa ji ba a wan gurin. Wa yasan na san ku da zai fada min an maku haihuwa ni yanzu nake ji a wurin ka Allah ya dada sa albarka ga abinda aka samu . Amin yace tare da godiya kamar shi akaiwa haihuwan ya tambaye ni jikin anty na nace da sauki na gode mukayi sallama ya kashe wayan. Wurin gi nayi da wayan gefe na naci gaba da karatun da nakeyi sai dai ban gane komai ba a cikin karatun yi dai nake yi kawai. Maryam ta shigo dawowan ta ke ban daga cikin makaranta gaida ita nayi ina fadi kin dawo ta amsa min da eh tana cire kayan jikin tace yanzu naga abin mamaki a waje zan shigo. May kika gani na tambaya ba tare da na dago na kalle ta ba tace zarah ki na gani yanzu ko kallo na batayi ba ta shige Napep. Zarah fa kika ce yaushe rabon da nasa ta a idona nima yanzu ina ganin ta watsar da zancen karatu ne tana abinda taga zai fishe ta. Maryam tace amma gaskiya tayiwa kanta tana ganin wanan rayuwan da ta zaba shi zai fida rayuwan ta watarana. Ba ace mutum kada yayi yadda yake so ba amma idan zakayi sai kayi yadda ya dace don kada gaba kazo kayi daka sani. Don maza mayaudara ne idan ka hadu da wanda baida tsoron Allah kin ga kamar wanan mutumin ki din yasan ciwon kan sa sosai haka nima MS yasan mutunci na amma kawai don kazo karatu sai ka biye wa maza suna bata ma lokaci bayan su sun gama gina tasu rayuwan a baya. Idan da basu tsaya sunyi karatun ba yaushe ne zasu zama haka har su samu kudin da take kwadiyi a wurin su. Wanan tunanen nake yi kika ga ina son rage hurda da kowa yanzu tace khadija Allah ya raba mu da wanan halin ita fa mace batayi sai da namiji haka namiji bai yi sai da mace. Abinda yasa nace maki haka don rayuwa ne na taimakawa juna a tsakanin mu dasu to amma idan zakayi kada kayi haramtaciya wanda Allah ya hanna yanzu rayuwan ne yazo da haka. Sai dai mutum kada ya shagala da ruden duniya ya biyewa shedanun maza sukai shi su baro tun farko a yadda na sanki da mutymin ki dan iska ne na tabbatar tafiyan ku ba zai yi nisa haka ba. Mu godewa Allah da ya dube mu ya hada mu da natsatsun mutane sai kuma muyi adduan Allah ya kara kauda shedan a tsakanin mu ko wani lokaci. Nikan har ta bar maganan amma abin ya tsaya min a rai sosai sai nake ganin may ma zai hana in watsar da kowa yanzu har sai na gama karatuna in fara dating. Yau tunda ya fita office ya rasa gane kan shi sai ta fara aiki yaji bai iya karasawa ya aje, a haka Yusuf ya shigo ya samay shi zaune ya tas files a gaba sai kallo yake yi. Kallon shi yake tun daga kofa har ya karaso tun bai kai zaune ba yake fadin lafiya dai ko naga yanayin ka ya canza a lokaci daya. Dan gyara zama yayi yana kama goshin shi yace wallahi haka kawai naji jikina ya mutu yaki fada mai gaskiyan maganan yadda yake jin gaban shi na yawan faduwa haka kawai. Kallon shi Yusuf yayi yace muje in sauke ka gida ka dan huta kila yawan jigila da baki ne ya jawo maka haka tunda baka saba ba. Shi ya sauke shi gidan shi don haka ba a san dawowan shi gidan ba babu kowa a falon sai tv dake aiki don haka ya wuce kai tsaye sama inda dakunan barcin su yake. Tun yana hawa yake jin hayaniya na tashi a saman sai ya dauka yan barka ne har saman suka hau a step din karshe ya fahinci dariyan wani abu suke sai yaji yana son zuwa ya duba baby shi kafin ya kwanta. Haba Nafisa kina bani mamaki namiji kamar mijin ki zai gagare ki kin kasa juya shi yadda kike so a hannnun ki. Itako Nafisa sai tace ba na kasa juya shi bane dama vikin nan dake jikina ne ya hanani aiwatar da sauran aiki na amma yanzu tunda na haihu lafiya may za a fasa sai in dora a inda na tsaya kawai. Sai na kama shi na mayar dashi marayan dole sai abinda nace kamar mahaifiyar shi zan koma duk wa yan nan dagin kala dake ganin dun samu kan shi har zasu zo gidan shi suyi yadda ran su ke so ba za su ga kafan sake gigin zuwa ba kuma. Don kafin su wuce sai na samu sherin da na kula masu gidan nan sun tafi ta baibai ai ni kowa yaci tuwo dani ya san miya kawai yasha. Da baya baya ya koma dakin shi ya koma ya bude a hankali ya shiga ya kwanta bai taba yarda Nafisa zata iya fadin magana ba haka duk da yasan halin ta amma bai dauka takai haka ba. Sai zuwa can ta raka madam ko may ta shigo dauka dakin taji shi a bude ta sa kai ta shiga kwance ta hango shi rigingine ya na tunane. Da sauri ta karasa wurin shi tana fadin lafiya kadawo a wanan lokaci yace ban jin dadin jikina ne na dawo in huta. Tace tun dazu ka dawo ke nan yace shigowa na ke nan kika shigo sai ta sauke ajiyan zuciya yana lura da ita. Zata zauna yace ki barni in huta please ko zan samu barci jikin nawa ya sake haka yasa ta mike ta fita daga dakin yabita da kallon mamaki yana fadin Allah ya kara kare shi daga kaidin ta. Ranan yayi tunane iri iri a ranshi barcin da yake son yi gaba daya ji yayi ya fice mashi a idon shi. Shiryawa yayi ya fice daga gidan ya rasa inda zai nufa yaji sanyi sai tunane na yazo mashi a da in yana cikin wanan yanayin guri na yake zuwa muka shi rikici dashi har yaji ya manta da komai a ranshi. Sai da yakusa kaiwa ne tunane yazo mai a rai yaushe rabon da yazo guri na ya dubani yanzu zai iya kai wata hudu fa tun cikin wancan hutu kafin muje gida. Gaskiya dole ya hakkura da zuwa sai kuma wata zuciya yace mai ya tafi kawai yasan abinda zai fada min uzurin rashin zuwan shi din. Waya ya dauka bayan ya iso ya kira ni ina ganin wayan shi gaba na sai da ya fadi nayi saurin kashe wa ya sake kira ba kashe don yasan naga kiran nashi kai ya girgiza ya kara danna kiran na sake kashewa. Tsaki yaja ya kira Yusuf yace kace ma wanan yarinyar ta dauki wayana na kirata ta kashe min waya Yusuf yace wata yarinya ke nan. Kai tsaye yace khadija a takaice Yusuf yace ko tana class ne yanzu bata don yanzu sun rufe ya kashe wayan nashi. Yusuf din ne ya kirani shima ban dauka ba har kiran ya katse ban daga ba karshe ma da naga zasu damay ni sai na kashe wayan gaba daya. Kiran shi tayi ya fada mai abinda ke faruwa yace bata dauki wayan nawa ba sai dai barin kira kawar ta maryam in ji. Maryam din ya kira yana tambayan ta ni ko ina ciki ne tace mai eh ina nan bari ta duba dakina ta gani sai zuwa can sai gata tace na duba bata dakin ashe tayi mai karya. Yace mata ya gode ya tayar da motar shi ya wuce badon ya yarda ba do yadda yaga maryam din ta da farko ranta a bace ta dai kare ni ne kawai kada ya dauki wani abu. Bakin cikin da yake ciki yaji ya karu mashi kai tsaye gidan Yusuf ya nufa yana aje mota ya fada ciki yana huci tare da fadin ni za a kawo wa iskan ci don ta samu na zubar da ajina ina kulata take daukan kanta wata mace can. Kaida waye kuma Yusuf dake zaune yana kallon shi yake fadin haka cikin kafa mashi idanun shi yana so ji ko shidawa ke fada. Sai cewa yayi duk haka suke dama irin daya mata basu da banbanci wurin karamin kwakwalwa wallahi ko wace taga kana kokari sata a inuwa sai tayi kokari kai ka rana kai. Wai may ke faruwa ne haka duk ka hargitsa kan ka haka yace Nida wanan yarinyar ne mana khadija don kawai yau na tuna da ita naje gurin ta shine har zata nemi ta wullakanra ni. Kai mutumi na cool down don Allah ka fa san khadija yarinya ce mai kaifin basira da aiki da hankalin ta kamar ba karamar yarinya ba. Ke nan ka goyi bayan wulakantani da nakai kaina tayi min ke nan ko may ? Dole in goyi bayan ta don itama mutun ce kamar kowa don may zata yarda ka bata mata lokacin ta a banza bayan ta gama fahintar ka ba don Allah kake tare da ita ba. Ba don Allah ba fa kace Yusuf Kwarai kuwa don hakane tunane ta a yanzu tsakani da Allah yau rabon ka da zuwa wurin yarinyar nan zaka iya tunawa ? Waye khadija da zan ta binta koda da yaushe don banda aikin yi ko may ko yaushe zan kama hanya gurin wata can daba matana ba ko wata nawa ? Yusuf yace ba wanan ba yanzu in tambaye ka may kaje yi gurin ta har tayi ma haka ? Wani kallo yayu mashi yace May naje yi kacs da ban kan lekata ne idan na tashi ko yanzu abinda ke kaini gurin ta ne ya kai ni ba wani abu . Kai mutumina kafito fili muyi magana kan yarinyar nan ni dai ba bako ka bane ko na khadija ka sani watau kaje ka ganta ka sata wani abin sai aka samu akasin hakan kake ganin laifinta don taki. Yace ko gani ta nayi ta ki daukan wayan mu na tura akira ta kuma wai ni zatace ace wa bata nan may ta dauki kanta ? Yace ita ce daidai da kai wallahi wace daga kai har Nafisa zakuyiwa ta tsaya ta kwatar wa kanta yan ci a gurin ku ba Fati bane ya dace tayi kishi da nafisa sai khadija ta dace da wanan. Kai duk mata a yau din nan daya na dauke su a guri na don may zanje gurin ta na debo baci rai a gida nazo gurin ta don inji sauki sai ita ta zuba min nata dafin. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU[28/10, 7:12 am] +234 706 638 5450: Yan uwa da abokan arziki ba laifi sun zo mashi karan suna sai dai taron ba wani dadi don mai jego ta tsare komai na gidan ta hana mutane suyi yadda suke so. Ganin haka ne tu sha biyu suka buga min waya suna tafe gurina don basu ga amfanin zama gidan da suke yi ba gara kawai su fita suga gari. Da waya har suka iso gidan da muke zama inda ake kira da up k na mata inda a nan nima nake da dakin na da aka kama min tun zuwa na Abuja. Ranan nayi mayan baki don karshen ta dole suka samu gaba wai mu zamu nuna masu gari shigan dai guda ne don ko yau wani abaya baki mai kyau ne ke saman lace din da nasa. Shigan yayi min kyau matuka don ya mayar dani kamar wata yar bukuwar haure dani munje wuse market mun dan leka gura re sai yamma lis muka bar SAHAD zuwa inda gidan yayan nasu yake inda suka zo suna. Don nace dasu ni ban sani ba can ko sai faman tambayan su ake don wata ta bar yar ta karama na barci a gidan ta biyo mu yarinyar ta tashi tana kuka sosai don haka ake tambayan ina suka je. Har shi kanshi maigidan da kukan yarinyar ya damay su yake tambaya akace mai suna gurina bai tsaya mamaki ba ya fara fadin may suka je yi wurin yarinyar dake makaranta. Mun shigo suna falo an gama rikici ke nan da buzuwa matar shi da Fauziya kanwar shi da su mommy don komai da ake shigowa dashi gidan buzuwa ta hana aba mutanen Abdulsamad sai idan kaje wurinta munafunci zata baka ko matan abokan shi haka bata ba abin sai taga dama. A daidai lokacin da suka gama rikici da Fauziya da tace sai an raba an basu nasu, ranan ta murje ido tayi ma buzuwa tas a gidan abinda a da suke tsoron mata. Shigowan mu ne gidan ya dawo da hankalin mutane a gare mu su tambaya ina suka shige haka ne ni da zainab ce da Binta sai maryam muka shigo daga karshe gidan ina tako dadaya duk kan mu kwaliyan mu ba laifi. Tsaye yake yana magana a cikin fada muka shigo da sallama falon sai da ya so rudewa a lokacin da mukai arba dashi nayi saurin kawar da kai na mommy da na hango zaune na nufi gurin ta har kasa na zube ina gaida mommy ta dafa ni tana fadin khadija kina garin nan nazo na dade a nan ban ganki ba. Yanzu ma nasan don su Binta ne kika zo gidan nan da bamu gan ki ba na san har mu koma Nafisa dake zaune ta cika ta batse sai huci takeyi tana kokarin son tuno a inda ta san fuska na amma ta kasa ban dade ba muka ce da su zamu koma ko dakin bamu shiga ba. Binta na fadin ba wani abu a basu mommy shi kuma maigidan ns fadin Fauziya tashi ki hada nasu snack din nan da aka yi da drink's lokacin har mun kai kofan fita daga katon falon nasu ko. Binta da zainab dake bin mu a baya ne ke fadin ku tsaya don Allah a kawo maku abin buki kutafi dashi na juyo nace da ita. No ku barshi kawai dama mommy muka zo gaidawa a a yan mata ashe kun samu shigowa bukin ku ma ? Muryan Yusuf ne dake fitowa daga cikin motar da ta parker a gaban mu yake fadin haka maryam ce ta bashi amsa da fadin wallahi fa. No ba buki ya kawo mu ba munzo mu gaida mommy ne tsaye Binta tayi tana kallon mu da mamaki tafiya na fara yi zan wuce wurin Binta tace don Allah ku tsaya ku karbi abin buki mana. Nace a barshi kaya zai muna yawa idan mun tsaya daukan wani abu kuma ke khadija wani kaya ke gare ki banda handa bag da kika rika nace shima ai kaya ne ko. Khadija ya kira suna na da karfi na juyo tsaya mana ku amshi kayan bukin maryam tace ya Yusuf muna sauri ne mu samu abin hawa kasan unguwar nan naku idan yamma yayi akwai matsalan abin hawa. You known each other ne dama ? Zainab ke tambaya cikin mamaki No ya dade da na san su ba irin familier din nan ba dai na fada ina yatsune fuskana. Barin sauke ku mana Yusuf yace da sauri nacevka barshi kawai zamu karasa ai na fadi ina ci gaba da tafiya na nufar get din zuwa waje. Da sauri ya shiga babban motar Abdul din yana fadin ku shigo in sauke ku nasu in ki amma Binta na ta kaudi motar yayan sune ai in shiga a kaimu hostel din . Zainab tace friend ku shiga don Allah bari muje tare a sauke ku sai yaya Yusuf ya dawo damu abubuwa ake fitowa dashi daga cikin gidan wai duk namu . Mommy ne ta fito waje lokacin da zamu shiga motan tana magana dani tace ga abin buki nan yayan su Binta yace a baku kuje dashi wai angode nace lokacin shima ya fito wajen. Yusuf ina zaka ne yace zan sauke su khadija ne hostel in dawo barin bi ka mu fita daga can zan tafi gidan MD dayani. Ga mommy tsaye ta kura muna ido dole na yarda muka shiga motar a tare dashi dasu Zainab da binta ya juyo yana fadin ku kuma ina zaku sukace zamu raka friend din mu ne yaya. Ba yanzu zamu dawo ba fa ku fita don Allah rike zainab nayi nace a tare zamu fita ke nan don saboda su nazo nan din da kuma mommy. Sun yi mamakin jin maganan da na iya fada ma yayan nasu wanda suke matukan tsoro da girmamawa su. Sun dauka zai yi wani abu sai sukaji yayi shiru bai sake magana ba sai tsawan da ya daka ma Yusuf akan ya tsaya mana su sauka kokarin sauka nike yi zainab tace ki bari gobe zan shigo wurin ki da safe ai. Ta fice daga motar da sauri ta rufo kofan da mu a ciki yusuf ya kama hanya ya tafi daga gidan ba wanda yayi magana a cikin motar. Ya Yusuf ka tsaya dan Allah in sauka ko sauraro na bai yi ba sai tukin mota yake a hankali kwance abinshi. Tsuki na naja daga inda nake zaune muryan shi ne naji yace kibi a hankali fa kada ki bata muna rai a nan sai kace wace aka ce za a sace ta. Nace ai in ma kunyi niya zaku iya hakan don iya yaudaran ku dariya sosai Yusuf yayi yace munyi kama da mayau dara ke nan khadija. Kasan ta iya shirme wani lokaci mu sace ki muyi may dake ai ba irin ki zamu sata ba har in muna satan yan mata. Yusuf yace nikan irin su zan sata don yanzu suna danyun su shar ai kaga daidai sata ke nan nace ai dama nasan zaku iya haka ba sai kun fada ba. Yace Yusuf ya tsaya a wani guri da ake sai da kaji ya mika mai kudi ya sayo muna da abinsha mai sanyi Yusuf ya fita ya barmu a motan tare dashi. Naji dadi da maryam ke cikin motar a lokacin ba a barmu mu biyu ba ko kallo gefen da yake ban yi ba maryam ne ta dan zugure ni wai in yi mai magana. Na kawar da kai kamar ban gane abinda take nufi ba tunane nake ta yadda zan fita motar nasu a lokacin Yusuf ne ya dawo dauke da ledoji a hannun shi ya shigo motan yana aje kayan a gefen shi ya ta da motar muka tafi. Ban akara ba sai gamu bakin hostel din mu da sauri nayi niyar fita daga motar amma motar tana rufe har lokacin ga sanyin A C motar daya damay ni. Suna zaune ba wanda yai magana a cikin su har dan wani lokaci can naji Yusuf yace daidai lokacin da nake fadin ka bude mu fita mana. Shikuma yana fadin gaskiya khadija ba a kyauta maki ba a kyauta maki ba da sauri ya dago kai yana kallon Yusuf din dake magana. Yusuf fitar masu da tsaraban sunan su su sauka don Allah zaka tsaya wani magana kuma yace ya zama dole mu bata hakkuri don bamu kyauta mata ba. Da akai mata may kuma ya tambayi Yusuf din cikin tsare shi da ido yace ai kaine mai lafin yaya zaka saka ta saba da kai daga baya kuma kazo ka share ta haka ba dadi wallahi irin haka kaima ka sani. Please ka fitar masu dashi mu tafi don ina da abinda nafito yi yanzu ba wanan ne a gabana ba zaiyi magana yace fito masu dashi nace please. Ai da ka barshi zuwa kawai mukayi in gaida mommy da su anty Fauziya da suka zo ya sake fafin don Allah ciro mata mu tafi ya sake maimaitawa. Fita Yusuf yayi daga motar ya bude bayan motar yana fitar da kayan da aka saka a bayan motar sai da nayi mamakin ganin yawan kayan da aka debo muna mu kadai. Haka na dake fuska daure na fita daga motan ban koyi masu godiya ba na fice fuuu a motar Yusuf ne ya tsayar dani yana fadin haba yar mama ki sasauta wanan fushin naki ku fahinci juna da mutumin ki. Dan Allah yaya Yusuf ka daina hadani da wanan mutumin don ba ajina bane shi mutumin da yake under control din mace macen ma yar haure ba jinsin nahiyar mu ba. To waima may kake son in kula shi aka in kula shi ya bata min lokaci ya hana mutanen arziki zuwa gurina ko may ? Subbahanalahi ina wanan maganan ya fito haka a bakin ki baki taba tunanen Abdulsamad son ki yake bane ko may ? Da sauri nace so so fa kace na girgiza kaina nace a,a dama kace kawai yana amfani dani ne wurin cin ma wani manufa nashi da zan yada da hakan amma ba wanan kalamin naka na so ba. Sam na sake girgiza kaina karo na biyu tare da fadin wanan wani sallon yaudarane kuma ka dauko yanzu. Yace to ko ki yarda ko kada ki yarda ni yau na fada maki son ki Abdulsamad keyi har cikin ranshi wallahi bai dai iya fitowa fili na ya fada maki ko ya nuna maki hakan. Wani irin kallo nayi mashi tare da girgiza kaina na juya na fara tafiya ina jin wani bacin rai a zuciya har na shige ba tare da na dauki komai nasu ba da suka aje muna. Kwanciya nayi ina tunane a raina maryam da wata suna shigo da kayan daki har suka gama ta debar masu ta basu daga ciki. Ta dawo ta zauna tana ta faman cicire kayan guda guda tace kai khadija akwai wanda ya samu abinda muka samu kuwa a wurin nan jifa wanan uban kayan da aka loda muna wai duk namu ne mu kadai ina zamu da wanan kayan haka ? Sai lokacin na dago kaina ina duban kayan data tara a gaban ta na maida kaina saman filo na kwanta magana Yusuf ne ke ta min yawo a zuciyana har wanan lokaci. Maryam ne naji tace wallahi khadija na yarda da Yusuf daya ce son ki Abdulsamad keyi har cikin ranshi ba karya ya fadi ba don ni na dade da sanin haka tun tuni. Ina jinta saidai ban yi mata magana ba har ta gama fadin abinda zata nace ke idan nace zan bata lokaci ga wanan mutumin ba zaki min fada ba maryam. May ke cikin gidan irin su Abdulsamad banda tarin rikici da tashin hankali kulun ni kwadayi bai kai idona ya rufe ga abin hannun shi ba wallahi. Salama nike nemawa rayuwana ko yaushe ba zan tsaya in yaudari kaina ga abin da nasan yafi karfi na tun yanzu akan matar shine fa ya daina kulani ke ma kin san da hakan. Tace da sauri Kin san uzurin shine da zaki yanke mai wanan hukucin haka khadaji idan yana son ki ko Allah ya kaddara akwai aure a tsakanin ku matar shi ta isa ta hana ne ko tayi kamar Allah ne. Sai dai in kece zaki bata kafan da zata hana din ta dauki kanta inda Allah bai kai ta ba kinatsu khadija ki san may son ki da zuciya daya. Ni na fahinci A,A irin mazan nan ne da furta kalman so ke wahala a bakin su sai dai suyi ta nuna ma mace alama amma basu iya furta mata da baki. Nace shine kike son in tsaya wahal da kaina gare shi ko may ni koda ya furta bai mun ba don ba zan so shi ba ma ban ra,ayin mijin tace a rayuwa na. Ban yarda ba wallahi ke ma kina son shi kishine dai ke damun ki ke ma kina ganin kamar ya mutu akan matar shi ya daina kulaki don ta. Haka zuciyar ki ta fada maki ashe nace mata bata ko fada maki daidai ba ke nan idan tace maki nima ina son shi. Tace idan baki son shi may yasa yanzu kika rage mashi tsiwa irin da don da dane da yanzu kunyi fada a motan nan yafi a kirga. Nace amma kin san wulakanci bai da kyau ko saboda haka ne na kyale shi badon komai ba yanzu dai ai kanku ake ji ku karaci gulman ku ku dawo hanya dai. Indai har kin san kina son shi ya kamata ku daina wanan shirmay tun wuri tun bazuwa bata kara kwace maki shi ba kuma. Ta kwace shi mana shi ya shafa bani ba nace mata cikin kunan rai tace dukkan ku dai ya shafa khadija bashi daya ba kin dai san so yanzu koda kike kirarin baki taba so ba a rayuwan ki. Washegari a wurina su Binta da zainab suka wuni don ba shiga school Friday ne yau sai sunday zasu koma kd. Don haka da yamma muka shiga gari dasu yawo sunyi mamakin sanin garin da nayi don sanin da sukayi min ba mai rigima bace ni. Munsha yawo sosai rana sai dare muka dawo hostel dasu bamu dade da dawowa ba wayan Binta yai kara ta dauko da sauri tana dubawa take fadin nashiga uku yayane fa ke kirana zainab. Zainab tace dauka mana kiji may yake kiran mu nasan dai sunga dare yayi ne bamu dawo ba suke neman mu ta dauka tana fadin hello yaya A,A yace kuna ina ne har wanan lokacin hankali mutane ya tashi. Tace gamu nan wurin khadija tun dazu ita ce zata rako mu mu dawo yanzu yace tana da motane tace a a yaya karatu fa take yi ina zata samu mota kuma ? Yace ganinan zuwa in dauke ku yanzu ku jirani in zo yace ya kashe wayan kallon ta mukayi nace yanzu ba zai bari ku kwana nan ba ke nan ? Tace tunda kika ga yakiramu ai haka yake nufi damu nace bari yazo ni zan fita nagan shi da sauri tace ke baki san halin shi bane bari kawai yazo din mu tafi gobe sai mu dawo muyi sallama ba shike nan ba. Zainab tace ni nafi sakewa a nan wallahi amma can gidan duk a tukure muke wallahi shegiyar matar nan tashi bata bari mutum ya wala a gidan. Dariya nayi mata sosai da take fadin haka ba a jima ba sai gashi ya kirats yana fadin su fito nace barin je in gashi tace bari dai mu tafi ban son fadan nan nasa wallahi. Maryam tace ku bari ta fita ta gan shi mana ai zai yarda ku kwana nan idan ta roke shi baku san ko waye bane yaya AA kawai. Mikewa nayi na fita batare da na kula da kayan dake jikina ba a lokacin yana zaune a cikin motar shi ya fitar da kafa daya waje yana shakan iskan dake kadawa a lokacin . Na iso gurin sallama nayi mai ya dago kai da sauri yayi min wani irin kallo ya kawar da kan shi kuma kallon da ada in yayi min nasan na bata mashi rai ke nan. Sai dai yau ban san may yake nufi da hakan ba da yayi min shi nace don Allah ka barsu su kwana guna tunda gobe ne kawai haduwan zasu koma gida jibi. Ya sake kallo na a karo na biyu yace su ke son kwana nan din sukace maki nace suke son hakan bani ba yace to shike nan indai zaki basu kulawan da ya dace may zai hana nace mai sai yadago ya dube nayi saurin kawar da kaina gefe daya nima. Nace na gode na juya zan tafi naji yace khadija nayi saurin juyowa sai naga ya kada kai kawai sai kuma yace may yasa kika fito waje haka da wanan kayan ? Don Allah ki bar fitowa haka na roke ki please kallon kayan dake jikin nawa nayi sai lokacin na ga kayan don na cire abayan da na dora sama da muka dawo daki. Ki kula daga yau ban son ganin mace a waje haka gara idan mace tana cikin gidan ta zata iya amfani dashi haka ko ga mijin ta. Kai na rausaya cikin wani irin jan aji da ban san nayi ba nace ga matar da bata da miji fa itama sai a hanatayin yadda take so ko may. Yayi tsuki yace na dai fada maki ban so ki kula daga yau kada in sake ganin ki haka a waje daga yau. Jikina ne yayi sanyi na kasa yin wani magana kuma ya kawar da kan shi gefe bai sake magana ba sai ya mayar da kafan shi daya dake waje tare da jan kofar motar yana fadin ni na tafi sai da safen ku. Kin dai ji abinda nace dake ki kiyaye duk abinda nace dake ban so ban so ne ya rufe motar yai mata key gurin nake tsaye kamar wace aka kafe har ya bace ma gani na naja kafata na koma ciki. Ina shiga na samay su har sun shirya suna jiran shigowa na dakin nace dasu yadda na gansu a takure yace ku fito bai yarda ba wai. Zainab tace ai dama na sani don kada kice mun hana ki ne do ba mu son kwana din amma ninasan ba zai yarda ba ta fada a sanyaye. Tare da fadin tashi muje Binta binta din taja wani tsuki tana shirin mikewa nace ya tafi fa tace don Allah ki bari nace wallahi ya tafi tun dazu na tsaya magana ne a waje. Wai da gaske kikeyi khadija nace wallahi ya tafi yace sai da safen ku tunda anan kuke son kwana indai kula daku naso ce mashi mudake nan wake kula damu ? Da sauri tace da kin muna tsiya wallahi nan dai muka sake muna ta hiran mu kayan bukin da muka dawo dashi a tare dasu mukai amfani dashi. Sai hiran buzuwa da Binta ke ta bamu a dakin wanda inda tasan yadda raina yake baci da ta daina bamu labarin abin haushi haka. Washe gari ma kusan tare dasu muka wuni a hostel din mu sai da yamma muka je gidan tare dasu yiwa sauran yan uwa sallama. Mommy tace khadija kice bakin naki ne dai wanan irin fresh da sukayo haka wurin ki dan kwana daya da rabi injin dai ba dan abincin naku suka cinye ba. Shine ya shigo nan ya gan mu kallo daya yai muna ya kawar da kanshi gare mu gaishe shi suke yi yace da alama kunji dadin zama a inda kukaje din ke nan. Mun dan jima tare dasu mukai masu sallama suka rako mu zamu tafi sai ga driver yace ance ida zamu koma a sauke mu . ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU [28/10, 7:12 am] +234 706 638 5450: Tun wanan ranan ban sake ji daga gare shi ba ban kuma koma ta kan su ba ina karatuna hankali kwance don komai ina dashi a tare da ni. Ashe suna da kwana biyu bayan tafiyan bakin shi tafiya ya kama shi nan Nafisa ta tubure akan may zaiyi tafiya yanzu bayan yan buki basu gama tafiya ba. Idan na zauna may zan maki a gidan ina kudi kika sani na kashe maki wanda ni kai na ban san iyakar shi ba. Yan uwana sun tafi da takaicin abinda kikai masu a gidan nan bayan sun san da komai nayawa kike kadagi a gidan nan amma kika rufe ido kika hana masu komai da na kawo gidan . Haka suka tafi da bacin rai a tare dasu don ma mommy mace ce mai tunane da sanin ya kamata ta sa na samo masu abinda zasu koma gida dashi. Don baki da kunya yanzu zakice ba zan tafi neman kudi ba idan ban fita ina samo kudin nan a zaune kudin da kike kashewa zasu samay mu ko may ? Tunda ya fara magana bata katse shi ba sai da yakai karshen maganan shi tace ina da sunana kasai abin bukin ? Baka ce da wasu yan uwa naka zamu raba shi ba idan bakayi ba wa kake son yayi min da ? Tafiya kuma kana nufin ni kadai zaka bari da wahalan dubar yar ka ko may tare muka samay ta don haka tare dakai zamu rene ta babu inda zaka a yanzu kaji na fada maka. Yace tunda ke kika ajeni sai ki hanani zuwa mugani idan zaman ki nake yi ba ke ke zama na ba a gidan nan Nafisa kin dauki kanki ki kai inda Allah bai kaiki ba fa. A da ana fadin ina ganin don ba a kaunar ki cikin mu ne yasa ake maki haka ashe halin ki ne hakan ban sani ba ina jiye maki ranan da reshen ki zai juye maki a gidan nan idan har baki nemi shiri da yan uwana ba. Tace wanan tunane kake a ranka dama akwai wani rana da zaizo min ba daidai ba gidan nan har in neme shiri da yan uwan ka to kasani babu wanan ranan a rayuwana da zan shirya da yan uwanka. Tunda tun farko sun iya nuna min rashin kaunar su gare ni yanzu may zai sa in dawo ina shiri da mutanen da basu so na ko kadan. Yace aike baki da kunyan fadin magana wani irin sone basu nuna maki ba da kika zo gidan nan musanman ma mommy amma kikai fatali da kowa don ke kan ki kawai kika sani . Ya ture ta gefe ya fita rai bace zuwa inda ake neman su dan bayanin tafiyan su ta tsaya tana kallon shi cikin mamaki. Don dai malamin ta yace da ita yanzu AA a tafin hannun ta yake saboda sun gama daure mata shi yadda take so kuma ba karamin kudi ta tura wurin yin wanan aikin ba. Shiko bayan ya fita daga gidan rai bace bai tsaya ko ina ba sai inda club din millonear in the world yake ya cika komai da zai cika na tafiyan shi kasan. Take a nan wurin suka maida mashi da amsa sakon shi ya karbu sai kudin da zaiyi tafiya da na komai suka turo mai yana barin haraban wurin ya wuce wurin Yusuf kai tsaye. Ya samu Yusuf wajen gidan yana shan iska taee da waya a hannun shi yana yi wuri ya samu ya zauna daga gefen shi ya tsiyaya lemon da yagani wajen yana sha. Yayi mamaki daya fahinci Yusuf da mace yake wayan yana kashe murya tare da zuba soyayya baki ya tabe ya kawar da kan shi gefe yana jiran ya gama wayan. Ya gama yana kallon shi fuskan shi dauke da murmushi yace ya dai ina ka fito yanzu haka sai da ya dauki cup din juice din ya kara korawa yake fada mai inda ya fito. Yace amma kasan may wai ni yar rainin wayon nan zata raina ma hankali wai bata yarda inyi tafiya yanzu ba. Nafisa ke nan Yusuf ya fada yace ai kaima ka sani wazaiyi wanan haukan idan ba ita ba yusuf yace wai may matar nan ta dauki kanta ne halan ? Komay ta dauka zan bata mamaki ai kwanannan kuwa don sai ta rena kanta wallahi yusuf yayi saurin fadin baka iyawa ne ai shiya sa take kawo maka raini haka. Haka kake gani ko kamar yadda kowa yake dauka na ban iya aiwatar da komai akan nafisa yanzu kaima hakan ka dauko ke nan ? Yusuf yace ai haka din ne yanzu fa don haihuwa kai mata wanan irin sayayan haka bayan wanda ka din ka mata wanda zata fita dashi ga kuma sayayya kamar na hauka da ka da mata daga baya. Wanan ba komai bane Yusuf har in zatai amfani dashi ni mutum ne mai son in ga iyalina suna shiga suna fita a gida don haka ban jin kyashin kashe ma iyalina na kudi ko nawa ne. Kasan wanan halin ne ya hadani da Fati bata sawa bata kuma gyarawa amma mutane basu ganewa ida matsalan mu yake da ita. Mutum ko yaushe baka gane dadin ran shi kullun ya zauna kamar an mashi wani abu babu marmari ko kadan. Ita nafisa tana maka yadda kake so ne halan da ita da fatin duk jirgi daya ya kwasosu a gidan banbanci dai kace ita nafisa tana sakewa da kai kawai ne. Yanzu badon yarinyar nan khadija da ta muka saya ma yara da ita fatin kaya ba a kwanaki ina ban dashi tunda suka tafi har yau bakai tunanen ka kara saya masu komai ba. Yarinya ta dauko saka ka a hanya tanayi hanyar alheri wanan bakar shu,umar ta shiga ta fita yanzu ta raba ka da ita nasan wurin shige shigenta can aka bata labarin khadija din ta sani. Khadija khadiji Yusuf ka fasan tafiyan mu ba zai zo daidai da wanan yarinyar da take daukan kanta wani tsiya ba. Yasuf yace yanzu ka gama fadi da bakin ka mace yar kwalisa da iya gyaran gida da jiki kake so a gidan ka. Daga cikin wanan wani khadija ta rasa a tare da ita ka fada min ya ja iska yace baka san wani abu ba wallahi ranan naje dauko su Binta da dare wurin ta. Kasan yarinyar nan sai da taso ta rikitani gaba daya Yusuf ya tambaya yace akan may kuma yace wallahi wani shegen shiga tayi tafito waje dashi sai da na kasa kallon ta. Ban san lokacin da nayi mata fadan haka na ba don wanan shigan sai ya rikita mutum a banza wallahi. Dariya sosai Yusuf yayi mashi har sai da yaji haushin shi yace malam na fada ma son yarinyar nan kake yi wallahi ka tsaya kana wani noke noke. Bari garin kallon ruwa wani ya rigaka jefa fatsan shi kana kallo dama ya samu ka fida zuciyar ka ka tsaya kana wani izza haka. Shiru yayi mai yace bazan bata lokaci na ba kan wanan da yanzu ma take zama mace bata gama mallakan hankalin ta ba. Zaka sha mamaki wallahi khadijan ne macen da bata san wani abu ba idan bata san komai ba yanzu akan may take fushi damu. Badon share tan da mukayi bane kwana biyu ta dauki wanan zafin haka kana tunanen ita ma bata fada tarkkn son ka bane ko may ? Kallon Yusuf din yake yi yace abinda take ma fushi ke nan dama yace don may baza tayi fushi ba kuwa ? Kwana biyu da yin maganan su ya shirya ya tafi club din su inda zai buga game a can . Banda labarin yayi tafiya sai dai ina murna a raina sun gaji sun barni ke nan tunda ban kara jin labarin su ba kuma. Sai dai tunanen su yana nan a zuciya na inda nayi wani sabon saurayi dan kabilar nufe koshi haduwan mu dashi a wani shago ne yana waya da yaren su na Nufe sai ya yar da dan wallet din shi kasa. Da yaren Nufanci da nake ji don zaman gari daya da nufawa da nakeyi nace dashi da yare kayar da wallet din ka fa. Ya juyo ya dauka yana min godiya a cikin yare yana fadin (Nufe wayyo ni )nace dashi a a ke yar ina ce ya tambaya a cikin yare nace ni yar Niger ce yace (kiyyo sunayo) nace dashi khadija. Sai yace Iam mamud by name yana aiki ne a CBN dake nan cikin garin Abuja shi mutumin garin Bidda ne dan murmushi nayi don kamar naga na gida ne da na ganshi. Nomber na ya tambaya na nuna bazan bashi ba ya matsa min sai na bashi da na sai turaren da nazo saye sai gashi mun hade wurin biya ya biya min nafito zan wuce sai gashi yace in zo ya sauke ni. Banyarda na bishi ba ashe ya biyo ni baya muna sauka shima ya tsaya yana dariya ya fito daga motar shi nan muka tsaya dashi yake fadi ashe karatu ya kawo ki, nan ke nan. Murmushi nayi nace may yasa ka biyo ni har nan kuma yace don in san zahirin ki tunda kin ki yarda in dauko ki ni kuma ba zan yarda ki bace min ba ina ganin nayi babban kamun yar garin mu haka. Tun daga wanan ranan muka hade dashi saboda nacin shi dole nasaba dashi don mutum ne mai saurin sabo da mutane ga baa da iya magana kamar shiyayi kan shi. Tun ranan da suka fara haduwa da maryam tace yanzu kan kin samu daidai dake khadija haduwa da mamud yasa na manta zacen wani AA can a rai na. Shiko yana can yayi nasaran tafiya don shi yazo na daya ga gasan da sukayi na wanan lokacin ya samo makuden daloli a wanan tafiyan. Tsaraba yayo wa iyalin daga ciki Allah ya ciyar dani ya sako min a wani jakka na daban tun daga can ya ware min nawa. Yusuf yazo gurina inda ya samu mamud yazo sai da ya jira ya wuce yana zaune cikin motar yana kallon yadda nake kwasan dariya daga inda nake tsaye. Yana mamaki a ranshi yaushe har na hadu da mamud har mukai nisa haka dashi muna irin wanan hira don yaga na sake jiki sosai da mamud din. Mamud ya wuce sai lokacin ya kirani yana fadin gashi nan tsaye bakin hostel din mu yana jirana waige na fara yi sai dai ban ganshi ya fara fada min irin kayan dake jikina da yadda nake tsaye ina waige waige. Har na gano shi na iso gare shi abinda ya fara tambaya na shine waye wancan danaga ya tafi yanzu khadija ? Mamaki nayi da tambayan shi nace wani abu ne halan sai yace a yanda naga kuna hira dashi yasa na sha jinin jikina khadija kada fa yayiwa abokina yankan baya. Kai na rausaya nace wani abikin ka kuma ke nan yayana yace haba khadija tun yanzu har kina nufin kin manta damu ne. Nace haba dai abokin ka ai ba saurayina bane kuma bai taba cewa yana so na ba asalima shiba irin mazan da nake so bane. What har akwai irin mazan da mace ke so ashe sai yau naji wanan a bakin ki nace kowa da abinda ke masa kasani . Yace kina Nufin bai maki ba shikenan ko ko sai wanan dan kyamazon ne yayi maki da sauri nace kada muyi haka dakai yayana. Yace Allah ganin shi nayi kamar dan tsurut a motar bai wani cika motar tashi ba sosai nace akwai dai kishi ga maganan ka ke nan , ? Dole muyi kishin ki khadija don kin cancanci hakan a gare mu saboda ke mace wance ko wani namiji yake fatan ya mallaka a gidan shi. Nayi dariya tare da fadin kazo da wata magana ta daban ke nan idan kai nayi ma ai shi abokin naka ban mashi ba. Ko ya taba cewa dakai son na yake da gaskiya kaga yayana mu bar wanan zancen muyi wanda ya kawo ka yanzu yace maganan tana cikin abinda ya kawo ni ai. Bashi ya kawo ka ba kadai zo ne don duba kanwar ka na sani kuma gani ka ganni ai na kuma gode kwarai da gaske. Khadija ya kira sunana wanda ya nuna maganan da zaiyi tana da muhinmaci sosai a lokacin gare ni amsawa nayi da naam yaya na. Yace don Allah ki natsu kiyi abinda ya kawo ki garin nan ki bar biyewa irin mutanen nan da suke zuwa da karya. Nace yayana ban yarda na tsaya da mamud ba sai da nasan ko shi waye da sauri yace dani shi waye din kika sani. Dariya nayi nace yanzu dai mu bar maganan don Allah don naga bazaka fahince ni ba a yanzu gaba mayi idan mun hadu. Yace to shike nan tunda kin hada ni da Allah yanzu ina maryam ina son ganin ta nace ayyah maryam yau taje gida da yamman nan gurin yayanta. Kasan ita anan garin take da zama yayan nata ne tayi tafiya ta dawo shine taje mata sannu da zuwa yace ashe idan Abdulsamad ya dawo zaku zo tarun shi ke nan ? Da sauri nace da zai tafi ya sallamay ni ne da zanje tarun shi yace kece baki bashi dama ba don kina fushi dashi yasa bai sallamay ki ba. Wanan maganan kane kana kokarin gyara shi a wuri na ne kawai wanda ba zai taba gyaruwa ba kuwa. Murmushi yayi yace zan gano ko waye wanan dake shirin hure maki kunne haka har kike son yin wa kanki zaben tumun dare. Haka dai mukai ta zubawa dashi har ya kaimu wani lokaci a wurin karshe dai yayi min sallama ya tafi. Maryam ta dawo daga gida tana fushi dani wai naki zuwa gidan su in gaida yayanta da dawowa nace ba haka na bane maryam kina dai gani ba fita nakeyi ba amma kullun Daddy fadan da yake min ke nan in natsu. Kada ki damu watarana zan tafi mu gaisa da ita har ma in kwana ba shike nan ba haka yasa ta sake jiki dani tana bani labarin yayan nata da abinda ta dawo dashi wanan tafiyan. Ta ciro wani dogon riga tabani tace yayan nata ne ta sayo muna ni da ita don yawan labarina da take bata ko yaushe. Nayi godiya tare da karban lanbata nace zan kirata inyi mata godiya tace mutumin ki baizo bane yau nace yayi tafiya ai da yanzu kin gashi nan.. Yusuf dai yazo bakya nan ya gan mu tare da mamud yake wani maganan robish a kan sa tace saboda Allah nace wallahi ko. Ai dama na fada maki ina jiye maki ranan da zasu san mamud ya shigo rayuwan ki gashi wanan mamud din da alama baizo ba kamar sai da ya shirya maki . Nace kin jjiki da wani magana kuma ba wani shirin da yai min sone kawai wallahi ni kuma ya kwanta min sosai a raina. Tunda bada wasa yazo min ba ke ma kin sani idan yau zan ba mamud baki ya fito a shirye yake da yafito din. Allah ya zaba muna abinda yafi zama Alheri a gare nace amin yama zaba min din Allah sa albarka ya rage kice. Kwana hudu da maganar mu na dawo daga class don yanzu karatun mu ya dau zafi sosai muyi nisa mun zama manya a cikin makarantan. Kwance nake ina hutawa ban cire kaysn da na dawo dasu ba wata ta shigo tana fadin wai ina da baki a wajen hostel nayi mamakin ko suwaye ? Sai lokacin na tuna wayana a kashe yake tunda zan shiga class na kashe wayan mikewa nayi daga kwancen ina gyara bujen jikina dakyau. Dinkin wasu material ne na india da mijin ya Amina ya sawo muna tsaraba nasa takalmana flats shoes na saka don ban faye sa takalma mai hill ba. Wani dan yalalon gyale na yafa akaina duk rabin jikina yana bude na fito don ganin wanda ke nema a wajen. Motar AA na hango can nesa kadan sun faka shi da Yusuf sai naji gaba na ya fadi ras don ban san may ya kawo su ba nasan kuma Yusuf ya fada mai zancen mamud yanzu haka ? In bashi ba may zai sa su zo gurin mutumin da bani a gabasa zai zo wurina yau kuma ? Haka na daure fuska na karasa inda motar tasu take aje cikin daure fuskana na isa inda suke sallama nayi masu irin na addinin musulunci. Tare da fadin sannun ku da zuwa Yusuf ne ya amsa min sallaman nawa don shi sai wani kallo yayi min ya kawar da kan shi gefe daya. Nima yi nayi kamar ban ganshi ba a wurin khadija ya kuke ya karatu nace Alhamdullahi kune tafe yanzu ashe yanzu ko na shigo hostel din ina cikin makaranta tunda safe. Aike ko alhudahuda ya kauce maki ga karatu yanzu kin zama ina zaki karatu, ina kika fito karatu . Dariya mukayi dukan mu dashi nace sunan da na samu ke nan kuma yanzu yace sunan ki ke nan ai bakiga mutumin ki ya dawo bane banji kin tare shi ba. Nace ai bansan yayi tafiya balle in gaida shi da dawowa yace a a fa kada muyi haka dake nace to an dawo lafiya ya hanya ya mutanen can ? Saida ya sauke wani irin sayayan ajiyan zuciya yace Lafiya kalau suna gaidaku ya karatu fa nace Alhamdullahi lafiya. Allah bada sa a nace amin yace ya naga kin ramay haka may ke damuwan ki kuma ko duk karatun ne haka ? Nace kila dai idon kane ke ma gizo amma ni ban ji na ramay ba Yusuf yace yaganine ya fada halan dan banufen ki bai fada maki kin ramay ba. Daidai lokacin Mamud din daya fito office ya biyo ta gurina ya faka motar shi gurin idon ni da Yusuf muka bi motar dashi. Bai fito ba nima banje gurin shi ba don wullakanci baida kyau Yusuf yace wanan mutumin ya zama maye ana maganan shi sai gashi. Rai bace ya juya yana kallon shi yace waye wanan din kuma ? Cikin dakiya na bashi amsa da fadin wanda zan aura ne in sha Allahu nan bada dadewa ba cikin wani yanayi yace What da mamaki nace barin kirashi ya gaida yayye na ai. Ban tsaya jiran abinda zasu fada ba na wuce wurin mamud nace mashi ga yayyena sun zo yazo ya gaida su da saurin shi ya fito daga motar yazo gurin su su gaisa. Sun dawo daga tafiya ne suka zo su duba ni ya mika masu hannu da kyat AA, ya bashi hannu suka gaisa dashi yana masu yaya hanya . Yace khadija zan tafi sai eight zan dawo tunda kina da baki yanzu ya juya tafi ya barmu nan dasu. Shiru gurin yayi na dan lokaci yusuf ne ya kawar da shirun da fadin khadija wai kina nufin da gaske wanan mutumin zaki aura ko may ? Kana mamaki ne da ba auren shi zan yi ba zan gabatar maku dashi ne a matsayin ku na yayyena a gaban ku. Yusuf don Allah ciro mata tsarabanta ka bata mu tafi kar mu bata lokacin mu anan nace ai da kun barshi ai ko ganin ka dawo lafiya yafi tsaraban da zaku kawo min . Don Allah ciro mata mu tafi don banda lokacin magana yanzu ban son damuwa akwai gajiya a tare dani ka sani. Fita Yusuf yayi ya bude bayan motar ya fito da wani jakka mai daukan ido yana miko min tare da fadin ga tsaraban ki nan aboki na ya kawo maki daga Italy. Nayi mamakin ganin wanan katon jakkan yadda ya dauko shi ba tare da matar shi ta gani ba godiya nayi bayan ya aje min jakka a gaba na. Ya koma mota ya tayar suka tafi na ja jakkan zuwa ciki ina mamaki a raina guri na samu na aje can kuryan dakina ina jiran shigowan maryam dakin. Sai da ta dawo tana shigowa da jakkan tayi arba tana fadin wanan kuma fa khadija ? Nace bari ke dai maryam wai tsaraba ne duk wanan kike gani su Yusuf ne suka zo min dashi A A ya dawo daga italy tace bakaji batun ba maye a ciki. Ban bude ba ina jiran ki dawo mu bude ne da sauri ta karasa wurin tare da jawo jakkan ta fara budewa tana ciro kayan dake ciki. Dogayen riguna ne a ciki har kala bakwai sai turare da su man shafi da jakka handa bag da sauran tarkacen mata a ciki . Zip din jakkan taja sai ga set din sarka da yan kune da awarwaro suma a ciki da sauri ta karasa fidowa waje. Sai da na gyara zama na alokaci don mamaki sai ta kara fida wani agogon hannu na mata mai ruwan gold mai daukan ido shima. Nauyi da kunyan kaina naji maryam ta dago kai tana kallona da mamaki fal a fuskan ta tace khadija kin ga wanan kayan kuwa ? Nagani maryam nace mata tare da lumshe idanuwana ni kadai nasan abinda nake ji a lokacin. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABUJikina yayi sanyi sosai da kayan da naga ya sayo min musu kya dagani kasan ai kashe kudi a wurin sarkan maryam ta daga tana fadin. Wanan kan kizo kiji kudin shi zai kai a kala dubu dari uku fa saurin kallon ta nayi nace kai haba wanan dai kila mafa fashion ne kawai. Khadija wallahi gold ne haba baki ganin shi ko agogon nan ban debe tsamanin shi ma fashion bane nace a wani dalili zai sayo min kaya haka masu tsada bayan yasan iyayyena talkawane idan naje gida dasu may zan fada masu akan wanan kayan haka ? Rigunan ta sake tabawa tana daga su tace wallahi ko kayan nan anan zasu kai dari biyu kila koma sufi zaune nakai ina fadin shi wani irin mutum ne da baijin wuyan kashe kudi haka ? Maryam dariya tayi tace khadija ke nan baki san ko waye shi ba yasa kike fadin haka bafa karamin mutum bane wallahi kudi na shigo mai ta kowani hanya. Zasu iya sai da fili daya a wuni su samu milayan dari riba bakomai bane wanan a gare su wallahi kwanaki da mijin yaya na zai sai wani fili AA akace sai ya gani ya sa mashi hannu zai iya samun filin. To mutum da ke samun kudi haka don ya sayo wanan ai kamar ki jefa allura ne a cikin teku gare shi gashi nan muna ganin shi a banza amma mijin yayana yakai wata uku yana neman ganin shi bai samu ganin shi ba. Da sauri nace shi din tace wallahi Allah khadija wanan AA din kuwa shine don na tambayi anty na nayi mata kwatancen shi tace shine kuwa wallahi ba karamin kudi yake dashi ba ai. Banda abinki duk wanda kika ga ya auri buzuwa gidan shi har ta zauna haka ai ya mallaki abinda ya mallakane. Dubi shadda da tasa ranan da gwalagwala a hannun ta da wuya ke ko shaddan nan da zaki ji kudin shi zaki sha mamaki wallahi. Ido na lunshe na koma na kwanta ina tunane a raina gaskiya ya zama dole in raba dasu kada suzo su batani haka da itin kayan nan in zo gaba abin ya damay ni na saba da saka mai kyau in sha in kuma ci maikyau. Ranan da banda mai bani irin wanan yaya zanyi ga iyayyena tallakawa ne lis muna neman abinda zamuci a gidan mu. Muryan maryam ne ya dawo dani daga tunanen da nakeyi tana fadin khadija zaki iya samun fiye ma da hakan gun samari don kyauki ne ya jawo maki haka . Don ke din baki da maraba da yan buzaye dole ne na miji ya ganki ya rude haka sai dai shi AA nashi sallon son yazo daban da na sauran maza ne. Yace dake sona yake yi da kike fadin haka kawai dai mutunci ne a tsakanin mu kune dai dake da Yusuf kuke ganin haka din amma ni ba wani abu makamancin so daya taba hada ni dashi. Balle yanzu nasan da wuya su kara dawowa inda nake don na fada masu mamud zan aura kuma har na gabatar dashi a garesu sun gaisa dashi dazun. Kikayi may khadija amma wallahi baki kyauta ma kanki ba wanan wani irin cin fuskane haka kikayi masu lalle kan da wuya su dawo gurin ki kuma sai dai da yake maza ne basu fushi da abinda suke so kai tsaye. Mun dauki lokaci muna maganan da ita har dai nagaji na kyake ta tanayi ita kadai na bata baya. Yau da wuri muka dawo dawo daga class bamu dade irin yadda mukan dade acikin makaranta ba maryam ta rigani dawowa har na samu ta gama abinci ko. Dafa dukan manja yaji atarudu ta hada muna sai naman datayi amfini dashi a ciki danye zaune nake ina cin don ita tace tasha tea da tadawo don maryam bata wasa da cikin ta ko kadan. Na kusan gama cine wata Ruth Samuel ta shigo dakin tana cewa ina da bako a waje yana jirana maryam ne ta kallo ni bayan Ruth tafita daga dakin tana fadin yanzun haka mamud ne dan kadafin tsiya ya biyo ki. Nace kada kiga laifin dan bawan Allah a banza don nagane ke son wanda baisan kinayi ba kike yi yasa kike ganin laifin mamud din. Hijjab dina karami na dauka ina sawa nake maganan na fita waje ban jira may zatace ba kada ta bata min rai. A zatona mamud din ne yazo amma ina fita sai banga motar shi ba a wurin fitowa Yusuf yayi daga cikin motar da yazo da ita yana min hannu. Zuwan Yusuf din ya bani mamaki matuka don banyi zaton zasu kara dawowa inda nake ba kuma . Na iso inda yake tare da sallama yanayin shi kawai ya nuna min bai cikin dadin rai a lokacin yace ya karatu nace Alhamdullahi. Shirune ya dan biyo baya sai ido daya kura min yace dama nazo ne neman alfarma a gurin ki idan zaki iya yi min . Da sauri nace in zan iya may zai hana in maka tunda har kataso kazo gare ni a wanan lokacin haka. Ajiyan zuciya ya sauke yace ina son ki shiga ki shirya yanzu ki fito in kai ki asibiti ki gaida Abdulsamad ne yau kwanan shi biyu kwance bai da lafiya ya dawo da ciwon ciki sosai tunda ya dawo. Subbahanallahi na fada mace ciwon ciki kuma kodai yaci wani abin ne baku sani ba yace ciki da kai yake fadin yana mai ciwo tun kwana biyu da dawowan shi waje. Ko ranan da muka zo wurin ki cikin karfin hali nasa shi muka zo ke kuma sai kika bata muna rai da dan banufen ki. Murmushi nayi nace kuka dai bata ranku ga banza amma ni ban bata maku raiba gaskiya yace kin ko san kishin maza yafi na mata khadija ? Kishi akan may zaiyi kishi kuma don dan wanan magana kawai yace wallahi ba don nasan Abdul tun farko baida lafiya ba da sai in ce har da maganar dan banufen nan ya sashi ciwo haka. Sai dai bai karamin magana ba tun wanan lokacin a kan ki yanzu ma ni naga