An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels *_Typing📲_* *_MAKAUNIYAR ƘADDARA😭_* *_Bilyn Abdukk ce🤙🏻_* *_Da sunan ALLAH mai rahama mai jinƙai. Ya UBANGIJIN al'arshi ka bani ikon rubuta abin zai amfani al'ummar MANZON ALLAH. Ka tsare harshena da alƙalamina rubuta abinda zai cutar da ni da duk wanda zai karanta littafin nan. Ka bani ikon rubuta abinda zai amfaneni duniya da lahira ni da masu karatun._* *_Ina mai farin cikin sake dawowa a wannan karon tare da ƴan uwana, yanda muka fara lafiya ALLAH ya sa mu gama lafiya, UBANGIJI ya bamu kariya yay riƙo da hannayenmu baki ɗaya._* *_Ya rabbi ka gafartama Mahaifina da sauran al'umma da suka rigamu gidan gaskiya. Idan tamu tazo ALLAH yasa mucika da imani. ALLAH ka wajabta mana tsoranka da soyayyar MANZON ALLAH😭🙏🏻._* _Zafafa Next level_ *Page 1* ..............“Inada tabbacin wannan itace tashar da zaki iya samun motar duk wani gari da kike buƙatar zuwa”. Mai napep ya faɗa dai-dai yana samun wajen fakin, da ɗan karkato kansa yana duban yarinyar dake a baya zaune.       Batace da shi komaiba. Sai ƙoƙarin kwance haɓar zaninta da takeyi jikinta na rawa. Ta miƙa masa ɗari biyar ɗin dake a ƙudundune saboda uban ƙullin da tasha a cikin zani. Baki ya buɗe kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa. Ya ɗan fisgi ƙudundunanniyar ɗari biyar ɗin daga hannunta yana ƙunƙuni ƙasa-ƙasa.       A yanzu ɗinma batace da shi komaiba, sai hawayen dake famar zarya daga idanunta zuwa kumatu. Tsohuwar ɗari biyu guda biyu da naira talatin a sama ya miƙa mata fuska a tsuke.     “Nagode”. Ta faɗa a karo na farko tana amsar kuɗin. Batare da ta jira amsarsaba ta fito daga Napep ɗin tana kalle-kalle da ƙoƙarin sake maida kuɗin daya bata a haɓar zani ta ƙulle kamar ɗari biyar ɗin ɗazun.      A kallo ɗaya zaka iya fahimtar ƙarancin shekarunta. Dan kuwa bazata wuce shekaru sha huɗu ba. A tsarin halitta batai kama da mai taɓin hankaliba, amma a yanayi zaka iya kiranta da mai ƙarancin hankalin. Duk da kuwa babu wani datti ko makamancin hakan a kaf illahirin jikinta.       Ƙara kai hannu tayi ta share hawayenta a karo na babu adadi, cikin rauni da alamun tsoron dake tattare da ita ta furta, “ALLAH gani gareka. Da kai na dogara, a gareka kuma nake buƙatar taimak......”      “Ƙanwata ina zakije?”. Karaɗin wani kwandasta ya katseta batare da takai ƙarshen addu'arta ba. Kallonsa tai da jajayen idanunta dake a kumbure saboda kuka tace, “Danya”.        “Danya? Ƙanwata sai kinyi ƙarin bayani, dan nikam bamma taɓajin sunan wannan garin ba”.     Shiru tai alamar nazari, ‘Gaskiyar kwandasta ɗin nan. Danya dai garinsu motama bata shiga sosai. To amma idan bata mantaba lokacin da zasu taho da Hajji Lanti bayan sun fito daga Danya a mashin, a Gozarki suka kwana, washe gari kuma daga Gozarki sukazo kusada, anan suka sami motar Katsina’.        “Wai kodai bakisan ina kika dosa bane ƴammata?”.      Kwandasta ɗin nan ya sake katseta. Da sauri tace, “Kusada zanje”.      “......Kusa da kano, nesa da birnin katsina” kwandasta ya faɗa cike da barkwanci. ita dai batace da shi uffanba, sai ma faman waige-waige da takeyi, har yanzu akwai tsoron ko wani zai iya biyo bayanta tattare da ita.      “Kinga ga motar da zaki hau can ta kaiki Gidan mutum ɗaya. Inada tabbacin daga can zaki samu motar kusada ƴar ƙyaƙyƙyawa”.      “Nagode sosai” ta faɗa tana ɗan risinawa. Daga haka tai gaba da sassafa batare data sake bi takansa ba.       Tana isowa motar daya nuna mata ko jiran ba'asi bata tsaya yiba saboda jin kwandasta ɗin motar nata faman faɗin, “Charanci, kankia, Gidan mutum ɗaya, Tsanyawa, Bichi, har kano.     Can baya ta shige inda wata mata ke zaune ita da yaranta biyu da bazasu wuce sa'annintaba. Ta sauke nannauyar ajiyar zuciya dasa hannu ta gyara ɗan labulen jikin gilashin yanda take fatan ko su Hajiya biyota sukayi bama zasu iya ganinta ba. Duk da hakan kuma roƙon ALLAH take a ranta ALLAH yasa motar ta cika da wuri su tafi.      Addu'ar tata kuwa ta amsu. Dan ko cikin ƙanƙanin lokaci motar ta cika. Ita dai tana duƙunƙune cikin hijjab har kanta. Ko wanda ya shigo ya zauna a gefenta bata kallaba sanda ya shigo. Ta sauke wata nannauyar ajiyar zuciya jin motar ta ɗaga alamar zasu bar cikin tashar.       Sunyi tafiya mai ɗan tsayi data tabbatar sunbar cikin birnin katsina ta tsinkayi maganar kwandasta na ambaton kowa ya bada kuɗin mota. Ciro kanta tai daga hijjab ɗin bayan ta kunto kuɗin data ɗaure a haɓar zaninta na canjin mai napep. Jin matarnan mai ƴaƴa na tambayar “Nawane gidan mutum ɗaya” ya sata tsaida hankalinta tana jiran amsar kwandasta ɗin itama.     “Ɗari huɗu ne kuɗinki hajiya”. Ya bata amsa yana amsar kuɗin na kusa da shi.     Matar tace, “Haba ɗana adai duba. Wlhy jiya a ɗari uku-uku mukazo. Yaran nanma ɗari bibbiyu na biya musu”.      “Ai jiya kikace hajiya. Jiya kuma ba yau bace. Dan haka kuɗinki keda yaranki dubu da ɗari biyu ne”.       Zatai magana wani dake can gaba yay saurin amshewa. “A'a fa gaskiya ɗari uku ne, ni kaina ɗazun nan da safe nazo a haka”.      A take rigima ta kaure tsakanin kwandasta da matarnan da mutumin da yay maganar da safe yazo a ɗari uku. Da ƙyar dai aka tsaya akan ɗari uku da hamsin.      Ita dai yarinyarnan dama bata tanka ba. Ta miƙa masa ɗari huɗun da mai napep ya bata canji.       “Ƙanwata ina zakije?”. A taƙaice tace, “Gidan mutum ɗaya”.      Canjin hamsin ya miƙo mata. Batare datace komaiba ta amsa ta maida a haɓar zaninta. Sai dai bata koma cikin hijjabinba tabi ayarin masu kallon hanya. Kasancewar motar mai lafiya ce bayan sallar la'asar kaɗan suka iso gidan mutum ɗaya. Danma sun ɗanyi tsaye-tsaye a hanya na sauke mutane.           A gidan mutum ɗayarma dai a rikicen take. Dan ba taɓa yin tafiya irin haka ba sai wannan karon. Sanda zasu tafi kuwa hajji Lanti ce tai musu komai. Da ƙyar ta samu ta tambayi wani yaro mai saida biredi inda zata sami motar kusada. Shine ya nuna mata. Tai masa godiya.        Ta iske ƙananun motoci kusan huɗu dake jere a kan hanyar da yaron yace mata itace hanyar kusada. Lokacin da suka tafi su tun daga cikin kusada suka shigo motar katsina.      “Ƴammata kusada ne?”. Wani tsamurmurin saurayi ya faɗa yana nufota. Saurin ɗaga masa kanta tayi alamar eh. Cike da jin daɗi yace, “Yauwa taho muje, dama mutum ɗaya muke nema”.     Har cikin ranta taji daɗin hakan. Ya nuna mata jar motar data gama fita hayyacinta. “Yauwa shiga nan. Bayin ALLAH a matsa mata mu kama hanya ko”.       Cike da mita fasinjojin suka shiga muskutawa dan sama mata waje. badan wajen zai wadacetaba ta shiga ta zauna. Sai dai kasancewar ta mai ƙaramin jiki yasa bata takuraba matuƙa. Sai dai waɗanda ta tarar a ciki sunata faman mita sukam an takura musu. Direban ya cika haɗama da son kuɗi. Yanda direba bai tanka musuba itama bata tanka ba. Sai dai acan ƙasan ranta daɗi takeji zata koma gida taga Babanta da su Yaya Tinene, duk da su ba son ganinta sukeba.       Tsabar rashin isashshiyar lafiyar motar basu iso ba sai gab da magriba, dan sun kwashe kusan awa ɗaya da rabi a hanya. Ga tsaye-tsaye da suka dingayi ana sauke wasu da ɗauka a ƙananun ƙauyika har kusan sau uku.     Hankalinta bai tashiba sai da suka iso taga kowa na miƙawa direba ɗari da hamsin kuɗin mota. Cike da tashin hankali da fargaba ta miƙa masa naira tamanin ɗin da suka rage mata. Wani banzan kallo yay mata sheƙeƙe yana nuna kuɗin.     “Naga kina miƙamin murtala huɗu (80n), bakiga abinda kowa ke badawa bane?”.       Cikin rawar murya da cikowar ƙwalla a idanunta tace, “Wlhy su kaɗaine suka ragemani, dama ɗari biyar ce na taho da ita da ga katsina, to sai naba mai ƴar ƙurƙura......”       “K! dakata. Wannan damuwarkice ba tawaba. Inda kinsan baki da kuɗin mota da baki bari nayi jigilar ɗakkoki ba ai. Dan haka ni kuɗina kawai na sani ba wai yanda kika taho daga katsina ba”.        Sharr hawaye suka shiga sakko mata. Ta durƙusa a ƙasa zata fara roƙonsa, hayayyaƙo mata yayi da masifa. A take hankalin mutane ya fara dawowa kansu. Ita dai duƙe take tana kuka da roƙonsa.          A mutanen da suka taru wajen duk basu bata goyon bayaba. Acewarsu miyyasa bata faɗa masaba kafin ta shigo. Idan data faɗa in yaso saiya taimaketa. Suma ɗin haƙuri take ta basu ita dai, dan harga ALLAH batasan adadin kuɗin motar ba. Hakama direba da zugar mutane ke sake harzuƙawa yana mata tujara.         Tun tana roƙonsu a duƙe harta koma gurfane abin tausayi. A haka wani saurayi da tausayinta ya kamashi ya ciri naira ɗari ya bama mai motar. Daga haka suka sama mata lafiya. Har ƙasa ta duka taima saurayin godiya. Yace karta damu, tadai daina shiga mota babu kuɗi. Gara ma idan bata da shi ɗin ta dinga faɗa kafin ta shiga zaifi sauƙi. Godiya nanma tai masa ta miƙe riƙe da naira talatin ɗin daya sake rage mata tunada an biya mata ɗari.        A kusada ɗinma ba sanin ina zata gano hanyar garinsu tai ba. Dan tunda tasan kanta bata taɓa zuwa cikin Kusada ba. Iyakarta ƙananun ƙauyukan dake gefen ƙauyensu kawai.       Tana son tambaya tanajin tsoro, ga wani azababben ciwon ciki da takeji yana taso mata kaɗan-kaɗan. Duk yanda taso cigaba da tafiya sai ya gagara. Da ƙyar taja ƙafafunta zuwa wata runfa ta zauna. Da alama runfar mai yin faci ne. Kasancewar magriba tayi harya tashi.      Zama tai ta duƙunƙune kanta cikin kafafu jikinta na rawa. Ga wata irin zufa na keto mata ta ko ina saboda azabar ciwon ciki. Tun tana zaune har sai da takai kwance a wajen tana juye-juye. Bata damu da cinnakun daketa galla mata cizo ba a jiki, dan ciwon da cikin nata ke mata ya danne komai.       Tsahon lokacin data ɗauka a yanayin ciwone yasa har dare ya rufa bata saniba. Sai jin garin tai ya rage hayaniyar jama'a. Ba ciwon cikin bane kaɗai matsalarta harda Yunwa da ƙishi. Dan rabonta da abincin kirki tun jiya a gidan Hajiya. Abincin da aka bata a gidan da aka kaita ƙinci tayi sosai, dan tana tsoron taci su yanke mata kanta kamar yanda zuciyarta ke bata danshi suka kaita gidan.     Tashi tayi zaune a hankali tana ɗan waige-waige. Titin babu haske. hakama jama'a duk sun nufi gidajensu sai ɗai-ɗaiku. Duk yawan motoci da mashinan ɗazun yanzu babusu. Sai wasu da basu wuce uku ba. Mashinanma bazasu gaza haka ba. Sai fitilar mai shayi da take hangowa can a wajen da motocin ke tsayawa (Tasha).      Komawa tai ta kwanta. Dan haka kawai taji wani shegen tsoro ya turniƙeta. Ta rufe idanunta gam tana karanto abinda ta sani na addu'a. Cikin amincin ALLAH kuwa sai ga barci ya kwasheta. Da alama hakan nada nasaba da gajiyar dake tare da ita ta wahalar tafiya da gudun da taci kafin samun Napep.. ★★★★★        Tun kiran sallar farko na asubahi ta farka da wani irin ciwon ciki. Murkususu ta dingayi tana kuka. Ta jima tana shan azaba kafin ya lafa mata. Zuwa lokacin anata ƙoƙarin shiga sallar asuba. Tashi tai a jikkace, dan yunwa takeji sosai. Ta taka a hankali zuwa inda massallacin tashar nan yake. Butocin da akai alwala ta dinga taɓawa harta sami mai ruwa. Ɗakkowa tai ta dawo wajen rumfarnan. Ta zagaya bayanta tai fitsari da yin alwala. Sauran ruwan kuma ta shanye. Sai a yanzune ta tuna ko sallar La'asar ɗin jiya batayiba. Rabonta da salla tun ta azhar da bayan idarwarta ta gudo.        A take ta fara maka sallolin nan batare da tabi tsarin daya dace na mai ramuwaba. Sai da ta gama jerosu har asubahi. Zuwa lokacin mutane nata fitowa, hakama masu mashina da motoci.      Da farko zaman kallonsu tayi. Daga baya kuma saita mike bisa shawarar zuciyarta. Ƙarasawa tai wajen mai  shayin nan daketa ƙoƙarin ɗora tukunyar garwar shayinsa yana raira waƙar shata. bayan ta masa sallama ya amsa ta gaishesa da girmamawa dan babbane ba laifi.       “Baba dan ALLAH tambaya nake?”. Ɗago kansa yay ya kalleta a karon farko. “ALLAH yasa na sani ɗiyata”. Ya faɗa da kafeta da kallon ƙurilla.    Kanta a ƙasa tana ɗan juya yatsun hannunta cikin juna tace, “Baba dan ALLAH inane hanyar Danya?”.       “Danya! Danya!?. To indai Danya dana sanice ta kusa da Gozarki hanyarta na nan gabas da mu”.       Jin sunan Gozarki ya sata kallonsa cike da jin daɗi. Ta kaɗa kanta fuskarta na sauyawa alamar farin ciki tace, “Eh itace baba”.          Yace, “To zaki zauna ki jira masu mashina dake shiga kenan. Idan kuma bazaki iya jiraba ki samu mai mashin anan ki biyasa talatin ya kaiki ainahin Gozarki ɗin anan zaki samu ƴan mashinan Danya”.       Taji daɗin shawararsa. Hakan yasata masa godiya. Duk da talatin din ta rage mata a jiki, kuma yunwa takeji gara tabi shawararsa. Babu wani jimawa kuwa ta samu mai mashin. Kamar yanda mai shayi ya faɗa talatin mai-mashin din yace zata bashi. Sai da ta bashima sannan ta hau.      Cikin mintuna ƙalilan suka iso Gozarki. Amma sai da ya kaita har hanyar ƙauyensu Danya. A take farin cikinta ya ƙara bayyana. Harta zauna da nufin jiran masu mashin dan babu wanda ya fito saboda akwai sauran safiya, sai kuma ta mike. Ba komai ta tunaba sai nasihar saurayin jiya daya cika mata naira ɗari. Bata da ko sile. Mizaisata zaman jiran mashin? Gara ta taka da ƙafa, duk da kuwa tasan akwai nisa. Amma ɗokin gata a kusa da gida sai ya gusar mata da komai har yunwar da takeji da rashin daɗin jiki.        Tafiya ta fara a doguwar hanyar jan birjin da batasan iyakar lokacin ƙarewarsa ba. Ga ɗan sanyin safiya na busawa kaɗan-kaɗan.       Tayi tafiya mai nisa ciwon cikin nan da batasan dalilinsaba a kwana biyun nan ya ƙara turniketa. Ƙarƙashin bishiyar dalbejiya ta samu ta zauna. Taci murƙususnta da kuka na wani lokaci kafin ta tashi ta cigaba da tafiya. Zuwa lokacin ƴan mashinan garinsu nata fitowa ɗai-ɗai da fasinjoji akai.        Kafin ta gama ankara rana ta ƙwalle. Ga yunwa na cigaba da ragaɗar hanjin cikinta. Haka ta cigaba da jurewa tana jan ƙafafu tamkar mai tsohon ciki. A lokacin da dukkan wani ƙarfinta ke gab da ƙarewa ne ta hango rufin ginin makarantarsu dake da matuƙar tsaho fiye da duk gine-ginen gidajen garin. Ta saki murmushin yaƙe idanunta dake ganin duhu-duhu na lumshewa. Sai faman sauke ajiyar zuciya takeyi da sauri-sauri. A hankali hajijiya ta fara juya mata hanyar, saiko gata ƙasa yaraf babu numfashi..........✍ *_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 _Na Safiyya Huguma_ *_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖 _Hafsat Rano_ *_★ DALAAL_*💝 _Na Miss xoxo_ *_★ UBAYD MALEEK_*💓 _Na Mamu gee_ *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 _Na Bilyn Abdull_ Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 *_08085405215_* IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   0903 234 5899 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 *_Typing📲_* *_😭MAKAUNIYAR ƘADDARA!!😭_* *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* _ZAFAFA 5 NEXT LEVEL_ Page 2 ............Saukar ruwa mai bala'in sanyi a jikinta ne ya sakata farkawa a firgice. Ta zabura zata ƙwalla ihu taji an riƙeta.        Kafin ta gama tantance abinda ke faruwa muryar da bata gama sanin ta wacece ba ta tsinkaya yana faɗin, “Haba innar Karima, yanzu yarinyar da aka tsinto cikin wannan halin akema wannan izayar haka? A ganina kamata yayi musan halin da take ciki ai k.......”         A fusace, cikin katseshi tace, “Sallau! Ince dai kai ka gama naka?. Kokuwa bayan taimakon kawota gida akwai wata a ƙasa ne a tsakaninku?”.        Da sauri Sallau ya dubi tsirarun mutane da tarin yara da suka biyo bayanshi saboda ganin a yanda ya shigo da yarinyar cikin garin tamkar mara numfashi.       Yace, “Haba! Haba! Innar Karima. Da ga taimakon yarinya kuma sai ki fassarani da neman laƙamani laihi. Naga dai na maki bayanin komai ban ɓoye maki a yanda na tsintota bisa hanyar shigowa gari a yashe ƙasa bata lunhwashi ba, kuma agaban kowa na hiɗi”.        