dacewan haka nazo daukan ki muje ki duba shi don Allah. Nace gaskiya ba zan iya zuwa ba da sauri yace khadija kada muyi haka dake mana na dauka zan iya saki abu kiyi don ni koma badon niba ai yaci kije ki gaida Abdulsamad din tunda akwai mutunci. Kai na girgiza tare da fadin Allah dai ya bashi lafiya amma ni ba zan tafi ba idan ma naje matar shi ta ganni may kake son in fada mata kuma don komai tamun tana da gaskiyan ta. Balle ma bazaku hadu ba don ita tana gida bata faye zuwa ba sai sa a mommy ce dai a gurin nashi take jinyan shi. Ko zan tafi bani kadai zan tafi ba sai inda maryam na fada yace gaskiya ne hakan yana da kyau ai wallahi ni ma kin ga na rude ban ko kawo haka ga raina ba sai yanzu. Don Allah ki daure kizo muje khadija yin hakan yana da kyau sosai wallahi ciki na koma na fadama maryan zuwan Yusuf din tace muje don Allah ki duba shi gaisuwa ai ladane gare shi so sai. Mun shirya ba laifi don zakace ba asibiti zamu tafi ba don maryam ne ta saka in shirya haka don kada muje mu hadu da buzuwa a can ta raina muna wayo. Nace in sha Allahu ma baza mu hadu ba har mu dawo muka fito muka kama hanya ina gaba tare dashi maryam na zaune a baya. Yusuf ya kawar da shirun da motar yayi a lokacin yace nasan zaiyi mamakin ganin ku yau saidai don Allah ki tuna a wani hali yake yanzu. Nan dai ma banyi magana ba sai murmushin da na danyi kawai yace maryam khadija ta fada maki abinda tayi muna ranan ko ? Wallahi ta fada min bata kyauta ba ai nayi mata magana kasan tayi nisa yanzu ga son dan banufen nan bata jin kira sai ta kai. Da sauri yace ehyehh tayi nisa fa kikace har ya shiga gidane bamu sani ba komay ? Amma khadija idan kin muna haka baki kyauta muna ba wallahi yaya zaki yi da abokina kuma idan kika fitar da wanan mamud din ? Nace Allah kadai yasan wa zan aura yanzu da kuke wanan magana niko mamud din ina shakku a gare shi ne don ban faye son mutum mai mata ba a rayuwana . Murmusgi Yusuf yayi yana kada kanshi yace yanzu dai kikai magana dama nayi zaton don ki musguna na munane kikai hakan. Nace a a wallahi ni gaskiya na na fada maku har cikin raina bandai son mai mata ne a rayuwana yasa nike shakkan shi. Tsaya yayi ya sayo kayan dubiya asibiti ya dawo ya shiga motar muka tafi dan jefi jefi yake dan jan mu da magana har muka kai inda zamu. Motar ta shiga cikin Turkeys hospital ya samu wuri ya faka muka fito zuwa cikin dakin da aka kwantar dashi wurin tsit yake baka cewa akwai mutane saboda natsuwan da wurin ke dashi. Da sallama muka shiga dakin yana gaba muna bayan shi biye har zuwa cikin dakin yana kwance rai,rai ya doran hannun shi daya saman goshin mommy tana zaune gefe saman kujera tana duban wayan hannun ta. Sallaman mu yasa ta dago kan ta tana amsa muna tare da zuba muna idanu don bata sheda ko suwaye tafe don maryam ce ke bin Yusuf din. Sannun ku da zuwa tace muka amsa da sannu mommy muna gaida ita sai can tace khadija kune tafe kun san baida lafiya ne ashe , ? Yusuf ya karba da fadin wallahi sunji mommy yanzu na gansu shigowa nan din na karaso dasu ya mai jiki nace da mommy . Mai jiki gashi nan yaji sauki yau ai mun ga hankalin shi jiya kan da muka zo abin ai ba dama wallahi. Maida hannkali na nayi inda yake kwance yana saye da wandon three quarter fari sai yar riga irin na shan iskan maza din nan mara hannu amma rigar na da kauri blue colour. Ya jikin nace a cikin wani irin murya mai taushi da sanyin jiki tare da dan kura mai manyan idanuwa na a hankali ya sauke hannun shi saman kan shi yace da sauki. Shirune ya biyo dakin na dan wani lokaci Yusuf ne ya karaso zuwa bakin gadon suna magana dashi wanda ba lalai ne mu jisu ba. Ledan da muka shigo dashi ya mika wa mommy yana fadin mu muka zo dashi tace kai khadija ina laifin zuwan da kukayi ke da ke makaranta kikaje yin wani dawainiya kuma haka ? Tana nuna mashi daga inda yake kwance tare da fadin kako gane ta yarinyar nan ne kawar su Binta da suka kwana wurin ta kawar matan officer na layin mu. Murmushi yayi mata kawai ba tare da yace komai ba muna nan tsaye jin yace yace Deedar akwai ayaba ki bare min in ci kai na gyada mai ba tare da nasan ko akwaishi ba. Na bude ledan ina ciro ayaba daga ciki na fara barewa na miko mai tashi yayi zaine ya dan jingina jikin shi da filo ina mika mai a hankali yana karba dakin yayi tsit a lokacin. Kofan aka turo wasu mata ne suka shigo dakin hamshakai dasu idon su caraf a kaina a yadda nake tsaye wurin kan shi ina bare mai ayaban ina bashi yana ci ko mommy ido ta zuba muna tana kallon mu sai take gani kamar da can musan junane ko kuma namu daine yazo daya bata sani ba. Shigowan matan ya dauke mata hankali ga barin kallon mu ta maida hankalin ta gare su suna gaisawa dasu. Kun fara jerabawa ne ko da saura ya tambaye ni mutum ba zai iya fahintar abinda yake fadi ba saini dake kusa nake jin shi nima a hankali na mayar mashi da amsa da cewa next week zamu fara insha Allah. A yadda muke magana zaka dauka wani magana mai ma,ana mukeyi idon matan nan da suka shigo su uku ya dawo a kan mu suna kallon mu gashi jikina na kusa da nashi kamar dai mata da miji. Mommy ke fadin yaji sauki sosai yau gashi ma yana cin ayaba har mun ga idon shi ai jiya abin ba dama wallahi. Basu tsaya ba suka yi ma mommy sallama tare da fatan Allah ya kawo sauki suka fita muma bamu dade ba mukace zamu tafi Yusuf ya taso yana fadin barin je in sauke ku ko ? Sallama mukai masu muka baro asibitin Yusuf ya fito ya sauke mu tare da yi muna godiya nace ba komai ai Allah dai ya bashi lafiya. Fitan matan kenan daga daki suna shiga motar su dayan tace nikan yau naga abu wallahi wai waye wanan yarinyar danagani tare da mijin Nafisa. Dayan tace aini yau imani ya kashe ni anan anya Nafisa batai sakaci ba kuwa ta yaya zata zaune gida ta bada damar wata na mata jinyar mijin ta don tsaban son jiki da sakaci irin nata. Wanan may ta sani banda karyan arziki da nuna son miji a baki kawai waya ta daga ta kiranta tana labarta mata abinda suka gani. Bata jira ta gama bayani ba ta kashe wayan tare da fitowa waje a sukwane tana zunduma ashar tare da fadin su Yanyala su biyu ta. A hanya take fada masu abinda ke faruwa a asibiti da mijin ta da wata sai dai kafin su zo mommy tasha ita da Yusuf da mijun nata uwa uba yarinyar da bata san ko wacece ba . A fusace ta turo kofan mummy dake zaune tana lazimi ta dago kai tana kallon ta da shigowan ta tace ina yar iskan yarinyar da tazo tana bare ma Ayaba ina karuwan yarinyar ta tafi ? Wacece ita wa ya bata dama tazo kusa da miji na haka tana magana tana zaran ido ta kalli mummy ta kalli Abdul di dake kwance yana kamllon ta. Nafisa you're very stupid zaki shigo ma mutane daki ba sallama kizo kina fadin rubish haka wakika ba ajiyan yarinyar da kike tambaya ? Mommy tace wace yarinya wai take magana ne wani kallon wullakanci tayi ma mommy din tace ko wace yarinya ce ai kun sani ni za a munafunta kuma ? Dama na sani ai abinda ake kulla min ke nan ba yau ba wallahi anyi kadan aga baya na a gidan nan balle aje a dauko wata karuwa tazo tana bare ma ayaba tana baka a baki. Subbahanallahi wani munafuki ya fada maki haka mommy barta an bare min ayaban an bani a baki may zakiyi ? Au ashe ma kasan karuwan ka tazo har ta baka ke nan karuwa kema kin san nafi karfin karuwa don yar kwarai ce ba irin ki ba da tashigo duniya tabar iyayyen ta. Babangida kubar maganan nan don Allah tunda kai kasan gaskiya tace dole kice haka mommy tunda dake ake hada bakin yin haka. Samad akan karuwa kake zagi na har kake min gori na baro iyayyena gida nazo nan ni kadai. Ba karuwa bane yadda na aure ki haka itama zan aure ta in kawo gida ta zauna dani tafiki komai da kike tunanen kina dashi. Ido ta waro waje kafin tai magana security din asibitin suka shigo suna kokarin jan ta waje suna fadin ba ai masu hayaniya anan kuma ba lokacin zuwa duban marasa lafiya bane yanzu. Samad aure kake fada min da bakin ka zakayi aure fa kace suka tura ta waje tana masifa tana zagi mommy mamaki ne ya cika ta da jin kalamin da ya furta. Bayan fitar ta tace Babangida dama kuna tare da khadija ne ko dai ka fada mata hakane don ka bata mata rai. Mommy bar yar iskan matar nan da bata da hankali zanyi maganin ta nan bada dadewa ba. Lamarin Nafisa ne sai hakkuri kabar biye mata kuna sai da hali haka haka ba tarbiyan ka bane wallahi. Bai iya mata magana ba don ranshi a bace yake da abinda nafisa tazo tayi masu yanzu sai mommy tace wai ma a ina taji wanan abin ? Har take aibanta yarinyar mutane haka khadija ne take kira da karuwa wanan bata da tarbiya wallahi. Har ta kare bai mata magana ba tace Allah ya kyauta taja bakin ta tayi shiru zuciyar tab da sake sake a cikin shi. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABUTunda muka muka bar asibitin shiru nayi ban iya magana ba sai su ke dan hira jefi jefi a motan ajiyan zuciya na sauke ina fadin yanzu baku ganin kamar yawan ciwon kan nan wani abune ? Da sauri Yusuf ya juyo yana fadin wani abu kamar yaya sai nayi shiru kuma yace tambayan ki nake yi mana kin yi shiru kuma. Nace akwai ciyon kai irin wanan da yake na shihiri ne in kunyi diba ga irin matar nan nashi zai yuyu wani aike tayi mai wanda bai zauna a jikin shi ba sai ya iya haifar mai da hakan. Idan ba kasan da irin shi ba ba kowa ne yake gane hakan ba zaka mutum na fama da ciwon kai mai tsanani ayi ta magani kamar ba a yi. Nima gani nayi a makwabtar mu haka ya faru koma dai ba shi bane ya kamata ku hada da na gargajiya tunda likitoci sun ce basu ga komai ba su . Shiru yayi na wani lokaci ba tare da yayi magana ba abubuwa da dama yake tunane a ranshi sai can yace maganan ki na da kamar gaskiya khadija. Don dai a yadda yake rike kai yana kugi zakace zai iya mutuwa ne a lokacin kuma kan sai cikin dare kawai yake damun shi . Nace abinda ya ban mamaki ke nan nima ace ciwon kai kamar na sihiri sai dare kawai yake tashi cikin ne ma wani lokaci yake dan tashi da safe ko idan ya ci wani abu. Allah ya sauwaka nace maryam dashi suka amsa da amin lokaci daya maryam tace gashi har ya ci ayaba ya zauna mashi ciki lafiya abin ya ban mamaki ai. Nidai har muka shiga hostel ban yi magana ba sai dai ido da sauraren su da nake yi kawai. Kwance nake tun bayan dawowan mu da nayi sallah magariba da ishai na kwanta nan iya cin komai ba na kwanta zuciya na cike da damuwa. Washe gari tunda safe da na tashi ina shiri jikina ba karfi a tare dani sai tunane nake na yadda na ganshi kwance jiya yana jin jiki sosai wai a haka yaji sauki ke nan. Waya na nadauko ba tare da na tsaya tunane ko yana barci a wanan lokacin ba na dana mai kira wayan ya shiga yana ta ringing ba a daga ba. Sai kusan zai katse aka daga wayan muryan shi da alaman barci a tare dashi yace hello Deedar ya kike nace ina kwana ya amsa da lafiya nace ya jikin yace jiki da sauki nagode. Sai nayi shiru yace hello dayaji shirun yai yawa nace kaji sauki sosai ko yace mm a ji sauki Deedar ya kuka koma jiya nace lafiya a sanyaye. Can nace nagode Allah saka da alheri yace namay fa nace na tsaraban da ka kawo min ranan nagode kwarai Allah saka da alheri tsaraba haka da yawa. Yace ba komai nagode sai an jima na kashe wayan ajiyan zuciya na sauke ina aje wayan cikin hand bag dina tare da lumshe idona. Haka na shiga makaranta jiki ba karfi duk yinin ranan haka nayi shi a sukurkuce dani yau ma kamar jiya na dawo ban dade ba a cikin makaranta na dawo. Yusuf tunda ya aje mu hankalin shi ya koma kan maganan mu kawu salisu ya kira yana fada mai matsalan Abdulsamad din. Kawu yace zai je a ga malam yayi mashi bayani komai kai tsaye asibiti ya nufo inda ya samu Nafisa na fada da security a bakin get. Nan ya tsaya rai bace yake masu magana abin mamaki sai ta maida fadan wurin shi tana fadin sune ai munafukan da suka ja a wullakanta ta din sun dauko karuwa sun kawo ma samad har cikin asibiti tazo tana iskanci. Da mamaki yace karuwa may ya hada AA da karuwa kuma tace in ba karuwa bane may zai sa tazo tana bashi ayaba a baki ? Kai ya girgiza yana mamakin inda maganan ya fito mata yayiwa security din magana akan su kyalesu su wuce basai sun tura ta ba. Ciki ya shiga fuskan su kawai da ya kalla yasan akwai damuwa a tare dasu yace mommy ya akayi har Nafisa tazo nan da fitina haka ? Yusuf Nafisa tana fada ne bisa ka,ida zuwa tayi nan tana hauka nasan kawayen ta ne da suka zo dazun suka fada mata don dun samu yana cin ayaban da suka shigo. Ya girgiza kai yana murmushi yace mun dai auna arziki bata samu su khadija a nan ba da ba karamin tashin hankali zasu yi ba don ko ita khadija ba baya ba da alama wurin fitina. Khadija ce kaidai zata yi daidai da gidan Abdulsamad a halin yanzu mommy don itace kadai nake ganin zata iya da Nafisa a yanzu. Shi babangidan yace yana son ta ne ko ya nuna wani alama na ra,ayin tane da dai zanyi hakan gaskiya da yayi dace da kamilan mace a gidan shi don ni yarinyar tanayi min wallahi. Don akwaita da natsuwa da girmama na gaban ta ga ilimi addini da na boko ta samu a tare da ita kaga kowa ma zaiyi kwadayin wanan mace a gidan shi ai. Tun farko ina ma yaran gidan mu kwadayin ta sai dai kasan yaron yanzu ba ai masa haka gara inshi yagani da kanshi yace yana yi shine za a zauna lafiya. Duk da nasan khadija tana da masoya ko anan kaduna din amma haka bai hanani jin wani nawa ya so ta ba. Amma kai da kake fadin haka akwai wani abu makamancin so ne a tsaka su dama kodai dacewan haka kaima ka hango yasa kai magana ? Mommy gaskiya ba zan boye maki ba akwai sai dai dan nakine miskilanci da ji da kai da izza yahana shi tsaya su fuskanji juna shi da ita kin san kuma ba a son mutum da haka. Shi yana ganin idan yaje mata da zancen so kamar ya zubar da kiman shi a gare ta ita kuma khadijan kallon yan uwa take muna a yadda na fahinta ni. Sai dai dukkan su suna boye feeling din su ga juna ne amma indan so akwai so gaskiya miskilanci shi dai ne ya hana ya nuna mata haka din. Murmushi mommy tayi tana fadin dana ai ba a haka yanzu matan yanzu sai da so ake saye zuciyar su bawai da kudi ba kawai don ba ko wace mace bace kudi yake gaban ta ba. Mommy dan nan naki in kiyi duba gare shi bai fa san so ba shi don a yadda ya auri Fati da Nafisa ba wai an tsaya anyi wani soyayya bane dasu. Auren fati dai kin san komai akai hadine na iyayye tun farko ita kuma Nafisa abu biyu ne nake ganin ya kai su ga aure. Na farko kin san akwai shi da son fararen mata dogaye sai na biyu ita din batazo mashi abanza ba sai da ta asirce shi. Wani kallo yayi ma Yusuf din dake magana yana kwane ya harde hannayen shi sama kirjin shi kafafuwan shi a harde yana karkada su a hankali. Ni kake wa sheri haka Yusuf kuma a gabana Yusuf yace ba sheri bane abinda nagani nake fadi ni baka son khadija ne karya ne maka ? Ke nan ashe sun dade tare da ita mommy ta tambayi Yusuf din cikin son karin bayani gare shi. Don ni na dauka zuwan nan na su Binta ne kuka hadu da khadija din har kuka santa yace a,a mommy ba zuwan su bane muka santa don gaskiya dama muna tare da ita. Ikon Allah a mu kuka boyewa mawa dama amma yaran nan kun iya taku har karshe yanzu ashe kuna tare da yarinyar nan kuna nuna ba komai a tsakanin ku da farko ? Hakan na da kyau da kuka boye ba laifi bane haka yayi daidai nima zan kama baki na inja ga wanan maganan badon komai zamuyi haka ba sai don matan shi. Duba yadda Nafisa tazo nan tayi muna yanzu bata san da komai ba ke nan ina ga inta sani din sai idan abu ya kankama a tsakanin su lokacin da wani bai iya komai za a fitar da zancen ga kowa yaji. Don idan ba haka ba maganar sai yazo yabi ruwa azo ba ayi shi ba sai dai babangida ya kamata ka daina wanan halin naka don ba haka ake neman ba yanzu. Kamata yayi ka bata lokacin ka ka nuna mata so da kauna ta yadda zata saki jiki dakai har a cin ma abinda ake so. Mommy sheri Yusuf ne kawai yarinyar nan a yan uwa ta dauke mu har ta gabatar muna da wanda take so ta aura fa. Tayaya zaice kuma ni na kutsa kaina ga abinda ta riga tayi nisa ga wani gare shi da sauri Yusuf yace. Wanan magana ba gaskiya bane dakai da mamud din da tace wa yariga wa ta riga sani cikin ku biyun kai ta fara sani kasani ba wancen ta fara haduwa dashi ba kaine ta fara sani. Yusuf kabar wanan zancen don Allah yarinyar da kaji mommy ma ta fada tana da masu son ta akan may zan tsaya bata lokacin gun ta karamar yarinya ma da ita haka da tara maza ai babu komai sai wulkanci a gurin ta. Da sauri Yusuf yace ta taba yima wullakanci ne da zaka fadi haka san nan kuma kowa ai da karfin shi yake zuwa ya gwada tashi sa,an akan mace idan tai ruwa rijaya idan batayi ba masai. Banda wanan lokaci kai ka sani so don Allah kubar wanan zancen na Deedar please zan dai yi hakkuri ina zauna da wa yan nan da Allah ya hadani dasu. Munyi magana da Abba Fati zata dawo dakin ta karshen watan nan ya kuke son inyi da mata uku yanzu biyun ma yaya na iya dasu balle na kara ma kaina wani wahala can. Aure ne kawai mafita gare ka a yanzu saboda ta haka ne kawai zai kawo fitar da zargin da ake maka akan Nafisa ta mallake ka don ni nasan matsalan ku da Fati wanda ma kowa ya sani in ba wani aure kara yi aka gani ba, bazaka fita bakin mutane da zargi su a kan ba. Mommy ban damu da abinda mutane suke cewa a gare ni ba tunda nasan ina tsare kaina ga duk wani abin hani. Mommy tace babangida kada kace haka idan kasan kana son yarinyar nan kada ka bari wani yazo ya kwace ta daga gare ka. Shawaran da zanbaka shine ba,a kin shawara idan na kwarai ne ka gwada a gani ko hakan ne mafita a gare mu kaga sai a wuce wurin a manta da komai sai fatan samun zuri, a masu albarka. Murmushi Yusuf yayi Allah yakawo lahadi don litinin yai niss inji maza ranan nasan ni za,a kira da munafuki yafi a kirga gun Nafisa. Yanzun dai maganan mommy ne mubar wanan zancen a yadda yake a rufe sai munga komai ya kan kama za a ji. Mommy kaifin basira irin na khadija yasa nake mashi kwadayin ta a gidan shi don khadija yarinya ce mai tunane wallahi. Mommy ta tashi taje yin alwala lokacin ne Yusuf ke fada mashi gobe yana son ya je zaria da safe akan ciwon shi yaga malamin nan na gurin kawu salisu. Yace kana ganin zuwan ka wurin shi yana da wani alaka da ciwo nane ko may ko wani abin ne zai kaika wurin shi. Sai da ya mike tsaye don zuwa sallah ya bashi amsa da cewa akan ciwon ka nake son zuwa can don yanzu wanan shawaran yazo min . Bai mai magana ba sai mikewan da yayi shima don zuwa yin sallah magariba data gabato a lokacin. Da dare yana kwance na kira shi muka gaisa na ba maryam ita ma tayi mashi yaya jiki yace da sauki ya gode muka kashe wayan. Maryam ne tace ni har yanzu sai nake ganin kamar jikin nashi da sauki a yadda naji muryan shi a yanzu nace haka nima nake tsammani danaji. Daga haka ban kara cewa da ita komai ba ina kwance rigingine ta dauko waya tasa muna kira,a shine naji hankalina yana kwantawa a hankali naji damuwan da nake ciki wanda ban san dalilin shi ya fita a raina har barci ya dauke ni daga hakan. Washegari na tashi wasai dani wanka nayi na shirya na kama hanya zuwa cikin makaranta don ina da test a ranan gashi banyi wani karatu ba isashe. Ban fito ba sai yamma lis na fito daga cikin makarantan alokacin yunwa ne ya addabe sosai a sukwane na shigo dakin ina wurgar da handbag dina ina cire hijjab din dake kaina a lokacin. Maryam kuma bata dawo ba nake gani alokacin don haka na fara kokarin hada jeloup din taliya don ina ganin shine mafi saukin dahuwa a gare ni a wanan lokacin. Agurguje nake aikin daidai lokacin da na kusan gamawa ne wayana kira ya shigo min sai da na duba abincin sama sama na dauki wayan. Ban tsaya duba mai kiran nawa ba naji murya shi yana fadin yau ba akira anji jikin nawa ba dan banufen naki ya dauke maki hankali ko ? Murmushi nayi a baiyane ta yadda har yaji a cikin wayan mommy bata nan ne daka bugo min waya ? Kina tsoron taji ina waya dake ne a gaban ta komay ? Ina da kunya da girmama na gaba shiyasa amma ba don tsoro ko wani abuba kawai don kawaici ga manya ne . Gata zaune tana jin ki ko in bata wayan ku gaisa ne kana fara shi wanan ma ai fadi ne kawai nasan mommy tafita yasa ka kirani kamar yadda nake da kunya kai ma nasan zakaji kunyan waya a gaban ta ai. Muryan mommy ne take fadin khadija kun koma lafiya jiya ya karatun Allah ya tsare ya kare ban iya cewa komai ba sai daburcewan da nayi a lokacin. Hello khadija ba kya jine ina magana kin yi shiru nan ma ban iya magana ba shiru nayi mata a lokacin sai naji tayi murmushi. Wayan na kashe sai da na gama girkin sai kuma cin abincin ya gagare ni duk da yunwar da nake ji din da farko . Waya na dauko na tura mashi text kamar haka baka kyauta min ba ya zakai min haka ka san girman mommy a idona kuwa ai sai kasa ta zargi wani abu a zuciyar ta a gare mu. Na gama na tura mai maryam ta shigo dakin tana fadin wai yau na gaji wallahi zama tayi tana kallon yanayin da ta samay a ciki. May ya faru tace tana kallon fuska na cikin damuwa ga yadda ta ganni din sake tambayana tayi tana maida hankalin ta gare ni. Ga abinci can ki diba ina kika tsaya har yamma haka lis wallahi mugun malamin nan namu ya tsaida mu haka yau test din yayi wuta sosai tamike tana fadin har kin ci ne ke tana kallo na. Kaina girgiza mata tace kin ci wani abin ke nan ko naga ko karyawan kirki baki tsaya kinyi ba kika fita yau. Wallahi da yunwa na dawo sai da na gama kuma naji ban son cin komai ki sha wanu abu mai ruwa kila yunwa ne yai maki yawa ya hanaki cin abincin. Ta debo ta fara ci tayi nisa ga ci nake cewa da ita kin san may wanan mutumin yai min yau maryam. Da sauri ta dago kanta tana fadin wani mutumi mamud ko wa nace wani mamud kuma AA fa don ya maidani karamar yarinya wai a gaban mommy zai kirani yai waya dani. Maimakon inga damuwa itama a fuskan ta sai naga sabanin hakan a fuskanta dariya ta soma tana fadin lalai wanan dan barki ne . Ya daure tamau yanzu a gurin mommy ta gama sanin komai a tsakanin ku ke nan ? Komai kamar yaya ya dai daure ni wallahi tace ai maganin ki ke nan tunda bakya jin shawara ai gara da ya fito maki tanan. Haushin ta naji sosai a rai na don rashin nuna jin haushin hakan dayayi min da ta nuna rashin damuwan ta akaina. Bayan ta gama ta mike lokacin nayo alwala zanyi sallah itama ta shiga bayin ta dauro alwala muka gabatar da sallah mu. Zaune nake bayan na idar da sallah ban bar wurin ba sai da nayi isha,i na mike ina nade sallaya maryam ta mike ta dauki heater tare da dauko cup ta hada min shayi mai kauri saida ta gama ta miko min. Kamar ba zan karba sai dai na mika hannu ko ba komai nasan shan tea din zai taimaka min ga yunwa da ke ciki na. Tunda na kwanta ban sake bi ta kan komai ba har barci ya dauke ni a haka yadda nake cikin dare na falka na ga ta rufe min kofa itama tana kwance a kusa dani ranan a dakina ta kwana. Zaune take a falon madam datai ma tsuke tunda safe ta isa gidan madam din a yadda ta ganta sai take tambayan ta ko lafiya haka da safe. Madam gaskiya yanzu samad ya rikice min tunda na haihu din nan na rasa gane kan shi gaba daya. Jiya fa a gaban wanan kishiyar uwar tashi yake fada min wai aure zai kara saboda kawai nace sai ya fada min wace yarinya ne tazo gaida shi har take bare mai ayyaba tana bashi ? Ke a ina kika ji wanan labarin ne wai waya fada maki ne shiya daure min kai tace kai tsaye su hajiya karima ne da suka je gaida shi. Baki ga irin wullakancin da security din asibitin nan sukai min bane suka fitar dani waje yana kallo baiyi magana ba. Haba Nafisa kullun ina fada maki magani fa bai ci sai da siyasa da kissa da kisisina da kutungwila na mata. Ya zama dole yanzu ki bishi a sannu ko banza kin zubar da jinin haihuwa a gidan ki kiga komai da kikayi na asiri yanzu ya karye. Ai ba karamin hikima bane aka samo na haihuwa asibiti da mata ke yi yanzu bature ya taimaka ma mata da ya fito da wanan hikimar haka na haihuwa asibiti. Kinga ko da za a dawo da mace gidan ta an wanke komai a asibiti kinga wanan uwar tafiyan na haihuwa yafi komai karya asiri ga mutane ba matan ba ba mazan ba. Shiyasa iyayyen mu na da basu wasa dashi a gida zakiga da sauri ake fitar dashi gida asamu gefe a binne shi amma mu matan yanzu sakacin mu yayi yawa ga komai wallahi. Yanzu ya zama dole gare ki ki lalaba shi ki kara sabon shiri sosai a kanshi dan kada yazo ya bijire maki nan gaba. Zancen kuma aure ni nasan ba dagaske yakeyi ba don ba abinda kika rasa da ake so gun mace yana kuma son ki tsakani da Allah. Zancen kuma ita yar iskan yarinyar dake dmson maki kutse a gidan ki ta dauke maki hankalin mijin ki tambaya zamu muji da gaskiya ne hakane ? Idan da gaske ne sai mu san ta inda zamu fito da zancen nata ga wanan irin arziki da ya taso ma mijin ki haka ina zamu bari muba wata daman da zata shigo ciki muna kallo. Yar iska bamu san ko wace iri bace ita tazo tafimu iyawa dashi babu yadda zamuyi ko wacece zata shigo maki kin san itama ta shirya. Don kishi da buzuwa ba wasa bane duk matan nahiyar nan namu sun sani shiyasa suke tsoron ku buzaye don cire ice har sayen shi komai tsufan shi ba wasa bane gare ku. Madam duk da haka ya zama dole gare ni in tashi tsaye in hana gaba da bayan shi motsi a gare shi ko mace ba zai iya daga ido ya kalla da sunan tausayi ba balle so. Yanzu dai duk ba wanan ba sai fa kin kwantar da hankalin ki ko ta siyasa zaki iya gano gaskiyar maganan gare shi idan kin kwanta amma. Tace a sanyaye naji zan gwada yin abinda kika ce min din tai mata godiya tare da sallama ta nufi gida tana ba kanta hakkuri. A ranan ya samu sallama bayan dawowan Yusuf da bayanin abinda ya girgiza shi daga malam don yace a lemon da ta tare shi dashi yasha batare da yayi bissimillah ba. Yayi arziki akwai tsari sosai na Allah a jikin shi da ba karamin wahala zaiyi ba don ba maganin alheri akabata tabashi ba. Ya iso gida zuciyar shi ba dadi wanka ya shiga don ya tsabtace jikin shi don baijin zai iyacin abinci ga yadda yake jin kanshi a lokacin. Yana zaune bakin gado ta shigo dakin ta saba diyar ta a kafada tana rangaji tana zuwa ta azamai yarinyar saman jikin shi itama ta samu wuri ta zauna a gefen shi. Yadda taga bai sake fuskan shi ba yasata fadin har yanzu abinda ya faru ne kake ma fushi haka ko jikin naka ne har yanzu. Kallon ta yayi yace may ya faru kamar bai fahince ta ba tace akan maganan nan na asibiti da ya faru raina ne ya baci a lokacin nayi haka ba tare da nayi tunanen komai ba. Wanan matsalan ki ne sai dai ki sani duk abinda zaki karbo daga yau da sunan malakana a gidan nan kada ki sake karbo wanda zai cuta min haka don ki sani nasan abinda kika zuba min a lemon da kika bani ranan. Kuma shiya haifa min wanan ciwon danayi ban hanaki yin abinda kike ganin shine mafita a gare ki ba don dama haka yawancin mata kuke da wanan shigeshigen din sai dai ki sani ba zaki taba mallakana ke kaidai ba domin ni din mijin mace hudu. Yana fadin haka ya mika mata yar tare da mikewa ya bar mata dakin nan ya barta cike da mamaki tana wasi wasin ko dai wani ya fada mai a gidan. To ina ma wani ya ganni nida na zuba a cikin dakina amma yaya akayi wanan maganan ya koma kunnen shi haka. Watau ke nan abinda ta zuba mai ne ya jawo mashi haka ba maganin kwarai aka bata ba kena cutar ta akayi akan maganin da ta kashe makuden kudi akan shk a bazan zai tafi ba zaiyi aiki akan shi ba tunda had ya gane may ake ciki. Ko dai shima yana irin nata ne har yaje wani ya fada mai abinda tayi mai tace kai wanda ke kwance haka ba lafiya ina zai iya zuwa ? ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABUKwance nake saman katifan dakina ina karanta handout dina maryam zaune a bakin katifan tana gyara kumbar kafan ta. Waka take wanda take damuna dashi sai ya hanani yin karatun tunanen mamud nakeyi wanda ya kai sati biyu yanzu bai lekoni ba kuma banji daga gareshi ba har wanan lokaci. Hijjab dina dake gefe na dauka na rufe jikina dashi tace sanyi kike ji ko may da zaki rufe jiki haka nace sanyi nake ji wallahi. Na kara jawo handout inci gaba da karatu tace wai ni ko dazun sai naji kina waya ina son in fito in tambaya wakiraki ko mutumin naki ne naga ya dade bai zo ba kuma banji yana kiranki ba. Maryam kin damay ni fa karatu nake kuma kin gani a, a wani karatu yanzu inga kina tunane ke kika ga wanan din na gyara kwanciya ina bata baya. Sai da ta gama abinda takeyi tace don Allah tace muje mini market mu sayo kayan miya nace ban zuwa tare da lumshe idona. Fada min a jiki naji tayi tana dariya tare da sake ihu daidai kunnuwa na a zabure na mike na biyo bayan ta da gudu zuwa waje. Dagani sai dan body hook da nake sakawa a ciki in dora abaya kaina ba dan kwali gashina dana daure ya fado min a baya don duk zuben filani na gajeshi wurin kakannin mahaifan daddy na. A daidai lokacin nz hango motar su tana fakin a daidai inda suke tsayawa da mota idan sunzo guri na ban dauka su bane sai da na duba da kyau don gurin na kowa da kowane masu zuwa wurin yan matan su. Itama maryam din ta gansu da sauri ta dawo inda nake tsaye tana fadin su yaya Yusuf ne can ko ? Ba yadda zanyi don sun gama gani na gashi ko dan kwali babu akaina da sauri na koma ciki ita ce ta tafi wurin su tana gaidasu. Yusuf ne ya tambaye ta gudun may muke haka kamar yara tace wallahi khadija ce ta biyo ni da gudu wai ina damun ta tana karatu. Na fito daga ciki na dora a baya saman kayan ina hararan khadija na iso inda suke tundaga nesa ya watso min harara yi nayi kamar banganshi ba na kawar da kaina ga kallon shi ina gaida su baki daya. Har muka gama gaisawa da Yusuf yana tambayana karatu da kwana biyu nace lafiya maryam taso ta bar gurin da dabara Yusuf yace ta tsaya ai . Munzo muyi maku sallama ne zamu tafi umura gobe idan Allah ya kaimu mukayi masu adduan adawo lafiya Allah yasa a karbi ibada. Daga ida yake zaune baiyi magana ba tun zuwa su yace ashe baki jin magana baki daina saka kaya irin wanan ki fito dasu waje ba ? Nace wasu kaya kuma ina duban kaina da shigan da nayi yace ai kema kin sani yaya kika fito waje dazun ? Haba yaushe zaka daina samin ido hakane aiko wanda zan aura yanzu bai isa ya zaba min kayan da zans saka ba a jikina sai idan naje gidan shi. Murmushi mai kama da yake ya sakar min yana fadin au haka ne fa kuma gaskiya na faye sa ido. Yusuf yace kajiki da wani magana kuma akwai wanda yafishi sanin ya kamata akan ki ne yanzu dole ya nuna bacin rai ga abinda yake da iko dashi. Dariya nayi sosai nace sai kace nice buzuwa ko anty Fati wanan dokan yanzu ai sai daddy na yakai can. A bari a rabu lafiya kin ga tafiya zai yi kada a rabu kuna halin naku kuma kinga zai tafi dake a zuciya kila ba zai maki addua ba idan yaje. Addua kan kulun ai mahaifa na suna min shi kuma yana tasiri gare ni wanan bakin naki kuwa anya wataran bazai mutu ba khadija ? Dariya nayi nace yau dai kun tuna mu ke nan aka kawo muna ziyara haka yace bakin ki zuwa gida ki kara gaida shi da jiki ba ai shi baiyi fushi ba gashi yazo. Dan satan kallon shi nayi naga hankalin shi baya gare mu nan dai mukayi sallama dasu suka tafi. Da yamma ina kwance sai ga kiran shi ya shigo min a wayana nayi makai dalilin kiran shi sai cewa yayi fito gani bakin hostel din ku kai tsaye kamar yadda ya saba ya katse kiran. Na shirya na fito shi kadai na sama kamar yadda nayi tsamani bayan na gaidashine yake fadin dawowa nayi don dazu muna barin wurin nan Abba ya kirani. Yana son mommy ta koma gida kafin in wuce don haka nake son ki rakani musai masu abinda ya dace diban lokaci nayi a wayana bakwai da rabi na dare don haka akwai lokaci. Ciki na koma na shirya sai da na zauna ya tayar da mota nace kana dai son ka ban wahala kai da sukai ma hidima dakai da matar ka ni may ye nawa a ciki yanzu. Na dauka yanzu ma ai da shigan dazu zaki fito tunda ban isa in baki umarni ba ban dai ga dama bai don ba mai iko dani a yanzu. Allah yakaimu in dawo lafiya zanyi maganin wanan fitsaran naki lokaci daya . Ka fara maganin fitsariyar matar ta gida mai fita rabi tsira wace bata damu da hijjab ba balle gyale kafin kazo kafa min dokan ka . Sallon yaudara kawai zaka wani gama kalle min jiki kawani ce kai baka son haka na bayan sai da ka kalle ni tsab. Dama badon akalle ki kika saka ba idan ni kadai zan kalla ba matsala bane a gare ni wasune kawai ban son suga abinda nagani din. Don kanawa a gare ni zaka hana wasu su kalle ni kada ka mata ni yanzu a kasuwa nake banda hakkin kowa ai kaina amma ga masu hakki baka tsa, , , Jinin hannun shi kawai nayi a jikina yana fadin barin fara gwadawa in gani ko tayi min tunda a kasuwa kike kinga idan yayi min basai kin tallata ma wasu mazan ba. Bugu nakai ma hannun nashi sosai da yakai ma jikina yana shafawa bai san ina yi ba sai kokarin gwaucewa nake yi ina buge hannun shi. Fuskan shi a daure bai fasa min abinda yakeyi ba wuri ya samu ya sauka daga titi. Da karfi nace bude min in fita ina kokarin bude kofar motar a gigice hannun shi naji yana cire min dan gyalen da na yafa saman dogon rigar da nasa. A take gashin kaina dana tufke daniyar in na samu lokaci inje gurin kitso ya bayana a fili hannu yasa yana wasa da gashin har zuwa inda ya tsaya. Take naji wani hawayen bakin ciki ya silalo min a fuska na haka bai sa ya daina abinda yake min ba sai ma ji danayi ta rungumay tsam a jikin shi yana sauke wani irin numfashi yana shafa na son ran shi. Kara sautin kuka na nayi a lokacin sai naji ya sake ni yana fadin are you crying bocouse of dis akasuwa fa kike yanzu. Hannun shi yakai saman fuskana yana wasa da hawayen dake zubo min din sai kuma naji ya rungumay ni zuwa jikin shi tsam na dan wani lokaci. Sai da ya gaji don karan kanshi naji ya sake ni ya koma saman kujeran motar ya kwanta yana maida numfashi a hankali. Kaina na dukar naci gaba da kukan abinda yai min din can kuma naji ya tada mota a hankali ya hau titi ba tare da yayi magana ba . Kofan bakin wani plaza mai girma ya tsaya ban taba sanin akwai wuri haka a abuja ya bude motar a hankali tare da fadin fito mu shiga ki zaba masu abinda ya dace dasu kuma ki share wanan hawayen kada ace satoki nayi. Sai lokacin na dago kaina na dubi wurin nace ka sani har kullun Allah ba zai taba baka sa a akaina ba mayaudari kawai. Dariya naji yayi yana bude motar yace banda wanda Allah ya bani yanzu a kanki kuma koko kina nufin karfin ki ne ya kwace ki a kaina . Kuma ki daina kira da mayaudari don da yardan ki muka fito nan ki sani banda niyar aikata komay yanzu a gare ki amma ki aje a ran ki time will soon come . Ko yanzu ke kikaja in maki haka da wanan bakin naki da bai taba mutuwa don ki san irin abinda zaki fada ma mutum. Fita yayi ya zaya ya bude min gefen da nake zaune na sauko motar a hankali na fito don girman jeep din nasa. Mun fara tafiya naji ya rada min a kunne anya kuwa ke ma ba buzuwan bace deedar wanan irin gashi da jiki mai dadin tabawa haka fa ? Hararan shi nayi idon shin kyam a kaina ya sake fadin nayi haka don ki san har gobe nafi wani banzan dake zuwa wurin ki komai. Banyi magana ba don mun kawo bakin shagon haka muka shiga a jera da juna sayaya nai wa mommy har da gaiya don har yaran ta na zabawa abu. Ya kalli kayan mai makon inji yayi korafin sunyi yawa sai ji nayi yace kina ganin wanan kayan sunyi ke nan idan kuma kin sai wa yaran mommy ita kadai su sauran yaran anty amarya fa ? Dole na koma na kara zaba muryan shi ne naji a bayana yana fadin ki zaba ma su ummi da su hajiyan mu kayan suma. Sosai ya kashe kudi bayan na mommy dana su iyan bawa gana su hajiya mama dana zaba masu super masu kyau su ma. Mun kai ya biya ko dar nanga yayi ba da akai mashi list din kayan aka saka ga wani katon buhu zuwa inda motar shi take tsaya nayi ban shiga ba sai da ya zauna ya leko yana fadin shigo mana mu tafi. Nace dashi katafi kawai zan bi taxis in koma ni da sauri naga ya bude kofan motan ban san lokacin da na bude na shiga ba muka bar wurin. Sai da mukayi nisa naji yace kina zaton abinda ya faru zai kara faruwa a tsakanin mu ne yanzu idan haka kike tunane kinyi kuskure. Don ni ko matana dake gida sai naga dama nake waiwayan mace do ba haka nake ba kowani lokaci. Sai dai nayi mamakin ganin yadda kika narke min a jiki kaman dama jira kike in taba ki haka ya nuna min ke nan dama a jirace kike da hakan ya faru. Ban san lokacin da nace mai mugu mayaudari kawai macuci ba wanda ya taba min haka a duniyan nan sai kai kai kasan wani mace ta narke ma ajiki dan, , , , Hannu yakai zai kara kamoni na gwace da zafin nama yayi murmushi yace gobe idan halin ki ne ki kara cika min baki haka. Ba sai ka kara ganina ba zakace in cika ma baki kaji dadin yaudaran da ka sabayi wa mata a kaina. Zaki bar Nigeria ne ko mutuwa zakiyi don wanan ne kadai abinda zai hana in ganki in kara kallon wanan suran da kike kasawa a kasuwa in riga kowa kwashewa. Haushi bai barni na sake magana dashi ba sai juya mashi baya danayi kawai shima bai sake magana ba sai da muka kusa tsayawa naji yace Wallahi shiyasa kike kara burge ni da wanan halin naki na dan juyo na harare shi yace yes i mean it da wata ce sai tayi nata sayayyan amma ke naga ko tsinke baki dauka a shagon ba naan kuma dole kin ga abinda zuciyar ki ke so a ciki . Kinga ke nan kin nuna min abin mutum baya gaban ki idan bai baki ba yana da kyau hakan keep on da wanan hali. Sai dai ai na biyaki ladan ki ko ina ganin ba sai an rubuta maki wani lada ba ko bani wanan lafiyan fresh body din da kika yin kin more ai ke ma. Ya tsaya da motar na bude najita a rufe na juyo na kalle shi nace bude min in fita hug me for d last time tunda kin ce baza mu sake haduwa irin haka ba. Malam ka bude min mota in fita ni ba yar iska bace ka sani wallahi ban sani ba zan dai sani nan gaba in Allah ya yarda ban fahinci abinda yake nufi ba bai kuma bude min motar ba yana jiran wai abinda yace. Na sake cewa da kai fa nake magana ka kyali ni yace even peck kiss yana lumshe ido kamar zan kai kiss din sai na cije shi a kumatunshi. Yana shafa wurin yana fadin wassh ko hakan ai na gode zan tunaki watarana na taba haduwa da wata manya yar Niger mai zubin half cas. Ya bude motar tare da fadin thanks ki kula da kan ki don Allah don kin bar min tarihi nace mugu kawai azzalumi mayaudari da sauri na fita do kada ya kara rufe kofan yana dariya yaja mota tare da min horn ya tafi . Ko da na shiga hostel na samu har martam ta kwanta ina shugowa tace kun dawo tare da duban time tana fadin ban dauka zaku dade haka ba ai. Zama nayi jagwal a wurin fuskana kawai zaka kalla kasan ina cikin bacin da sauri ta mike zaune tana fadin wani abu yayi maki ne. A takaice nace may ye bai mun ba yau maryam AA ya cuci ni ya shammace ni sosai wallahi da sauri naga ta fida ido waje. Nace ban taba sanin dan iska bane sai yau wai nifa AA ya ruguma maryam har da taba min kai kiji min dan iskan banza. Ajiyan zuciya naji ta sauke tare da fadin wallahi har kin saka gaba faduwa na fa dauka ko raping dinki yayi wallahi wani irin harara nayi mata nace ya ma isa. Tace cikin dariya yadda kikai maganan ai dole mutum ya tsorata yayi zaton hakan ne ya faru a tsakanin ku. Nace may ye marabin wanan da hakan don Allah bada hakan ake farawa ba har aje can daga magana kawai sai naji ya rungumay ni don kawai ya nuna min dan iska yake macuci kawai. Tace akan kayan dazu ko na kada mata kai nace ashe kin san abinda zai min kika bari nabishi ke nan tace kema kin faye baki wallahi . Ai gara da kika zabi law don kin iya bakin ki don Allah bani labari nikan in sha dariya don nasan yau ashe yasha zagi a gunki. Nace ban sani ba cikin hararan ta ina mike tace indai gulma kuka kai shi ke dashi kuna son juna kuna wani noke noke . May zanyi da wanan dan iskan ni bakiji ba ma wai shi ko matan shi sai yaga dama yake kara waiwayan mace idan yaga dama. Dariya mai karfi ta kwashe dashi tana fadin ashe akwai aiki kuwa kuma yake sha, awan kara mata fadi dai yayi wallahi. Toni ina ruwana da rashin kula matan shi ko ya kula ko kada ya kula duk uwar su daya a gun khadija don ba abinda ya shafe ni da hakan na fada mai. Nan nabarta tana min shakiyanci alwala na dauro ina son yin waka don kada ta zarge ni haka na fito na tayar da sallah na gama na kwanta banci komai ba ranan. Sai dai ba barci nayi ba don tunane ya hana ni shakat a zuciya na don da zaran na rufe ido abinda ya faru tsakanin mu ne yake zuwa min. Har dai barci yazo ya dauke ni ranan na makara da sauri na mike ina shiryawa sai ga wayan shi ya shigo min. Kamar ba zan daga ba kallon da maryam ke min yasa na daga wayan murmushi naji yayi tare da fadin nasan dai kamar yarda banyi barci ba kema hakan bazaki barci ba daren jiya. Akan may zan hana idona barci nace mai, yace akan dan gidan mommy mana kema kin sani , nace Allah dai ya sauwaka kana ganin kayi wani abun gwanewa kenan, mutumin da ko runguma bai iya ba sai ta hanyar karfi, zai sa na kasa barci na kashe wayan. Yayi kiran duniya naki daga wayan sai ga text din shi ya shigo min kamar haka. Saboda kin san kin zuba min dahin ki a jiki daren jiya yasa kika fara garani ko may ? Niba macijiya bace ai, balle in zuba ma dafi Na tura mashi, ba a jima ba sai ga amsa shi kamar haka , Kin fi macijiya dafi karfa ki manta ke mace ce, mace ko shu,umace ko wace iri ce ita tasan sallon sheri ga da namiji. Kai dai ka sani da kayan sherin ka in ma dafi ne kai kazubawa kan ka bani ba ya karanta yana dariya bai san shigowar Nafisa ba dakin. Sai jin muryan tana tambayan shi kaidawa ke waya haka kake dariya ? Dakewa yayi duk da kaduwan dayayi cikin ranshi amma a fili cewa yayi da ita nida Yusuf ne don yasan ba karatun boko ta iya ba balle ta amsa ta karanta. Ba don ta yarda ba ta kyaleshi kawai tana zargin shi a cikin ranta don yanzu ya fara bata tsoro gaba daya don ya daina sayin ta da yake yi a da can baya. Daga haka ya sauka kasa yana yana kiran yaran aikin gidan shi ya shigo mashi da buhun da ya dawo dasu jiya. Ya sa akai masu dakin da su mommy suke tare dasu iyan bawa a gidan daidai lokacin Nafisa ta sauko kasa tana fadin Sabel wanan kayan haka daga ina kuma ? Yaro gidan dan yaren su na buzaye yace maigida yace ya dauka yakai dakin dabakin shi suke ciki tabi buhun kayan da kallo nan ta so sanin abinda ke ciki. Don haka tabu shi a baya wai taje da sunan gaida mommy yau da kwana yana zaune saman kujeran dakin suna hira da iyan bawa ta shigo tana gaidasu idon ta akan buhun dake gaban shi nan ya fahinci buhun ta biyo a lokacin don ganin may ke ciki. Idon ta ya gano mata atamfan da ya fara fitarwa kasa yana son fitar da sauran sai gata ta daure fuska tamau idan da dane da ya shiga hankalin shi ga yadda ya ga ta daure fuskanta. Sai ci gaba da fitar da kayan yake yana bin sunaye su yadda na rubuta ajikin ko wani ledan kayan yana ajewa gaban mommy bai fara bayani ba ta juya ta bar dakin a fusace cikin bacin rai. Sai bayan fitan ta daga dakin ya fara yiwa mommy bayanin kayan tare da dora ma ko wani kudi a saman kayan yace suyi dinki sai Allah ya dawo dashi lafiya zai shigo yayi masu ban gajiya. Kallon shi mommy tayi da kyau bayan ta gama sauraro shi tace wanan hidimar yayi yawa haka babangida don haka kabar kudin nan abin kuma ya koma biya , ? Mu da mukazo aikin lada zaka saka muna da wanan irin alherin haka mai yawa gaskiya hakan bai muna dadi ba gaba baka son inzo zama da diya ta ke nan in Allah yayi abin. Murmushi yayi yace ko baku zo nan ba mommy zan iya maku fiye da hakan don haka wanan ba komai bane Abba yace a tura ku gida yau kafin in wuce. Nasan ya kiraki ya fada maki komai ai don haka idan da sauran wani abin sai ku fada min a sayo maku kafin ku wuce na kuma gode kwarai da kokarin ku a kaina. Sai dai ayi hakkuri da yanayi matar gidan don Nafisa sai hakkuri nima dai kun ga shinakeyi. Ka dauki kudin nan ko ka rage dawainiyar yayi yawa haka abin ya zama kamar biya mu kayi ke nan ya mike yana murmushi yana fadin ba komai iyan bawa ai yima kaine. Na shirya driver da zai sauke ku idan kun gama sai aimin waya zan dan leka office don tafiyan mu sai dare zamuyi shi akwai dan sauran lokaci zuwa yanzu. Godiya sosai sukai mai ya fita nan dai mommy suka fara shirin tafiya don ba a ketare maganan Abba a gidan. Yana fitowa bai koma ciki ba ya nufi hanyar fita daga gidan muryan Nafisa yaji a bayan shi tana fadin dama nasan abinda ya zaunar da su ke nan a gidan nan tun bayan suna basu tafi ba kamar yadda kowa ya wuce. Suwa ke nan kike nufi wanda kasai wa kaya bada sani ba yanzu Allah ya tona ma asiri na gani do baku so in gani ba. Wai nafisa kina da hankali kuwa iyayyen nawa ma bakin ciki kike dasu akan nayi masu alheri tace ai ba su kadai suka wahala a gidan ba har dasu Yanyala sun wahala . Don may ba zaka saya masu tare ba ka ware naka kadai watau sune ka sani ke nan kai ya girgiza cikin kunan rai yace ba laifin ki bane sai kawai yaga ta sha mai gaba ta inda zai wuce ta. Hayaniyar su ne ya fito dasu mommy waje ganin su mommy ba sa ta fasa ci mai mutunci ba mommy ce ta hana shi magana. Duk ta hade dasu mommy tana zagi tare da fadin tayi ma kowa nashi iyaka da gidan tun da ba zuwan arziki suke yi ba jifa samun wuri a gurin wanan matar ita ha gida taf da yan uwanta kullun sai kara yawan su takeyi a gidan. Kowa yazo da sunan ganin ta sai ya nemi wuri ya zauna ba maganan zuwa gida kuma gare su an shafe ke nan. Haka ya fita gidan ranshi bace ranan su mommy sun ga fitsara a gurin Nafisa inda tayi ta aiban ta su suna ji suna gani ba abinda zasu iya yi tana gani taci gaban su. Ranan haka dai ya wuni cikin bacin rai halin Nafisa ya jutayin irin zaman da suke na rashin jin dadi a gare shi kuma bai jin zai iya rabuwa da ita ko kadan. Bayan su mommy sun gama shiri suka kirashi yace gashi nan zuwa ya samay su a shirye don haka basu bata lokaci ba suka fito da kayan su Yusuf suka loda a mota sukai sallama dasu suka tafi suna kara bashi hakkuri. Da yamma ya fito cikin shirin shi ya samay ta a dakin ta tana zaune tana waya ganin shi bai sa ta katse wayan ba sai data gama yake fadin su zasu tafi. Wani sabon lalura ta kirkiro mashi aladole kudin da take hasashen ya kashe ma iyayyen nashi sai ya kashe mata su bayan ya riga da ya sallamay ta da safe ta lissafa mai abinda take so ya bata. Nafisa wai may zakiyi da kudin da kike karba ne haka ya tambaye ta wani kallo tayi mashi tace idan zaka bani ka bani ba sai ka tsaya ka tambaye ni ba kuma ina sin idan ka dawo zan tafi gida inyi gyaran gidan mu na can. Dole ya bata daga cikin kudin da zaiyi amfani dashi don kawai su rabu lafiya da ita. ZAINAB IDRIS MAKAWA Tun bayan rabuwan mu dashi ban kara jin labatjn su ba haka yasa nasan sun tafi ke nan tun tafiyan su kuma ban sake ji daga gare su ba bakuma labarin mamud. Duk da son mamud da nake a zuciya na yanzu na fara fitar dashi a raina don na fahinci ba wani son gaskiya yake min ba . A cikin haka muka gama exam din mu na wanan zangon kaduna ya kamata in tafi amma don gudun haduwa da mommy a can yasa na kekeshe kasa nace ma Ya Amina ba zan tafi can ba gida nake son yin hutu dole ta kyale ni don tasan tunda nace haka ba zan zo ba. Tunda na dawo gida in ba islamiya ba ban fita ko ina don haka ba kowa ne yasan ina garin ba yau satina biyu da zuwa gida na shirya zuwa gidan anty mu dake aure a falamingo easthe. Tare da karamin kanina muka fito daga gida mun zo bakin titi inda zamu tare Napep din da zai kai mu unguwar nasu mun dan tsaya a gurin na hango wata mota daga can gefe tafe. Zuwa mai shi yayi roud ya dawo inda muke tsaye da kanina a hankali yazo inda muke tsaye ya tsaya ban daga kai na kalle shi ba wata taxis tazo tana tambayan inda zamu. Sai lokacin na cikin motar yace wai ba khadija bace wanan a hankali na dago ina kallon shi mamud ne ya kara yin fresh dashi har bakin shi na sheki. Ya