Baki ta ƙyaɓe tana wani juya idanunta abin tsoro, ta nuna masa hanyar ƙofa, “To ga hanya kama gabanka. Taimakonka kuma angode ince dai shikenan daɗa”.      Cike da takaici Sallau ya buga ƙafarsa ya fito a gidan yana huci. A ransa kuwa sai tsinar Inna ya keyi akan mugun halinta da kowa ya sani a ƙauyen nasu.       Duk mahawarar dake faruwa a tsakanin Inna da Sallau tana kwance a gefe cikin laimar ruwan da inna ta jiƙeta tana murƙususun azabar ciwon ciki. Yayinda yara da waɗanda suka shigo a manyan ke tsaye cirko-cirko na kallonsu. Matan makwafta nason taimakon yarinyar amma tsoron Inna ya hanasu iya yin komai, dan ba ƙaramar jarababbiya baceba kowa ya sani.      A wannan halin wani dattijo ya shigo gidan ɗauke da icce saman kansa, sai gatari dake rataye bisa kafaɗarsa ta haggu. Tun a ƙofar gida yaci karo da tsirarun mutane, hakanne ya sakashi shigowa gidan da matuƙar sassafa. Ya jefar da iccen gefe guda saboda ruɗewar sake ganin wasu mutanen da sukafi waɗanda ke a waje yawa. Kafin yace wani abu nishin kukan yarinyar ya sashi saurin kai dubansa gareta.       “Subahanallahi Zinneerah!!” ya faɗa a firgice yana nufar inda yarinyar take. Duk da yanda jikinta ya ɓaci a laimar ruwan daya gauraya da jar ƙasar garin bai fasa saka hannu ya kamota ya ɗago ba. Cike da firgicin da yafi na farko yake sake faɗin, “Zinneerah! K Zinneerah mike hwaruwa dake haka? Daga ina kika hito ne?”.        Ina Zinneerah batasan yanayi ba, sai faman cigaba da murƙususunta takeyi a jikinsa. Duk ta naɗe masa ƙwaɓaɓɓiyar ƙasar jikinta akan matacciyar rigar yadinsa.      Duk yanda yaso Zinneerah tayi magana bai samu hakanba. Su kuma waɗanda ke tsaitsaye a gidan tsoron Inna ya hanasu cewa komai. Yayinda ita kuma taketa sakin ɗanwakenta a tukunya tamkar batasan da shigowar mai-gidan ba ma.      Tsahon lokaci suna a wajen har ciwon ciki ya lafama Zinneerah tai luf a jikin dattijon tana sauke tagwayen ajiyar zuciya. Da tsananin damuwa tattare da muryarsa yace, “Sannu Zinneerah, sannu kinji”.        Kanta ta ɗago a karon farko ta dubesa, sai kuma ta yunƙura da ƙyar ta tashi zaune tana faɗin, “Baba!” kafin ya bata amsa ta maida dubanta ga sauran mutanen dake a gidan har zuwa kan Inna dake gyara wutar ɗan-wakenta. Ta duba jikinta matsanancin tsoro na bayyana mata a kan fuska.      Kafin wani ya samu damar cewa komai Inna ta miƙe a hasale, dan takai matuƙar cika da haushi. Bakin wuta ta ɗauka tana miƙewa. Kafinma tace wani abu an fara rige-rigen fita a gidan da gudu dan kowa yasan hali.     Da sauri Zinneerah ta kalli dattijon dake mata kallo irin na tsananin damuwa. “Baba yunwa nakeji”. Ta faɗa tana mai raba hankalinta biyu a kallonsa da kallon Inna dake masifa tana bin mutane da bakin wuta.        Duk da tsoron Inna dake cike fal da ransa bai ƙi amsa ɗiyar tashi ba. Ya miƙe da rawar jiki yana faɗin, “To Zinneerah jirani”.        Buta ya ɗauka ya nufi bayinsu, yana shiga ya ajiye butar yana waige-waige. ta inda katangarsu ta faɗi akai dannin itacen geza yay dabarar ficewa a gidan, yasan mutum ɗaya ce zata iya zuwa gidan ta taimaki Zinneerah daga halin Asabe. Duk da yunwar dake cin hanjin cikinsa shima bai fasa ɗaukar hanya ba zuwa ƙauyen Sanni inda babbar ɗiyarsa ke aure. Da yake babu nisa sosai, rafi ne ma kawai ya rabasu.       A ƙasan ransa yana matuƙar jin ƙuna da zafin halin da ɗiyarsa Zinneerah ke a ciki, sai dai tsoron matarsa Asabe bazai barsa yay maganaba. Shi kansa yaga ƙarfin halinsa ainun a yau da har ya iya fuskantar Zinneerah kai tsaye, sai dai yasan shirun da Asabe tayi bana alkairi bane dan cike take da shi.      Da wannan tunanin Baba ya iso ƙauyen Sanni.        Ƙauyen Sanni ƙaramin garine da ko rabin rabin Ƙauyen Danya bai kaiba. Gaba ɗaya gidajen garin basufi goma sha biyarba. Sai dai a kowanne gida zaka samu family house ne mai tarin iyalai.  Kasancewar irin wannan lokacin na rani babu yawan maza duk sun tafi neman kuɗi birni sai mata kawai a gari da yara. Tun daga ƙofar gidansu Gajeje dake jerin gidaje uku da sukafi kowa yawan iyalai a ƙauyen ake jiyo arerewar mata da ihun yara da luguden daga.     Baba yaɗan matsa ga yaran dake a gindin bishiyar ƙatuwar ceɗiya suna wasan langa. Ɗaya daga cikinsu ya taɓa yana faɗin, “Ɗana ko Gajeje na ciki?”.        Wanda aka taɓa ɗin ya sauke ƙafarsa dake a ɗane yana kallon dattijon. “Eh baba tana nan, yanzuma suka gama sussukar maiwa anan”.      “Yauwa dan ALLAH sanar mata ana sallama”.         Kamar yaron bazaijeba sai kuma ya kwasa da gudu yana faɗin, “Kai Garzali ku jirani indawo”.       Ba'a wani ja lokaciba wata mata ta fito, a yanayinta zaka ɗauka wani shekarune da ita masu yawa. Sai dai a kallon idanu zaka samu amsar ƙarancin shekarunta. Wahalar rayuwace kawai ta maidata tamkar mai shekaru arba'in a duniya. Ta gyara gyautan zanen data yafo a kanta tana washe baki da fadin, “A'a lale-lale. Baba kaine tahe a tsakkiyar ranarnan haka?”.        Baba dake duban ɗiyar tashi daso da kauna ya murmusa yana jinjina mata kansa, “Nine kuwa tahe Gajeje”.       “To sannu da zuwa Baba. Bara na kawo maka tabarma da ruwa ko...”     Saurin dakatar da ita yayi ganin zata juya. “A'a Gajeje dakata, tahiyarnan tawa bata lahiya bace. Dan haka zama bai ganni anan ba”.      Cike da tsoro tace, “Wani abune ya faru kuma? Ko Innace tsiyar tata ta motsa yau?”.       “To ba'ace ba dai Gajeje. Ƴar uwarkice ta dawo cikin wani yanayin da sam ban gane masaba. Yanzu haka na barota a gida tana maɗoɗowar yunwa. Gashi kuma naga ran Asabe a ɓace yake, dan ko uffan taƙi hiɗi mani, kinsan kuma bata barin kowa ya hiɗi yanda akai ko?”.        “Wai Baba kana nihin Zinni ce ta dawo gida?”.     Da damuwa ƙarara a fuskarsa ya ɗaga mata kai.        Zanen kanta ta gyara kawai rai ɓace tace, “Muje baba. Dan inna zumace sai da wuta. Karta sake bi ta hanyar da tabi a baya ta maidata wani gun kuma”.       Sosai yaji daɗin hakan. Dan haka suka kamo hanyar komawa Danya suna tattaunawa akan matsalar Inna Asabe da halin da Zinneerah ke ciki a dalilinta. ★★★          Baba da Gajeje sun iske ƙofar gidan a yamutse da hayaniyar Inna da wasu a mazan maƙwafta da suka kasa haƙuri suka tanka mata akan dukan Zinneerah da tahau yi tun bayan barin Baba gidan. Yayinda Zinneerah ke gefe tana murƙususun ciwon ciki.      Ran Gajeje a ɓace da halin mahaifiyar tasu ta shiga cikin rikicin da ƙyar ta lafar da kowa. Kusan minti talatin aka samu wajen ya nutsa. Inna ta shiga gida mutanen dake a ƙofar gidan kuma kowa ya kama gabansa ana zagi da ALLAH wadai da halin Inna Asabe na rashin tausayi.       Sai a lokacin Gajeje ta samu damar kama Zinneerah dake kwance gefe buɗu-buɗu da ƙasa tamkar an tonita a rami. Gidan ta shiga da ita, Inna zata fara sabuwar jaraba Gajeje ta haɗe fuska tana faɗin, “Innarmu! Innarmu!”.      Shiru tayi saboda sanin halin babbar ƴar tata itama. Sannan duk yanda takai ga hawa akan masifarta da Gajeje tayi magana bata iya cigaba saboda wani dalilinta daba kowa ya gama saninsa ba.        Itama Gajejen bata sake cewa komaiba sai kallon Tinene ƙanwarta tayi. “Ke Tinene ɗaukamin karauni a ɗakinku”.      Baki Tinene ta cika da iska tana ƙunƙuni, sai dai kuma babu damar ƙinyi. Fuuu ta shige ɗakin kwanansu da ada can shine ɗakin mahaifiyar Zinneerah kafin tabar gidan. Wata tsohuwar tabarmar karauni ta ɗakko zuwa gindin bishiyar mangwaro dake a kusan tsakkiyar gidan. Zinneerah na zaune an jinginata da bishiyar, Baba na daga tsaye gefenta kaɗan yana kallonta dayin hawayen zuci. Sai Gajeje dake can kusa da Inna a gaban murhu taɗan kara ruwa jikin wutar ɗan waken Inna na saidawa dan yay ɗumi.             Gidan yay tsit babu mai cewa uffan duk da kuwa kowa nada abin cewa a bakinsa. Musamman ma Baba, sai dai tsoron matarsa Inna bazai barsa iya furtawaba duk da tsantsar tausayin ƴarsa dake ransa.       Gajeje ta juye ruwan ɗumin a wani roban wankansu ta sirka takai banɗaki tazo ta kama Zinneerah ta miƙar. Har banɗaki ta kaita da kanta. Bata wani tsaya jan zance ba ta ɗaurayema Zinneerah jiki da kanta duk da kuwa tanata mammaƙewa dan nauyin yayar tasu da suke kallo tamkar uwa a garesu. Tinene ta ƙwalama kira ta kawo mata zani da riga.             Sosai Zinneerah taji daɗin jikinta da wannan wanka. sai faman sauke ajiyar zuciya takeyi da lumshe idanu. Baba dake tsaye har yanzu da kansa ya gyara mata tabarmar ta kwantar da ita.       Inna na kallonsu a kaikaice, watsama Baba wata uwar harara tayi tana yin ƙwafa. Sai dai kuma batace komaiba ta cigaba da tsame ɗanwaken ta.         Duk da Gajeje taga harar da Innar tasu taima mahaifinsu bata tankaba. Sai ma kwance gefen zaninta tayi tana ciro nera hamsin data sha ƙudindina. “K Tinene zokije nan wajen Dijen kamaye ki sayo mani kunu da suga”.      “Yaya Gajeje tallafa zan ɗauka, kina ganin Inna harta gama kwashe ɗanwake, gahi Sa'a bata dawo ba, Karima kuma na rimaye”.       Wani mugun kallo gajeje ta watsamata, a hasale tace, “Ni kike hiɗima haka Tinene?”.       Kafin Tinene ta bata amsa Inna ta dubesu a hasale. “Wai Gajeje miyasa ke baƙya son zaman lahiyane? Ai gaskiya Tinenen ta hiɗi, inke idonki bai gane miki na kwashe ɗanwakenba”.        “To amma Innarmu koda shirin ɗaukar ɗanwaken take nanda gidan Dije ne zai gagareta zuwa ta sayo mani kunu? Kenan iya shegen da sukema kowa nima ya hwara zuwa bisa kaina?”.        Yanda Gajeje ke magana a hasalene ya saka Inna cewa, “K Tinene amshi ki sayo mata, ni bansan wani kace-nace”.       Tinene na faman tunzura baki da ƙunƙuni tazo ta amshi hamsin ɗin ta fice bayan ta ɗauki wani tsohon kofi. Babu jimawa sai gata da kunun kuwa. Kusan tare suka shigo da Sa'a ɗauke da ƙaton botiki mai ɗauke da sauran gyaɗa da riɗi da taje talla.       Da sauri ta ƙarasa shigowa tana fadin, “Kai, Kai, Zinni! Yaushe kika dawo?”.        Murmushin ƙarfin hali Zinneerah taima Yayar tata da itama ke ƙaunarta a gidan, sai dai kuma ta kasa bata amsa sai Yaya Gajeje ce dake zuba suga a kunun da Tinene ta sayo ta bata amsar.     Kafin Sa'a da hawaye suka cikama ido tace wani abu Gajeje ta maida hankalinta ga Tinene. “K samo mani lidde”.       “Mu bamu da lidde nan gidan”. Cewar Tinene tana murguɗa baki.     Jikake bamm! A goshin Tinene, Gajeje ta jefa mata murfin kwano dake kusa da su.      A take ta zube ƙasa ta fara kururuwar ihu kamar wandda aka kashe. Inna ta saki kwanon yaji a ƙasa ta nufi ƴar tata da sauri. “Gajeje kashemin yarinya zakiyi akan wannan sheɗaniyar yarinyar data gudu yawon tambaɗarta?”.       “Kaɗanma na mata Innarmu”. Gajeje ta bata amsa rai ɓace.       Cikin raɗa-raɗa Sa'a data je ta ɗakko mata ludayin tace, “Yaya Gajeje ki ƙyalesu dan ALLAH, karki tahi gida a huce kan Zinni. Kindai san halin Innarmu ai”.      Shiru Gajeje tayi bata tankaba. Baba ma dake tsaye har yanzu bai tanka musunba, hasalima hankalinsa na kan Zinneerah da ke shan kunun cike da zalamar yunwar da takeji.       Zuwan Gajeje gidan ya matuƙar taimakawa wajen bama Zinneerah kulawa. Inda kuma ya katange duk wani bala'i da masifar dake cin Inna a rai. Dan bayanma ta kammala saida ɗanwakenta su Tinene sun ɗauka wani sun wuce talla zani ta ɗauka ta fice gidan wai taje barka wani ƙauye dake can gefensu shima.      Hakan yama baba daɗi sosai. Dan koba komai sa samu damar jin yaya akai Zinneerah tabar gida a kwanaki ashirin da shida da suka shuɗe, da kuma yanda akai ta dawo musu yau a wannan halin?.           Suna zaune shi da Gajeje suna tattaunawa akan hakan Zinneerah dake barci tun ɗazun ta farka a firgice da ciwon ciki. Duk kanta sukayo suna tambayar ko lafiya?. Bata iya amsasuba sai da ya lafa mata.     Ta share hawayen dake sauka a kumatunta. “Yaya Gajeje cikina kemin ciwo”.      Basu kawo komai a ransuba sai yunwa. Dan haka Gajeje tace, “Zinni yunwace nasani. Sannu kinji. Idan zaki iya tashi kiyo alwala kiyi sallar azahar da la'asar sai kizo ga abinci kici”.            “Zan iya yaya Gajeje”  Ta faɗa tana maida kallonta ga baba dake kallonta cike da raunin zuciya dana idanu.    “Baba ina wuni”. Murmushin ƙarfin hali yay mata da shafa kanta. “Lafiya lau Uwata yaya jikin?”.       “Da sauƙi baba”. “To madalla. tashi kiyi sallar maraice na ƙara yi”.       Bata musaba ta miƙe. Jin gidan shiru ya sata sanin Inna da su Tinene duk sun fice. Hakan ya mata daɗi. Alwala tayo tazo ta wucesu zuwa ɗakin kwanansu. Babu abinda ya canja a ɗakin nasu sai ma shirgin kayan dauɗar su Yaya Sa'a. Dama itace mai kimtsa ɗakin dayi musu wanki. Kayan taɗan ture gefe ta tayar da salla cike da ƙarfin hali dan batajin daɗin jikinta gaba ɗaya. Duk da sallar ba'a cikin tsari akayitaba tadai gabatar ta sake komawa wajen baba da yaya gajeje.           Abinci yaya Gajeje ta fara bata taci. duk da yunwar da take ji har yanzu taci abincin a nutse dan sam dama ita bata da garaje ko gaggawa. Bayan ta kammala ta wanke hannu ne Yaya Gajeje ta ce, “Zinni kinga marece yayi inason na koma gida nabar su Rabi'u. Munason ki nutsu ki faɗa mana yaya akai kika bar gida ne batare da sanin kowaba? Ina kuma kikaje?”.           Duk da ƙarancin shekarunta hakan bai hanata jin ɗaci ba a ranta. Ta share hawayen dake rige-rigen zubo mata tana gyara zama. “Baba wlhy ban gudu ba. Bayan tafiyarka kasuwa sai I.......        Jin tayi shiru tana kallon hanyar shigowa yasa Baba da Gajeje saurin kallon wajen suma. Inna ce ke shigowa cikin gidan tamkar wadda aja jeho.      Ganin yanda duk suka watso mata idanu ya sata fara magana a harzuƙe. “Halan cin nama na akeyi kuka watso mani idanu haka?. Wani annamimancin kike hiɗi masu a kaina ko?”.      Ta ƙare maganar tana watsama Zinneerah mugun kallo.         Gajeje ta dubi Baba da yay ƙasa da kansa. ta dubi Zinneerah da itama kan nata ke a ƙasa tana hawaye. Wani irin tausayinsu da jin zafin mahaifiyar tasune ya ɗarsu a ranta, musamman yanda take ƙasƙantar musu da mahaifi a gabansu duk da tsufansa. taɗan girgiza kanta tana dubanta. “Amma Inna miya kawo wannan zancen daga shigowarki? Yarinyar da ke cikin halin ciwo wane kuma munahincinki zatayi?. Ni a ganina kamata yayi kema ki shiga jerin masu murna da dawowar Zinni gida kodan tashin hankalin da muka shiga na rashin sanin inda take a kwanaki ashirin da shida ɗin nan”.        “Tunda uwatace ta ɓata ko? Kune kuke ɗauka ɓata tayi dama ai, yarinyar da ta tafi yawan taɓaɗanta data saba har kuke damuwa da inda taje. Inda ba guduwa taiba wane shege ne ya dawo da ita yanzu da ƙahwarta?. adai jura zuwa rafi, wataran muna zaune za'a shigo mamu da ɗan dakan kuka na tabbacin yawon tazubar....”     Tsam baba ya miƙe batare da cewa uffanba ya fice gidan. Itama Gajeje rai ɓace ta miƙe tana magana cike da rawar murya. “Innarmu wannan hurucin naki dai kau sam bai dace ba. Dan koba komai itama Zinni ɗiya take garegi, yanda kuwa take mace haka Sa'a da Tinene da Karima suke mata. Baƙya tsoron mugun alkaba'in da kike hiɗi gareta ya dawo bisa kanmu ne”.       Wani mugun kallo Inna taima Gajeje. Kamar zatai magana sai kuma tai shiru. Itama Gajejen bata sake tankawaba sai miƙar da Zinneerah da ke kuka tayi suka shige ɗaki. Sai da taga ta kwanta sanann ta fara magana. “Zinni bara naje gida, insha ALLAHU gobe da hwarar sahiya zan dawo, dan akwai raɗin suna gidan malam mato dama da zamu shigo. To daga can nan zan wuto na yini. Ki ƙara haƙuri da halin Innarmu watarana sai labari kinji”.        Kai Zinneerah ta ɗaga mata tana share hawaye. Muryarta na rawa tace, “Nagode Yaya Gajeje”.     Murmushi kawai Gajeje tayi da shafa kanta ta fito a ɗakin. kai tsaye ɗakin Inna ta nufa dan tanaso suyi magana.............