samu wuri ya parka motar shi da kyau ya fito daga cikin motar zuwa inda muke tsaye tare da fadin hajiya khadija ke nan ashe kin shigo garin namu. Nadan yi murmushi nace mamud manya ashe kuna kasan na dauka baka kasan murmushi yayi yana fadin i am sorry wallahi na bar Abuja ban samu leka wuri ki ba sai yanzu gashi mun hadu. Mun gaisa duk da ban wani sake mai fuska ba sai kame kamay yakeyi yace ya labari nace kai za a tambaya kai dana ga sauyi a tare da kai. Yace sauyi gare ni ko a gare ki jifa yadda kika koma dan kwana biyun nan danayi ban ganki ba kin koma wata danya dake kamar wata diyan larabawa wai ma ko kina karatu kuwa ? Dariya nayi nace kai mamud bari bani dariya haka akan titi muke fa yace haka fa ina zaku naga kamar mota kuke jira nan. Filamingo easthe zamu na fada kai tsaye yace muje in sauke ku nace ka barshi kawai zamu samu taxi anan yanzu . A a khadija kada muyi dake please ai ko ba siyasa akwai daga hannu ko dariya nayi nace ashe dai hausa ya zauna a bakin ka haka ? Yana dariya muka taka zuwa bakin motar shi ya bude min gaba na shiga ya bude baya mansur ya shiga ya zagayo ya shiga mazaunin driver ya fara tuki. Mun dau hanya yace van san yaya zan fara maki bayani ba ma sai dai da farko na gode da kika fahince ni har baki nuna min komai ba haka. May kake son in nuna maka gudu da kayi daga wuri na ko may yace wallahi khadija ba laifi na bane ba naki bane. Laifin waye na tambaye shi cikin kallon fuskan shi yace ba zaki gane bane khadija amma tunda kina gari zanzo har gida in maki bayanin komai. Nace kasan gidan mu ne yace zandai sani yanzu daga bakin ki idan kin bani dama can kuma yace gaskiya khadija kin kara wani itin kyau da girma a lokaci daya. Nace kai mamud wanda ke karatun wahala kake fadan haka gareshi dan kallo na yayi yace kin ko ga yadda kika koma kuwa ? Ina dariya na kalle shi nace yaya na koma kuma ya dan bugi sitiyarin motar da hannun shi yace I don't know how to say. Amma ai kema kin san kin sake gaba daya wallahi nace dama ance ku Nufawa mayu ne to kurwa na kur kada ku cinye ni. Dariya yayi sosai yace amma kin kusa gama karatun naki ko yanzu dariya abin na mamud ke bani don na gane nufin shi sarai. Katse shi nayi da fadin ina madam din ka ya fadada murmushin shi yace yaya akayi ki san ina da aure yanzu ? Nace tambayan ka ai nayi suna lafiya yace lafiyan su kalau wallahi daidai lokacin muka shigo Filamingo din da kwatance har muka iso kofan su antyn nawa. Godiya nayi mashi ina bude kofan motar yace khadija na juyo ina kallon shi cikin jan aji yace wani time zaki koma gida inzo in dauke ku ? No ka barshi kawai mun gode da hakan sai anjima nafita daga motar Mansur kanina ya kira yasa hannu a aljihun shi ya ciro kudi ya ba yaron ya tafi bayan yayi min horn. Gidan Ya Hauwa muka shiga da sallama na bude labule falon su da danta babba na fara cin karo zai fito yana ganin mu ya saki ihu yana fadin ga mommy khadi . Murmushi nayi ina kamo shi nace Lawal kaine ka girma haka ina yan uwan ka yace suna ciki jin ihun yaron yasa Ya Hauwa ta fito daga kitchen din su tana fadin sai yau kika ga daman zuwa gidan mu ? Haba dai ya hauwa kema kin san ba halina bane haka na dawo da gajiyan karatu ne wanan karon na dan tsaya in huta. Mansur ne ya gaida ita tace a a mansur tare kuke tafe da antyn naka ashe nace ai kin san mutumi nane shi nan dai muka zauna a falon shi wanda ke bukatan gyara ba halin yin hakan gare su don yanayi. Ranan ni na girka masu abincin rana a gidan yaran suna ta murnan kasancewa tare da mu bayan na gama na gyara mata gida don haka take ba gwanan gyara bace ita amma idan ka ganta a waje sai ka dauka ko agidan ta haka take da tsabta. Ranan sai magariba muka koma koma gida na samu daddy yana fadan rashin dawowan mu da wuri gida. Muna shiga ya mayar da fadan da yake wa mama akan mu may yasa na bari nakai wanan lokacin ban dawo gida ba idan na fita kada in kara kai dare haka bamu dawo gida ba . Kaina yana sunkuye a kasa na amsa da toh daddy daga haka ya fita daga gidan rai bace buta na dauka naje na kewaya na dawo na daura alwala don har an sallamay sallah a lokacin. Sai da na idar da sallah na gaida mama da gida da take dakin ta zaune saman sallaya tana jan tasbaha. Tace khadija may yasa kuka kai wanan lokacin a waje haka kika bari har magariba yayi maku a waje haka baki san fita a wanan lokacin baida kyau ba. Mama kuyi hakkuri ba zan kara kai haka ba tsayawa nayi gyara ma ya hauwa gida shine yasa mukai wanan lokacin a can . Tsuki tayi tana kawar da kanta tare da fadin ita ke nan malalaciya bata iya gyaran gida kullun sai dai ai mata ina amfanin a ganta a waje fes amma a gidan ta baya kalluwa. Ban san inda ta dauko wanan hakin nata ba nidai nasan na koyar daku abinda ya dace koda kun kama dakin ku zaku iya kulawa dayi amma sai dai kayya bata dauki wanan tarbiyan dana baku ba ita. Wanka nashiga don inji dadin kwaciya saboda yau na aikatu a gidan yar uwar tawa bayan na fito na tayar da sallah isha,i mama ta turu yaro wai idan na gama inje in debi abinci nace a koshe nake munci abinci gidan ya hauwa kafin mu dawo gida. Wani yaro ne ya shigo yana sallama da bazan iya sheda muryan yaron ba yana fadin wai ana sallama da khadija a waje. Da mamaki daga cikin dakin da nake, nake tambayan yaron ko waye yace shima zai wuce ne ya aiko shi don haka bai san ko waye ba. Jekace dashi tayi barci yaron ya fita can sai gashi ya dawo yana fadi cikin daga murya wai yace kiyi hakkuri kizo minti biyu . Na fito daga dakin ina fadin bana ce kace dashi nayi barci bane yaron yace na fada mashi yace indawo in fada maki haka. Zan sake magana mama tace da yaron ya tafi ganin nan zuwa tace kije giga kowaye kin san damay yazo gurin ki wulakamci bai da kyau ina fada maku. Hijjab na dauko na aza saman rigar dake jikina na fita tun daga nisa na gane motar mamud ta dazun da ya dauke mu dashi. Mamakin abinda ya kawo shi nake yi da wanda ya nuna mashi gidan namu yazo yana ganina ya fito daga motar zuwa guri na. Bayan mun gaisa ne yace kin yi mamakin hani na yanzu ko nace kwarai kuwa yace to kibar mamaki don abin jiya na dawo maki dashi. Da sauri nace meke nan sai da yayi murmyshi yace khadija ke nan So mana da kaunar ki khadija don tun dazun dana ganki na kasa natsuwa tundazu na kasa control din kaina akan ki abin ya dawo min sabo yanzu a raina. Mamud ke nan abinda ya wuce ai ya riga da ya tafi don ni kuma sai naji yanzu sam baka kwanta min ba a raina. Da sauri yace saboda may khadija nace halinka bai mun a yanzu don ba zan kara yarda ka sa min miki a zuciya ba. Kasan ina son ka da farko mamud sai da ka bari na gama yarda dakai ka gudu ka barni babu bayanin komai daga gare ka Allah ya taimake ni, ni ba mai sa abu ga zuciyana bane . Khadija ba haka na bane wallahi don koda muke tare dake already ina da mata karawa nake son yi sai kuma naje ma iyayyena da maganan ki amma sukaki banin goyon bayan haka don basu son in auri wace ba yaren mu ba. Kin ga kuma bazanki maganan iyayye na ba sai naji kunyan komawa gare ki in maki bayanin halin da nake ciki . Katse shi nayi da fadin basu sona yanzu may kadawo yi wuri na kuma yace ina da daman yanzu in zabi wace nake so tunda ina da yaren mu mutum biyu . Kai na girgiza tare da fadin mamud kasan tun farko ban kika ba kai da kanka ka guje ni yanzun kuma baka da bakin cewa ka dawo gare ni. Ko banza na farko ba zan shiga inda ba a sona ba sai na biyu yanzu ni mai zai kaini wurin mai mata biyu in ba daukan magana ba. Dariya yayi a lokacin tare da fadin khadija ke nan watau kin mayar da laifin a gare ni ni daya to naji na dauka kuma ki kwantar da hankalin ki ba a gida daya zan ajeki dasu ba. Don haka ai min hakkuri muci gaba kamar yadda muke da don son ki yana son ya min illa a rayuwana. Mamud gaskiya sai dai kayi hakkuri don ba zan iya ba yanzu gidan ka yafi karfi na da sauri yace what ? Nace yes I mean it don bazan dauki wanan risk din ba da hankali na ina ji ina gani. Shiru yadan yi na dan wani lokaci kafin ya dago kai yace is ok naji amma zaki yarda ina kawo maki ziyara lokaci lokaci don ban sani ba koda rabo na ciki. Dadai kayi hakkurin kamar yadda nace dakai zafi kyau don ban son ka dinga wahal da kan ka yace ke kika dauke shi a wahala. Ni abinda nake so ne na damu dashi don haka ban hakkura ba ki sani nace wanan kuma matsalar kace ni dai na fada ma gaskiya. Bai dade ba mukayi sallama ya tafi na shigo gida alwala nayi na gabatar da shafa,i da wuturi na samu wuri na kwanta. Amma ranan sai barci ya gagari idona saboda tunanen dayayi min yawa a lokacin a raina nace ohh ni khadija haka rayuwa zai kasance kuma sai masu mata ne ke zuwa ne mana ni ban san ko may yakawo haka ba gare ni. Gashi ni kuma banda sha,awan auren namiji mai mata don ban son yawan fitina daga anayi a gidajen masu mata nasan da laifi nane kin kula samari amma yanzu ban san dalilin rashin samun su ba, da haka har barci ya dauke ni ban sani ba. Matafiya umurah sun sauka lafiya don haka yan uwa da abokan arziki suke shigowa gaida shi gidan shi wanda ba wasu mutane ke zuwa ba don sanin hslin matar gidan da sukayi sai wa yan da ya zama ma dole sai sun zo ke zuwa gaida shi. Bata san cewa Fati ta koma dakin ta ba sai a bakin wani abokin shi da yazo yana mashi sherin yaushe zai leka can kaduna yaji ance fati na gidan shi yanzu. Wani kallon mamaki ta aikawa AA din sai da yasha jinin jikin shi don yasan akwai rikici babba yau a tsakanin su dakewa yayi kamar bai ganta ba yaci gaba da hira da abokin shi. Sai dai hankalin shi yana gurin ta duk abinda yake yi din bayan tafiyan mutumin tun a falo ta fara tambayan shi Fati ta dawo gidan ka ne baka fada min ba. Yace ta dawo suna nan gida yanzu haka shewa tayi tare da mikewa tsaye tana fadin haukan banza ke nan yadda ta dawo haka zata koma inda ta fito. Wanan kuma maganan ki ne don dama ai ba wanda ya kore ta ita da kanta taga daman fita yanzu kuma ta dawo tace ashe ko zamu zuba daku mugani a gidan nan. Ke ban fa son haukan naki na bazan Fati bakuwa ce a gare ki ko yanzu ne na fara zama da ita zaman ki na nan Abuja ita kuma yanzu bayan shekaru ta zabi zama kaduna ita da diyan ta. Don haka ban son jaye jayen wani matsala kima da zai kawo muna tashin hankali ba gaira ba dalili haka, Yana fadin haka ya mike ya haura sama ya barta a falon cike da mamaki halin irin na Nafisa da bata iya boye kishin ta . Satin shi biyu abuja yana hutawa ya kama hanyan zuwa kaduna gida don ya hana kowa yazo daga can yace yana nan tafe. Nafisa bata yarda cewa iyayyen shi zai tafi gani ba ta shirya wai tare zasu tafi ba yadda ya iya dole a tare da ita yayi tafiyan. Tunda suka shiga garin ta hana komai a tsakanin shi da Fati din bayan gaisuwa bata yarda komai ya kara hada suba don ko abinci da Fati ta gama sai cewa nafisa tayi abincin yayi mai nauyi ba zai ci ba. Suna zaune da dare ta na kokarin hana shi shiga wurin Fati da kissa da iyayi wayan hajiya mama ya shigo mashi nasiha tayi mai sosai wanda ya kashe mai jiki inda take mai tuni da cewa ya tuna hakkin ko wace yana a kanshi do haka ya daure yana ba kowa hakkin ta. Bayan sun gama waya ne da mahafiyar shi bai wani dauki lokaci taga ya mike da sauri take tambayan shi ina zai tafi kuma. Kai tsaye yace mata gun Fati zan tafi bata iya boye bacin ranta ba ko kadan tace bai isa ba don tare suka zo fati ta bari idan bai zo da ita ba sai ta kwana dashi. Yace a garin ku haka akeyi wanan dokan hakan wai Nafisa may kika dauke ni kamar wace ta haife ni zaki dinga bani umurni kai tsaye. Ba sake kula ta ba ya shige sashen Fatin kamar yadda yayi tsamani hakan ya samay ta sunyi barci da yaranta a saman gadon dakin ta tana saye da kayan data wuni dashi a jikin ta tunda suka zo, Ya dade tsaye a kansu bata san ya shigo dakin ba sai da ya dan bubuga mata kafa ta falka ina zan kwanta yace da ita kai tsaye dan watsake idon ta takeyi daga nauyin barcin da ya fara kama idon ta din. Sai can tace dakin ka fa yace Nafisa na cikin dakin kin sani mikewa tayi tana gyara ma yaran kwanciya tare da gyara dan wurin da ta bar mashi ya kwanta. Kallon ta yayi daga inda yake tsaye yana tambayan ta wai dakin su fa da kika dawo da kwanan su nan kamar ba zata bashi amsa ba sai can tace ban san anan zaka kwana ba ai tare muke kwana tunda ba kowa a gidan. Tsuki yayi yana hawowa gadon ya takure kan shi a guri daya kamar may kyankyamin dakin amma kin san hakan ba daidai bane nasha fada maki haka kwana da yara a daki daya. Banza tayi dashi ba wai banzan bane ya sani halin ta daine nakasa da kyaluwa haka take kindis da ita ko yaushe fuska ba fara, a. Tunda ya samu barci ya dauke shi bai falka ba sai karfe hudu da rabi na asuba da bugun kofar nafisa ke masu ya tayar dashi a firgice. Tambaya yayi yana zura riga a jikin shi tace itace ya bude kofan ya bude da mamakon ta a fuskan shi yana tambaya lafiya take cewa dashi. Banan ce bata da lafiya basuyi barci ba kallon yarinyar dake sabale a kafadan ta yayi tare da fadin ta miko mashi ita. Sai da tayi mai wani kallo tace ka karasa fitowa daga dakin mana murmushiin gefen fuska ya sauke kafin ya fito din muryam Fatine take tambayan make damun yarinyar ne ? Kada ki soma ki taba min ya ta yanzu ranki ya baci a gidan nan tana fadi tare da watsa mata harara da saida taja jikin ta ta koma daga bayan shi. Karban yarinyar yayi ya nufi falon kasa da ita suna biye a bayan shi dukan su ruwa ya fara ba yarinyar tasha sosai tare da ajiyan zuciya ta lafe a jikin shi. Dakin da bai koma ba ke nan ya zauna nan falo da yarinyar data koma barci a jikin shi tana sauke ajiyan zuciya . Juyawa fati tayi ta koma dakin ta don ta san kadan ne daga cikin sherin Nafisa ko ba yarinya a tsakanin su haka take masu idan zai kwana a dakin Fati din tace bata da lafiya karshe a dakin ta zai kwana. Do haka ta juya abinta taje ta kwanta bata kara ganin shi ba har rana breakfast din da ta hada mai baci ba wani aka kawo masu daga gidan Auta amiyar Nafisa din. Haka fati tayi ta hadiyan bakin ciki da wanan zuwan nasu ita da ganin miji sai dare idan zai kwanta zai lalabo ya dawo dakin ya kwanta da safe ya fice kuma ranan nafisa tace itace zatai girki . Dole Fati ta kyaleta tayi yadda ranta ke so tunda har mijin ma ya biye mata ita yanzu burin ta shine ta zauna a cikin yaranta kawai su girma a tare da ita. Nafisa bata shiga gaida sarakkanta ba balle suga yar jikan tasu data haifa da dan su sau daya ta shiga gaidasu ana gobe zata koma bata ba kowa yar ta ba suma basu taya zasu dauka ba. Sai kuma abin ya bata mata rai don yadda ta shirya bata samu yi ba sai taji haushin basar da ita da sukayi takoma fadin wai yanzu har kiyayyan da suke mata ya shafi yar ta jikan su. Haka ya sa AA yaji haushin abinda sukai mata a ranshi har ya kira mommy yana fada mata abinda sukaiwa Nafisa da yar shi baiji dadin hakan ba. Don ba halin ya kira mahaifiyar shi ya fada mata yasan kwanan wasa yanzu za a jisu da ita idan ta fara mai fada yasa shi kiran mommy. Mommy tace dashi babangida kasan halin matar ka fa ta make yarta a jikin ta bata ba kowa ba mune zamu karba tai muna wullakanci amma munyi kuskure gaba zamu gyara insha Allahu. Bayan kwana hudu suka nada suka koma abuja tun da suka kama hanya ta washe ranta da ya rasa gane mata da suke a kadunan. Yanzu ko kamar ba ita ba sai hira take jan shi a motar tana faman dariya tana kuma wasa da yar dake zaune a cinyar baban ta din. Tunda ya dawo ta samu kansa da kyau sai dai abinda bata sani ba yanzu asiri bai faye tasiri ya dauki lokaci a jikin shi don maganin tsarin da malam na zaria ya bashi. Kuma abokin shi Yusuf bai zauna ba akan shi yana tsaye da alamarin shi haka ma mahaifan shi suna tsaye da mashi addua sosai yanzu. Yau tunda na dawo daga islamiya nake kwance ba wai don banda lafiya ba sai dai ina jin jikina ba dadi ne ko aikin gida da nake taya mama ban iya tayata yi ba. Barci nayi sosai a ranan can zuwa rana yaro ya shigo yana fadin ana sallama dani a waje mama ta shigo ta tadani tana fadin min wai ina da bako a waje. Mikewa nayi da kyar don barcin dake idona na ban tsaya gyara fuskana ba na fita daga gidan haka na mamud ne zaune a motar shi da yaran shi biyu. Na iso inda suke ina gaida shi bayan motan na bude inda yaran suke zauna kafa na suna waje ina gaidasu tare da tambaya su yaya makaranta. Kafin yaran su bani amsa ya jefo min tambaya yaya naga fuskan ki haka kuma ko baki da lafiya ne ya tambaya ? Nace daga barci na tashi yanzu ba tare dana kalle shi ba hannu na mika wa yar karamar yarinya dake saye a cikin uniform din shekk lemo sai yarinyar ta noke taki zuwa. Tambayar ta nayi yaya sunan ta yace sadika dayan kuma nasir ina taba kafar yarinyar nace zakici biscut ta daga min kai nace to sai kinzo wurina sai ta kara makewa. Ina zuwa nace dashi cikina koma na hado masu kayan kwalama na yara wanda na dawo dashi muna ci da kanne na nafito rike da leda a hannuna namikawa yaran. Da sauri suka karba nan dai muka taba dan hira yace zai maida yaran gida daga islamiya ya dauko su mukai sallama ya tafi. Bayan sun isa ma sai da ya kirani muka taba hira ya kashe wayan tare da fadin zai zo amsa gudane wurina nace na hutar dakai kada ka wahal da kan ka. Yace to zamuyi waya nace sai najika aiki gida na taya mama ta koma folo tana kallo sai dana gama zuwa dare na shiga daki na samu wayan mamud har six miscall ya kira ban dauka ba. Kiran layin shi nayi aka dauka ban tsaya sauraren ba nace ina waje ne ina aiki banga kiran ka ba. Ban karasa magana na ba naji muryan mace tana fadin ke wacece da zaki kira lamban mijina kin san ko waye mamud kuwa ? To bari kiji daga yau kada ki sake shiga harkan mijina in ba haka ba zan sa ayi maganin ki a garin nan shiru nayi ina sauraren ta sai da ta gama nace. Ke kuma wacecd a guri mamud din bari ki ji ki sani ba don ki ke kadai akayi shi ba daga yau ki gyara kalamin ki inzaki magana akan shi ki dinga cewa mijin mu. Ina fadin haka ban tsaya jin haukanta ba na kashe wayan ina dariya nace banza mahaukaciya ni mijin ki bai a gaba na yanzu da kin ga tsiya wallahi. Bai kirani ba nima ban kirashi ba sai bayan kwana biyu sai gashi ya aiko kirana wai ace mamud ne mace ace ban samun fitowa aiki nake yi. Mamace ta samin baki dole na fita naci karo da dan aiken ya dawo wai yace don Allah inyi hakkuri minti biyu kawai zanyi. Tare muka koma da dan sakon na samay shi zaune a cikin motar shi yana duban wayan shi karasowa na ya fito yana washe baki. Fuska na a daure na gaida shi magana yake na kyale shi sai ko umm ko ummumm nake bashi amsa dashi kaina a kasa ina dakilan wayana. Muryan shi naji yana fadin yau gimbiya may ya faru ne naga an fito min haka a daure nace wani abu ka gani halan ? Yadan motsa kafan shi kadan yana murmushi tare da harde hannayen shi guri daya yace ko gimbiyar tawa mulki take jine haka ? Sai da nayi mashi wani irin kallo shekeke nace mulki ai mulki yana gidan ka don ko wayan ka sai an baka izinin dauka kake dauka ko zuwa gurina yanzu waya sani ko santan hanya kayi kada matan ka su gani. A cikin rashin kuzariya dago kai yana kallona yace wanan wani irin magana ne haka khadija kikeyi kai tsaye ba tare da tunane ba. Nace irin wamda matar ka tayi min jiya daga kiran wayan ka ta dauka tana zagina a wayan ta daukar min waya fa kikace nace ka duba nan ga kirana a wayana kana gani katuna ina kaje jiya a daidai wanan lokacin ? Look mamud na fada ma soyayya dakai a yanzu akwai matsala ka nace akan sai munyi gashi tin ba a je ko ina ba an fara kirana ana zagina daga gidan ka har da yimin iyaka dakai. Ya kai duban shi gare ni tare da sake dan murmushi yace mai shi tayi nasara gare ki ke nan tunda gashi har kin karaya zaki bar mata ni. Haka muka kasance dashi muna musayan maganan karshe dai yaban hakkuri nace ya wuce amma ya daina zuwa wurina. Yace ba da sanin shi ba amaryan shi ce ta dauka daya shiga wanka kuma da ya fito bata nuna mashi akwai wani matsala ba. Nace wanan kai ta shafa ni dai na gama magana kuma. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU SEENABUHutun mu yana karewa na fara shirin komawa makaranta bayan na kara sati daya a sama agida ina tare da iyayyena da yan uwa na. Duk da ba so daukan kaya nake yi ba hakan bai hana mama ta dan tanadar min irin abubuwan da uwayen mu mata suke tanadarwa yaro idan zai koma karanta. Inda mahaifina ya bani kudin da zanyi sayayya na raba kudi biyu na mayar mai da rabi nace ina da kayan abinci da ban ci ba a daki na. Bayan na shirya ina shirin zuwa Abdulsalam garage da kayana inda zan shiga motar zuwa abuja na fito a cikin shiri na yan uwana suna a bayana zasuyi min rakiya bakin titi. Gaban daddy da mama nazo na durkusa har kasa ina fadin daddy zan tafi ya dago kai ya kalle ni tare da fadin khadija kin fito ke nan. Yace do Allah khadija ki kula da kanki kamar yadda kika saba a baya ki maida hankali ga karatun ki kinga lokaci na tafiya yanzu. Kaina na kasa nace in sha Allahu daddy na gode mama tace banda kai kai inda Allah bai kaika ba kawar da kanki ga komai sai kiga komai yazo maki a cikin sauki nace na gode mama na mike tsaye jiki a sanyaye. Ban dade ba na samu mota naba kanne na kudi su raba daga cikin wanda daddy ya bani in rika din muka tafi tare da kanina dake bin min. Na isa Abuja da wuri inda na samu maryam ta rigani dawowa lokacin ranan mun jima tare muna hira ko barci bamuyi da wuri ba dan shaukin juna da mukeyi duk da muna waya kusan kullun da ita. Dayake muna da abinci ga kuma wanda maryanm ta karo don haka ban damu da nashiga gari in sayo komai ba don akwai shi a dakin. Mun samu sabbi fuska a gidan namu don an dauki sabbin dalibai yanzu wasu sun tafi kuma koda zan dawo ban bari mamud ya sani ba . Idan ya tambayeni yaushe zaki koma nakan ce dashi ba yanzu ba idan na tashi zan sanar da kai lokacin da ya samu labarin na koma school ranshi ya baci sosai dani. Kirana yayi ga waya yana fada wai ya fahinci gaba daya yanzu ban damu dashi ba don may zan koma school ban sanar dashi ba saida yazo gidan mu ya samu labarin na tafi. Nace dashi na fada maka tun farko kada ka wahal da kanka gare ni don ba auren ka zanyi ba na riga na rufe babin nan ko a raina. Satina biyu da dawowa sai ga mamud din ya kawo min ziyara gaskiya banji dadin zuwan shi ba don na gane yana son da karfi da yaji ya shiga raina again. Yadan jima a guri na muna hira dashi wanda hiran duk a kan zaman mu dashi ne anan maryam da wata Aisha da yanzu muke tare da ita suka samay mu. Da zasu tafi ya basu alheri sukayi mai godiya yace ma maryam ta taya shi kanfen a guri na dariya tayi tace ban maka wanan alkawarin ba don abaya ka gujemu ba wani dalilin komai. Haba maryam banyi zaton jin haka a gare ki ba yace tace gaskiya na fada don yanzu tace karatun tane a gaban ta doon kaga muna gab da gamawa ba wasa a gare mu. Kaya masu yawa yazo min dashi irin na bukatan yan makaranta na nuna mashi hakan da yake yi ba daidai bane yace yace bai son irin kalamin nan da nake mashi. Bayan tafiyan shi ne muka bude kayan da yazo min dasu muna kallo Aisha tace amma ni kan sai naga kun dace dashi very handsome dashi wallahi. Nace Aisha ba handsome bane abin damuwa abinda ke cikin gidan mamud din ne ai maryam tace da ita ai khadija haka take samun handsome guys don baki ga AA bane har kike ganin mamud a matsayin handsome a gare ta. Nafitar da zancen wani mamud da AA a raina karatuna kawai nake fuskanta a yanzu da ya dau zafi gare mu banda lokacin kowa a tare dani ban kuma shiga gari ko yaushe ina cikin makaranta ko hostel din mu. Zaune yake a office din shi yana aiki a wani file aka turo kofan office din nashi aka shigo baidago ya kalli wanda ya shigo din ba don yasan daga Yusuf ne sai ko masinjan office din nashi. Muryan da yaji yana mashi sallama ne yasa ya dago a lokacin wani hamshakin Alhaji ne ya shigo office din tare da wata mata a bayan shi. Yana ganin su ya kara daure fuskan shi tare da amsa masu sallaman su wuri suka samu suka zauna tare da fara gaida shi hakan yasa ya aje aikin da yake a lokacin yana fuskatar su. Bayan sun gama gaisawa ne mutumin ya fara magana da cewa yau ma gamu mun dawo gare ka bayan wahalan da mukasha kafin mu iso gare ka. Cikin daga hannu ya dakatar da mutumin ga maganan da ya fara yace Alhaji na fada ma wanan business din ba zai yuyu ba tun farko. Ba haka muke sake fili ga mutanen da basu san darahan shi ba suna gina abinda suka ga dama a cikin gari. Mutumin yace ba zancen gina wancen company a yanzu gare mu ni buri na kawai a yanzu shi ne in mallaki filin nan isan yana a matsayin nawa ne. Zan baka ko nawa kake bukata muddin zaka yarda ka saka min hannu in malaki daga milayan daya har zuwa hamsin zan baka idan kana so don wallahi ina , , , , , Table di gaban shi ya buga tare da mikewa tsaye yace na fada maka tun farko ba haka nake aikina ba kada kayi tsamanin da cin hanci ire iren ku na dogara. Ina da abinda zanyi a wuni daya million dari ya shigo min a accout dina ba tare da nasha wani wahala ba nafison in ci halan dina da na tsaya amsan cin hancin ire iren mutane irin ku. Matar ne ra katse shi da cewa ba wai cin hanci muka kawo maka ba kanina ka sani gogi bai ki kari ba balle mutum mai lalura da jama, a irin ki ko yaushe. Ina son ki sani wani gogin ne ke son kari wani ko an zuba mai wani ruwan aman shi yake yi don ba wurin zaman shi yazo ba. Don haka na roke ki ku fita min office yanzu ina da abubuwan yi a gabana da yawa da zanyi kada ku bata min lokaci. Matar zatai magana don ranta ya gama baci a lokacin mutumin ya daga mata hannu yace barshi mu tafi Allah ya bashi hakkuri bata mai rai da muka. Ya mike yana fadin mun barka lafiya sai dai ka sanin haka ba zai sani fushi dakai ba don abinda nake so nake nema a gare ka. Kuma ka sani ni ma ba irin mutanen ne da kake zargin suna sayen filin gwanati su gina abinda bai dace ba dashi nima kamar yadda zuciyar ka yake fari a kan kasan ka haka nawa zuciyar yake fes ga komai. Do haka mun barka lafiya matar tace bai kamata kana saurin yanke hukunci haka ba akan abinda bakai bincike akan shi ba. Binsu yayi da kallo har suka fice a office din nashi wani iri tsuki yaja tare da dafe kan shi da hannu shi daya yana fadin wai may mutane yanzu suke daukan kan su ne ? Yana jan tsuki tare da bude file din gaban shi yana gyara zaman shi da kyau Yusuf ne ya turo kofan ya shigo da sallama ciki. Tun daga nesa yake kallon yanayi abokin nashi yace may kuma akayi naga yanzu yanzu ka sauya gaba daya mana ? Bai yi magana ba sai duban files din yaci gaba dayi wuri Yusuf din ya samu ya zauna yana fuskanta abokin nashi tare da kara maimaita tambayan shi gare shi. Yace wanan mutumin mai bakin nacin tsiya akan sai ta mallaki filin da yake so mu bashi ne ya sake zuwa yanzu tare da wata mace dake son karanto min hauka. Wai har ni zasuce zasu iya ba daga million daya zuwa dari don dun mai dani mubukaci ban san ciwon kaina ba ko may ? No ba haka bane wasu ne ke bata wasu ga alumma shiyasa suke daukan haka ga kowa idan da sun san ko kai waye da ba zai tunkare ka da wanan zancen ba. Kai din ne ka faye boyon kurwa ga jamma, a kaki fitar da kan ka fili mutane sunan kokai waye may zai hana irin mutanen bazasu dinga tunkaran ka da suna baka ci hanci ba ko yaushe. Murmushi ya sake a fuskan shi yace dole ne sai na fito na nuna ma duniya ko ni waye san nan zasu sani kana ganin ko a gidana da matsalar Nafisa kawai bai isheni ba yanzu. Ni ba wanan ba ma gida nake son ka sama mun mai dakuna da yawa inda zan sai wa yan uwata su koma nagaji da zaman da suke min a gida na wallahi. Mutum da gidan shi baida halin ya huta yaji dadin gidan nashi sai a hana shi shaka wanan abin yana damun raina sosai wallahi. Ya zakayi abinne sai hakkuri tunda yan uwar matakar ce kaga ko don yar uwasu zasu zo gidan da son ka ko ba da son ka ba. Iska ya furzo daga bakin shi tare da ci gaba da aikin shi yayin da Yusuf yake dan tunane a zaune a gaban shi. Can ya dago kai yace ina ganin fa hutun su khadija ya kare don haka nake ganin tana garin nan duk yadda akayi yanzu ta dawo school din. Ummm nima abinda nake tunane ke nan do hutun su ya kare ai ita ba zata iya neman mutane a ida take ba tana jira a nemay ta ko ? A, a kaiko yaya zata nemay ka kafa san halin mata da jan ajin su ko yaushe aji kawai take ja muna ita ma a matsayin ta na mace. Ashe ko zata tsunke idan nine ya fadi ba tare da ya dago kanshi ba ya kalli Yusuf din dariya Yusuf yayi yace idan bata tsunke ba kai ai zaka tsuke din. Nayi mamaki da tunda muka dawo ka daina maganan khadijan amma acan kusan kullun kana min zancen ta har ina jin dadin ta shiga ranka yanzu ashe abin ba haka yake ba a gurin ka ban sani ba ? Au so kake banda aikin yi sai na ta yanzu kai ni fa tunda yanzu muna lafiya da Nafisa wani batun karama kaina wahala ya kawu min a zuciya. Ban gane may kake nufi ba yace Yusuf amma dai kaga aiki nakeyi ko yana mikewa yake fadin nagani barin baka wuri ka taba aikin ka. Har ya mike yake fadin ina son ka turawa Fati kudin da ta bukata na bukin da suke dashi don jiya take fada min bukin ya gabato. Kallon shi Yusuf yayi yace baka fada min nawa zan tura mata ba and kuma ina ganin ya dace ka tura ma da wanda zasuyi suturan fita bukin dashi. Katura mata biyar dakomai da komai don saboda laluran yara idan zai ishesu dariya Yusuf yayi yace indai fati ne ko bai isa ba baka jin korafin ta akai shiya nake ganin zubin su daya da khadija wallahi a wani gu. Baiyi magana ba sai murmushin da yayi a baiyane tare da fadin yar matsala wai ita a dole fushi take ba a kulata ba. Mata idan suka samu guri sai so wuce limit din su akai ni dake da mata biyu wata mace zata tsaya jawa rai a waje yanzu ? Fita Yusuf yayi yana mashi dariya tare da fadin ni dai nasan yanzu akwai nadi a lauje muje zuwa dai a hakan . Kwance nake a dakina ina so in huta don yau a gajiye nake ga test ga pratical da muka fita da rana maryam ce ta shigo dakin tana fadin malama tashi zakiyi fa mu fita. Don har kayan miya nake son mu sayo kin ce kuma kina son kayan make-up ke ma da sauran abubuwan bukatan ki. Wani kallo nayi mata nace cabdi jam a yanzu yadda nake din nan don Allah ki tafi ki dawo yau na gaji wallahi sosai maryam. Ke ma kin san dole zaki tashi mu tafi don yau kadai kike free kara kwantawa nayi na fita batun ta tana ta shirin ta har na fara barci sai naji takai min doka a baya. A zabure na mike tana fadin don Allah tashi muje khadija kada ki bata muna lokaci mana nace maryam ba zaki barni in huta ba don Allah wallahi na gaji ne yau. Matsa min tayi dole na mike na fara shiri ba don naso ba dogon riga na saka kaman kullun don sune kayana ko atamfa zan dinka nafi inyi dogon riga dashi yanzu nafi sakewa a cikin shi. Mun fito maikon mu tsaye kusa sai da ta jamu zuwa ciki gari a shagon da take ganin zamu samu kaya da sauki a gurin. Raina na bata ina fadin ni ban iya wahalan ki wallahi shiyasa nace kizo ke daya don ban iya wanan wahala saboda son banza zaki jawo mu zuwa nan. Dariya take min tace kin dai riga da kin fito yanzu sai yadda nayi dake kuma ai shagon babbane so sai kaya iri iri ne a cikin sa . Binta nake a baya kamar dole banko iya magana don gajiyan da nake ji din ta sai wanan ta dauki wancan. Wani set din kaya make-up na gani mai kyau na mika hannu zan dauka naga hannun wata mace ta mika itama zata dauka. Duk tare da ita muka dauka a lokaci guda na juyo ina kallon ta Nafisa ce a baya na ta ke daukan set din ita ma nace cikin wani irin murya sake don na rigaki dauka. Nawa gare ki da zaki biya wanan make up din halan ta na shirin bangajeni ta dauka na riga ta rike kit diin nace don Allah ban wuri malama. Baki isa ba mara kunyar banza nace marasa kunya din ke wacece da zan dauki abu kice wai na bar maki kamshin turaren shine naji a hancina yana fadin may ke faruwa ne Nafisa ke da waye kuma ? Yana tsaye bayan ta rungumay da yarsu a kafadan shi tana barci tace dashi cikin zafin rai wanan mara kunyar mana tana ganin ina da raayi abu kuma zata sa wani kazamin hannun ta ta dauka. Bar mata mana tunda ta riga ta daukan wanan ba sai a kawo maki wani ba tunda baza su rashi ba anan din . Haba malam yaya zan ce ina son abu sai kace wai in bar mata ita wacece da zan bar mata murmushi nayi nace au shagon dama na gidan ku ne ashe. Maryam ne ta iso take tambaya ganin shi kuma sai duk ta daburce tana gaida shi tare da gaida nafisa wace ke ta kunduma ashar a bakin ta. Nace da maryam muje ko ban tsaya kulataba na raba su na wuce maryam ta biyo ni baya duk a tsure take bamu tsaya magana ba muka mika kayan wurin biya suma a lokacin suka iso gurin biyan kudi yace hada kudin da nasu ka cire a katina lokacin nafisa ta iso ta samay shi tace dani. Karya kike yarinya zanyi magananin ki a garin nan dani kike wasa wallahi nace kafin kiyi magani na ni zan fara yin naki a garin nan na watsa masu harara har mijin nata naja hannun maryam muka tafi. Bayan mun fito muna saman titi da maryam muna jiran abin hawa sai ga su sun fito daga cikin shagon suma suka shiga wata hadadiyar motar su a gaban mu ta leko glass din motar tana fadin matsiyaciya ko mota ashe baku da. Tsawa mukaji ya daga mata tare da fadin wai manene haka nafisa ya ja motar da karfi suka bar gurin tsuki naja gami da harara na raka su dashi. Maryam tace yau naji takacin barin mota na a gida wallahi da dashi muke wanan matar bata isa tayi muna haka ba. Nace au ke kin damune da maganan ta ita uban wa ya bata motar gidan su badai da namijin nata take barazana ba. Matar nan lallai bata da hankali khadija jifa yadda take abu kamar wata yar bariki can nace guri ta samu tayi abinta amma ni bata isa ta fada mi in kyale ta ba. A can kuma cikin motar su fadi Nafisa keyi wai ni ina ma nasan wanan fuskan ne na mance ida nasan wanan yarinyar wallahi ? Bai mata magana ba sai tukin motan shi yake yi shi kadai yasan abinda yake ji a ranshi a lokacin wai a haka zai hada wa yan nan yan zafin rai guri guda. Tace wai ashe ba yarinyar nan bace kuwa sai kuma tacce ba ita bace don waccan bata waye haka ba koma waye taci bashi wallahi in dai nice zamu hadu wata rana ai zata raina kan ta. Tana takama don tana da kyau da diri wa zata nunawa kyau da fari anan kai dake dani a gida tana ganin kyauta zai rude kane take wani far da idanuwan ta haka. Murmushi ya danyi cikin kunan rai tare da fadin ki san abinda zaki fadawa mutane don baki san ko ita din waye ba a garin nan kizo ki jawo wa kanki matsala wata rana. Maryam ke ta zuba a mota nace please maryam ki rabani da maganar wanan matar mara mutunci wallahi sai na gwada mata ita karamar yar iska ne daga yau . Ni fa laifin ki nake gani da kika bata wanan daman take ganin ita wata tsiyace da kin jaye hankalin mijin ta ai da zata gane bata da wayo. Nace cikin mata wani iri kallo wani mijin kike magana badai wanan mijin da baida ta cewa ba a gaban matar shi kike nufin in sace zuciyar shi in kai ina idan na sace ga mai iko da zuciyar shi kina gani. Jifa yadda yau ya nuna bai sanmu ba a gaban ta kwata kwata wallahi saboda tsoron mace da yakeyi. Ta kada kai tana fadin wallahi ba tsoro bane mutunta matar shi ce kawai yayi kuma ko wani namiji ne ma haka zai yi ai a gaban kowa. Don dai kawai a zauna lafiya amma da gidan shi kike yai haka shine zakice wani abu kyale ta nayi don ina ganin don ba ita akaiwa hakan ba yasa take fadin hakan. Har muka isa hostel din ba wanda yayi magana da dan uwa wanka nashiga na fito da alwalana na tayar da sallah ina gamawa na kwanta tare da bata baya . Muryan ta naji tana fadin bazaki ci komai ba ke na kike nufi zaki kwanta yanzu banjin cin komai murmushi tayi tare da fadin . Ai ba haka ya kamata ki bullo mata ba da fushi da abinci don ita ko shi basu ma san kina yi ba ai yanzu wallahi khadija lokaci yayi da zaki falka daga barcin da kike yi. Kamar yaya na katse ta tare da juyowa ina fuskantan ta nace may kike son in yi mata tace wallahi ki cusa kanki ga A A shine mafita a gareki. Kaina girgiza nace haba maryam wanan zubar da ajin kike son inyi komay kuma ni nasha fada maki ban ra, ayin wanan A A din sam. Tace ko baki son shi ki girgiza buzuwan nan don Allah tasan shayi ma ruwa ne ba ita kadai bace mace a duniya har duniya ta kare akwai mata kyawawa a duniya. Nasan wallahi kyau ki da zatin ki kadai ya ishe ta ballw uwa uba karatu da kike dashi wanda nasan ko bokon primary ita batayi ba kila acan . Dama na farko da zaki fara nuna mata kai tsaye shine gorin motar da taimaki kona kwana gudane kice mashi mota kike so anan zamu gane idan yana son ki sai muci gaba da aiwatar da shirin mu akanta sannu a hankali. Kallon ta nayi wani iri nace mota fa kika ce maryam ina zankai mota tace baki zaiyi kai tsaye akace maki balle ki damu. Fada mai hakan kawai zakiyi don mu gani kina da tasiri a gurin shi ko baki dashi ajiyan zuciya na sauke tare da fadin zan gwada in gani to. Har na kwanta kuma na juyo nace mata maryam idan ya bani motar fa ai na kashe kaina a gurin iyayyena wallahi. Kyautan mota wasa ne khadija ai ba baki zaiyi ba kai tsaye anan kin ga zamu san abin yi kuma nace to shike nan tunda haka kika ce tare da juya mata baya. ZAINAB IDRIS MAKAWAWanan magana ya tsaya min a rai sai dai gaskiya ban aminta da maganar maryam ba don ba zan iya bude baki na in roki namiji koda kwandala ba balle har mota. Ina zan kai mota idan ya bani a gida ince dasu ina nasamo mota kana wa yaban motan akan wani dalili zai min kyautar mota haka inma har zai bani din. Gaskiya maganar ta bai karbu ba a wuri na sam zandai gwada mata nima ba kyale bace zan mata abinda sai tarena kanta da kanta anan na aje maganan azuciyata. Sai dai ban fada ma maryam abinda na yanke a zuciyana ba nabar abin a raina don ita maryam ba abinda ya damay ta wanan nake ganin a gurin su ba komai bane hakan sai abin alfahari. Washe gari na mike kamar komai ba faru dani ba ajiya ganin yadda na sake yasa maryam dauka ko na dauki shawaranta ne. Ban damu da fita ba don yanzu karatuna shine a gabana ranan mun dawo maryam ke tambaya na wai har yanzu taji shiru mana ko ban buga ma AA waya bane akan batun motar. Banza nayi da ita kamar badani take magana ba sai da ta sake tambayana nace mata don Allah maryam ki bar wanan zancen . Don bashine a gabana ba yanzu abinda nazo yi nake fuskanta ban son abinda zai raba min hankali ko kadan. Amma dai khadija kin kwabsa wallahi don kawai kin tambayi AA abu shine kike ganin rage ajine a gurin ki wanan ai ba komai bane wallahi. Yan mata nawa samari ke sayawa mota kuma a zauna lafiya so maye bai sakawa a yi wanan ai kara ma kanki daraja ne ba wani abuba. Wani kallo nayi mata nace rokon shine karin daraja ga mace rokon ma irin na rashin hankali haka wai ma idan har ya bani motar ina kike son in kai mota yanzu. May yasa kike magana kamar wata bagidajiya ne khadija samu yafi iyawa aida samu din ai yadda zakiyi dashi ba abu bane mai wahala. To bazan roka din ba period sai kuma may a take ta bata ranta a wuri banza nayi da ita na mike ina dauko kayana da zan goge itama batayi min magana ba. Yana zaune a falon shi kiran Fati ya shigo mai a waya bayan sun gaisa dashi dan shiru ne ya biyo baya sai can ta kau da nata miskilancin tace naga dubu dari biyar ga account dina dazun. Shima cikin magana kamar yana gune dayin maganan ya bata amsa da cewa eh kudin da kika bukatane nace a tura maki har wanda zaki wanin abin. Angode tace mashi zata kashe wayan yace ke baki taba kiran mutum sai idan wani lalurar kudi ko wani abin ya taso maki zaki kira. Bazaki kira kiji halin da mutum yake ciki ba anan tace yanzun kiran nawa inyi godiya ya zama laifi ne kuma ? Tsuki yaja tare da kashe wayan ya lumshe idon shi yana jin takaicin wanan baki halin na fati a kulun ita bata taba wayewa tana nan a yadda ya san ta a baya. Karan takalma daji ne yasa shi bude idanuwan shi ya sauke a gare ta ba laifi idan zata fita tana kwalliya na kure a daka. Sai dai a gidane baka taba samun ta a cikin shiri yadda ya kamata gashi shi mutum ne mai son yaga mace ko yaushe a cikin kwalliya hakan nayi mashi dadi sosai. Karasowa tayi gare shi tana fadin zan fita don kasan yau saura yan kwanaki kadan bukin namu zan leka inga may ake shiryawa a gidan kareemay din. Yanzu wa kike fadawa da zaki fita kin nemi izzinina kan zaki fita din kallon shi tayi tana dariya tace wata sabuwa ke nan ? Yanzu fitan ma da zanyi nan cikin gari sai na nemi izinin ka ko may bafa gari zan bari ba wanan wani magana kake nema kuma ? No ba sai kin nemi izzini ba tunda haka kika daukar wa kanki amma ki sani komai daren dadewa watarana wace zata nemi izzini na a gidan nan tana tafe. Da sauri ta gimtse fuskan tace bako a gidan nan ba idan ma mafalki kake ka falka ba wata shegiyar mace da zata sake shiga rayuwan ka kuma muddin ina raye kai koma ban raye na fada maka haka. Kina zancen ki dai yanzu don kin ga ban tashi ba cikin daure fuska tace don Allah mu bar wanan zancen zan fita lafiya kana son bata min rai na. Ta juya ta fita ba tare da tayi mai sallama ba don ranta ya gama baci sosai dashi a lokacin nan ta fita ta barshi zaune a falon . Zaman falon yaji ya ishe shi daga inda yake zaune yake jin kukan yar shi na zuwa mashi haka yasa ya mike yabi inda kukan nata yake zuwa. A dakin Yanyala ne kukan ke fitowa ya tsaya daga kofa yana kwakwasawa ba a karba ba yasa kai dakin ya samu yarinyar ta tashi daga barci tana zaune tana kuka ita kadai a dakin. Dauko ta yayi zuwa sama yayi mata wanka ya bata abinci har ya shirya ta ya fito gidan ba wanda ya nemay ta cikin gari ya fita da ita yawo. Gidan Yusuf ya nufa ya samu zai fito sai suka fita tare da yusuf din Yusuf ne ya kalle shi yace ina mukayi yanzu ga yarinya ka dauko kuma ? Yace dashi kaini gun khadija please batare da ya kalle shi ba murmushi Yusuf din yayi yace yau ranka a bace yake halan ? May kagani kace haka yace naji kace in kai gun khadija abinda na dade banji ba a gare ka shiyasa nasan an bata maka rai ke nan. Ya furzo iska daga bakin shi tare da kara rungumay yarinyar a jikin shi yace ban san irin rayuwan Nafisa ba Yusuf yau da yake ranan hutu ga kowa daya kamata in zauna gida in huta da iyalina. Sai gashi ta kirkiro fita wanin unguwar da baida dalilin komai wai kawar kawarta ne zata buki shine suka fita gin shirye shiryen bukin. Aka bar wanan yarinyar tana kuka ita kadai a dakin da sauri Yusuf yace subbahanallahi ina masu kula da yarinyar suka tafi kuma ? Yaja tsaki yace itama ta iya fita tabarta don may zasu tsaya kula mata da ya suma sun tafi nasu mana. Kai Allah ya sauwaka da halin bariki wallahi ba don nasan ka tun farko ba Abdulsamad da sai ince auren bariki kukayi da nafisa. Yanzun dai ni kaga ina jin kunyan Khadija wallahi na dade ban kirata ba kuma ban nemay ta ba tasan kuma muna garin . Ranan yakai three weeks mun hadu da ita da Nafisa a shago nakaita taiwa Bannan sayayya sai gasu ita da maryam har dan rikincin kayan shafa yaso hada su a gurin. Kasan halin nafisa da rashin hakkuri nan dai suka rikece ya bashi labarin komai da ya faru a wurin a tsakanin mu. Dariya Yusuf yayi sosai yace dakyau khadija baki daukan ta kwana ko kadan AA yace shine matsala ta da ita wallahi. A bakin hostels din mu suka tsaya aikawa sukayi a kirani bayan an tabbatar masu da ina ciki wata Annah ce tazo ta fada min ina da baki a waje. Ban tsaya wani gyara ba nasa kai na fita ganin kowaye yake nemana din tun daga nesa na hangoshi yana ma yarinyar wasa a mota. Har na iso inda suke fuska daure bai dago kai ba hannkalin shi naga yarinyar muryana yaji ina gaida Yusuf. Ya dago ya dan kalle ni bance dashi komai ba lafiya dai na gan ku a wanan lokacin na tambayi Yusuf din cikin daure fuskana. Haba kaunata kin daure fuska haka kamar ba gobe ai kya gaida dayan yayan naki ko tunda kin gan mu tare dashi nace ai ba wuri na yazo ba. Ka taba ganin mai arziki mijin hamshakiya yazo wurin diyar matsiyata wace bata kai matsayin a tsaya da ita ba ? Haba khadija ina wanan maganan ya fito haka kuma nace gashi nan ai ka tambaye shi idan nakai matsayin yazo inda nake sai ya fada ma . Murmushi AA din yayi yace da zaki shigo daga ciki zaifi don wanan zafin ranan zai iya maki illa anan har lokacin bai daina wasa da yarinyar ba. Ido na waro waje nace mota ai sai ku da matan ku yar matsiyata da bata gaji shiga mota ba ina zan taba motar ku in sha maku talauci a ciki. Motan ku na gama shigar ta tun ranan na dogara ga yadda Allah yayi mu ni da mahaifa bamu kai kan mu inda Allah bai kai mu ba. Ido ya runtse yana jin maganan da nake fadi har cikin ranshi Yusuf yace dakata kauna na nasan abinda yasa kike wanan maganan yanzu ma shi yace muzo mu duba ki don tun ranan bai samu lokacin zuwa nan ba. Ga kuma yar ki nan ya kawo maki ita ki ganta mun san Nafisa bata kyauta a yadda kukayi din nan ina ganin shine dalilin ramshin zuwan shi gurin ki don yasan dama a jirace kike dashi gashi kuma ashe har yanzu baki huce ba ke ? Akan may zanyi fushi da abinda ta fada ai gaskiya ta fada ba karya ba ni yar tallakace bamu da ko keke a gidan mu ita kuma da ya mayar yar masu arziki ba rawa taiwa Allah ba ya bata shi. Sai dai ta sani daren baiyi ko balle gari ya waye tajira taga zuwan daren tukun kafin ta wullakanta mutum. Yarinyar ne tasa rikici don haka hankalin mu ya koma gare ta yana dan jijiganta ta kallon inda nake tsaye a side din Yusuf tana mika hannun ta. Yusuf yace kin ga Banan tana ba mamanta hakkuri on behave of her father murmushi nayi ina kallon yarinyar nace fine girl wanan bai shafe ki ba ko ? Daga inda nake na mika hannu sai yarinyar ta zillo zuwa gurina banyi gigin karban ta a wurin shi ba sai cewa nayi ku kaita gida mana. Taga kuna kama da uwar ta ne take dauka ko ita ne nace Allah dai ya tsare min kama da wanan matar yarinyar bata bar kukan ba haka yasa naji har cikin raina na mika hannu ya miko min ita in dauke ta. Da sauri ko tazo wurina karban yarinyar nayi ina dan jijiga ta a hankali tare da shafa mata bayan ta sai tai shiru tana ajiyan zuciya a jikina. Ikon Allah banan kin san ta ne Yusuf ke fadan haka yana dariya AA yace daga inda yake zaune dauka ta ko maman ta ne don ta ganta fara. Farin mu ba daya da ita na na fadi a tsiwace shi dai murmushi yayi kawai bai yi dogon magana ba sai Yusuf ne yace dani wai yanzu na fahinci gori motar nan ya bata maki rai sosai fa. Wallahi ko daya raina bai baci ba don nasan rashin ilimi ne yasa ta fadi haka ba wai tasan ni ko wacece bane don ita halinta ne wanan. Khadija kina son mota da sauri na dago kai ina kallon shi kamar bashi yayi maganan ba sai kuma na mayar da hankali na gurin yarinyar dake kokarin yayemin gyale dana yafa a kaina. Yusuf yace ana tambayan ki wai kina son mota ne kai na girgiza nace ina yar tallaka dani ina zanje da mota ita mota ya dama a yanzu har take fankama da hakan. Kiran sallah azahar aka fara yi Yusuf yace tau ashe har lokaci ya jane haka ban an kara ba zamu tafi da fatan kanwana ta huce ko ? Murmushi nayi don ban son jan zance ina son fara aiwatar da shiri na akan buzuwa yanzu ina kokarin mika yarinyar gare su tare da fadin . Sai ko yarinyar ta make a jikina taki zuwa karshe da na matsa da mikata sai tasa muna kuka tana lafewa a jikina. Yusuf ya juya ya kalle shi tare da fadin yaya ke nan za ayi yace mutafi kawai anjima zan dawo in dauke ta in mai da ita gida. Bazatai kuka na na tambaya da sauri yace ba gashi kin gani da idon ki ba taki zuwa wurin mu ku shiga da ita don ba gida zan tafi ba dama. Haka suka ja motar su suka tafi yarinyar kuma bata damu da tafiyan su ba din muka shiga ciki da ita maryam bata nan sai da ta dawo ta samu ina bata indomie dana dafa mata tana ci. Tambaya na tayi