✍       *_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 _Na Safiyya Huguma_ *_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖 _Hafsat Rano_ *_★ DALAAL_*💝 _Na Miss xoxo_ *_★ UBAYD MALEEK_*💓 _Na Mamu gee_ *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 _Na Bilyn Abdull_ Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 *_08085405215_* IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   0903 234 5899 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 *_Typing📲_* *_😭MAKAUNIYAR ƘADDARA!!😭_* *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* _________________________ Duk wacce batayi anfani da sabulunnan ba anbarta abaya acan karshen bayama kuwa duk Mai tantama akan sabulai nagyaranjiki cewa basa Aiki toh yacire mg's domin kankat ne insha Allah babu Wanda yayi anfani dasabulunmu yace baiyi ba koyaushe mg's sai sanbarka amare da uwargidaye hardama yanmata kuhanzarta kusamu naku ba karya domin bama cika Baki kugwada kubada labari da bakunanku sabulu daya tamkar dubu wadandama basasan using cream sabulun mg's herbal whitening black soap yawadacemuku jikinku zaiyi kyau koyaushe kukasance clean cikin kamshi Kuna glowing koda bakusa turare ba🤗 Kayanmu bana bleaching bn organic ne sunagyarajiki fiye da tsammaninku zaifiddomuku da ainihin natural beauty dinkine Wanda yagwada shi zaitabbar amare kuyi kokari kumallaki mg's domin baruwanku da zuwa adirjemuku jiki zakuga yanda fatarku zata dinga walwali Ina masu pimples Tabo(spot) Sunburn dama dukwani matsalar fata kuyi kokari kunemi soap dinnan before 2weeks zaisharemuku hawaye kuzama abun kwatance Sister's masu nankarwa kuma kunemi soap dinnan Yana rage nankarwa sosai🧖🏻‍♀️duk me shakku tayi kokari tagwada mg's insha Allah bazakiso rabuwa dashi ba Akwai maisa haske Amma kayanmu nafada bana bleaching bn zaifiddomiki d ainihin halittarkine yagoge dukkan dattin jiki Akwai Kuma Wanda zaimiki maintaining skin dinki yasaki fresh fatanki tazama kalar hutu Pls bamacika Baki you HV to try it and see for yourself 100%tested nd trusted Soap price:3k Location:kaduna buh munaturawa ko Ina Amma delivery is not free Maiso kindly message 08062991549 Call 08064532391 Note:Babu inda zakusami mg's herbal whitening black soap sai a number dinnan bairiga yakai market b inyakai we will let you know buh as for now wnn numbern ne kawai🙏 Maiso yahanzarta before yaji sold out akwaisu available now insunkare you HV to wait akawo so maiso yahanzarta🙏adade anayi sai gsky🤭🤝 Mg's skincare Mg's bakery You can still order ur birthday cake, cupcake,slice cake,meat pie,shawarma,samosa nd spring rolls for ur event @mg's bakery Kindly call or chat 07046881166 07067210195 08062991549 Masu bukatar abayas,takalma da jakunkuna,ashobe,laces d atamfofi, materials nd the rest 07046881166 👏🤝 _________________________ _ZAFAFA 5 NEXT LEVEL_ *Page 3* ............Gajeje bata wani jima ba a ɗakin Inna tafito rai ɓace alamar dai wani rikicin suka sake tafkawa. Tana fita a gidan kuwa Inna ta fito a matuƙar hasale itama.     Ɗakin su Zinneerah ta shiga. Zinneerah dake zaune tana hawaye har yanzun sai jin saukar lafiyayyen mari tayi. Zabura tayi zata ƙwalla ihu Inna ta daka mata tsawa.       “Munahika yimani shiru kona lallasaki. Dan uban daya haiheki sheri da kikai shirin ƙullamani ashe? Wa billahillazi koda wasa kika sanarma wani a yanda kika bar gidanga sai na lahira ya hiki jin daɗi. Idan kuma kiji ƙarya don ALLAH ki hiɗi masu yanda akayi. Aradun ALLAH ubanki ma sai na ci masa bura-uba bamake kadaiba dan buhun ubanki. Lalatacciya kawai mai shegen nunkuhurci irin na uwarta”.        Ita dai Zinneerah kuka kawai take jikinta na rawa dan tsoron Inna da takeyi. Sai da ta gama zazzage mata ruwan bala'i iri-iri sannan ta fice a ɗakin.     Kuka kam Zinneerah ta shashi matuƙa. Ga ciwon da cikinta kanyi lokaci zuwa lokaci. Dawowar Sa'a gidan da kayan ɗanwake ta samu tsagaitawar kukan saboda lallashinta da Sa'a ta zauna yi. Ganin yanda Sa'a ta nuna matuƙar damuwarta yasata shanye sauran kukan nata dan ba yaune farauba a gareta ga halin Inna matar ubanta. WASHE GARI.        Da safe kamar yanda ta saba kafin tayi tafiya tanayin sallar asubahi ta fito tsakar gida ta hau shara. Duk da sanyin dake busawa na sanyin safiya haka taima tsakar gidan ƙwal da shara, ta gyara turken dabbobin Inna ta zuba musu sabon abincinsu. Sannan tazo ta fara haɗa wuta. Cikin dauriya take komai, dan wani irin zazzaɓine ke ratsa dukkan ɓargon jikinta a hankali. Haka ta cigaba da daurewa harta kammala dukkan ayyukanta wajibabbu a gidan.      Babu wanda ya fito a mutanen gidan sai can gyallowar rana. Sa'a ce ta fara fitowa tana mata sannu, sai ga Tinene ta fito itama tana mika da hamma dan sai yanzu zatai sallar asuba. Can sai ga baba ya shigo gidan, da alama tunda ya fita salla masallaci bai shigoba sai yanzun.      Dukawa sukai har ƙasa ita da Sa'a suna gaishesa. Ya amsa idanunsa aka Zinneerah da ya kwana da damuwarta a cikin ransa. Murya ƙasa-ƙada dan kar Inna taji yace, “Zinneerah yaya jikin naki?”.       “Da sauƙi Baba”. Ta amsa kanta a ƙasa.     Kafin ya ƙara cewa wani abu Inna ta fito wuff. Da sauri yabar wajen saboda wani shegen kallo mai kama da harara data watso masa. Taja tsaki tana duban Zinneerah dake durƙushe har yanzu.         “Ki tashi ki ɗebo mani ruwan rahi dan randunan gidanga duk babu ruwa. Kuma na rahin yamma nakeso dan ruwansa yahi garɗi da haske”.      “To inna. Ina kwana?”. A takaice ta amsa mata tana karasowa wajen murhun inda wutar da Zinneerah ta haɗa ta kama sosai.       Fuskar Sa'a babu walwala tace, “Inna dakin barta sai anjima rana ta ƙara dagawa sama, kinga akwai sanyi garin sosai”.          “To uwata, yanda kikace ai haka zanyi”. Inna ta faɗa a hasale..       Shiru Sa'a tayi, dan tasan gatse Inna tai mata.      Zinneerah dama bata tsayaba, tuni ta ɗauki botikin fenti da hijjab ta nufi ƙofar fita cike da dauriya. Hakan ba sabon abu bane a gareta, shiyyasa fita ɗibar ruwan a yanzu bai dametaba. Kawai yanda takejin jikinta babu daɗine matsalarta. Amma haka ta nausa kanta hanyar jeji domin ɗebo ruwa. Harta isa babban rafinsu da su kansu basusan iyakar inda ya tsayaba bata haɗu dako kare ba. Ta ajiye botikin a gaban rijiyar da aka gina a tsakkiyar yashi wadda bawani zurfine da itaba. Hasalima a gabanta ake duƙawa asa kwano a kwarfo ruwan dake kwance. Bismillah ta ambata tana saka kwanon cikin ruwan, sai da ta kwashe na ciki tas ta watsar waje sannan ta jira ya sake taruwa ta diba a botikin nata. Bayan ta cikashi taf ta miƙe da ƙyar ta ɗora bisa kanta.          Koda tai sallama Sa'a ce kawai dake wankin baki da gawayi ta amsa mata. Inna ko dake bakin murhu tana yanka tuwon dare daya rage tana jefawa a ruwan data saka a wuta ko kallonta bataiba. Hakama Tinene dake gefen Innar tana shan koko.       Sai da ta wanke duk randunan gidan guda huɗu sannan ta juye ruwan ta Sake komawa. Haka ta dinga kai kawo tsakanin gida da rafi ɗibar ruwa. Tun bata haɗuwa da kowa har mutane suka fara fitowa. harma da irinta masu zuwa sakkon ɗibar ruwan na rafi. Duk wanda ta haɗu dashi gaisuwar mutunci ce tsakaninsu. Har ALLAH yasa ta kammala gaba ɗaya.         Zuwa yanzu Inna ce kawai a gidan, Baba ya fice wajen sana'arsa. Sa'a da Tinene kuwa sun ɗauki tallar gyaɗa da Riɗi da itama tasan tata tallan na jiranta ne.      Sai da ta gama ɗauraye ƙafafunta da sukai futu-futu da ƙura tazo inda Inna ke tankaɗen garin ɗan-wakenta.      “Inna na gama ɗibar ruwan”. Yanda tai maganar murya na rawa yasa Innar kallonta. Duk da yanayinta ya nuna bata jin daɗi hakan baisa Inna tambayarta ba. Sai ma sake tsuke fuska tayi da faɗin, “Zauna inason magana dake”.      Babu musu Zinneerah ta zauna duk da ranta fal tsoro.          Ƙare haɗe fuska Inna tai tana dubanta da ƙyau. A tsawace tace, “Miya maidoki garinga?”.        Sosai gaban Zinneerah ya ƙara tsananta faɗuwa. Murya na rawa tace, “Inna sune suka koroni. Sunce basa buƙatar baƙauya irina. Kuma saida suka shinhiɗa mani uban bugu da aibantani kahin su bani jikka biyu da rabi su sani a mota....”       “Munahika, halan wata tsiyar kika ƙulla masu acan? Saboda kina buƙulu da abunda zan samu na hassahi daga kuɗin aikin naki?”.       “Wlhy Inna ba haka bane. Matar gidance bata sona dai na rantse”.        “Ruhwa mani baki dan bantan ubanki. Ai hajji Lanti zatazo ne, zanji gaskiyar zance a gareta. Wa billahillazi naji saɓanin abinda kika hiɗi yanzu ina halakaki na halaka banza wohi babu mai sanin yanda akai. Ƴar banza, kinhi son mu zanna ga ƙugunki ga nawa a gida. Sabidda kina kishi dani tunda uwarki bata gida? To mu zanna ga hili ga mai doki ai. Dan uban mutum yayi idan yana iyawa dani ko. Tashi ɓacemin a ido kahin naita tsinarki har se zaman Danya ya gagari ubanki ma bake kaɗai ba”.        Mikewa Zinneerah tai tana shartar hawaye. Duk da cin zarafi ga inna ba yaune farauba a gareta. Sai na yau ɗin yay mata zafi ainun. Karon farko taji tana kwaɗayin son sanin inda mahaifiyarta ke rayuwa a yanzu.     Ɗakin kwanansu ta shige, ta faɗa akan yamusashshiyar katifar da Yaya Sa'a da Tinene ke kwana. Dan ita bisa tabarmar karauni take kwana kamar yanda Inna take buƙata. Dauɗaɗɗun kayan dake gefe ta jawo ta shiga rufawa a jikinta saboda sanyi da takeji.      Sosau ta ringa rawar sanyi tana sambatun zazzaɓi. Har tsahon lokaci babu wanda ya shigo ɗakin. ba kuma ta ƙarajin motsin Inna ba. A haka barci yay gaba da ita mai nauyi.       “Zinni!! Zinni!!. Wai dan buhun ubanki baki jina inata kware baki?”.      A firgice ta tashi zaune jin irin kiran da Inna ke ƙwalla mata tamkar ana yaƙi. Ta amsa a kasalance tana ƙoƙari janye kayan data nausama kanta gefe dan ta samu damar mikewa.        Fitowar tata yay dai-dai da shigowar Yaya Gajeje gidan da sallama. Inna ta sake tsuke fuska tana kallonta. sai kuma ta ɗauke kai ta maida ga Zinneerah dake fitowa tana rawar sanyi da yamutse fuska alamar bata da lafiya.       “Oh sannu ƴar gata! Ina nan tsaye ke kina can kina jan nashari a ɗaki? To kizo ki haɗa mani wutar ɗan wake kar rana tayi..”       Da sauri Yaya Gajeje tai saurin tare numfashin Inna, “Haba Inna, wane haɗa wutar ɗanwake kuma kike magana haka? Diba kiga yanda take rawar ɗari da alama bata da lahiya”.        “Mtsoww!!” Inna taja tsaki. Kafin ta cigaba da magana a hasale. “To ina ruwana da ciwon nata. A yanzu ma wagga duniya waye ke da lahiyar. Gajeje ki hita idanuna, karki kaini maƙurar randa zan maki bankaɗa wallahi”.       Murmushi Gajeje tai tana kaiwa zaune. Cikin kwantar da murya tace, “To inna idanma kin mani bankaɗa ai kin isane tunda kece kika haiheni. Ni dai kin sanni ban ganin gaskiya na riheta ai. Amma dai kiyi haƙuri ni bara na haɗa miki wutar tunda ita batajin daɗi. Harma sakin danwaken yau nice zan miki Innarmu kwantar da hankalinki”.     Baki taɗan taɓe. sai dai batace komaiba. Hakan yasa Gajeje fahimtar taci nasara. Tai murmushi da tura hannu a zaninta ta ciro leda dake a lalitarta ta bujen ciki. Goro ne da alawa da biscuits guda biyu ƴan goma-goma. “Innarmu ga kayan suna”. Tai maganar tana miƙa mata.       Ɗan sakin fuskarta tayi da miƙa hannu ta amsa. “Yo kuma ƙya bani duka. Su su Rabi'u fa?”.       “Karki damu na ba Salame ta kai musu nasu suma. Wannan nakine. Nima Agali ya bani shi bayan mun hito”.       “To, to maddala. Ni bamma sami leƙawaba yau na tashi da ƴar mashashshara ne. Sai zuwa anjima zanje nai masu an raɗa suna. Miye sunan ɗiyar ne?”.        “Ai Hadiza aka samu, sunan Innar Bilkin aka saka”.      “Tofa ɗigifi. Shi yanzu duk yawan gidansu ya rasa wazai saka sai sunan uwar matarsa?”.       Ƴar dariya Gajeje tayi tana yafito Zinneerah dake tsaye rakuɓe jikin bango da hannu. “Inna kenan, ashe babu daɗi Lawal ya sakama Ummita sunanki shima”.      Shiru tai bata tankaba. Dan an ƙure tsoguminta kenan.     Zinneerah ta zauna tana gaida Gajeje. Cike da kulawa ta amsa mata da kai hannu a jikinta. Jin uban zafin ya sata ambaton, “Ya subahana. Zinni ai masassara ce a jikinki sosai. Kin karya dai ko?”.       Ƙasa Zinneerah tai da kanta tana haɗiye hawayen dake neman zubo mata. Dan harga ALLAH yunwarma tanajinta mai tsananima kuwa. Saboda Inna batai mata tayin abinciba yasa ta haƙura.      Shirunta yasa Yaya Gajeje fahimtar bataciba ɗin. Tasan za'a rina. Dan innarsu lamarinta sai du'ai. Bata sake cewa komaiba kamar yanda itama Innar bata tanka musu ba. ta dai miƙe zuwa gindin murhun inda tukunya ke aje saman duwatsun murhun. Tuwone a ciki na dawa da aka yanka aka ɗumama. Duk ma ya zama gutsatstsari alamar masu gidan sunci. Yaya Gajeje da ranta ke mata ƙuna ta ɗauka kwano ta zubama Zinneerah, tare da koriyar miyar kukar dake gefe. Har gabanta takai ta dire tana fadin, “Maza ci na samu mai sayo miki magani nan gidan Rahine idan bata fita tallar kayan koli ba”.       Jan kwanon Zinneerah tayi gabanta, babu musu ta hau ci dan yunwa takeji sosai..      Inna dai bata sake tankawaba har Zinneerah ta gama cin tuwon nan. Yayinda Yaya Gajeje ta koma can wajen murhu tana haɗama Inna wutar ɗanwake da ƙoƙarin saka ƙatuwar tukunyar da take amfani da shi.                  Kasancewar Yaya Gajeje a gidan yau sai ta samu ƴar salama. Dan har Baba daya shigo shima ya ɗan samu sakewar bata kulawa, harda siya mata awara.      Washe gari kam Inna bata saurareta ba. Duk da ta fahimci har yanzun bata da lafiya, dan ba'a ƙulla awa biyu Zinneerah bata raɓe gefe tana riƙe cika ba alamar dai cikin na mata ciwo.       Sai dai tsabar rashin tausayi ko'a fuska Inna bata nuna ta fahimtaba, daga ƙarshema tallar riɗi da gyaɗa ta sakata ɗauka. Da Sa'a tayi magana kuwa ta hayayyaƙo mata da masifa kamar zata daketa. Dole tai shiru tana maijin babu daɗi da halin mahaifiyar tasu. ★★★             Yau satin Zinneerah ɗaya kenan da dawowa da ga Katsina. Tun Inna na zuba idon ganin Hajji Lanti ta biyo bayan Zinneerah harta fara sarewa. Dan har ranta ta ɗauki alwashin sai Zinneerah ta koma, bazata taɓa yarda kuɗin data ƙwallafa ran samu su wuceta a banza ba.        A ɓangaren Zinneerah kam a kwanakin nan daka kalleta kasan bata da lafiya. Musamman yanda ta wani rame sosai. Gashi sam bata da kuzari a jikinta. Yanda ta saba aiki ada da kazar-kazar yanzu sam bata iya hakan. Komai zakaga tana yinsane da sanyin jiki kamar mara ƙashi. Inna tayi masifar harta gaji ta barta, sai dai zagi da tsina ne tana shansa, dan ranar har marinta tayi.        Yau ma kamar kullum tana gama ɗibar ruwa da dukkan aikinta na gidan tai shirin ɗaukar tallar riɗi da gyaɗa. Tinene kaɗai ta samu a tsakar gida tana suyar wainar fulawa. Inna kuwa ta fice barka wai.       Ɗakin Inna ta shiga ta ɗakko ƙaton farin botikin da aka cika da gyaɗa da riɗi, ta sake fitowa tsakar gidan. Cike da sanyin murya tace, “Tinene idan Inna ta dawo ki hiɗi mata na wuce”.       Kallon banza Tinene tai mata ta ɗauke kanta. Cike da rashin mutunci tace, “Inma wannan allagiran kike mawa kima cire rai yarinya, dan aradu baki cin ko ranyo anan”.      Murmushi Zinneerah tayi kawai ta fice, dan tasan inhar ta biyema Tinene zama su iya faɗa, itako bata da wannan ƙarfin yanzu kam.          Dai-dai fitowarta ƙofar gidan nasu gabanta ya faɗi. Tai ƙasa da kanta saboda cin karo da fiska mafi daraja a zuciyarta bayan ta iyayenta. Ba kowa bane face saurayinta Babawo wanda a yanzu ya maida akalar neman auren nasa kan yayarta Karima da yaya Sa'a ke bimawa. Babawo ya sota tun bata san kantaba. Da farko matsin rayuwar data tsinci kanta a hannun Inna dalilin rashin mahaifiyarta a gidansu Babawo yake tausaya mata. Shine silar cigaba da karatunta bayan gama firamare , shine ya tsaya tsayin daka harta shiga makarantar gaba da firamare (Secondary), tana aji ɗaya wani kawunsa ya zo ya tafi da shi kaduna. Bai dawo ba sai da ya shekara. Kamar yanda ta ɗokantu da zuwansa haka shima ya ɗokantu da ganinta. Yazo mata da tarin tsaraba, tare da burin iyaye su shiga akan maganar aurensu, a cewarsa data kammala aji uku na sakandire zasuyi aure. zai wuce da ita can kaduna sai ta cigaba a gidansa har sai taga ƙarshen biro. Hakan yama Zinneerah daɗi a zuciya da ruhi, sai dai kuma a kwana biyu da zuwan Babawo labarin ya canja alƙibla. Dan kuwa bai komaba sai da tsuntsun soyayyarsa ya tashi daga kanta ya koma kan yayarta Karima yar wajen Inna ta uku. Ƙiri-ƙiri ta gaza gane kan Babawon ta, ya canja mata gaba ɗaya. Kosan ganinta bayayi. Taci kuka sosai, ta kuma shiga ruɗani, dan har ciwo tayi. Mutane sunta kace nace akan wannan al'amari, wasu na faɗin asiri Inna taima Babawo ɗin, wasu suce kuma shine dai yake ganin Karima ta fiye masa tunda ita babbar budurwace wadda akema surutu akan rashin samun miji. Dan Karima shekararta sha takwas da wasu watanni, a ƙauyen kuma sa'annin su Zinneerah sune dai-dai aure ƴan sha biyu. Amma sai dai ita ƴaƴan Inna dama sukanyi jinkirin samun miji a ƙauyen saboda mugun halinta, shiyyasa ma har yau babu wacce ta taɓa aure a nan cikin Danya. Gajeje na kauyen Sanni, Atine na can Rimaye. Sai yanzu ga Karima da Sa'a waɗanda duk sun zama manyan ƴammata. Karima nada sha takwas Sa'a na sha shida. Sai Tinene sa'ar Zinneerah itace auta.          Bayan wucewar ruɗanin canjawar Babawo da shekara ɗaya da wasu wattani, dan har manya sun shiga maganarsa da Karima sai kuma Inna ta haɗata da hajji Lanti da tai sanadin kaita birnin Katsina da niyyar aikatau, inda ita kuma ta gudo ta dawo gida........          “K! Wai baƙyaji ana miki magana”.    Tsawar da Babawo ya daka matace ta dawo da ita daga dogon tunanin da ta tafi batare data farga ba. Saurin haɗiye hawayen da suke neman zubo mata tayi tana girgiza masa kanta.          Ta ɗan risina kaɗan tana faɗin, “Kayi haƙuri Ya Babawo banji bane wlhy”.       Tsaki yaja yana taɓe baki da jifanta da wani irin mummunan kallo na tsana, wanda a da idan wani yay kuskuren yimata irin wannan kallon sai inda ƙarfinsa ya ƙare. A gadarance yace, “Kiramin Karima nace”.         Idonta ƙasa-ƙasa tana mai satar kallon yanda ya ƙara ƙyau da cikar zati tace, “Yaya Kareema bata nan, tana Rimaye wajen Yaya Atine, nima ban dawo na sameta ba”.        Tsaki yaja yay gaba batare da ya sake tanka mataba. Ta bisa da kallo cike da tsananin so da ƙaunar da take masa har yanzun. yayinda ƙamshinsa daya bar mata take jinsa mafi daraja da tsada a cikin iskar da take shaƙa. Duk da ƙarancin shekarunta zuwa yanzu tasan minene soyayya, dan shine ya rene ta akan bigirenta, tun bata fahimta harta fara ganewa da banbancewa, sai gashi rana tsaka rabuwa tazo musu bisa tafarkin MAKAUNIYAR ƘADDARAR da batasan sila ko mafarinta ba, tunda har yanzu bazata iya faɗin dalilin rabuwar tasuba balle dalilin komawar Babawonta kan yayarta.      Hannu tasa ta sharce hawayenta tana gyara riƙon botikin gyaɗa da riɗinta ta cigaba da tafiya ranta na mata zafi da ƙuna.............✍ *_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 _Na Safiyya Huguma_ *_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖 _Hafsat Rano_ *_★ DALAAL_*💝 _Na Miss xoxo_ *_★ UBAYD MALEEK_*💓 _Na Mamu gee_ *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 _Na Bilyn Abdull_ Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 *_08085405215_* IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   0903 234 5899 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 *_Typing📲_* *_😭MAKAUNIYAR ƘADDARA!!😭_* *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* _ZAFAFA 5 NEXT LEVEL_ Page 4 ...............Ƙarfe kusan biyu na rana Zinneerah ta dawo gidan a gajiye. Duk uban riɗi da gyadan data fita da shi kaɗanne ya rage a botikin. Tun a sallamar farko na shigowa gidan dukkanin ɗan guntun farin cikinta ya gushe. Ba komai ya kawo hakanba kuwa sai cin karo da Yaya Kareema datai, wadda ta dawo daga Rimaye wajen yayarsu ta biyu dake bima yaya Gajeje dan ita acan take aure.         Zaune suke a ƙarƙashin bishiyar tsakar gidan nasu sun baje kaya ita da Sa'a da Tinene. Inna na daga bakin murhu tana talgen tuwon dare. Dariyarsu suke sha cike da nishaɗi dajin daɗi.      Sa'a ce kawai ta amsa sallamar Zinneerah tare da mata sannu. Ta amsa a ɗarare tana duban Karima data haɗe girar sama data ƙasa. “Yaya Karima ashe kin dawo, sannu da zuwa, yaya kika baro su Yaya Atinen?”.         “To uwar iya, halan kin aikenine da kike lissaho mani wannan tambayoyin? Kai wagga ɗiya hi'ilinki yayi yawa wallahi, k.......”         “Haba Yaya Karima, minene laihinta anan kuma? Danta maki barka da dawowa da tambayar su Yaya Atine?”. Sa'a ta faɗa cikin katse ƴar uwar tata rai ɓace.      A fusace itama karimar ta katseta da fadin, “To kema waya saki a ciki, ALLAH ina ci maki uwa yanzun nan Sa'a. Ita ɗin uwarki ce ko mi?”.        “Ba uwata bace, amma ƴar uwatace kamar yanda take ƴar uwarku kema. Daga hiɗin gaskiya sai laihi. Ni banga abinda Zinni ta tarema wani a gidan nanba da kuke tsangwama mata, itama fa ɗiyace kamar yanda muke ɗiyan gidan. Duk da baba baya magana akan abinda ake mata na tabbatar yanajin ciwo a rans........”           Timmm!! Kake jin saukar dundu a bayan Sa'a. Ta gyantsare saboda azabar zafi tana sosawa. Inna dake tsaye a kanta tana huci tace, “Kaɗanma nai miki dan ubanki. Wa kike hiɗima waɗanan maganar banzar to? Sheɗaniya munahika. Anya kuwa nice uwarki Sa'a? Kodai kema Hauwar ce ta haiheki taimin mucanje ban saniba?”.          Baki cike da iska Sa'a tace, “Amma inna dan na hiɗi gaskiya sai kimin wannan uban ƙullin a baya?”.        “Kaɗanma nai miki shegiya ƴal bura'uba bai baki kamar na reza, hita kibar gidan nan kona sauya miki wannan shegiyar huskar da maruka”.       Fita Sa'a tai tana ƙunƙuni da cigaba da shafa bayanta inda yasha dundun.      Sum-sum Zinneerah ta wuce ɗakin Inna zata kai botikin tallar tata Karima ta daka mata tsawa. “Munahika dawo a lissahwa sannan”.        Dawowa Zinneerah tayi jikinta na rawa ta  mikama Karima kuɗin da botikin. Fisgar botikin Tinene tayi, Karima kuma kuɗin ta ƙwata tana buge mata hannu.       “Innarmu na nawa kika aza mata?”.     Karima ta faɗa tana fara irga kuɗin.            Daga inda Inna take ta bata amsa da, “Na jikka sha huɗu ne cir gaba daya, dan na rantse da ALLAH kona hicika ya ɓata ina miki ɓatanci da shegen bugu a gidan nan. Kuma sai ubanki ya biyani kuɗina babu ɗagin ƙahwa”.      Zinneerah dai batace komaiba. Sai su Tinene ne suka kwashe da dariya. Karima ta gama irga kuɗin tana jijjigasu da faɗin, “ALLAH ya sota Inna sun cika. Kuɗin anan jikka goma sha ɗaya da murtala uku, sai kayan daya rage na jikka uku ba murtala uku”.       “Ta taimaki kanta. Ga tuwo can kije ki ci idan kina so, dan nasan dai abokan iskancinki sun gama cika maki ciki da shinkahwar tasha”.       “To” kawai Zinneerah ta ce ta nufi hanyar ɗakinsu. Dan wani irin jiri takeji yana neman kwasarta. Tana shiga ɗakinsu ta zube a katifar su Tinene tana sauke numfashi. A hankali barci ya fara rinjayar idanunta mai daɗi.        “Baƙo na sallama da Zinneerah a waje”.      Ta tsinkayo muryar yaro sama-sama da ga tsakar gida. Tsawar da inna ta dakama yaron ce ta sakata buɗe idanunta gaba ɗaya babu shiri. Sai kuma ta jiyo Sa'a na faɗin,          “Inna bafa wani bane ba, malam badamasi ne malaminsu”.      Tsaki Inna taja batare data tankaba. Yayinda Sa'a ta ɗaga labulen ɗakin tana kiran sunanta. “Zinni ki tashi ga Malam Bade yazo nemanki”.       Yinƙurawa tai ta tashi zaune tana gyara hijjab ɗin jikinta. Cikin sanyinta dana barcin data fara tace, “To Yaya Sa'a”. Daga haka ta miƙe ta fiti cike da dauriya.             Matashin saurayine, dan gaba ɗaya shekarun nasa bazasu wuce talatin da ɗoriya ba. Zinneerah data fito a ɗarare saboda tsoron Inna ta rissina tana murmushi. “Sannu da zuwa malam. Ina yini?”.      Shima tashi fuskar faɗaɗe da murmushi ya amsa yana kallonta. “Zinneerah Sulaiman ashe kin dawo gida babu labari? Sai ɗazu ina bisa mashin na hangeki da botikin gyaɗa da riɗi a bakin yara”.       Har yanzu tana a duƙe kai a ƙasa tana murmushi, cikin ƴar muryarta tace, “Na dawo Malam, dama naje wajen mamana ne gaisheta”.        Yanzu kam da mamaki yake dubanta. Cikin kasa haɗiye abinda ke a ransa yace, “Amma a gari aketa hiɗin guduwa kikai bama asan ina kika nuhwaba? Kai mutane sai dai a barsu da halinsu. ALLAH ya ƙyauta to, kin baro maman naki lahiya ko?”.        “Lahiya lau suke Malam”. “To Alhmdllh, Yanzu ni bama wannan ba, nazone dama akan jarabawarku ta jsce. Ina hwata dai baki manta nanda kwanaki takwas zaku hwara ba ko?”.       Karan farko ta ɗago taɗan kallesa ta sake maida kanta ƙasa. Kafin tace wani abu Inna ta banko ƙyauran langa-langar ƙofar gidan nasu ta fito.             “Uhyimm! Kaji farkar taka ta dawo kazo kenan? To billahillazi bari kaji yanzu bazan ɗauki wannan sheɗancinba. Kaji da ƙyau karna sake ganinka ƙohwar gidan nan. Idan son ganinta kake ta bika can mahaɗar taku man......”       “K dalla malama saurara, tsohuwar banza da bakinta bai hiɗin alkairi sai sheri wa ɗiyan mutane. Na rantse da ALLAH kika ƙara hiɗin wani kalmar ɓatanci garemu yau sai kin kwana ofishin ƴan sanda. Ni nazo ne akan maganar jarabawa da zasu yi ta koma makaranta....”         “Anƙi ta koma ɗin munahiki algungumi. Dama can niya nai na barta take zuwa. da ga yau da ga yanzu kuma na hwasa. Bata sake zuwa talla zataimani”.       “Ashe kuwa zaki gurfana gaban mai-gari......”        “Kaini gaban sarkin katsina ma ƙarewar mai-gari mana. Ke kuma munahika dan ubanki tashi ki shige ciki, ƴal bura'uban yarinya kulin bata iya komaiba sai janyoma mutane jidali da yaye-yaye a ƙwar gida. Zanyi maganin rawar kanki ne ai...”        Yanda ta kaima Zinneerah duka ya sata miƙewa da gudu ta shige gidan. Shima Malam Badamasi bai sake tanka mataba ya bar ƙofar gidan rai ɓace. Inna kuwa masifa ta cigaba da zazzagawa har sai da Sa'a da Karima suka fito suka shiga da ita gida.      Tana shiga ta hau dukan Zinneerah babu ji babu gani. Sai da tai mata lilis ta barta kwance tana numfashi da ƙyar. Zinneerah akwai taurin zuciyar tsiya da kafiya wani lokacin. Duk wahalar da take sha wajen Inna akan jima ba'aga kukanta ba idan ba ita taso ba. Idan kuwa kaga ta cika yawan kuka to lallai abin ya kai babba gareta sosai.       Inna na tsaka da cigaba da jarabarta aka buga sallama. Sa'a ce ta amsa tare da nufar zauren gidan nasu dan taga wanene. (Sanƙira) mai shela idan abu ya faru a garinne tsaye yana baza babbar riga. Ta rissina tana gaidashi dan dattijo ne sosai, amma Baba zai iya girmarsa.      “Tsohuwar taki na nan ko?”. “Eh baba tana nan”. “To maza sanar mata mai-gari na biɗar ganinta. inko bata zuwa cikin salama ƴan doka zasuzo su kaita da kansu. Tazo tare da ƴar uwarki zinneerah”.       Sosai gaban Sa'a ya faɗi, amma ta daure cikin girmamawa ta amsa masa tare da juyawa cikin gidan.        Inna ta dubi Sa'a cikin haushin Zinneerah da bai gama sakintaba tace, “Ke kuma minene kika shigo ma mutane haka? Halan shegen nanne bai tahi ba?”.      Kan Sa'a a ƙasa tace, “A'a Inna. Baba Lado sanƙira ne fa, wai ana kiranki gidan mai-gari ke da Zinni....”        “Ki koma ki hiɗi masa ba'a zuwa. Ba'a kamar ana zuwa ɗin...”     “Inna wlhy cayay fa idan baki zuwa ƴan sanda zasuzo su tahi da ke”.        Shiru Innar tayi ƙirjinta na bugawa. Ta tsani harkar ƴan sanda, dan tun sanda sukai faɗa da Lamunde aka adashi ta kaita kusada ofishin ƴan sanda akazo har gida aka kamata sai da tai kwana biyu a kusada hannunsu take shakkarsu. Ba ƙaramin wuya taciyo a kwana biyun datai wajensu ba. Amma a fili sai ta ƙyaɓe baki zata fara masifa kuma.......        “Shin wai Asabe saƙon mai-gari bai iso gareki bane?”.     Karaɗin Sanƙira daga ƙofar gida ya katse mata masifar datai nufin farawa. A tsorace Karima tace, “Innarmu dan ALLAH kije, tunda kinga harda ita akace kuje. Kinsanfa mai-garin nan ba mutuncine da shi ba wlhy yana iya kira maki ƴan dokar”.       Kamar zatai magana sai kuma ta fasa. Ta kai dubanta ga Zinneerah dake kwance barci ya fara ɗaukarta. Tsawa ta daka mata wadda ta sakata tashi a firgice babu shiri.       Ran Inna fal masifa ta tasa Zinneerah gaba Sanƙira na biye dasu suka tafi gidan mai-gari. Acan suka iske malam badamasi. Tun daga nesa Inna ta dinga antaya masa uwar harara kai kace idonta zasu zubo ƙasa ne. Shiko baima san tanaiba. Dan hankalinsa dana mai-garin da fadawa duk yana kan Zinneerah ne dake ɗingishi.        “Ranka ya daɗe ka ga abinda nake hidi maka ko! Da alama bayan barowata gidan bugunta tai”.       Ran mai-gari a ɓace ya wurgawa Inna mugun kallo. “Ke dai Asabe baki gamawa da duniya lahiya inhar baki canja halinki. Ace mutum shi dai baisan komaiba sai mugunta, ke shikenan zicciyarki tamkar ta kahiran hwarkon ƙarni! Kai ALLAH ya wadaran halinki wlhy Asabe. shi dai malam Sule bai sa'ar mace irinki ba. Ya auri ta arziƙin kin koreta a gidan kina kuma gallazama abunda ta haihwa. Wlhy ina mai tabbatar maki wata rana sai kinyi nadama, dan wanga ɗiya sai ta zame miki ɗan hakkin faka raina, RAINA KAMA kuma mara mutuncin mata”.         Kan Inna a ƙasa tanata faman kumurya da kumatu babu damar magana, sai da mai-gari ya ƙare mata zagi tas da gorin asalinta kafin ya ɗora da gargaɗi.       “To naji kince baki sake barin yarinyar nan taje makaranta. Kece kika sata ne?”.      Kan Inna a ƙasa har yanzu tace, “ALLAH shi sawwaƙa ranka ya daɗe. Niko miya ja mani kai ɗiyana boko. Ubana bai saniba bani kai ɗiyana su tabaɗe. Can abokan cin mushenta ne suka kaita......”         “E, ai shi abokin cin mushen nata da kike magana shine kika asirce ya koma kan ɗiyanki, kinga ashe kema abikiyar cin mushen tashi ce ko?”.      Malam badamasi ya faɗa a harzuƙe cikin katse Inna. Babu wanda ya dakatar da shi, dan kowa yasan Babawo take nufi, tunda shine yay tsaye tsayin daka har Zinneerah ta shiga makaranta saboda tana so. Amma yaran gidansu daga firamari basa cigaba. Sa'a ce ma taɗan fara sakandire ɗin itama zango ɗaya tayi ta gudo saboda wani malami ya daketa Inna taje tai masa tijara tace Sa'ar bata sake zuwa. Daga nan kuma bata sake zuwan ba.        Mai-gari ya cigaba da faɗin, “To bara na gaya miki a gaban kowa ki riƙe a ranki yarinyarnan zata cigaba da karatunta har sai ta gama. Ni nan mai-gari zan ɗauki nauyin ɗawainiyar karatun natama daga yau, tunda ance dama yaron daya kaita ya janye dama daga yi saboda sherin da kikayo ta ƙarƙashin ƙasa. Wlhy kinji na rantse, dai-dai da rana ɗaya yarinyarnan kika hanata zuwa makaranta sai kin kwana a kusada ofishin ƴan sanda. Kowa dake nan ya shaida”.        A take duk suka amsa masa da cewar sun shaida. Banda Inna dakeji tamkar zata haɗiye zuciyarta ta mace. Zinneerah kam a ranta wani irin daɗi ne ya lulluɓeta.         Sai da mai-gari ya ƙarama Inna dogon gargaɗi sannan ya sallameta banda Zinneerah.        Bayan wucewar Inna Mai-gari ya shiga yima Zinneerah tambayoyi tana bashi amsa kanta a ƙasa. Sosai tausayinta ya sake mamayesu, suka shiga mata nasiha akan muhimmancin haƙuri da ribar da mai yinsa kanci a duniya ko a lahira. Sannan ya damƙa amanarta hannun malam Badamasi. Tare da tabbatar masa duk abinda za'a buƙata na ɓangaren makaranta na Zinneerah yazo gunsa ya amsa. Daga haka aka sallamesu bayan mai garin ya bata ƙyauta jikka biyu da rabi (500).        Godiya tai musu sosai cike da girmamawa itama, tare da addu'oin fatan alkairi sannan suka taso ita da malam badamasi daya rakota har gida yana ƙara mata nasiha.       Koda Zinneerah ta dawo gida tayi tunanin inna zata hukuntata akan abinda ya faru a gidan mai-gari. Amma sai taji shiru batace da ita ƙala ba. sai dai tana ɗaure mata fuska fiye da yanda ta saba. Sannan komai ƙanƙantar aiki ita ake kira tayi koda su Sa'a na zaune a kusa da ita. ★★''★★"★★"★★            Akwana a tashi babu wahala wajen UBANGIJI, haka rayuwa ta cigaba da shuɗawa. Yau fari gobe tsumma a gidan su Zinneerah. Ita dai batasan minene farin ciki ba ko jin daɗi a gidansu.        Tun randa sukaje gidan mai-gari da inna sai ta sake ninka gallazawar da take mata fiye da da. Makaranta dai ta barta tana cigaba da zuwa. Amma kafin ta wuce ƙa'ida saita kammala ayyukanta. Idan kuma ta dawo ta iske wasu na jiranta him. Ga tallar riɗi da gyaɗa babu fashi gareta. Tsangwama wajen Karima da Tinene sai abinda yay gaba. Idan kaga taji daɗi sai wajen Sa'a da Yaya Gajeje idan tazo gidan. Shi dama Baba ba'a sakashi a lissafi. Dan tamkar bashi da wanima amfani a gidan. Idanma baiso ba sai ya yini a gona tun safe sai yamma zai dawo. Duk abinda Inna zatai a gidan ƙala bai iya cewa saboda tsoron da yake mata.        A haka su Zinneerah suka fara jarabawar junior waec ɗinsu. Zinneerah ba wani ƙoƙari ne da ita sosai ba. Sai dai tanada naci akan abu sosai. Duk abinda takeso takan dage a kansa domin ganin ta cimma nasara. Hakan yasa sam bata da wasa, musamman ma daya kasance itaɗin miskilace ta gaske. Ga halin gidansu ya sake maidata shiru-shiru da rashin son sakewa da mutane.      Zuwa yanzu ta daina jin ciwon cikin nan da kasala. Sai wani irin ƙiba take mai ban mamaki da haske. Ɗan matashin ƙirjinta na ƙara fitowa fili sosai fiye da da.       Kowa ya ganta sai ya tanka canjawar tata na ƙanƙanin lokaci, dan abun na bama mutane mamaki sosai. Musamman da aka san bawani daɗi takeji a gidan nasu ba. Ita kanta Innar bata gajiya da kallon Zinneerah ɗin a ƴan kwanakin nan. Sai dai tanayi tana jan tsaki da ƙyaɓe fuska.             A yau ma data kasance juma'a bayan tasowarta makaranta gida tayo. dan jarabawa ɗaya kacal sukayi, wadda daga ita sai ta ƙarshe da zasu zana. Cike ta iske gidan nasu da ƴan kawo lefen yaya Karima, wanda aka kawo da ga gidan su Babawonta. akwatina uku zuƙa-zuƙa ƴan yayine. Itace kuma budurwar farko da akaima akwati uku a garin, dan ɗaya sukeyi kacal su haɗa rio irin na saka kayan yara ɗin nan babba. Wasuma basayin Rio ɗin. Amma sai ga Babawo shi yayi har uku, ga kaya fal.            Sosai hankalin Zinneerah ya tashi, dan zuwa yanzu dai ta tabbatar Babawo kam ya barta har abada. Sum-sum ta lallaɓa ta shige ɗakinsu tunda babu wanda ya ganta hankalinsu nakan ganin kayan. Hijjab kawai ta cire ta zauna tana haɗiyar zuciya da ƙoƙarin ganin hawayenta basu zuba ba. Tsawon lokaci tana zaune hayaniyar mata da yara na daɗa ƙaruwa harda guɗe-guɗe. Ganin abin nasu bana ƙare bane ta zame ta kwanta hawayen da taketa ƙoƙarin dannewa suka shiga silalowa a kumatunta. Daga haka ta lula duniyar tunani mai zurfi har barci yay gaba da ita bata farga ba.        Timmmm!!! Kakejin ƙarar saukar dundu. A firgice Zinneerah ta farka tana sosa gadon bayanta inda Karima ta daketa.        “Munahika ƴar buƙulu. Ashe nan kikazo kika ɓuya kina baƙin ciki da abun hwarin cikin daya sameni ko? To bara ki ji sai dai ki mutu wlhy. Ni Karima kamar na zama matar Babawo na gama. Dan nan da sati biyu za'a ɗaura mana aure ma”. Ta ƙare maganar da ƙyalƙyalewa da dariyar rashin mutunci.      Ita dai Zinneerah ko ɗaga kai ta kalleta batayiba. Ta kuma ƙi yarda tai kuka. Dan dama wani lokacin haka take da shegen taurin zuciya. Musamman akan abinda ta tabbatar da natane akai mata fin ƙarfi. Haka Karima ta cigaba da mata tujara har sai da Yaya Gajeje da bata tafi ba ta shigo tana zaginta sannan tabar Zinneerah.              Karan farko da baba ya nuna tsananin ɓacin ransa akan abinda akema Zinneerah har takaisa da yima Karima faɗa. Dan duk abinda tayi ya farune a kunnensa kasancewar ya shigo gidan.       Babu wanda ya iya magana har Inna. Dan ita kanta yau sai taji wani shakkar Baban a cikin ranta. Dama ance mai haƙuri bai iya faɗa ba.       Ɗan Murmushi Zinneerah dake a ɗaki zaune har yanzu tayi. A ranta kuwa tana mai tsananin jin tausayin mahaifin nasu da ta tabbatar anfi ƙarfinsa ne dama game da al'amarin gidan nasa, bawai dan Inna ta gagaresa bane ba. ★★★          Tun daga wannan rana su Inna suka hau shirin biki. Dama can a shirye suke tsaf dan sun daɗe suna jiran wannan ranar dan dai kawai Babawon nata musu yawo da hankaline kamar ma zai suɓuce. Sai kuma gashi cikin lokaci ƙanƙani hankalin nasa ya sake dawowa ga Karimar a bazata.............✍                      *_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 _Na Safiyya Huguma_ *_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖 _Hafsat Rano_ *_★ DALAAL_*💝 _Na Miss xoxo_ *_★ UBAYD MALEEK_*💓 _Na Mamu gee_ *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 _Na Bilyn Abdull_ Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 *_08085405215_* IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   0903 234 5899 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 *_Typing📲_* *_😭MAKAUNIYAR ƘADDARA!!😭_* *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* *_HAPPY HAUSA DAY!!🎈🎉🎊🪄_* _Inama ɗaukacin al'ummar HAUSAWA na duniya baki ɗaya murnar zagayowar wannan rana ta HAUSA ta duniya. Alkairin ALLAH yakai gareku a duk inda kuke, ALLAH ya ƙara ɗaga darajar HAUSA da ɗaukacin HAUSAWA baki ɗaya. Harma da sauran yarukanmu🥰🥰_🤗 *Page 5* ..........Lallai da gaske shirin biki ake na ƴar gata. Dan bama Inna kawai ba hatta da Atine dake aure Rimaye ta shiryama bikin. Ko kayan ɗakin Karima daga can akayosu. Ita dai Yaya Gajeje bata biye musu. Sai ma nuna musu illar ƙulla wannan aure takeyi. Dan ta tabbatar an cuci Zinneerah. Tun abin bai kai hakaba take ma Inna magana amma bata saurarenta. Sai ɓacin rai dake biyo baya a tsakaninsu akan hakan. Zuwa yanzu kuma data tabbatar sunyi nisa saita zuba musu ido. Dan akwai ranar ƙin dillanci ai. Kuma nasihar baba ta shigeta. Dan shima da kansa yace ta barsu karta sake cewa komai akan auren. Inhar an cutama Zinneerah ne akan hakan ALLAH na nan baya barci.          Tun ra da aka kawo lefe lafiya taima Zinneerah ƙaranci, a haka ta daure take komai na rayuwarta data saba. Harma ta ida zana jarabawarta ɗaya data rage ranar litinin. Sun kammala junior secondary school kenan suna jiran result kuma ya fito aga abinda ALLAH zaiyi.          Biki kam dai shiryashi ake sosai kamar yaune aka fara aurar da ƴa a gidan. Ita dai Zinneerah nata ido ne kawai, sai idan ta keɓe ne takan sha kukan zuci. A randa aka saka Karima a lalle jikinta yay tsanani, har takaita da kaiwa kwance dole.       Cike da damuwa Yaya Gajeje ta takura mata taci alala da suka girka a gidan saboda baƙi da sukazo daga marabar musawa dangin Inna. Da ƙyar Zinneerah ta iya cinye guda ɗaya sai amai. Kowa ya tausaya mata anata mata sannu. Harma wata ƙanwar Inna na cewa shawara ce a nemamata sassaƙe tasha. Itadai bata iya magana sai amsawa da kai harta samu ta koma ɗaki ta kwanta.      Cikin tsoffin da sukazo daga maraba ne ɗaya ta dubi Yaya Atine dake gefenta tana shayar da ƴarta da take goyo. “Niko nace Atine”.       “Na'am Gwaggo ladi”. Yaya Atine ta amsa tana kallonta tana maido hankalinta gareta. Wadda aka kira da Gwaggo Ladi tace, “Wanan ƴar uwar taku tayi aure ne dama bamu da labari?”.       Da mamaki a fuskar Yaya Atine tace, “Gwaggo wai kina nufin Zinneerah? Indai itace batai aureba. Yaya zatai aure baku jiba”.      Cikin waro idanu na alamar gulma tace, “Kanjakar ubancan kayyasa. To lallai idon Asabe a rufe yake a gidan nan bata bahimtar komai daɗa”.       “Gwaggo miyasa kika hiɗi haka”. Yaya Atine ta sake faɗa tana duban Gwaggon nasu da ƙyau.      “Uhm-uhm babu komai Atine. Kawai dai naga abinda yafi ƙarhin ganina ne. Dan wannan ɗiyar ciki ke ga jikinta, harma ya tasa gashi nan”.       A razane Atine ta saki ƴarta ƙasa da dukan ƙirjinta tace, “Gwaggo ciki?!! Zinni ɗince ke da ciki!!?”.      Yanda tai maganarne ya jawo hankalin sauran mutanen dake a gidan kansu. Ga ƴarta data saki ƙasa ta tsage da kuka saboda zafin faɗuwar da taji..             Yaya Gajeje ma a ruɗe ta saki kwanon data ɗakko zata saka a sayoma Zinneerah kunu ko zata iya sha. Ta ƙaraso gasu Atine da sassarfa tana faɗin, “Atine wannan wane irin mugun alkaba'ine kike hiɗi dan ALLAH?”.         Da sauri Atine tace, “A'a yaya Gajeje bafa ni na hiɗi ba....”      “To waya hiɗi?”. Gajeje ta katse ƴar uwar tata.          “Kunga bafa zancen hayaniya bane ba Gajeje. Ku kira yarinyar tazo nan”. Gwaggo Ladi duk ta katsesu.        Zinneerah na ɗaki kwance tana sauke numfashin wahalar amai da tayi wata cikin ƴan bikin ta shigo ɗakin tana ƙwala mata kira. Miƙewa tai daga kwancen da take a razane tana dubanta batare data amsaba.     Matar tace, “Kinga taso ana kiranki a waje”.          Batare da tunanin komaiba Zinneerah ta miƙe ta biyo bayanta cike da dauriya. Tana fitowa gabanta ya faɗi ganin kowa na gidan ya zubo mata idanu, har waɗanda ke a cikin ɗakin Inna duk sun fito tsaye cirko-cirko. Rasa ina zata dosa tayi dan ruɗiya. Sai da yaya Gajeje tai ƙarfin halin kiran sunanta cike da tashin hankali. Dan ita kanta kam zuciyarta ta fara gaskata zancan tsohuwar saboda wani irin canjawar da Zinneerah tayi, wanda ada sam hankalinta bai taɓa bata abu makamancin ciki ba akan canjin....      Ƙarasowar Zinneerah inda suke ne ya katse tunaninta. Tsohuwa Gwaggo Ladi ta kamo hannun Zinneerah ta buɗe tafin tana kallo, ta kuma ɗago fuskarta ta gwale mata idanu nanma. Sai kuma tace ta buɗe bakinta ta turo harshenta waje. Ita dai Zinneerah babu musu komai yi take cike da tunanin ko wani ciwone ya kamata. dan a watani uku ɗin nan data dawo gida ƙwarai da gaske tanajin canji sosai a jikinta wanda batasan kansa ba.....        “Wlhy wannan yarinyar ciki ne da ita Asabe. idanma baku yarda ba ku kaita ayi gwaji wajen likita”.      Zancen Gwaggo Ladi ya katse tunanin Zinneerah. Yayinda a take gidan ya harmutse da salllami da gulma. Sam Zinneerah bata fahimci komai a zancen Gwaggo Ladi ɗinba, duk da yanayin mutanen dake gidan ya sake sakata a tashin hankali.      A haukace Inna tazo ta kai hannu zata kai mata maguza wata ƙanwarta ta tare tana janye Zinneerah ɗin. “Haba Asabe, ita dake cikin wannan halin zaki kaima wannan bugun? Kamata yayi a bita a sannu asan inda al'amarin ya hito ai ko?”.          “A ina ya hito banda wajen yawonta na tazubar Haule. Idan na hiɗi ya rinyarnan nabin maza sai ace sheri nake mata dan ban haiheta ba. Kwanan nan fa tahiya tai babu wanda yasan ina taje kusan mako huɗu sannan ta dawo. Amma da yake ubanta shashasha ne bai ɗauki wani mataki a kantaba. Wace irin makauniyar rayuwace wannan? Na rantse da ALLAH bata zaunamin gida da cikin rariya. Sai dai ta koma can gidan wanda ya ƙunsa mata masihwar su ƙarata tambaɗaɗɗiyar yarinya”.       Yanda Inna ke masifa kamar zata haɗiye harshentane ya saka gidan yin tsit kowa yana saurarenta. Yayinda hajijiya take juyama Zinneerah garin a hankali. Babu zato sai ganinta kawai akai ƙasa ta zube.      Babu wanda yay yunƙurin taimaka mata sai Sa'a dake kuka tun farkon fara maganar, ta taho da gudu ta durƙusa gabanta tare da ɗagota jikinta tana jijjigata. Tsawa inna ta daka mata akan ta tashi a wajen kota tsine mata.      Cikin kukan Sa'a ke girgizama Inna kanta. “Haba Innarmu! Haba Innarmu!. Wlhy Innarmu Zinni ba ƴar iska bace. Wlhy Zinni bata iskanc......”     Ta kasa ƙarasawa saboda kukan daya sarƙeta. Yaya Gajeje ce ta tako inda suke itama tana share hawaye da bakin zaninta. Ta durƙusa ta kamo kan Zinneerah dake a jikin Sa'a ta maido kan cinyarta tana fashewa da kuka maiban tausayi.....          Bayyana irin tashin hankalin da Zinneerah ta tsinci kanta a cikin wannan rana da duk wani masoyinta ma ɓata lokacine. Hatta da maƙiyan nata jimami suke nunawa a zahiri, a baɗini kam ransu fari tas musamman ma Inna da ke ganin fatanta ya tabbata.        Kamar yanda Zinneerah ta yanke jiki ta faɗi sai da aka zuba mata ruwa haka Baba ma da labarin ya riskesa tamkar saukar aradu ya zube babu numfashi sai da aka zuba masa ruwa ya farfaɗo da ƙyar.       Kafin wani dogon lokaci garin ya ɗauki zance Zinneerah tayi cikin shege. Tofa abin nema ya samu ga masu ƴancin faɗin albarkacin baki. Wasu suce mugun alkaba'in Inna ne ya kamata, wasu suce wahalar da Innar ke batace ta kaita da fara bin mazan ai. Wasu suce babu wani dama halintane. Dan kawai tana shan wahala a gidansu sai ta bi maza.      Kowa dai da inda nasa furucin ke sauka. Duk da ba yaune ainahin ɗaurin aure ba sai ga mutane na tururuwar shigowa gidan gulma da son ganin ƙwaƙwaf. Ƴammata kam harda waɗanda Karima ma bata gayyata zaman ƙunshin ba sai gasu.       Inna kam tanata zabga bala'i sai Zinneerah ta bar mata gida ƴan uwanta na tausarta. Yayinda Zinneerah ke a ɗakinsu tare da Baba da Yaya Gajeje da Sa'a. Sai wasu ƙanen Baban maza su uku da mace ɗaya sun turketa akan saita faɗa musu a ina ta samo wannan jidalin?…       Kuka Zinneerah keyi tamkar numfashinta zai rabu da gangar jikinta. A karo na babu adadi ta sake faɗin, “Wlhy! Ta-kwaran-kwatsa Kawu ban taɓa aikata iskanci ba. Wlhy ni banda ciki.”        Cikin daka mata tsawa Kawu haruna yace, “Kinci uwarki Zinni. Su waɗanda sukace kinada cikin zasu maki ƙarya kenan? Bayan duk ga alamomin mai juna biyu tattare da ke. Idanfa baki hiɗi mamu wanda kukai wannan lalatar to kuwa kina barin garinga kije can ki nema wasu iyayen bamuba. Dan bamu zama da mai halin banza cikin zuri'armu kau...”         “Ai bama barin gariba ni nan da kake gani rami zansa amani na bizneta da ranta har sai ta mutu idan bata hiɗi mamu gaskiya”.      Tirƙashi. Tunfa su kawu nabin Zinneerah da lallami akan sanin gaskiyar magana har takai Kawu Sabi'u da fara bugunta amma ta kafe akan itafa bata taɓa aikata abinda ake tuhumarta ba. Tsabar tashin hankali kowa kansa ya ɗauki zafi. Baba ma ya kasa magana sam.      Ganin suna neman halaka yarinya wata a cikin ƴan uwan Inna dake aure a kankia tace, “Kunga karkuce ta wannan hanyar zaku tuhumi yarinyarnan. Sannan har yanzu babu tabbacin cikinne a jikinta ko saɓanin haka. Kamata yayi ku sami likita yay mata gwaji, idan an tabbatar cikinne sai a bita ta hanya mai sauƙi a binciketa bawai ta kwakwazo da azabtarwaba. Dan yanzu idan cikinne ai sai kuyi mata lahani ita da shi k.......”        “K Halima bamu son tsarin banza da wohi. Kinason hiɗin ita Yaya Ladi ƙarya tayi kenan da tace akwai cikin? Bayan duk wanda ya kalla wannan sheɗaniyar yarinyar zai tabbatar da alamomin mai ciki tattare da ita...”        “Ba haka nake nihi ba yaya Asabe. Tayaya zan ƙaryata Yaya Ladi ni kuwa. Ni dai ina nuna maku muhimmancin bin komai a sannune. Yanzu wannan ruɗama yarinyar tunani da bugun nata da akeyine zaisa ta hiɗi gaskiya? A ganina idan anbi komai a sannu sai a kamo gaskiyar al'amarin da mahwarinsa basai anbi hanyar ilatata ba a dawo kuma ana dana sani”.     Inna zata sake magana Yaya Gajeje ta katseta. “Maganar Gwaggo Halima gaskiyane. Ya kamata mubi komai a sannu kawu. Dan kowa yasan halin Zinni bazata aikata wannan al'amari da ganganba inma har ya tabbata hakane. Ba muba ko jama'ar gari idan zasu hiɗi gaskiya sunsan Zinni yarinyace mai nutsuwa da haƙuri. Wlhy inaji a raina inhar da gaske ciki ne a jikin Zinni sai dai ɗayan biyu ne ya hwaru. Kodai wani la'ananne ne yay mata wayo ya ɓata mata rayuwa. Ko kuma acan inda ta baro wani yay mata hin ƙarhi ya aikata mata wannan zaluncin. Ku tunafa yarinyarnan nemarta akai aka rasa rana tsaka. sai kuma gata ta dawo babu zato. Abin mamaki kuma tamkar an rihe mana bakuna har yanzu bamu sake bi takanta muji yaya akai tabar garinga ba ta kuma dawo? Miya hwaru da ita data tahi? Ina taje? Waye silar hitar tata? Duk bamu binciketa b..........”        “Gajeje!!!”   Inna ta faɗa da wata irin mahaukaciyar tsawa tana nunata. Ta cigaba da faɗin, “Na rantse da ALLAH idan baki hita batun wannan ƴar iskar yarinyar ba daga yau sai na tsine maki a gidan nan ke da Sa'a. Har uban waye zai hiddata a gida da gari banda abokan iskancinta wanda ga sakamakon abibda takeyi ɗin nan ya bayyana kowa ya gansa”.       Dubanta Gajeje tayi zatai magana. Sai kuma mita tuna oho tai shiru kawai tai ƙasa da kanta tana sharce hawayen dake sakko mata.         Har dare gidan ya gagara komawa dai-dai. Zinneerah kam tana can ƙuryar ɗakinsu ta ɓuya tana cigaba da kukanta. amma duk da haka bata kasa jiyo yanda ake aibantata a tsakar gidanba ita da mahaifiyarta a bakunan wasu a cikin dangin Inna. Yayinda ƴammata masu zaman ƙunshin Karima suka fara raira mata waƙa cikin habaici da izgili kamar yanda Karima ta sakasu.      Babu wanda ya hanasu, dan Yaya Gajeje tabar gidan tun ɗazun. Baba kuwa yana zaune daga can bayan runbunsu shiba mai rai ba shiba gunki ba. Sam zuciyarsa da ƙwaƙwalwarsa basa aiki irin na mutane.         Duk da ƙarancin shekarunta yinin yau ya sake tabbatar mata da rayuwa ta sake kaita wani ajin jarabawar da yafi zaman gidansu ƙunci da tashin hankali. Ita dai ko Al-qur'ani aka bata zata iya rantsewa da shi akan bata taɓa aikata iskanci ba, amma sai gashi yau an wayi gari ita ake kira da suna mai ciki, cikinma cikin shege. Ta sake fashewa da kuka mai cin rai. ★★★         Zamu iya cewa a wannan dare barci ɓarawo ne kawai ya saci Zinneerah kasancewarsa gwanin iya sata. Amma badan taji sha'awar yinsaba ko buƙata.       A kiran sallar farko ta tashi, taji daɗin jin gidan shiru alamar kowa bai tashiba. Ta lallaɓa ta fito zuwa bayi. Bayan ta kammala lalurarta tai alwala ta sake shigewa ɗakinsu. Daga haka bata sake fitowa ba har sai da rana ta haska. Zuwa lokacin gidan ya cika da hayaniyar baƙi da yaransu. Kamar jiya dai kowa da zancen cikin nata ya tashi a baki, hakan yasa ta sake maƙurewa a ɗaki taƙi fitowa.     Tana zaune kanta cikin gwiwarta taji muryar Gwaggo Laritu ƙanwar su baba na kiran sunanta. Kanta ta ɗago muryarta data sha kuka a dusashe tana amsawa. Fuskar Gwaggo Laritu a haɗe tace, “Taso ki hito”.        Sosai gabanta ya faɗi, sai dai babu damar musu dole ta miƙe tana rangajin yunwa da damuwa. Kamar jira ake ta fito tsakar gidan yay tsit idanu caahh a kanta. Tai ƙasa da kai zuciyarta na tsitstsinkewa dan tashin hankali...       “Munahika, ƴar iskar yarinya. Ƙyahwa ta duƙar da kai kamar balamar tunkiya tunda kin kwaso mamu abin kunya”.     Inna ta faɗa tana jan tsaki. Ita dai Zinneerah kanta a duƙe bata yarda ta kalli kowaba. Ta kuma kasa ɗaga ƙafarta dan batasan ina zata dosaba.         Sa'a ce ta taso daga inda take zaune tazo ta kama hannunta, itama muryar tata a dasashe alamar tasha kuka tace, “Muje Zinni, su baba na jiranki a zaure”.      Da ƙyar ta iya ɗaga ƙafafunta tabi Sa'a har zauren. Baba na zaune shi da su Kawu Haruna. Ƙasa ta zube cikin rawar murya tana gaishesu. Babu wanda ya karɓa mata, sai Gwaggo Laritu ce tace, “Ya kamata mutahi kar rana tai tsaka tunda ta hito”.      Nanma babu wanda ya iya cewa komai, sai miƙewa da su kawun sukai amma banda Baba da kansa ke ƙasa. tunda Zinneerah ta fito ko motsi baimayiba. Koda sukai masa sallama zasu tafinma bai motsa ba. Bai kuma ce uffanba har suka tasa Zinneerah gaba suka fice.       Mashina biyu dake jiransu suka taras a ƙofar gida. Kawu Sabi'u da Kawu Haruna suka hau ɗaya. Ita kuma da Gwaggo Laritu suka hau ɗaya batare da tasan ina suka nufa ba.          Ƙasa zinneerah tai da kanta har suka baro cikin garin Danya. Wanda tasan tunda kasancewar safiyane kowa yaga tahowar tasu, waɗandama basu ganiba zasu samu labari ga waɗanda suka gani ɗin.                 Har cikin Kusada masu mashinan nan suka kaisu babban asibitin Kusada. Kasancewar ɗan mashin ɗin daya goyo su Kawu babban ɗan Kawu Sabi'u ne shine yay musu shige da ficin komai har suka sami ganin likita kusan sha ɗaya na rana. Duk da a matuƙar tsorace Zinneerah take bataƙi amsa tambayar da duk likitan yay mata ba. Bayan ya gama mata tambayoyin yasa aka kira masa wata matashiyar budurwa. Zinneerah ya nuna mata yana faɗin, “Maryam kuje da ita tai hitsari akaima Bashir”.       Budurwa daya kira da Maryam ta amsa da to a girmame tana duban Zinneerah. Tashi Zinneerah tayi ta bita zuciyarta na ƙara shiga damuwa da firgici. Bayan ta kaita wani banɗaki tayi fitsari a wata roba suka fito. Zinneerah wajensu Gwaggo Laritu ta dawo. ita kuma Maryam ta tafi cika umarnin likita.      Sunyi zaman kusan mintuna arba'in Maryam tazo ta wucesu zuwa ofishin likita. Dansu tuni sun dawo waje sunba sauran marasa lafiyar damar shiga suma.. Kusan mintuna goma Maryam tazo tai kiransu.      Kamar ɗazu daga ita sai Gwaggo Laritu suka shiga. bayan sun zauna likita ya dubesu da murmushi yana faɗin, “Masha ALLAH mamana ga sakamakon gwajin hitsarin da mukai mata ya hito. Duk da dama dai kafinma hakan na fahimci ciwon na ƙanwata abin so ne. Amma duk da haka dai nafi yarda da'a gwada ɗin......”        Cikin ƙosawa Gwaggo Laritu tace, “To madallah, mike damunta?”.        Sake faɗaɗa murmushi likita yay yana duban Zinneerah da kanta ke a ƙasa tana wasa da yatsun hannunta. “A'a Inna ba wani abu baneba face ƙaruwa muka samu. Tanada ciki na kusan watanni huɗu. Kuma Alhmdllh yana cikin ƙoshin lafiya kamar yanda itama alamomi suka nuna tana cikin ƙoshin lafiya, sai dai kuma ya kamata a ringa kula da abincin da zataci saboda shima yaron cikin nata ya samu nagartaccen raino.......”      Sam Gwaggo Laritu da Zinneerah ba fahimtar bayanin likitan sukeba tunda ya ambaci ciki. Dan Zinneerah ma wani irin hajijiya take gani. Tun ofishin na juya mata har ta koma ganin duhu a cikin idanunta. Sai kawai ganinta sukai a ƙasa daga ita har kujerar robar da take zaune a kai.        “Ya subahana”. Doctor ya faɗa yana zabura saboda faɗuwar Zinneerah. Hakan kuma yay dai-dai da dawowar Gwaggo Laritu datai suman wucin gadi itama hayyacinta. Yayinda su Kawu Rabilu suka shigo da gudu saboda jin sallalamin da likita da budurwar nan Maryam keyi akan Zinneerah da alamomi suka tabbatar da suma tayi............✍ “Hummmm!!!! Turƙashi, masu karatu wannanfa shi ake kira da ANA DARA GA DARE YAYI. shin yaya akai hakane? Yaya kuma za'ai? Mi kuma zai faru?. Gadai likita ya tabbatar da ciki a jikin Zinneerah baiwar ALLAH. yayinda Zinneerah ta tabbatar mana kuma bata taɓa iskanci da kowa ba. Shin tayaya aka samu ciki idan babu mahaɗi? Shin wanene uban wannan cikin? Ta yaya aka samar dashi? Da sanin Zinneerah ko fyaɗe ne? Mi Inna ta sani akan barin Zinneerah gida? Anya kuwa babu lauje cikin naɗi masu karatu? Ina mahaifiyar Zinneerah? Yaya Baba zai kasance da tabbatuwar wannan cikin dake jikin ƴarsa dake a matsanancin rayuwa a gidansa? Yaya jama'ar garin Danya zasu cigaba da ɗaukar Zinneerah yanzu? Yaya rayuwar Zinneerah zata cigaba da kasancewa a gidansu da garinsu?. Wannan amsoshin duk suna ƙumshe a cikin littafin MAKAUNIYAR ƘADDARA da zai zo muku akan naira 300 kacal insha ALLAH. Dan girman ALLAH ina roƙonki ƴar uwata. Kibi ta hanyar data dace domin mallakar naki cikin kwanciyar hankali. Idan kin zama mai shigewa gaba wajen girmama sana'armu kema sai ALLAH ya ɗaga darajar taki komai kanƙantarta. Idan kin zama jagora ko mai burin ruguzamu UBANGIJI ya fimu sanin ke wacece.. Fatanmu kowa ALLAH yay riƙo da hannunsa akan neman halak ɗinsa. Dan ALLAH kuzo ku saya kafin ku karanta. Dan ALLAH idan kin saya karki zama ɗaya daga cikin masu fitar mana dan kawai ganin mun koma baya ko kuntata mana. Ku tuna da tarin alkairinmu na baya gareku, koda bazaku rama manaba karku cutar damu dan girman ALLAH mun roƙeku dan shine kaɗai zamu iya haɗaku da shi🤓🙏🏻. ALLAH kai mana jagora. Yanda zamu fara lafiya ALLAH ya bamu ikon gamawa lafiya. Masoyanmu da basu gajiyawa wajen sayen hajarmu da mun fitar muna sake godiya a gareku, ALLAH yabar zuminci. Masoyanmu da basu taɓa sayaba kuma ku garzayo dan bana Zafafa shiri sukai na musamman domin farin cikinku. Masu jira a fiddo ku karanta kuma dan ALLAH kuzo ku biya ku mallaki naku a wannan karon kuma sai ALLAH ya kawo muku Customers akan naku kasuwancin. Mun gode. Mun gode irin trillions ɗin nan😘😍😘😍🤗😊😉. *_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 _Na Safiyya Huguma_ *_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖 _Hafsat Rano_ *_★ DALAAL_*💝 _Na Miss xoxo_ *_★ UBAYD MALEEK_*💓 _Na Mamu gee_ *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 _Na Bilyn Abdull_ Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 *_08085405215_* IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   0903 234 5899 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 *_TYPING📲_* *_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_* *Page 6* _________________________ Duk wacce batayi anfani da sabulunnan ba anbarta abaya acan karshen bayama kuwa duk Mai tantama akan sabulai nagyaranjiki cewa basa Aiki toh yacire mg's domin kankat ne insha Allah babu Wanda yayi anfani dasabulunmu yace baiyi ba koyaushe mg's sai sanbarka amare da uwargidaye hardama yanmata kuhanzarta kusamu naku ba karya domin bama cika Baki kugwada kubada labari da bakunanku sabulu daya tamkar dubu wadandama basasan using cream sabulun mg's herbal whitening black soap yawadacemuku jikinku zaiyi kyau koyaushe kukasance clean cikin kamshi Kuna glowing koda bakusa turare ba🤗 Kayanmu bana bleaching bn organic ne sunagyarajiki fiye da tsammaninku zaifiddomuku da ainihin natural beauty dinkine Wanda yagwada shi zaitabbar amare kuyi kokari kumallaki mg's domin baruwanku da zuwa adirjemuku jiki zakuga yanda fatarku zata dinga walwali Ina masu pimples Tabo(spot) Sunburn dama dukwani matsalar fata kuyi kokari kunemi soap dinnan before 2weeks zaisharemuku hawaye kuzama abun kwatance Sister's masu nankarwa kuma kunemi soap dinnan Yana rage nankarwa sosai🧖🏻‍♀️duk me shakku tayi kokari tagwada mg's insha Allah bazakiso rabuwa dashi ba Akwai maisa haske Amma kayanmu nafada bana bleaching bn zaifiddomiki d ainihin halittarkine yagoge dukkan dattin jiki Akwai Kuma Wanda zaimiki maintaining skin dinki yasaki fresh fatanki tazama kalar hutu Pls bamacika Baki you HV to try it and see for yourself 100%tested nd trusted Soap price:3k Location:kaduna buh munaturawa ko Ina Amma delivery is not free Maiso kindly message 08062991549 Call 08064532391 Note:Babu inda zakusami mg's herbal whitening black soap sai a number dinnan bairiga yakai market b inyakai we will let you know buh as for now wnn numbern ne kawai🙏 Maiso yahanzarta before yaji sold out akwaisu available now insunkare you HV to wait akawo so maiso yahanzarta🙏adade anayi sai gsky🤭🤝 Mg's skincare Mg's bakery You can still order ur birthday cake, cupcake,slice cake,meat pie,shawarma,samosa nd spring rolls for ur event @mg's bakery Kindly call or chat 07046881166 07067210195 08062991549 Masu bukatar abayas,takalma da jakunkuna,ashobe,laces d atamfofi, materials nd the rest 07046881166 👏🤝 Page 6 .........Tun bayan wucewar su Zinneerah kusada Inna ta kasa zaune ta kasa tsaye. Ba komai ke mata kai kawo a rai ba sai maganar Gajeje da take cewa babu wanda ya binciki Zinneerah yaji ina taje. Idan har bata ɗauki matakiba to lallai abinda bata buƙatar ya fito da ga bakin Zinni shine zai fito, dan suna dawowa gida kowa zaiso jin ina taje ɗin? Yaya akai kuma ta dawo?.      Tsulum ta miƙe da ga zaman da tayi a bakin gado, ta rarumo yamutsatstsen gyalenta daketa tsamin dauɗa. Tana ƙoƙarin warwaresa ta yafa Magajiya ta shigo ɗakin...         “A'a, Asabe ina zuwa kuma?”. Ɗan duru-duru tayi na alamun rashin gaskiya. Sai kuma tai saurin faɗin, “Uhm Magajiya zanje nan ƙauyen kwangi ne na amso kuɓewar dana bada a daka saboda miya. Na sha'ahwa gaba ɗaya sai yanzu na tuna. Gashi Atine tace tuwo aka ɗora yanzu da za'aci da rana. Kinga kuma dole ne miyar ɗaurin aure ma na gobe a haɗa da miyar yauƙi dan taushe ɗin nan ba isa zataiba”.       Kai Magajiya ta ɗan kaɗa mata, sai kuma tace, “Amma nikau da dai kin aiki ko Tinene ko Sa'a mana. Ke da mutane keta shigowa kuma ace kinje wani waje ai babu daɗi. Sannan waɗanan masu tahiya asibitin ya kamata ki jira kiga dawowarsu ko”.      Nannauyan numfashi Inna ta sauke tana ƙyaɓe fuska. Tace, “Kinga Magajiya hita batun waccan watsatstsiyar yarinyar. Dan babu mai ɓata mani taro aradu. Maganar amso kuɓewa kuwa gara naje da kaina. Dan daga Tinene har Sa'a mashiririta ne da kike ganinsu”.        Magajiya tace, “To ni haɗani da Tinenen muje. Ai in dani dai batacewa bata zuwa ko?”.             Sosai wani irin tuƙuƙin baƙin ciki ya turniƙe zuciyar Inna. Ji take kamar ta kaima Magajiya duka. Da ƙyar ta shanye abinda ya tokare maƙoshinta ta ƙaƙaro murmushi dan tasan nacin Magajiya batun yanzu ba. Tace, “To nahi yarda da wagga shawarar kau. Bara naga giccin Tinenen saina hiɗi maki ku tahi”.       Da to Magajiya ta amsa, tare da ɗaukar buhun da garin masara ke ciki wanda dama shita shigo ɗauka ta fita. Da wata muguwar harara Inna ta raka bayanta tana jan tsaki. Ta sauke gyalen nata tana ƙudundunesa ta cusa cikin lalitar bujenta na ciki. Ganin ya kwanta babu mai ganewa ta fito a ranta tana ayyana. (Ai idan kinsan wata bakisan wataba magajiya).      Shigewa tai cikin masu hidimar aikin abinci ta cigaba da harkokinta. Sai da taga kowa hankalinsa baya kanta tai wuff zuwa bayinsu tabi ta cikin dannin geza da akai musu sakamakon zubewar katangar bayin lokacin damuna daya wuce. Har yanzu kuma ALLAH baiba baba damar gyarawa ba.        Saurin zaro gyalenta tai ta warware ta aza bisa kai. Cike da sauri da sassarfa ta dinga ratsawa ta cikin gonaki dan kar wani ya ganta........ ★★★★                      A asbiti kam bayan tabbatar da Zinneerah ba suma tayi ba ruɗanin maganar likitace kawai ta haifar mata da hajijiya sai suka saka mata ƙarin ruwa. Hankalin su Gwaggo Laritu bai kwanta ba sai da likita yay musu bayani.      “Ku kwantar da hankalinku tana cikin ƙoshin lafiya. Kuma Alhmdllhi bama suma tayiba. Yanayin da take cikine ya kawo hakan, da alama kuma ko karin kumallo bataibama kuka fito”.       A kusan tare suka sauke ajiyar zuciya. Rabilu yaron Kawu Haruna daya kawosu yay saurin faɗin, “Likita to ko za'a samo mata wani abune taci?”.          “Eh za'a iya. Amma a yanzu dai mun saka mata ƙarin ruwa ta samu barci. a cikinsa kuma akwai abinda zai taimaka mata akan yunwar, da alama dai kai ne mai-gidan nata ko?”.       Murmushi kawai Rabilu yayi batare da ya amsawa likitan maganarsa ba. Sai dai Cikin ƙarfin hali duk sukai masa godiya. Amma a ƙasan ransu su kaɗai sukasan irin tashin hankalin da suke ciki game da wannan ciki na jikin Zinneerah. Suna tsananin tausayin yarinyar saboda halin data tsinci kanta a ciki a gidansu na rashin mahaifiya. Ga yayansu shi da babu duk ɗaya a gidansa saboda makircin matarsa Asabe. Sunyi iya ƙoƙarinsu dan ganin sun maidosa hayyacinsa tun tuni amma Asabe ta sake shiga ta fita ta raba tsakaninsu da shi. A yanzu haka ko mu'amula bayayi da kowa a cikinsu, ko maganar auren Karima bai sakasuba sai ji sukai a gari. Abin bai ɓata musu rai ba sosai saboda sunsan baya a cikin hayyacinsa ne sam. Yanzu haka maganar cikin nan Sa'a ce taje ta sanarma Gwaggo Laritu tana kuka, kuma da'ace ba Zinneerah abin ya shafaba cikin ƴaƴan Inna ne ko takansu bazasubi ba. Lallai lokaci yayi da zasuyi wani abu game da gidan yayan nasu kam a wannan karon. Dolene kuma susan wanda ya shiga mutuncin Zinneerah kar rayuwarta ta ƙarasa shigewa cikin garari sunaji suna gani.         Kusan su dukansu haka suka dinga tanani a cikin zukatansu har ruwan da aka sakama Zinneerah ya ƙare, sai dai barci takeyi sosai. Sallar azhar su Kawu suka tafi yi massallaci. Itama Gwaggo Laritu saita fito dan neman inda zata gabatar da tata. Bayan duk sun idan da sallarne Rabilu yaje ya samo musu abinci dan su ɗanci, dan su kansu akwai waɗanda basu karya ɗinba a cikinsu.......... ★★★★            Sauri sosai Inna ta dinga zabgawa harta iso ƙauyen mahuta dake can yamma da su. Ƙauyene sosai dan gidajen garin bazasu gaza biyarba ma gaba ɗaya. A farkon shiga garin ta gamu da yara sun dawo ɗibar ruwa rafi. Tsaidasu tai ta ɗiba ruwan tasha sosai tana sauke numfashi a jajjere. Dan ba ƙaramin sauri ta zabgaba a tafiyar tata.      Daga haka ta isa gidan dake ƙarshe a jerin gidajen ƙauyen. Tun a ƙofar shiga zauren gidan ta zabga sallama. Daga ciki akai gyaran murya tare da amsawa, sannan aka bata iznin shigowa. Babu kowa a soron, sai dai akwai ƙofar dake nuna alamun ɗakine, dan akwai labule da takalma a ajiye, sai wata a gefe ta shiga ainahin gidan kuma.       “Gahwaranku dai”. Inna ta sake faɗa tana matsawa ga ƙofar ɗakin. Daga ciki muryar namiji dattijo ta sake amsa mata da “ALLAH yay mana aikin gahwara shigo”.        Labulen ta ɗaga ta shiga ɗakin dake cike da shirgin da zama lissafasu ma ɓata lokacine, sai Dattijon dake zaune yana rubutu a allo da tawwada da alƙalami. Kallonta yay cike da fara'a kamar yanda itama take faman washe haƙwara.       “A'a Asabe ce a garin yau?”. “Wlhy nice malam kallamu. Kasan gobe ne ɗaurin auren ƴar wajen tawa, gashi kuma banzo na amshi abinda ka ce ba tun kwanaki idan auren yazo. Bayan nan kuma ga watama matsalar datake neman sake taso mani kuma”.       “Tofa babbar magana. Ai dama inata tsumayen zuwan naki, dan kwanaki hudu da suka shige na shigo Danya ɗin nakejin auren yarinyar wajen naki ya tashi. Harma naita mamakin banji daga garekiba”.        “Ayya, ka gahwarceni malam. Abubuwane sukaima kaina yawa a tsakanin nan wlhy. Amma zuwa nanɗin yana raina kodan a shiryamin yarinyar tunda kaima kasan dai yanda abubuwan suke ai”.      Murmushi yayi yana ajiye allon da yake rubutun da gyara zamansa. Ya jawo wani ƙwarya yana tura mata gabanta. “Kinga komai ma na haɗa. dama ko bakizoba ni zanje ɗaurin auren gobe, to niyyata dama naje miki dasu ai”.         “Kai madallah madallah malam kallamu, nagode nagode sosai da wannan karamci naka. ALLAH ya saka maka kaima da alkairinsa”.      “Amin. Yanzu minene gudar matsalar kuma?”.       Nannauyan nishi Inna ta sauke tana gyara zama. Cike da takaici da baƙin ciki tace yarinyarnan da uwarta ta bar mani ciki ya bayyana ga jikinta jiya. Tofa shine shaggun dangin uban nata sukazo sukai tsaye akan lamarin har suna iƙirarin sonjin ina taje kwanaki. Kasan kuma munyi aiki kwanaki akan rihe bakin kowa bai sake tambayarta ina taje. Itama kuma karta hwaɗi ma kowa ɗin. To wlhy yau malam kallamu suna neman ɓalloman aiki musamman ɗiyar wajena dake aure Sanni. Kasan nayi-nayi na rabata da yarinyar abun ya hwaskara”.        Kai malam kallamu yaketa girgizawa yana saurarenta. sai da taje har ƙarshen zancenta ya fara magana. “Kamar yanda na hiɗi maki tun kwanaki uwar yarinyarnan shu'umace ta gaske. Dan duk da kin hiddata a gidan nan bawai ta barki bane, sannan tana aikoma yarinyar da wasu ayyuka, shiyyasa da munyi aiki akan yarinyar baya wani nisa yake warwarewa. To amma ke kin tabbatar akwai cikin kuma?”.         Cikin wata lalatacciyar dariya Inna tace, “Ciki kau akwaishi malam kallamu, dan ƙuru-ƙuru ya bayyana kansa ga mutane”.          “Tohwa babbar magana. Amma yanzu kunsan wanene yay cikin?”.     “Inaaaa! Babu wanda ya sani, inada tabbacin acan inda nasa ƙawata ta kaita aikataune wani ya ɗura mata shi. Kasan yaran birnin nan akwai basira. Balle ƴar banzar yarinyar tanada ƙyau irin na uwarta. Yanzu haka jiran Hajji Lanti nake tazo naji miya hwaru. Amma itama bullum kakeji kamar an aiki bawa garinsu”.         “Shikenan, yanzu dai ayau ɗinnan zanyi wani aiki. Kamar dai yanda na hwahinta ke dai bakiso yarinyar ta hiɗi ta sanadinki tabar gari ko?”.        “Kwarai ko Malam Kallamu wannan shine hwatana. Dan nahi son kowa ya dinga kallonta da hita tai yawon tazubar ɗinta harta samo wannan cikin. Nihwa idan san samunane tabarma garin baki ɗaya yanda mutane zasu sake yarda komawa tai wajen farkan nata. Bazan ɓoye makaba zaman yarinyarnan a gidan na baƙantan rai, dan ji nake kamar har yanzu uwarta na tare damu, duk da na nisantata da garin tuni, to itama ɗiyar sonake na nisantata da Danya har abada, nahison na rayu gidan mijina dagani sai ɗiyana aradu”.         Kai Malam Kallamu ya jin jina yana murmushi saboda shima mugunne na haƙiƙa, shiyyasa tasu tazo ɗaya da Inna. Kuma wai a haka shiɗin malamine, harda almajirai a ƙarƙashinsa yana basu ilimi🤦🏻.       Ya sake haɗa mata abubuwa da yawa. Tare da tabbatar mata a daren yau zaiyi wani aiki akan Zinneerah. Ta ajiye masa kuɗi tana masa godiya ta taho akan sai gobe yazo ɗaurin aure zai tahoma da Karima wani haɗin neman sa'a a gidan Babawo. (Humm ALLAH ya shirya mana zukatanmu. Babu wani banza daya isa baki ƙyaƙyƙyawar rayuwa a duniya sai UBANGIJI. Domin shima idan kura na maganin zawo yayma kansa mana. Idanma asirin kikayi akan wani kikaga yacisa dama can ƙaddararsa kenan koda bakiyi komaiba tunda ALLAH yay alƙawarin shigarsa wannan halin saiya shiga ɗin. Abindama jahilai suka gaza ganewa shine. Da yawan jarabawa tsanice na kaiwa ga nasarorin rayuwa ga bawa. Dan da wahala kaga mutum yaci wahala a rayuwarsa daɗi da farin ciki basu biyo bayansaba. Bawai dole sai a duniyaba. dan UBANGIJI yay mana alƙawarin samun babban tagomashi a lahira da yafi na duniyar komai. Dan kaci wahala a rayuwarka ba dolene sai kayi arziƙiba a ƙarshe. Ba dolene saika zama mai ɗaukakaba a ƙarshe. ba dolene saika zama tauraron al'umma ba a ƙarshe. UBANGIJI zai iya sakanka makane ta hanyar da kaima bakai zatoba. Amma fa saika zama mai juriya da haƙuri wajen karɓar jarabawarka da ƙaddararka. ALLAH kai riƙo da hannayenmu a komanmu😭🙏🏻). ★★★★            Bayan farkawar Zinneerah a barci kusan ƙarfe huɗu suka baro Kusada zuwa danya. Kallo ɗaya zaka fahimci ransu a dagule yake su duka. Zinneerah kam bama a iya tantance halin tashin hankali da ruɗanin da take a ciki. Sam zuciyarta da ƙwaƙwalwar kanta basa aiki irin na kowanne mutum. Abubuwa da yawa ke zuwa mata a rai game da wannan ciki, har kashe kanta ta ayyana yi amma wani ɓangare na zuciyarta ya ƙwaɓe akan wannan ba mafita bace.       Tunda mashinansu suka shigo garin idanu caa a kansu. A take ƙananun magana suka fara tashi akan wai ankai Zinneerah kusada ne an zubar da ciki. Su dai basu san sunayi bama. Wani matsanancin tsoro ne ya shiga zuciyar Zinneerah ganin sun iso gida. da ga ita sai Gwaggo Laritu suka iya shiga gidan. Su kawu juyawa nasu gidajen sukai abinsu dan basusan yanda zasu tunkari yayansu da wannan magana ba. Gashi likita yace abar Zinneerah ta huta na kwana biyu kamar yanda jikinta ke buƙata.      Mata ne cike da gidan danƙam anata arerewa da guɗa. Dan masu kiɗan ƙwarya Inna ta kira suke wasa a gidan wai yau take nata yinin bikin. Da farko har suka shigo gidan sukama kusa kaiwa ɗakin kwanan su Zinneerah babu wanda ya kula da su. Suna gab da shigewarne Inna ta hango Zinneerah. A tsawace tace, “K! K! K! Dakata mani. Masu kiɗa ku saurara kaɗan ina zuwa”.       Kamar wadda tai busa da sarewa a kunnuwan jama'a a take gidan yay tsit, hankalin kowa ya dawo kan Zinneerah da Yaya Gajeje yasata saurin nufosu itama. Kusan a tare suka iso gaban Zinneerah ɗin, inna ta kalla Gwaggo Laritu datai kamar batajiba tana neman shigewa ɗakin su Zinneerah ɗin.          “Lallai ko ba'a faɗaba yanayin da kuka shigo mani gida kawai ya tabbatar da zancen ciki......”       Da sauri Gajeje ta katseta da faɗin, “Haba Inna wacce irin maganace haka? Wannan ai zancene na cikin gida ko”.      Harara Inna ta watsama Gajeje, ta kai hannu ta finciko hannun Zinneerah da kanta ke a ƙasa hawaye masu zafi na ziraro mata a saman kumatu. Hannu tasa ta yaye hijjab ɗin jikinta ta jefar. Ta kama rigarta zata cire Gwaggo Laritu ta riƙeta a fusace. “Wlhy! Wlhy wlhy kinji na rantse sau uku, inhar kika hiddama yarinyar nan riga yau saina nuna miki ni jinin gidan baduku ce Asabe. Wai kina tunanin ana tsoronkine ko me? Mi yarinyarnan ta tsare maki a gidan nan ne wai shin? Idan ma cikkinne da gaske a jikinta ai kece silarsa. Dan kece kika hana mata rayuwa zaman lahiya kamar yanda kika hana ubanta. Ya auro mahaifiyarta dan yaji sauƙi kika shiga kika hita sai da kikaga tabar gidan saboda son zuciyarki. Wama yasani yanzunma ko kece kika biya aka lalatama yarinya rayuwa, dan wlhy duk abinda akace kinyi Asabe nasan zaki iya mahiyinsa saboda son duniyarki”.       Tofa babbar magana. Waɗan nan zantuka na Gwaggo Laritu a take ya hargitse gidan, kafin kace mi taron biki ya zama taron faɗa da bala'i. Tun anayi a cikin gida har aka koma ƙofar gida, abu kamar wasa sai ga ƙaramar magana ta zama babba. Dan kuwa dai faɗa ya juye tsakanin dangin Baba dana Inna. Yayinda jama'ar gari suka rabu gida biyu, wasu na goyon bayan Inna wasu na goyen bayan dangin Baba da Zinneerah. Abu yay tsamari har magriba babu alamar zasu sarara, daga ƙarshe dai sai da zance ya kaisu ga gidan mai-gari daya aiko aka tattaresu zuwa can.          Sosai zancen ciki a jikin Zinneerah ya tayarma mai-gari hankali. dan har ransa yakejin ƙaunar yarinyar da tausayinta. Tun a randa sukazo shari'arnan shi kaɗai yasan abinda ke ransa game da Zinneerah. Dan ya ɗaukama kansa alƙawarin zai tsaya mata tai karatu, kuma ɗansa dake karatu yanzu haka a Katsina shi yake burin zama mijinta. Sai kuma gashi yau wannan magana maiban tashin hankali ta ɓullo rana tsaka.      A yau ma tambayar duniya anma Zinneerah akan wanene mai ciki tace ita bata taɓa aikata iskanciba, dan haka batasan ina ta samo ciki ba. Lallai wannan al'amari ya kai a kirasa MAKAUNIYAR ƘADDARA, ita da ciki ke jikinta batasan yanda samuwarsa ta wanzuba, su kuma dake tuhumarta ina zasu kama?.       Ganin dare yana neman rufawa mai-gari yace suje gida gobe idan ALLAH ya kaimu zai nemesu, dan wannan magana babbar maganace dolene sai sunje ga hakimin kusada ko a samo bakin zaren a can. Wannan magana ta tadama Inna da Zinneerah hankali matuƙa. Ita Inna tsoronta ALLAH tsoronta a gano gaskiyar da sa hannunta Zinneerah ta tafi Katsina. Saukinta ma Hajji Lanti bata dawo garinba ai tun tafiyar da tai dasu Zinneerah ɗin. To amma tasan akaje gaban hakimi ai ca za'ai sai wajen ƴan doka (Police) da ga haka kuma sai wajen alƙali. Lallai tsugunne bata ƙare ba kenan, ba burinta kenanba, babban burinta kawai Zinneerah tabar mata garin baki ɗaya dan bata ƙaunar ganinta a cikinsu kamar yanda ta tsani mahaifiyarta sanda tana tare da su.        Sanin halin inna yasa Gwaggo Laritu tafiya da Zinneerah gidanta, bayan ta saka Sa'a ta tattaro mata duk kayan Zinneerah dake a can gidansu dan dolene ta dawo zama a gidajen ɗaya daga cikinsu har ALLAH ya sauketa lafiya.           Tunda suka shigo gidan sam hankalin Zinneerah baya a jikinta. A hankali wani irin tsanar garin Danya da komai nasa ke shiga jikinta. Koda Sa'a ta kawo mata kayanta tana zaune can rakuɓe kanta cikin ƙafafu, ba kuka takeba ba kuma tunani ba. baƙon al'amarin dake shiga cikin jikinta ne kawai ke ratsata. Ta ɗago ta kalli Sa'a data dafa ta, ganin yanda Sa'a ke hawaye ya sata sakin wani murmushi maiban mamaki, batare da tace komaiba ta maida kanta yanda yake.         Hankalin Sa'a ne ya ƙara tashi, dan a duk sanda taga irin wannan murmushin a fuskar Zinneerah to takai ƙololuwa a shiga tashin hankalin rayuwa kenan. Dan duk lokacin da takurawa da matsawar Inna yaymata yawa bata kuka. Ko nuna tausayinta sukai kuma sai dai tai musu wannan murmushin bazata taɓa ta tanka ba.           Zuciyar Gwaggo Laritu a kusa take ainun da baƙin cikin halin da suke ganin Zinneerahn ta jefa kanta. Da kuma haushin Inna dana Baba da ya koma tamkar mara amfani agaresu, yanzu haka a kaf ruguntsumin nan da akeyi yaƙi cewa ƙala. Wanan takaicin da sukai mata yawane ya sata shigewa ɗaki tabar Zinneerah waje zaune batare da tace taje ta kwanta ba. Sauƙinta ma itama su kaɗaine a gidan sai matan ƴaƴanta biyu, suma kuma an katangema kowa sashensa babu mai ganin wani.        Abinka da ƙauye ahankali garin ya fara ɗaukar shiru. Har takai Zinneerah dake zaune a ƙofar ɗakin Gwaggo Laritu barci ɓarawo ya saceta har takai ga zamewa ƙasa ta kwanta akan sumintin wajen tai filo da jikkar kayanta da Sa'a ta kawo da yake ba wata babba bace, dan kayan nata basu wuce a ƙirga ba.         Barci ne sosai mai nauyi yay gaba da ita, yayinda itama acan Gwaggo Laritu datai tunanin idan Zinneerah ta gaji da zaman wajen zata shigo ɗaki ta kwanta barcin yay gaba da ita dan gajiya.          Tamkar wadda akace ta tashi Zinneerah ta miƙe zumbur, babu wani tunani ta ɗauki jikkar kayanta ta nufi hanyar ƙofar gidan nasu Gwaggo Laritu. A hankali ta zare sakatar murfin gidan ta fice kamar tana tsoron wani ya jita koya ganta. Kallon gabas da yamma kudu da arewa tayi, garin tsit babu alamar akwai wani rai mai numfashi, ga wata yayi nisa babu wani hasken kirki, ga sanyi kasancewar lokacinsane sai dai farko-farko dan baiyi ƙarfi ba. Ta sauke wani nannauyar ajiyar zuciya ta fara tafiya babu alamar tsoro ko fargabar jin garin shiru tattare da ita sam.            A cikin daren nan Zinneerah ta nausa kanta cikin daji batare da alamun akwai hankali a jikintaba, dan yanda take matsoraciya ko fitsari ya kamata da dare sai ta tada Yaya Sa'a ta rakata. Amma yau sai gata a hanyar daji cikin tsakkiyar dare babu ko gezau.............✍ Hasbinallahu wani'imal wakil. Ya rabbu ka iya mana da abinda yafi ƙarfinmu, harma da wanda mukafi ƙarfinsa.😭🙏🏻        *_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 _Na Safiyya Huguma_ *_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖 _Hafsat Rano_ *_★ DALAAL_*💝 _Na Miss xoxo_ *_★ UBAYD MALEEK_*💓 _Na Mamu gee_ *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 _Na Bilyn Abdull_ Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 *_08085405215_* IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   0903 234 5899 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 https://youtu.be/NgqdCTVKOF8 Channel name Abdul-rahmaan. He's a very young boy who's passionate about becoming one among the huffaz, he loves reciting the Holy Qur'an even at his younger age. He has memorized so many surahs within juz ammah. please help him grow his channel fisabilillah and also pray for him to be come a Hafiz in future in sha Allah. Jazakumullah khair ________________________ *_TYPING📲_* *_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_* *Page 7* ...........Tafiya take batare da tasan ina take dosaba. Gashi babu alamar gajiyawa tattare da ita, duk da mai kallo a kallo ɗaya zai iya fahimtar lallai tana tare da gajiyar, amma ita kasancewar bata cikin hayyacinta bata saniba. Babban burinta kawai tai nesa da garin Danya baki ɗayansa. Bata damu da yunwa da ƙishirwar dake damunta ba, balle ta tuna bayan ita akwai wata halitta a jikinta dake buƙata idan ita bata buƙata.             Kusan dai-dai ketowar alfijir ta iso bakin titin da batasan kona wane gari bane. Batai kuma tunanin son ta sani ɗinba ta zube a ƙofar wani shago ta kwanta cike da gushewar hankali dana tunani. Wani irin nannauyan barcine ya ƙwasheta kuwa, kafin wani dogon lokaci ta fara sauke numfashi...... ★★★★          Tsabar gajiyar da suka kwasone a yinin yau ya saka Gwaggo Laritu barci mai nauyi sosai, har takai da sai da babban ɗanta ya leƙo sashen domin tada ita da asuba. Dan da kullum itace mai tashinsu, amma sai gashi yau sun rigata su. Rashin jin motsinta kuma ya tabbatar masa da makara tayi kenan.        Tashi tai da ƙyar tana mamakin barcin da tai haka mai nauyi. ga ƙofartata buɗe alamar Zinneerah bata rufe musu ba. Kallon saman gado tayi inda ta bar mata ta kwanta dan ita dama bata iya kwanciya a gado sai ƙasa. Ganin babu kowa a gadon tai tunanin ko Zinneerah bayi ta shiga ita ta tashi ne.      Bata damuba ta fito gabatar da alwala. Saboda tunanin Zinneerah na bayin ya sata zuwa can wajen dabbobinsu tayo fitsari tazo tai alwala kar makarar tai yawa. Hankalin Gwaggo Laritu bai sake tashi ba sai da taga harta idar da salla gari yay ɗan shaaaa babu motsin Zinneerah. Ajiye carbin da take ja tayi ta fito tsakar gidan. Ganin babu alamarta ya sata nufar ƙofar bayi tai gyaran murya. Shiru. ta sakeyi, nanma shiru. Sai kawai ta danna kai. Gabanta ya faɗi ganin babu alamar anyi amfani da bayin ma. A rikice ta fito, hakan yay dai-dai da dawowar Awwal babban ɗanta daga masallaci, shi Safiyanu yana Lagos neman kuɗi.       “Mama lafiya kuwa? Mi kike nema?.”        A rikice tace, “Zinneerah wannan yaron (bata faɗar sunansa saboda ɗan fari). Ban gantaba”.       Da mamaki shima yace, “Dama anan ta kwana? Ko zuwa tai yanzu da sahe?”.         “Anan ta kwana mana. tare da ita muka taho nan saboda gidan nasu kasan akwai mutane bazai yuwu zama gareta ba ai ko?”.       “Hakane Mama”. Ya faɗa yana cigaba da lalleƙa ko'ina na sashen nata. Har takaisa ga fita nasu sasssan. Har sashen ƙaninsa Safiyanu ya tambayi matar tace bataga Zinneerah ba itakam. Bama tasan anan ta kwanaba, dan sanda su Gwaggo Laritu suka dawo gidan tayi barci kasancewar tanada tsohon ciki dama.      Wani tunani ne yazoma Awwal a rai, dan idan bai mantaba dazai fita salla a buɗe yaba ƙofar zaure. Ya dawo sashen Gwaggo yana faɗin, “Lallai Mama akwai matsala. ALLAH yasa yarinyar-nan ba guduwa tai ba, dan wlhy a buɗe naga ƙofar soro yau, kuma na tabbatar bazaki kwanta baki rihe ba”.         “Hazbunallah! Wlhy na rihe wannan yaron, ni kuma takaici da damuwar da suka haɗu sukaimin yawa ya sani shigewa na barta anan zaune akan idan ta gaji da zaman zata shigo ɗaki ta kwanta. Aiko zama bai ganniba bara muga ko tana gidan nasu”.        “A'a mama yi zamanki ni bara inje”.       “Kai dai barsa naje. Ai ba fasa zancen za'aiba cikin hikina za'a dubata. Dan dama dole naje gidan saboda aiki tunda yau ne ɗaurin auren Karima ”.       Badan hakan ya masaba ya haƙura. Dan har ransa yana son Zinneerah da tausayinta matsayinsa na ɗan-uwanta.        Koda Inna taje gidan bata shigaba. Dan dama batazo danta shiga ɗinba. Tayi alƙawarin har agama wannan bikin bazata leƙa gidanba. Sunbar Inna da ƴaƴanta kamar yanda tafi buƙata. Yaro ta samu ta aika ya kira mata Sa'a anan maƙauftansu da yace sun kwana ita da su Karima.. Babu jimawa kuwa sai gata ta fito tana mutstsukar ido alamar yanzu ta tashi. Ko gaisuwarta Gwaggo Laritu bata tsaya amsawaba tace, “Sa'a shiga gidan nan naku cikin hikima ki dubamin Zinneerah ”.         “Gwaggo Zinni kuma? Ba'a gidanki ta kwanaba dama?”.       “Nidai ba surutu na tambayeki ba, jeki fara dubawa”.       Kai Sa'a ta kaɗa tana nufar cikin gidan da ƴar hayaniyar waɗanda suka tashi ta fara kaurewa. Babu wanda ta tambaya ta shiga neman Zinneerah a gidan. Sai dai babu mai ko alamarta. A rikice ta dawo ta sanarma Gwaggo Laritu. Itama sai ta sake ruɗewa...... ★★★★          A ɓangaren Zinneerah kuwa barci tasha sosai a ƙofar wannan shago har fitowar rana. Sai da mai shagon ya fitone ya tadata domin buɗewa. Tashi tai kawai ta matsa gefe batare data tanka masa ba. Shima ɗin bai tanka ba dan kallon mahaukaciya kawai yake mata duk da babu alamar datti a jikinta. Saɓanin kwanciyar yanzu kam zama tai tana kallon motsin mutane dana wucewar motoci. Babu abinda take fahimta dan ƙwalwarta ba aiki take irin na mutane ba. Ga yunwa mai tsanani na cinta. Dan haka ta ƙurama mutane dake a runfar mai-shayi dake acan tsallaken titi idanu sunasha suna kwasar hira da dariya da gaddamar siyasa. A hirar tasunema takejin sunan garin da take a yanzu mai suna Tsanyawa.        Mai shagon ne ya lura hankalinta na ga masu shan shayi, haka kawai yaji tausayinta, dan haka ya fito zuwa tsallaken ya siyo mata shayin da biredi harda indomie.        Wajenta ya dawo yana murmushi, “Baiwar ALLAH kina son kici ko?”. Ya faɗa yana kallonta. Batace komaiba tai ƙasa da kanta kawai tana wasa da yatsun hannunta. Murmushi ya sakeyi shima ya ajiye mata filet ɗin indomie ɗin da kofin shayin da aka ɗora biredi a sama. “Gashi to kici”. Kanta ta rausaya masa kawai taja filet ɗin nanma batai magana ba. Batai ko tunani wanke hannu ba balle yin sallar asuba. Tasa hannu ta hau cin abincin a nutse kamar yanda nutsuwa ta kasance jinin jikinta dama can. Citai ta ƙoshi tai gyatsa. Batare da wanke hannunba ma a yanzu ta zame ta sake kwanciya sai barci.        Sosai tausayinta ya sake cika zuciyar mai-shagon nan. Yazo ya kwashe kayan data gama cin abincin batare da yayi magana ba.        Yanzu ma barci sosai Zinneerah tasha a wajen, dan bata farkaba sai gabanin la'asar. Zama tai tana kallon mutanen garin daketa faman kaiwa da komawa, dan wajen ya sake cika fiye da ɗazu da safe. Ga titin motoci nata kai kawo suma. Mai-shagon nan ne dai ya fito salar la'asar ya ganta zaune ta tashi. Cike da tausayinta yace, “Baiwar ALLAH kin tashi ashe?”.      Bata tanka masaba yanzu ma. Tadai ɗago kai tai masa kallo guda ta maida kanta ƙasa. Yanzuma kamar ɗazun murmushi yayi, ya nufi inda masu abinci suke ya siya mata yazo ya bata. Kamar ɗazu bata tankaba bakuma ta wanke hannu ba tahau ci, tare da ɗaukar ledan ruwan ta fasa tasha ta ƙoshi tana lumshe idanu. Tamkar ɗazun sai ta sake zamewa a wajen ta kwanta sai barci.      Mai shagon ya dawo sallar la'asar ya ganta ta koma barci, mamaki ya kamashi sosai ganin barci bai mata wahala. Yama fahimci yunwarce ke tadata kenan. Barcin kuma shine salon nata lalurar.      Har lokacin tashinsa yayi kusan ƙarfe takwas na dare bata tashiba. Ya sai abinci ya ajiye mata bayan ya rufe shagon ya wuce gida.          Zinneerah bata farka ba sai kusan sha biyun dare. Yanda ta tashi tana riƙe ciki da matse fuska zai baka tabbacin yunwace. Idonta na sauka akan roba rufe da leda tai saurin jawowa kuwa. Ganin abinci jikinta har rawa yake ta hau ci. Sai da ta cinye tas tasha ruwa sannan ta miƙe tamkar an tsikareta. Jakkar kayanta ta ɗauka ta fara tafiya tamkar daren jiya dan jitai gaba ɗaya nanma ta tsanesa. Burinta kawai ta ƙara gaba tai nesa da garin na Tsanyawa.         Tafiya take cikin gushewar hankali da tunani tamkar daren jiya. Gashi abin tashin hankalin yau a kan titi ne. Sauƙinma darene babu yawan mitoci sai jefi-jefi. Haka dai ta cigaba da nausa kanta cikin kariyar UBANGIJI a wannan dare ma..... ★★★            Hankalin kowa ya tashi na rashin ganin Zinneerah ɗin, dan Gwaggo Laritu kasa haƙurin ɓoye rashin ganin nata tai sai da ta fasa. A take aka shiga nemanta lungu da saƙo na garin, sai dai ganin har wani daren ya sake rufawa kowa ya fahimci dai da gaske Zinneerah ta sake guduwa kamar yanda Inna ke faɗi cike da gadarar tabbatarwa tana dariya kuma.         Kuma duk da tashin hankalin rashin ganin Zinneerah ɗin a haka aka ɗaura auren Babawo da Karima. Aka kuma kaita gidan mijinta a wanann daren. Dan zasu fara zama anan Danya kafin su wuce Kaduna kamar yanda ya faɗa.        Washe gari an sake tashi da neman Zinneerah a ƙauyikan kusa da su har zuwa kusada ko za'aji labarin tahau mota zuwa wani waje. Babu wani labari makamancin an ganta da suka jiyo. Haka suka dawo gida cike da damuwa da tashin hankalin wannan al'amari.         Ran Inna ya ɓaci dan ba haka tasoba. Sotai ace kowa ya dinga zagi da faɗin Zinneerah guwa ta sakeyi wajen karuwancinta. Amma sai taga saɓanin hakan kowama sai tausayinta yakeyi da damuwa da halin da zata shiga bayan wanda ta tashi a ciki. Sa'a kuwa kuka taci na tashin hankali ita da Yaya Gajeje, har takai Sa'ar da kwanciya zazzaɓi mai zafi. Duk da Atine ba damuwa tai da Zinneerah ba ita kanta saita wuni sukuku da ita, dan jini ya wuce wasa ai. Wannan yasa duk bikin na Karima yaƙi armashi kamar yanda Inna taci buri. An ɗaura aurene kawai hankalin mutane ba'a kwance ba.        Kamar ko yaushe yanzunma Baba baice ƙalaba akan al'amarin, sai dai a kallo ɗaya zaka fahimci tsantsar tashin hankali da damuwar dake a tattare da shi. Yana tsananin so da ƙaunar Zinneerah, musamman daya zam soyayyar da yakewa mahaifiyarta bayan barinta gidan nasa duk sai ya tattarata akan Zinneerah bayan itama wadda yake mata. Dan wannan tsantsar soyayyar Inna ta hango tattare da shi ai ta shiga ta fita ta raba tsakaninsa da ƴar tasa har bai iya cewa uffan akan al'amarinta a gidan.       Haka wannan dare ya kasancewa duk wani masoyin Zinneerah a cikin tashin hankali da damuwa da tausayinta. Inda washe gari kuma suka sake tashi da wani sabon tashin hankali na barin baba shima garin.     Wannan tashin hankalinne ya sake ruɗasu suka sake ƙare yinin ranar da neman Zinneerah da Baba a dukkan garuruwan dake da maƙwaftaka da su. Sai dai babu koda labarin ɗayansu. Yau kam saɓanin jiya harda Inna a wannan tashin hankalin. Dan bata taɓa tunanin Baba zai iya bin bayan Zinneerah ba. Duk haukanta da rashin tausayi tana bala'i-bala'in son mijinta uban ƴaƴanta. Dan badanma soyayyar da take masanba bazata taɓa  zuwa wannan ƙauyen ta zauna ba da sunan aure. Saboda garinsu Marabar musawa yayi ashirin din Danya yawa da komai na kayan more rayuwa. ★★★         Tamkar jiya yau ɗinma sai gabannin asuba Zinneerah ta yada zango a wani ƙaramin ƙauye da ke a bakin titi. Yau kam a ƙarƙashin wata bishiya ta samu ta kwanta sai barci. A haka mutanen ƙauyen suka wayi gari suka ganta. Da farko ma su tsoronta suka farayi, dan a fuska da jikinta babu mai ɗaukarta mara hankali kasancewar komanta fes yake. Haka yara suka zagayeta harma da manyan kowa ya kasa zuwa inda take. To duniyarce babu gaskiya ai.        Barcinta tasha sosai sai wajen sha biyu ta farka da yunwa kamar jiya. Ta shiga bin mutanen dake zagaye da ita da kallo ɗaya bayan ɗaya. Batare da tayi magana ba ta maida kanta ƙasa ta duƙar tana yamutsa fuska da dafe cikinta dan yunwa takeji sosai.          A ɗan tsorace wani dattijo a cikinsu yace, “Mutum ce ko aljana?”. Banza Zinneerah tai bata amsaba, sai faman riƙe ciki take ita dai. Kusan min tuna biyar ta ɗago tana kallonsu hawaye na zirara mata. Cikin rawar murya tace, “Dan ALLAH ku bani abinci”.       Kallan kallo suka shigayi a junansu batare da wani ya amsa mata ba. Cikin fisgar numfashi ta kuma faɗin, “Abinci dan ALLAH zan mutu”.          Tausayintane ya kama wani matashin saurayi dake tsaye gefe da jikka a hannu alamar abin hawa yake jira. Ya matso kusa da ita yana faɗin, “Komi aka baki zakici dai ko?”.      Da sauri ta kaɗa masa kanta. Fuskarsa cike da tausayinta ya zaro hamsin a aljihu ya bama mai wainar ƴar tsala ta gero a gefe yana faɗin, “Bata ta duka”.        Amsar kuɗin mai ƴar tsala tayi ta zuba mata wainar a roba, tasa yaji a gefe ta miƙawa saurayin. shine ya ajema Zinneerah gabanta, zata saka hannu ya dakatar da ita akan ta bari ta wanke hannun. Ina bata sauraresaba ta hau cin kayanta hannu baka hannu ƙwarya. Sai gashi cikin ɗan ƙanƙanin lokaci ta cinye tas. Ruwan da ya ajiye mata dan wanke hannu ta raruma ta kafa kai tasha sosai. Sai gata tana lumshe idanu da sakin murmushi, a fisge tace masa “Nagode”. Daga haka ta zame ta kwanta a wajen sai barci.         Yanda tai din ya bama kowa mamaki, sai dai bayanin wani tsoho ya sakasu maida kallonsa garesu.        “Wannan yarinyar ba mahaukaciya bace, da alama kurciya akai mata ko makamancin hakan”.       “Baba lado miye kurciya?”. Saurayin da ya sai mata ƴar tsala ya tambayi tsohon. Kamar tsohon bazai sake magana ba, sai kuma ya ɗan girgiza kansa yana mamular goron dake bakinsa. “Kurciya asirine mana shamsu. Akan yima mutum idan ba'a son ya zauna a waje. Akanyi asirin a jikin tsuntsuwar kurciya. Duk inda kurciyar ta nufa can mutum zai nufa shima”.          A take jikin mutanen wajen yay sanyi, tausayin Zinneerah da batasan sunayiba ya shigesu sosai, suka shiga ambaton ALLAH ya saka mata.          Yauma kamar jiya yunwa ce kawai ke farkar da ita. Data samu taci saita koma barci, da daddare tsohon nan ya saka aka kama masa ita zuwa gidansa da nufin zai taimaketa. Babu musu kuwa matarsa ta amsheta hannu bibbiyu dan dama ya mata bayani akan Zinneerah ɗin hasalima itace ta bada shawarar su taimaketa.      Sai dai kuma yauma cikin daren ta farka a firgice kusan ƙarfe ɗaya. Cikin sanɗa ta silale tabar gidan dan ko katangar kirki tsoffin basu da ita. Haka ta ɗauki hanyar titi taita tafiya cikin ficewar hayyaci. Sai dai wayar gari sukai babu ita. Sun tausaya mata matuƙa. Dan basusan inda ta nufaba kuma. gashi ko jikkarta bata ɗaukaba nan ta barta a gidan nasu.        Haka al'amari ya cigaba da kasancewa akan Zinneerah. Duk inda asuba tayi takan tsaya ta yada zango, a wani garin ta samu tallafin abinci, wani garin kuwa babu mai kallonta. Dan zuwa yanzu kamanninta sun fara canjawa saboda rashin wanka da sauran buƙatu. Ba kullum take samun damar yada zango a gariba. Watarana a daji take yada zangon, haka zata yini kuka da juye-juyen yunwa har barcin nata na ƙa'ida ya ɗauketa.        A randa ta cika kwanaki goma sha ɗaya da baro gida ALLAH ya iso da ita cikin garin kano, inda ita batasan inane ɗinba. Sai dai taga yawan jama'a da gine-ginen nan yafi na duk garuruwan data baro a baya. Anan ɗinma ba a hayyacinta takeba. Dan kamar yanda ta saba kwanciya da tashi taita tafiya haka ta cigaba dayi, hakanne yasa taita nausa kanta cikin ƙwaryar kano sosai har batasan tanayiba.      Zuwa yanzu har takai kowa kallon mahaukaciya yake mata, dan yaran kan tsokaneta. Harma manyan sukan koreta idan ta ɗan laɓaɓa wani gurin zata huta ko tana neman abinci. A haka ta sake share kusan sati biyu cikin ƙwaryar kano, indan kuma an haɗa da barowarta gida tana neman ƙulla wata ɗaya. Ɗan cikinta ya fara fitowa fili kowa yana gani, duk da ba wani uban girma yayiba na azo a gani.            Duk da yanayin da take ciki haka take kasancewa cikin laulayi, dan kusan kullum da zazzaɓi take kwana, wani abin kuma idan taci takanyi amansa dan baya zama.      Yau data kasance juma'a mutane nata kai kawo na zuwa masallatan juma'a a cikin garin na kano, wanda a yanzu haka Zinneerah na gab da barin garin tana neman ɗaukar hanyar jigawa dutse. Tafiya take a hankali cike da kasala saboda rashin samun inda zata raɓa ta kwanta tun ɗazun, dan tun barcin gabannin asuba data kwanta a ƙofar wata maƙaranta gari na wayewa aka korota. Shine har yanzu bata samu ta sake samun wajen kwanciyarba kuma. Ga yunwa na cin hanjinta da zazzaɓi. Tun tana tafiya tana kallon inda take saka ƙafarta har takai idanunta sun lulluɓe da duhu.              Gudu motar takeyi sosai daga hanyar jigawa tana nufo cikin Kano. Yanda passengers ɗin cikin motar basu damu da gudun da direban keyiba zai tabbatar maka da suma son