ina na samo yarinya haka diyar AA ne na bata amsa kai tsaye ido waje take kallona da mamaki a ina kika samota kuma ? Shiya kawo ta na bata amsa in bata wanan in bata wancan har barci ya dauki yarinyar . Ina da wasu set din ribon a jiye kana na a hankali na kama kan ta ina mata kitso tana barci . Har na gama bata tashi ba na daura mata ribon din a kowani tukuwa yarinyar ba tashi don yadda nake kama mata kan a hankali. Wayan shi ne Nafisa ta kira a gigice wai basu ga Banan ba a gida yace kamar ya ba a ganta ba may kike nufi. Nan ta rikece mashi tana koro mashi bayanin yadda yanyala ta kirata daga gidan buki tana fada mata basu ga yar su ba wai. Yace maganan banza ke nan duk inda suka kai min yarinya na su fito min da ita kafin in dawo gida ko rayuka ku su baci ya kashe wayan cikin hasala. Ranan dai nafisa ta kirashi a waya yafi a kirga bai dauka ba kuma bai koma gidan ba kamar yadda suke jiran shi ya dawo duk ta fita hayacin ta yar ta ta bata a gidan. Yanzu baiji kunyan idon ki ba khadija ya dauko yar shi ya kawo maki yar matar da tayi maki zagin wulakanci a saman hanya. Wallahi da nice ba zan ko kalli inda yarinyar nan take ba balle ya bar min ita da sunan lalashi duk wanan abin fa sallon ba da hakkuri ne irin na maza. Shi a dole matar shi ta saba maki ya wani dauko yarta ya kawo maki nan don ya nuna maki ya isa da gidan shi ko may ? Dariya nayi nace ke ma kin san in dai wanan mutumin ne ba zai taba bani hakkuri ba bakina da nashi ba kuma kawo min yarinyar yayi ba nan . Sun zo da itane tagani ta lakemin taki yarda su tafi da ita shine yabar ta har anjima zai zo wai ya dauke ta yace . Tace bakin ji ba may ye na kawo maki ya kina makaranta kina fama da karatun ki ni dai nasan akwai wani abu a bayan wanan abin. Tashin da yarinyar tayi ne tana kuka hankali na ya tashi na rarashe ta tea na hada mata tare da bata cup cake sai tayi shiru taci gaba da wasan ta. Sai bayan magariba ya dawo daukan yarinyar ya bugo layina yana fadin gashi ya dawo in fito da yarinyar ya mayar da ita gida. Tun daga nesa ya kura muna ido yana kallon mu cikin mamaki yadda yarinyar batai min kiuya ba har muka iso gurin tana ganin shi ta washe baki tana dariya. Sai dai yana tara hannu tazo ta make tare da lafewa saman kafaduna ban san lokacin da murmushi ya subce min ba yace Banan yau fushi kike damu ne a gidan haka ? Nace kasan yaro kamar kyanwa yake yana son a kyautata mashi ko da yaushe indai zai samu jiki gurin mutum . Wanan ne kuma bata samu a gurin mu daga ni har uwar ba mazauna gida bane dukkan mu nace kuna daukan alhakin ta gashi babu ruwan ta wallahi. Dan shafan ta da nakeyi daga tsaye yasa ta koma barci nace kaga tayi barci yanzu lalaba ka maida ita wurin uwar ta tun kan ta tashi tasa rikici. Banji yace komai ba haka yasa na dago ido ina kallon shi sai naga yana wani lumshe ido yana kallon mu. Da sauri na kawar da kai daga kallon shi kamar bangan shi ba muryan shi naji yana fadin . Kun dace da Banan kamar kece uwar ta kenan goyo zai maki kyau sosai fa nace don Allah kakai yarinyar nan gida tun bata tashi tasa rikici ba. Yace af koran mu kike yi don na fadi gaskiya gaskiya kuma da kama da ita kamar kece mahaifiyar ta fa. Nace kaidai ka sani da jan magana a bayan idon uwar ta zaka iya fadin komai yanzu . Tsoron idon uwarta nake ashe nace ai naga zahiri ne ranan don Allah ka karbe don hannuna ya fara tsami da daukan ta. Miko jikin shi yayi don ya dauki yarinyar numfashin mu ne ya hade a guri daya nayi saurin ja da baya jikina yana rawa rigumay ta yayi a jikin shi yana fadin Thanks for today Banan da baban ta sun gode. Yana kallon kan yarinyar da ya sha kitso fuskanta ya fito shar da goshin ta saboda kitson da akai mata din yace wayayi mata wanan kitso haka nace gun wa ka kawo ta. Matsala na dake kenan tambaya a cikin tambaya halin ku na yan Africa leda na miko mai ciki da kayan ciye ciye nace a rika mata wanan idan ta tashi yai min godiya muka rabu yana cikin farin ciki da ya kasa boye wa. Sai da ya wuce a zuciyana nace ko yaya akayi yazo da wanan yarinyar nan yanzu kuma may zai koma ya fada mata kai halin maza sai su wallahi maganan maryam ne ya dawo min a raina. Ya na isa gida suna waje bakin get cirko cirko dasu sai da ya gama seta kan sa ya fito da yarinyar a kafadan shi. Gaba daya suka nufo inda yake nafisa ta mika hannu zata karbi yarinyar ya gwauce ya wuce ta ba tare da yayi mata magana ba. Sai da ya kwantar da yarinyar dake barci a saman gado ya juyo zai wuce ta tace ashe kaine kafita da yarinyar nan baka fada muna ba. Ke ki fita min a ido banson maganan banza har kina da bakin tambaya na haka da kikasa kafa kikabar ta agidan tana kuka iidan wani abu ya samay ta fa. Wallahi kasan su Yanyala na barwa ita amma sai suka bugo min waya suna fada min wai basu ganta ba. Yace bari kiji akan yarinyar nan zan iya bata muku rai baki daya a gidan nan duk sanda kuka bari haka ya kara faruwa. Kitson dake kan yarinyar dake barci saman gado take kallo muryan ta ne take tambayan shi a wurin mace kakai ta ke nan wani kallo yayi mata sai lokacin ya tuna da zata iya tambayan shi haka. Kallon yarinyar yayi da take a kwance shar kamar zaiyi magana sai kuma yaja kafar shi ya wuce zuwa dakin shi. Zuciyar shi a cunkushe yana jin bacin rai wanka yayi ya fito ya shirya gado ya koma ya kwanta da niyar taba aiki a laptop din shi . Amma sai yasamu kan shi da jin kasala nan ya fara tunane abinda na fada masu yau tunane ya zurfafa dayi sosai har zuwa daukan yarinyar daje yi da yamman nan. Ido ya lumshe yana tuna irin yanayin dayaji lokacin da muke hada jiki wurin amsan yarinyar yace a fili khadija khadija yana girgiza kai a hankali. Bude idon shine yaga Nafisa tsaye tana mashi kallon tuhuma dakyat ta iya daga kafa zuwa wurin da yake kwance tace yaya naga yanayin ka gaba daya ya sauya ne ? Samad ina kakai min yarinya yau wuni guda ace batai kuka ba nifa wanan abin ya daure min kai. Gun wa kakai ta baka fada min ba yace muna gidan Yusuf da ita muna aiki shiyasa kika ga ban damu da kiran da kike min ba din tunda nasan yarinyar na wuri na. Wani irin ajiyan zuciya ta sauke tare da zama a bakin gadon tana fadin sai yanzu hankalina ya kwanta wallahi. Gobe da safe zan bar gidan nan zamu je gyara ma amarya gida juyowa yayi yana kallon ta tare da tambayan ta wai a wakike cikin wanan bukin ne don naga kin mayar dashi kamar bukin gidan ku . Ga buki can za a yi a kaduna amma banji kina shirin zuwa ba sai wanan bukin da baki da wani dalili dashi kike maganan shi haka. Tace bukin wa za ayi a kaduna din idan ma na sani bazan tafi ba wanan kai ya shafa don ni bai shafe ni ba yace haka kika ce tace kwarai kuwa. Gyara kwanciyan shi yayi ya bata baya tace don kawai za ai bukin kannen Fati zan kwashi kafana in je don ban san ciwon kaina ba ko may ? Mutanen da basu sona basu kauna na basuki su bude ido suji ance na mutu ba a yau din nan kake son in kusance su. Ban son Fati ban kaunan ta da duk wani nata don su, , , enough Nafisa ya ishe ki ya isa haka baki zuwa ya isa wanan kalamin ba da Fati kikeyi ba dani kike yi don nima zurian gidan ne ko kin manta ne da hakan ? A kusan tsatso daya muka fito da Fatin da kike aibantawa haka da yan uwan ta may Fati ta tare maki a duniyan nan da baki kaunar ta haka saboda wani bakin kishi naki can mara dalili. Matan nan tun shigowan ki gidan nan kika dauki tsanar duniya kika dagwara mata katse shi tayi da fadin muka dai dagwara mata don bani kadai takewa abinda takeyi ba. Yace matsalan ki daban nawa daban ko may Fati tayi min nimijin tane kuma uban diyan ta zan zauna da ita a ko wani irin hali. Samad ni kake fada ma kai mijin Fati ne kuma uban diyan ta kake ni kake fadawa haka a gaba yace an fada maki kiyi abinda zakiyi. Wani shuumi murmushi ta sauke tace dama maza haka kuke don kana takama da wanan dandanin da taima shine har kake ganin ta a mace take yanzu. Kutawa tayi tafita daga dakin rai a bace ita samad zai kawo wa wani maganan wata matar shi can wai fati wai may yasa shirin ta akoda yaushe yake lalacewa ne idan tayi. Tasan dai tanayi amma kuma maimakon yayi aiki yadda take so sai komai yazo ya lalace daga baya taki jinin fati da diyan ta a duniyan nan amma mace kamar kaska duk wanan abinda takeyi sai fatin ta dawo a rayuwan samad din. Tana ganin taje gida tayi aiki akan kowa nashi amma kuma yanzu ta lura asiri bai cika kama samad din ba idan tayi ko tayi bai wani dadewa yana tasiri a jikin shi sai abin ya kare. Kudi dai bata da matsalan shi ko nawane ta bukata tana samu a gurin samad din yanzu abinda tafi zargi shine mahaifiyar shi take lalata mata aikin ta don haka wanan karon da hajiya mama zata kara don na samad din mai sauki ne. Don ko yanzu a tafin hannun ta yake don dai sai abinda tace dashi a gidan bai musa mata inba wani lokaci da yakan dan turza mata ba wai shi a dole ga namiji. Tasha alwashin wanan karon sai taga bayan duk wani mai mata aiki ta bayan fage akan samad din zata raba shi da kowa nasa taga yarda uwan nashi zatayi. Da haka barci ya dauke ta tana rungumay da yar diyar ta mumunan mafalkin da tayine ya falkan da ita sai gumi take hadawa a dakin duk da sanyin ac dake dakin alokacin. Wacece wanan macen da tayi mafalki da ita samad din ta ya rike ma hannu yara na binsu a baya kodai don ta kwanta da zancen Fati ne a ranta tayi wana mafalkin haka. Mace tare da samad din ta kaita kada tana fadin wanan ba gaskiya bane koma may ne gobe zata je wurin malamin ta a duba mata agani. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU SEENABUGanin zamu dan huta har kwanaki yasa na yanke shawaran zuwa kaduna wurin Ya Amina in masu hutun dan break din da muka samu a can. Bayan mun fito daga lectures ne na shigo na fara shirin tafiya kaduna maryam ma da tasa rai a gidan su zamu yi dan break din sai ganin ina shiri takeyi ta tambaye ni nake cewa kaduna zan tafi in duba ya Amina kin san hutun nan ban samu zuwa can ba. Ranta ya baci amma na bata hakkuri akan wani lokaci ai zan tafi nayi Sa,a ina zuwa na samu mota ta cika saura mutum biyu. Bamu dade ba motar ta bar tashan motar na da gudu sosai sai dai muna wuce maraba mun dan ba kauyen dage gaba baya kadan motar tamu ta tsaya. Drivern yayi tsaki yana fitowa daga motar ya fita ya bude gaban motan ya dan taba ya dawo ya tayar taki tashi bude motar yayi yace mu fita daga waje mu sha iska zai duba motar. Abu wasa wasa muna wurin har hudu na yamma motar bata gyaru ba raina duk ya baci nayi tunane kala kala a wurin tsaye. Wasu motoci ne guda uku tafe a jere da gudu suka wulga a gaban mu, ina jin mutanen dake cikin motar suna fadin kai jama,a akwai dai motoci a duniyan nan hadadu wallahi duba motocin nan kamar su suka kera kan su don Allah. Kuran motan da suke magana akai nabi da kallo sai naga motan suna dawowa baya a hankali zuwa inda muke kawar da ido na nayi daga kallon su na mayar da hankali na ga waya. Muna charting da maryam ina fada mata abinda ya faru damu a hanyar jin muryan masu hiran nayi suna fadin wai Allah yaba wasu duniya duba mutanen cikin motar nan don Allah. Daidai nan na dago ido na in ga abinda suke magana akai Yusuf ne yake kokarin fitowa daga motar tare da AA a daidai inda sukai parking yana kallon mu. Yi nayi kamar ban gansu ba na dukar da kaina a kasa ina ba maryam amsa ya karaso yana gaida mutane tare da sallama suka amsa mai a mutunce suma don yadda yazo masu din. Bayan ya gaisa dasu ne yake tambayan driver motar ce ta samu matsala yace wallahi Alhaji lafiya kalau kuma na fito da ita halin karfe ne kawai. Wurina ya mayar da hankalinshi yana fadin khadija ina zaki haka a wanan lokacin bamu sani ba kuma ? Ko kaina ban daga na kalle shi ba nace KD a takaice wata mata da muke mota daya ta dan manyanta matar dama akwai zuba don bakin ta bai huta ba tunda muka tsaya din. Sai cewa tayi malam hala matar ka ce matar oga nane gashi can a cikin mota zaune tace haba. Tun shigowan mu nasan yarinyar nan diyar manya ne ko kuma matar wani babba dama ina mamakin abinda ya shigo da ita motar hanya yanayin ta kawai ya nuna min haka. Dago kai nayi ina kallon matar da mamaki karara a fuskana zan yi magana tace in kina ma Allah kiyi hakkuri kibi mijin ki yarinyar nan kila shiya sa motar tamu tsayawa haka nata tashi ba kin ko san girman tashi (yaji)ga diya mace wurin Allah. Aiko jin haka sauran mutanen suka sa muna baki a lokaci daya ga abin dariya abin kuma haushi har da drivern suna ta bani hakkuri. Drivern da kan shi ya dauko jakkata wanda dan karamin traveling bag ne na saka kaya na a ciki dama, driver ya dauka yakai wurin motar tasu. Hannu Yusuf yasa a aljihun shi yaciro kudi yaba duk mutanen dake wurin dubu bibiyu wai su shiga wani mota su tafi. Godiya sosai sukai mashi suna kara min nasiha akan hakkurin aure anan kan dariya saida ya subce min a fuska na. Bude min baya yayi wai in shi ga naja na tsaya a wuri daya bakin motar tare da fadin kada ka manta na fada ma bazan sake shiga motar ku ba again. Haba khadija ai ko don idon mutane nan da nayi wa karya ki daure ki shiga ji yadda matan nan ke hada ki da Allah tana fada maki yaji fa baida kyau ga mace . Wa nayiwa yaji din ai gara su san gaskiya tinda ban san inda zan kara haduwa dasu ba yanzu idan mun rabu don haka please sauke min kaya na in tare wani motar in tafi. Don gidan mu a motar haya muka saba tafiya tunda bamu da motar yace please kanwa na kada mu tsaya jayayya anan kiyi hakkuri don girman Allah mu tafi yamma keyi yanzu hanyan kuma babu kyau kin sani. Girman Allah da ya ambata ne yasa na shiga motar ba tare da nayi wani magana ba kuma sanyi da kamshin motar ne suka daki fuska na a lokaci daya. Kira, a ke tashi a cikin motar a hankali muna shiga sauran motocin suma suka tashi muka kama hanyar kaduna ga yamma yayi. Sai da muka danyi nisa da tafiya yace kin daiji abinda manyan mata suka fada maki fushi baida kyau khadija don ko wanan tafiyan ya ishe ki ki gane mu da alheri muke bin ki khadija. Sai yanzu AA yayi magana da cewa ke kina haukane ko rashin sanin ciwon kai ne yakai ki bin motar haya cikin wa yan nan mutane haka masu yawa. Idan wani abu yaje ya samay ki a cikin jejin nan fa kina son ki salwantar da rayuwan ki ne a banza ko may ? Tunda ya fara magana ban dago kai na kalle shi ba kaina yana a wayata sai da naji ya fadi hakane na dago kaina nace a tsiwace . In salwantar da kaina kamar yaya don kawai nabi motar haya zan salwantar da rayuwana yace a zurke yana kallona. May yakai ki shiga motar haya a wanan hanyar ? Nace ai kasan ubana tallakane ko banda motar da zan shiga inwa mutane tsiwa asan ina dashi, don banda motar ya wuce ta haya a yanzu don kowa yasan ubana ban kwadayin karaya ko abin wani a rayuwa. Wani kallo ya watso min daga inda yake zaune ya kada kai ya koma ya zauna yana maida numfashi. Yusuf ne yace kaunata kin san kowa ke din mai tsada ce a yanzu don Allah kibar wanan gangancin da rayuwan ki murmushi nayi nace ganganci kai nama rasa may zance dasu alokacin. Gudu suke shararawa da mu sai can ya juyo kamar mai maganar lalama yana fuskantana yace kina jina daga yau duk inda zaki ki buga ma Yusuf waya a turo maki mota bana son shiga irin wa yan nan motocin please I hope you understand me ? Malam bafa don na shiga motar ku bane yanzu zaisa ka dinga bani commad son ranka ina dai nike da rayuwana bawani ba. Ya ce haka kika ce nace kwarai kuwa don may zan ka so takura min kamar wani wanda ya ajeni can a gidan shi. Ya juyo ya kara fuskantana yace haka kike so kiga an adanaki a gida ko sanan zaki bi maganan da ake fada maki na kula da kan ki ? Nace haka din ne ai shiya na fada haka kawai ba matar aure nake ba zaka wani kafa min doka kamar wace ke karkashin wani. Yusuf yace kai kanwa ta ba kayau ne haka yasa kikaji ana maki magana kada ki dauki zancen da zafi mana. Yace barta ai ka santa da bakin tsiya wanan bakin naki ya kai karshen tsiwan sa daga yau zaki kula kisan abin fadawa mutum. Wai ma may zaki je kaduna a wanan lokacin haka kuna karatu ko kin fara wasa da karatun ki ne yanzu ? Nace kai wanan ya dama ni gurin yar uwata zanje in dubata karatu kuma nike da abina ba wani ba. Murmushi yayi yace yarinyar nan ina tausayawa ranan da bakin nan naki zai dinke ya koma shiru wallahi kaina na kawar wanan karon ban biye mashi ba ya koma ya jingina da kujara ya dafe kan shi da hannun shi daya. Sai Yusuf ne ke dan jana da hira jefi jefi ban bashi amsa sosai sunyi sayayya a hanya sai ba a wani dade ba sai gamu mun shigo garin kadauna garin gwauna. Lokacin duhun yamma ya fara a yi sosai nace ku sauke ni in karasa a motar haya wani irin kallo ya watso min daga inda yake zaune yace saboda kin saba shiga motar hanya baki mai dashi komai ba ko ? Koda muka shigo layin mu har an fara kira a wasu wurare na magariba daidai get din gidan Ya Amina Yusuf ya tsaya da motan da muke ciki na fito tare da fadin yayana na gode sai da safe. Ki gaida sister idan kin shiga kice muna mata yaya jikin kafin mu shigo gaida ita zataji kawai nace dasu na dauki jakata na nufi ciki. Sai dai may daga get din har ciki a rufe na gansu waya na ciro ina kiran ta har ya katse ba a dauka ba nan dai na sake kira karo na biyu yana gab da katsewa ne aka daga wayan nace. Ya Amina kina ina nazo gida ban samay ku ba gida a rufe khadija ce nace eh don ba muryan ta naji ba a wayan. Tace mommy ce Amina tana gidan mu sallah take yi nace ok ina wuni mommy tace lafiya kalau yaya hanya nace Alhamdullahi mommy. Na kashe wayan don ban son dogon magana da ita nasan dai tunda mommy tasan nazo kamar Ya Amina taji ne na zo din. Na dan jima a tsaye sai can na hangota da saurin ta tana fadin ke tafiya haka babu sanarwa ashe kina hanya ne ? Don Allah bude min gida ni fitsari ya damay ni tun a mota nake jin shi wallahi tace kika ki magana a tsaya maki kiyi haka fa na jawo matsala ga mata. Tsuki nayi lokacin da ta bude gidan na fada da sallama a bakina ban tsaya ba na aje jakka kawai na fada ban daki da sauri. Har da alwala na dauro kafin in fito na zo falo na tayar da sallah don bata cikin falon a lokacin ban daga gurin ba sai da na gabatar da ishai. Wayana ake kira na dauka maryam ne take tambaya na yaya hanya kuma mun isa kd din nace mun iso yanzu tace an gyara motar ne nace ina fa ke dai bari maryam. Muna wurin ana gyara motar ba sai ga dan fitinar ga ba mai shegen izzan tsiya tace wa nace wa kika sani ni wallahi da nasan yau zai shigo kaduna ne da ban zo ba wallahi. Wai kina nufin su AA wallahi maryam su muna tsaye a jejin nan da na fada maki sai kawai ganin su nayi daga sama kamar a mafalki a gurin. Fitowa yaya Amina daga dakine yasa nace ma maryam ta bari idan na huta zan kirata muyi magana, muryan Ya Amina ne naji tana tambayana mota ce ta baku wahala a hanya. Nace bari ya Amina banji dadin wanan tafiya ba yau don dai kawai na kwallafa son ganin ku ne nayi shi dana koma wallahi. Gashi ko abinci ban tsaya nayi ba na ranane na rage wa yara don mun shiga gidan su mommy kin san ana buki a gidan nace buki kuma ina suka samu buki ? Tace a, a kin san ai da gidan su da gidan su Fati matar Abdulsamad kamar Family daya ne kannen ita fati din ke aure ai. A raina nace no warder ashe shi yasa mutanen nan nan suka zo garin ashe buki suke yi gaskiya naga an shake mota da kaya haka ? May zakici yanzu in dafa maki ko in shiga aurin mommy in karbo maki abinci don ni naci ko acan tun dazu. Nace barshi ko tea ne zan sha idan na watsa ma jikina ruwa zan kwanta muna wurin zaune muna hira sai mukaji sallama. Binta ce da zainab da wasu kawayen su biyu da ban san su ba suna dauke da basket din abinci a hannun su. Da ihu Binta ta karaso inda nake ta rungumay ni tana fadin wallahi khadija Adamu nafi kowa farin cikin zuwan nan naki ko kema dama kin san da zancen bukin ne wai ? Nace cikin fara,a wallahi bansan da zancen wani buki ba zuwa nayi duban ya Amina na kawai don nayi kewan ta da yarana. Aiko wallahi kinzo a sa,a don akwai casu wallahi nace ke har yanzu baki daina maganan wani casu ba can tace ba dole ba mutumiyar fa za aiwa engament jibi . Da sauri nace wa kenan kuma ta nuna min zainab tana fadin gatanan a gaban ki kuwa wallahi wayo take son muna nidake. Kallo na mayar ga zainab din dake zaune tana faman taba wayan ta nace wai da gaske ne ko sherin Binta ne kawai dayar yarinyar tace da gaske ne wallahi. Dan ihu nayi nace amma zainab kin bani mamaki ashe da Allah bai kawo ni ba da saidai inji labari. Tace a wani yanayi ba haka bane khadija nima ban dauka a yanzu za, ayi abin ba na dauka ko da sauran time ne shiyasa ban fada ma kowa zancen ba. Ta fada cikin izza da yanga sai yau nake ganin mugun kamar su da yayan nata komai nasu iri dayana sosai sunfi dauka kamanni da mahaifinsu fiye da kowa a gidan. Nayi murna kwarai sai can na kallo ta nace wai waye wanan lucky guy din da ya iya sace zuciyar wanan yar kwalisan yarinyar haka a lokaci daya. Binta ne ta bani amsa da fadin ina guy fin nan abokin yayan mu da always Suna tare da yayan mu Abdulsamad mijin buzuwa din nan wanda ake ce Yusuf. Shine ya sace zuciyar wanan mai zurfin cikin tsiyan da kike gani nima da muke daki daya da ita ban taba sanin wanan labarin ba sai da abin yanuna ya fashe naji. Kin san matar shi ta rasune a wurin haihuwa shakara biyar da ya wuce shine bai yi wani aure har yanzu ashe rabon zainab ta shiga gidan shi ne ya kashe matar . Harara zainab din ta aika mata na ki kama kan ki dinan nace amma zainab kinyi dace da mutumin kirki dan arziki daya san mutuncin mutane. Binta tace kin san shi khadija da kike fadin haka wallahi kin canka daidai kuwa don har yau ban taba jin wani hali nashi na assha ba da aka fadi. Na dafa zainab din ina fadin yar uwa ina tayaki murna da wanan babban kamu da Allah yayi maki muma Allah ya kaimu ga danshin ki. Zainab tana murmushi tace baki dai so bane khadija da tuni wani yayi wuf dake wanan zubin naki sai kace wata halfcas dake wani namiji zai ganki ya kau da ido gurine kawai maza basu samu ba. Kiba da dama yanzu ki gani in bakiga layi a kofan gidan nan ba har ba iyaka na maza a kofan gidan nace ba zasu samu ba yanzu zainab baki ba dai in nan gaba na kammal karatuna na fara aiki ko shi sai kila. Ya Amina da tunda muka fara magana baita magana ba sai yanzu tace yarinya in tunanen ki ke nan ki canza don baba a jirace yake dake wallahi. Nace Ya Amina baba ai yafi kowa sanin matsalana karatune burina inga na zama babban lauya wata rana Binta tace wai da mun sha dauri wallahi. Nace kamar ko kin sani don da na gida zan fara sharia na kada ma kiji wai binta ki rike dakayau a ranki. Zainab tace kinga mun kama zuba kamar ba gobe ga abincin nan mommy tace mu kawo maki a gurin ta ma muke jin zuwan naki yanzu. Daga inda Ya Amina take zaune tace wai mommy dai bata gajiya yanzun fa muke maganan abincin nan kamar ta sani sai gashi ta aiko muna dashi. Mommy ai tafi danan wallahi inji dayar yarinyar ta fada kowa yace wallahi halin mommy ai yayi ne sosai. Basu jima ba sukai muna sallama akan gobe zamu hadu sai mu kara tatauna abinda za a yi nace dana san da wanan zance ai da tare muka zo da maryam. Binta tace Allah sarki ban tambaye ki maryam din ba nace tana can na barta tace gobe ita ma gida zata tunda na wuce na barta. Har bakin get na rako su suka tafi na dawo ciki a inda na bar ya Amina zaune a nan na samay ta nace wai ina yaran suka tafi ne tace suna can gidan kakannin su zasu kwana masu biyu. Ban san zaki zo ba aida ban kai su can ba don in samu yadda nake so ne yasa nakai su can inji dadin shiga mutane babu takura. Wanka na shiga na fito na saka wani dogon riga a jikina na shan iska mai dan karamin hannun yadin rigar baida kauri sosai falo na dawo na samu ya Amina tana kallo. Zama nayi ina jawo kulan abincin da mommy ta aiko min dashi nayi mamakin ganin abincin haka kamar na wata hamshakiya. Ban san lokacin da nace wai mommy irin wanan hadin haka wallahi ni har kunyar matar nake ji Allah kuwa. Dariya Ya Amina tayi min tace ko har kun fara sarakutane da ita ban sani ba nace wa zata bani cikin diyan ta haka dai kawai nake jin nauyin ta yanzu. Wai ni ina Abdulsamad ne ina zancen ku ya kwana dashi ne tun lokacin ban kara jin labarin ba ko da yake yanzu kin fi zama minna ai. Tsuki nayi ina zama kasa nace ina ruwa na da wanan miskilin mutum da bai san darajan mutane ba halin su au daya da matar shi shiyasa nasu yazo daya da ita. A,a wallahi baki ko fahince shi ba khadija Abdulsamad mutum ne wallahi mai mutunci da sanin ya kamata ke dai kice Allah ya hada shi da yar banza mata ne mara mutunci kwanaki fa har gari nan tazo taci ma iyayyen shi da matar shi mutunci. Don Allah ya Amina abinci zan ci kada ki fada min maganan haushin nan ai ita bata da laifi shine mai lefin don ni wallahi da nice Fati da tasha takaici a wurina. Don wallahi tsab zan zauna da ita don tun yanzu na karanci iya shegen ta balle fati da suka zauna tare tasan halin ta da komai nata may zata gwada mata. Ke dan Allah can kin san aure ne da kike wanan haukan haka auren fa akace maki khadija ba wani abu ba ita mace dama ta gaji ganin haka walau mai kyau walau akasin hakan. Abincina naci gaba daci ban taka mata ba ganin nayi shiru itama taja bakin ta tayi shiru tunda ta fahinci ban son zancen . Ina gamawa tace min a dakin ta zan kwana tunda ita kadai ne a gidan kuma ba a gyara dakin nawa ba don bata san ina tafe ba. Nace aiko dakin baiyi wani datti ba dan fes na ganshi har da ban dakin tace duk sati ina shiga ina gyarawa don gudun irin haka duk da haka ki bari sai gobe idan an gyara ki kwana a ciki. Bayan nagama don naci abincin sosai na kwashe kayan zuwa kitchen daki na koma nayi shirin kwanciya wayana kawai na dauka da hijabin da zanyi sallah da safe na fito xuwa dakin ya Aminan. Na samu ta shiga wanka haka yasa na kwanta abina don dakin ba bako na bane wayana kunna na bude data sakone ya dinga shigo min daga ciki biyu kawai na duba na farko sokon mamud ne yana tambayana karatu. Sai kuma karshe da yake ce min ya matsu in gama muyi aure in haifa mai yara masu kama dani yana yawo dasu a mota a gari. Tsuki naja ina fadin baka da hankali mamud nice zan shiga ma ta uku gida don na rako matan duniya komay ? Sai sakon maryam tana fadin hostel din ba dadi dana tafi don haka gobe gida zata tunda safe duk da tasan yayan ta basu gari da mijin ta. Zatai zamane na kadaici koda taje amma yafi mata zama a hostel bani amsa na bata nace niko kinga nazo na samu ana buki anan har da engement din zainab da Yusuf alama murna ta nuno min tace yaushe ne bukin nace mata sturday idan Allah ya kai mu. Gobe zaki ganni tace kai maryam da gaske tace insha Allah ko naje gida Anty basu kasan suna waje da mijin ta ai gara inzo inda kike muyi hutun tare. Mukai sallama ina murna har ya Amina ta fito ta samay ni hakana nake fada mata gobe maryam zata zo tace ashe ina da bakuwa gobe a gidan kin ga sai kin min list din abinda take ci a sayo maku kada tazo nan ta takura. Dariya nayi nace da kin hutar da kanki don maryam suna masu kudi ne kawai amma bata da matsalan komai wallahi komai da kika san muna ci tana son shi. Allah ya kawo ta lafiya nace amin daga haka had barci ya dauke ni nayi mafalkin ga mutane sun taru ina kuka haka yasa na kasa barci har safe nakai a hakan. Haka na tashi da safe a cikin damuwa ina tsoron in fadi wani abu mumuna ya faru dani da gari ya karasa wayewa nace da anty zan fita bakin titi in ba da sadaka. Bata tsaya tambaya na ba na fita zuwa titin in da nayi saa na hadu da wata mata mabukayi tana neman abinda zataci da yaran ta na bata dubu biyu tana min addua na juyo zuwa gida. Ban yi nisa ba ina karyo kwanan unguwar mu tun daga nesa na gane A A tafe a cikin kayan motsa jiki yana judging shi da su mutum biyu a bayan shi. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABUKawar da kaina nayi gefe kamar ban ganshi ba ko ban san shi ba karfin gudun ya rage ya dinga sarsarfa zuwa wurina yayin da ni kuma nake sauri in shige get din gidan Ya Amina din. Ke ji mana yace bai juyo ba sai saurin da nakeyi na kara harda dan gudu nashige ciki tsayawa yayi ya rike west din shi da hannun shi biyu yana dan murmushi. Yadda na shigo gidan kamar wacce aka koro yasa Ya Amina fadin ke lafiyan ki kuwa nace ina waigen kofan shigowa lafiya sauri nake na bar wayana daki. Ajiyan zuciya ta sauke ta kalli kofan sai ta juyo ta kalli inda na shiga ta tabe baki na dade a ciki zaune kafin in fito danaji shiru. Wanan kaaton da soja yaje daya fi mai yya more karfin shi a can nace ina dagawa wanka nayi na fito na shirya na fito falo. Na samu yaAmina bata falon sai gata ta fito daga uwar dakin ta tana fadin zan dan shiga gidan su mommy akwai aikin da zamuyi da safe nan kin san ance ka rama alheri ga mai maka. Dana haifi Na,ima mutanen nan baki ga irin alheri da sukai min ba wallahi banda abin basu in ba ta haka zan maryar masu da alherin su ba gare ni. Adawo lafiya nace mata ina lafewa saman kujera tare da danna wayana ta juyo tana fadin idan ban fito da wuri ba sai ki dora girkin abinda zamuci da rana kada bakuwan ki tazo ta samu ba abinci. A kwai komai a kitchen da zaki buka wanda babu ki buga min waya ko ki fita ki samu nan bakin layi sai kin dawo nace da ita tafice daga gidan. Ban dade ba barci mai nauyi ya dauke ni a guri firgigit na tashi daga zaune don mafalkin hajiya mama da nayi ta sani gaba tana min murmushi. Firgigita na falka daidai lokacin da ta mika hannu zata share min hawayen dake bin fuska na ina mamakin wanan mafalkin da nake yi tsakanin jiya da yau. Na dade zaune a gurin kafin in mike in shiga kitchen ban ankara ba ashe har shadayan rana ya gwauta ban sani ba a gurguje na dora muna girki ina yi ina duban time. Wayana naji yana ruri daga falon inda nasa chagi da sauri na nufi gurin maryam ne a layin na dauka ba ko sallama naji tana fadin wani unguwa zan ce a kawo ni nace GRA na fada mata sunan layin mu. Isowan ta yayi daidai da gama girki na na fito na tare ta a waje muka rungumay juna muna dariya tare da shigewa ciki sai bin gidan takeyi da kallo. Falo muka shiga na karbi jakkanta nakai dakina da na gyara na dawo falin ina dariya tambaya na tayi ina ya Amina nace humm kin san sune kan buki tun safe ta shiga wai aiki a family house din su AA. Nikan na matsu in san wanan uwar gidan nashi abin tausayi na kallo ta nace may abin tausayi a ciki an fada maki tana cikin wani hali ne ? Khadija labarin dasu Binta suka bamu nata ne ai matar abin tausayi ne wallahi malama kice dama gulma ya kawo ki ba taya zainab murna ba. Sannan ita fa Fatin nan halin tane haka shiyasa mutane suke mata kallon abin tausayi tana da sanyi hali da rashin nuna kulawa ga abu shiyasa mutane ke fadi haka. Amma ni ina ganin lafiya kalau take da mijin ta yanzu don ban kara jin wani maganan haushi ya faru ba koda yake idan ma ya faru ni ina zan sani. Mikewa nayi na shiga kitchen na fito mata da abinda zata ci mun dade muna hira har bayan azahar muka mike zuwa sallah. Ina idarwa wayana na karan kira ya shigo min na dauka da sauri Zainab ce a layin gaisawa mukayi take fadin khady har yanzu baki shigo ba mana bamu shirya komai ba fa ke ake jira. Nace gani nan da maryam ta iso dazun tana hutawa ne amma mai zai sa sai nazo kuyi duk abinda kuka ga ya dace mana zainab. Look indan ba zaki zo ba ni ganin nan zuwa dayani in gaida maryam da zuwa don binta sun fita sai kin zo din nace Allah ya gani yanzu kunyan shiga gidan su nakeyi. Ba a dauki lokaci mai tsawo ba sai gasu tare da Binta sun shigo da murna suna taron maryam din nace ga gandoki muje buki ta iso daga ina fata mata kawai tace gata nan zuwa ai. Wayan zainab ne yayi kara ta dauka da murmushi tana mikewa wurin da muke din Binta tace ango yayi kira ke nan dariya nayi nace au shine ake gudun muji yadda ake soyewan ta dan waigo tana fadin wallahi yayana ne ai ba wani soyewan da muke yi ke dai. Munafuncin banza sai ki fada masu su da basu sani ba nikan nasan komai ai yanzun tana dauka yake tambayan ta tana inane haka waya ke ta ringing bata dauka ba? Tace nazo wurin kawar mune Khadija da tazo nan makwabtan mu ba nisa damu murmushi yayi yace khadijan na kusa ne ki bata waya tace eh sai gata tazo tana miko min wayan. Yayana ashe kwanan nan zakayi wuf da kawata gaskiya munyi murna sosai Allah ya sa albarka ga alamarin. Ameen khadija Allah yasa ayi namu da naku a lokaci daya ya fadi da sauri nace dani dawa kuma ai ni ban ko tsayar da miji ba balle aje ga zancen aure . A yadda muke magana dashi yasa dukan su zuba min ido a cikin tuhuma sai kuma ga maryam tace kice ina gaida shi ina taya shi murna. Ga mayam tana tayaka murnan samun zukekiya kamar zainab na fada cikin zolaya yace haba yaushe tazo nace yau din nan ina fada mata jiya tace da ita za, ayi komai shine ta taso yau aba maryam din waya yace. A lokacin da nake mika wa maryam waya binta tace wai tsaya nifa ban gane ba ? Dama kun san shi ne ko may maryam ta karbi wayan tana fadin yaya Yusuf ashe wani abin arziki ya samu kuma munyi murana sosai wallahi. Yace ya gode ta mika wa zainab wayan ta zainab din ta juya tana make murya muka sa mata dariya wai tsaya don Allah dama kun san yaya Yusuf ne khadija ? Mun san shi mana farin sani kuwa kallon da tati min ne yasa na gyara zancen da fadin ai a sanadin ku ne muka san shi kin manta ne. Zainab ne ta juyo tana fadin wai yana waje yana jiran mu mu fito gaskiya something is fishing here don ina mamaki har da gidan ku yaya Yusuf wai ya sani. A yadda nasan yaya Yusuf bamai yawan magana ba ne da zai san ku haka farat daya dariyan da maryam keyi ne yasa ta mayar da hankalin ta gare ta. Mikewa mukayi zuwa wajen inda yace yake a waje bakin get muka samay shi ya fito daga motar shi gaidashi muka fara yi muna tayashi murna. Yace in Allah ya yarda khadija na fada maki da naku za ayi bukin mu nace don Allah yayana kabar zancen nan wai dawa zaka hada nine halan. Koma da waye kin fi kowa sani don yanzu lokaci yayi da kowa zai sani na gaji da wanan wasan boyar naku maryam tace ashe ka gane su yaya ? Maganan mu ya daure ma su Binta kai nace cikin daure fuska don Allah yayana abar zancen nan anan kada kasa in koma yau Abuja. Yace an gama ama watarana ai dole kowa zai sani nace wai asan may da kake ta fadin haka yace ai na bar zancen tunda baki son matana ta sani ko ? May kuka shirya zakuyi ne goben nayi saurin cewa ba wani bidia zamuyi mai yawa ba kawai dan get together zamu da kawayen mu su ma su sheda. A ina zakuyi ke nan binta tayi tsagal tace yaya a kama muna holl a gamji kawai muje can mu cashe da sauri nace a, a wallahi nan dai kusa zamu samu wani gida muyi event din mu wanan ai kya jira har aure yazo. Zainab tace ga gidan yayan mu nan ai ya ishe mu muyi komai don ko falon gidan kunga babba ne sai dai in ba zai bari ba kun san shi da rashin son hayaniya. Cabdi akan may zai hanamu shi da matar shi tayi buki na banza ma a ranan fa Yusuf yace to shike nan kunji madam ta gama maga dole ko zai yarda da hakan. Balle ma ai bazai hanaku yi ba a gidan sai ka fada mai da kanka Binta tace yace kedai ki bar zancen tunda kin ji khadija tayi magana ai an gama. Yayi muna sallama yace zai tafi idan munyi list din abinda muke so sai mu turo mai amma ga wanan ya ciro kudi a motar shi yana miko min wai mu fara amfani dashi. Kai na kada nace a a yayana kudin nan sunyi yawa wallahi bafa wani abu mai yawa zamuyi ba a wurin just friends din mune zamu hada su tayamu murna. Binta tayi saurin mika hannu tana karban kudin wai din may zance sunyi yawa inda wani ma a karo. Murmushi yayi yana fadin khadija dama nasan halin ki ba karba zakiyi ba amma ita kaunar nan nawa da tasan dadi kashin kudi kinga ta karbe da sauri ai. Duk muka sa dariya ya wuce ya barmu a gurin nan gardama ya kaure muna akan abinda zamuyi sai zainab tace ba fa wanan ba shi yayan mu yasan gidan shi zamuyi event din gobe ? Maryam tace ai mashi magana mana aji ko zai bari indan bai bari ai da wurin yi da yawa bashi kadai ke da gida ba khadija baki san halin yayan mu bane da masifa. Amma mu gwada kiran shi mu gani yanzu da sauri binta tace wa zaiyi magana idan mun kirashi din maryam tace a ba khadija tayi. Kira Binta tayi ta miko min wayan kafin in magana kamar ba zai dauka ba sai can aka daga yace wake magana ? Malam gidan ka muke son aro gobe zamu danyi get together ne da kawayen mu na engament din Zainab yace kuna da hankali kuwa ? May zakuyi wa wasa ko kun manta matar shi mutuwa tayi kada ko fara gigin yin wanan abin na fada maku wai ma wake magana ne ya tambaya. Nan sani ba nace na kashe wayan da sauri Binta tace ke zaki ja muna masifan shi ne baki san shi bane wallahi . Maryam tace yanzu yaya ke nan don maganan yaya AA gaskiya ne fa tunda mutuwa matar shi tayi binta tace humm ummm wallahi sai munyi shekara nawa da mutuwar matan shi yanzu. Zainab tace mommy zamu fadawa ita kadai ne zatace ayi ya yarda ayi don kun san hajiyan mu ba zatai magana ba don haka muje wurin ta kawai. Da sauri nace wa nikan sai kun dawo maji yadda kukayi amma nikan gaskiya ban iya zuwa wurin mommy kan wanan magana. A take Zainab ta nuna min bataji dadin haka ba don nine hope din ta yanzu kuma nace ban zuwa dole na yarda muje wurin mommy din . Mun koma ciki na dan gyara jikina muka fito muka tunkari gidan nasu a dakin mommy muka yada zango bayan mun gama gaisawa da mutanen gidan sai dai bamu je aurin hajiya mama ba sai mun fito. Ni da maryam a kasa muka zube muna gaida mommy cikin fara,a take amsa muna tare da tambayan mu munzo lafiya ? Ta kalli maryam tace wanan ne kuka zo asibiti ranan tare ko nace itace mommy tace yarinyar nada kirki wallahi ku yi hakkuri da junan ku kun ji nace to mommy mun gode. Binta ce ta fara mata bayanin abinda ke tafe damu mommy tace shiko dai abinda ba a gari daya ake ba may zai sa ya hanaku yin farin ciki ai wanan farin ciki ne ga kowa. Ya barku kawai kuyi abin ku tunda ba wani abu can zakuyi ba dan taruwa ne kawai mommy ayi addu,a binta ta fada wani addua kuma binta abinda za a tara yan mata. Kada ki kawo min wanan karyan naki yanzu dai ku bari zan ganshi in mashi magana kafin goben ya kyale ku kuyi abinku tunda shima yusuf din baiki ba. Zamu daga mi bar dakin mommy tace khadija an kusa gama karatun ko nace mommy da dan saura kadan insha Allahu. To ai mu mun matsu ki karasa ansan abinda ake ciki don na matsu in kai ga sarakuwa irin ki sai dai ki matsa da addu, a fa don Nafisa ba wasa. Mun fito wurin mommy dakin hajiya mama muka nufa muka gaida ita da fara,a take fadin ikon Allah ashe Allah ya nufa ayi dake sai gashi kin zo garin. Dan dariya nayi ciki ciki nace wallahi mama basu fada min ba zuwa kawai nayi duba ya Amina don na dade ban zo ba tace ina zakizo wanan karatun naku mai wuyan sha, ani Allah yasa dai a gama lafiya nace amin mama nagode. Muka shige dakin su Binta suna ta faman buga ma abokan su waya kan event din mu dai muna gefe muna jin su. Hajiya mama ne ta kwala ma binta kira tafita tadan jima sai gata ta dawo tana fadin ga su yaya AA nan sun shigo yanzu kuzo ku gaida su. Nace daga inda nake kwance ku tafi kawai ni ina nan ba inda zanje sai kun dawo su fita sai ga zainab wai mama tace muzo mu gaisa da yayan su. Dole na fito muka gaida su na tsaya can baya daga kofa maryam ne ta dan fita fili sosai yace kinzo lafiya maryam ? Ai ba ita daya tazo ba ga diyana nan a bayan ta ai ina kun san ta khadija itama jiya tazo daga Abujan kasan acen take karatun ta. Mama wanan diyar taki mara kunya ce baki ga inda ta tsaya tana gaida mutane ba daga nesa gaisuwan ma sai da kika roka mana tazo. A a ban yarda ba kai kadai naji ka fadi haka ga khadija amma khadija ai tana da tarbiya ko dan hararan shi nayi daga inda nake lokacin da yake maganan. Mommy ce tashigo dakin inda shigowanta baisa mama ta fasa maganan ta ba tace kai ai kowa ba daidai yake ba saboda murdaden halin ka. Mommy tace may kuma yayi yanzu da shigowan shi yaya tace haka kawai zai saka min diya a gaba daga gaida shi wai bata da kunya. Ina shi kunyan ne gare shi yaya ki barsu kawai don sun fi kusa idan kika shiga maganan nan kunya zakiyi . Au to haka zancen yake to Allah ya tabbatar muna da alheri da nafi kowa farin ciki da hakan kuwa da sauri nace mama ba haka zancen yake ba mugune shi kawai nama rasa may zance dasu a wurin. Dariya mommy sukayi tace na fada maki barsu kawai su gama boye boyen su kyaji may ke nan watarana. Mommy ai ba sai watarana ba gashi sun nuna a gaban ku ai yanzu kowa ya sani haka da kika gansu muke fama dasu wallahi ko maryam ? Yana tambayan maryam din tace mama kyale su haka suke ko yaushe ba a shiga tsakanin su don ko an shiga zasu dawo su shirya ba a sani ba. Ji nayi wurin bai dauka na da sauri na koma ciki ina jin wani bacin rai tare dani ban san yaya suka kwashe a falon ba na daiji binta ta shigo tana murna wai an mashi magana yace muyi. Suna murnan su nikan raina a bace yake da maryam da yusuf har da mommy data biye masu din. Sai da kyat na saita kaina na dan koma normal kada a fahince ni bamu bar gidan ba sai dare so sai muka koma gida tare da ya Amina da dawowan su ke nan daga gidan jere. Wanka nayi na kwanta don raina a bace yake da kowa nayi dana sanin zuwan danayi kadunan a yau da nake ganin ana son kula min sheri wurin matan da nake jin nauyin su. Shi kuma munafukin bai fada masu ba gaskiya bane dan ya kullamin sheri kawai a wurin su komay yake nufi oho zan gani idan ana kula abinda ba alaka ne a cikin sa. Da safe tun safe su zainab suna gidan mu ana sha,anin buki a cikin gida mu muna shirin namu event din. Unguwar yacika da baki nakusa dana nesa ko ina mutum ya duba motane na masu zuwa daurin aure a haka muka ratso tarun mazan har kafana yana hardewa. Kamar ance in daga kai can na hangoshi tsakiyan mutane daga nesa muka watsa ma juna harara mun shiga ciki zakace a gidan ne ake buki don jama, a da suka cika gidan. Nan na kara yarda ba karamin alaka ke tsakan gidajen biyu ba mun zauna ke nan massage ya shigo a wayana na dauka ina dubawa. Kina da hankali kuwa da zaki ratso wanan taron maza haka da dan gyale karami. Haushi naji har cikin raina na mayar mashi da amsa ina ruwan ka da ni ka fara tsare matan ka kafin ka fito sa ido waje. Yarinyar dani kike wasa ida na kara ganin ki haka a garin nan sai na bata maki rai . Kaji min mutum da sa idon tsiya kai waye da kake son saka min doka na rubata mashi. Ya sake rubuto min barin shigo ciki in nuna maki ko ni waye a gaban su mommu da hajiyan mu yanzu. Ban bashi amsa ba don tsoro ya kamani kada bakina yaja min jin kuya sai hira muke a falon hajiya mama ban yi aune ba sai ganin mutum nayi ya shigo falon. Da sauri na noke kaina kasa ina hajiyan mu ya tambaya cikin daure fuska take dakin yayi tsit kamar ba kowa a ciki lokacin. Sai zainab ne tace mai yanzu ta shiga dauko abu a ciki sai gata ta fito yace a hada muna abinci akwai bakin da suka zo daga Abuja yanzu. Kai babangida shine kaki fada da wuri a cire masu tun farko ai da ko matar ka sai kasa ta aje masu yace ni kaina wai bata aje min ba tace. Kai wanan irin abu naku damay yayi kama ace ana buki a gidan ku bazaka aje ma mijin ka abinda zaici ba sai ya tambaya mama ta fada cikin bacin rai. Nan ya fice daga falon na sauke ajiyan zuciya muna zaune kafin wani lokaci an hada masu aka kai ina jin mommy da mama suna ta fadan abinda banji dadin shi ba kan fatin. Mun dage bukin mu sai washe gari don hidimar bukin da yayi yawa a gidan dole muka dage namu din sai washe gari four na yamma zamuyi inda nasa rai ya wuce a lokacin don Sunday ne dole ya koma aiki na manta akwai hutu Monday da za ayi. Kamar yadda muka tsara zamuyi four mun gama shiri a cikin dogayen riguna bakake gaba dayan mu sai zainab ne tasaka fari kwal a cikin mu. Mun gyara wurin dakyau kawaye na zuwa guda guda har wurin ya dan cika mu mata zalla ne a gurin muna gidan Fati ta dawo daga gidan su daukan abu. Maryam ta zuba mata ido tana kallon ta ina gefe ni kuma ina kallon maryam din bata tsaya ba ta fice ta barmu a gidan . A falon su ne zamuyi event din so ba wasu maza a gurin sai wanda zai muna dj da aka dauko bayan yan bayane aka fara gudanar da event din gwanin ban shaawa. Mun sake sosai don mu kadai ne a gidan haka ya bamu daman sakewa yadda muke so a gidan kira ake guda guda mu fito mu taya zainab din murna a fili muna fitowa har akazo kaina na fito na fara takawa kamar ance in daga kai sama tsaye yake da waya a kunnen shi yana saukowa kasa. Da sauri na rage rawan na fita fiilin suka sa ihun basu yarda ba don time din da ake ba kowa baiyi ba na fita. Gyaran muryan da yayi daga bayan mu ne yasa kowa dake wurin ya natsu sai da ya fita muka koma abinda mukeyi din wayana naji yana kugi da sauri na ciro a jakkana ina dubawa fito nan waje yace dani. Sai na basar da sakon naki fita wani sakon ne ya kara shigo min again ki fito ko inzo wuei in samay ki cikin bacin rai na fito cike da rashin mutuncin wanan takuran haka da yake min. Ina fitowa na duba ban ganshi ba sai naji horn a gabana na gane yana cikin motar shi zaune wurin na nufa na samay shi zaune a motan. Shigo yace min nace bazan shiga ba nan yayi min nace dashi kai tsaye yace ki shigo tun ban fito ba wallahi ban shiga nace kai tsaye yana fitowa na fara ja da baya baya har nakai jikin wani mota na tsaya. Ashe karya rashin kunya kike yi may kika rubuto min jiya tsakanin mu bai wuce tako daya ba nace may ka gani ya tako kenan zuwa gare ni binta tafito daga ciki tana kwala min kira. Da sauri ya ja baya na sauke ajiyan zuciya kirana ta kara yi ya juya a fusace yana cewa da ita stupid wanan kira haka fa kamar makauniya. Ta juya simi simi zata wuce nace jirani muje Binta yace bace min da gani ta wuce ba ko waige ta shige ciki da sauri ya dawo da kallon shi gare ni da zuman nufo ni na zille da gudu na bar wurin. Sai gab da magariba muka gama muka kwashe kayan lokacin har ishai yayi kai tsaye gidan ya Amina muka nufa ni da maryam. Binta mamaki ne ya cika ta ta kasa sakin jikin ta na abinda ta gani yana aukuwa tsakanina da dan uwan nasu sai da sukaje gida ne take fada ma zainab abinda ta gani. Zainab tace nima naso in fahinci hakan tun ranan da taje waje tayi mai magana a hostel din su amma koma may ye zan binkici yaya yusuf inji ko akwai wani abu a tsakanin na su. Wai har khadija taban tausayi wallahi ina zata iya da Nafisa anty Fati da take babba yaya ta iya da ita balle khadija da take karama ? Zainab tace ai abin badaga nan yake ba in fada maki sai ko kiga khadija ta iya zama da ita tsab balle khadija da take da baki. Magana may naji kuna yi haka baku kwanta ba muryan hajiya mama ne a dakin nasu take tambayan su zainab tace a a magana mukeyi kawai. Binta tace mama wani abin mamaki na gani yau wallahi yayan mu tare da khadija nagani sun ban mamaki don akwai wani abu a tsakani su nake gani. Koma may ye a tsakanin su Allah ya tabbatar muna da alheri shi muke fata ga kowan ku yanzu ta fice ta bar masu dakin cikin sanyin jiki. Kodai dama hajiyan mu tasan da wani abu a tsakanin su ne ga yadda tayi magana yanzu kamar tana da masaniya akan abinda nagani. Kokarin rungumay khadijan fa naga yanayi sai dai ita khadijan kamar a tsorace take a lokacin kai Binta banda sheri fa. Au kin dauka karya nake yi ai koma may gobe zan tambayi khadija din don nasan ba zata boye muna komai ba inji Binta. Zainab tace yau zan tambayi yaya Yusuf idan ya kira ni inji don shi zai san komai akan haka ? Washegari Mun sha barcin gajiya don haka bamu tashi da wuri ba gashi ina son zuwa hidan kakanin yaran Ya Amina in duba yaran dake can. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU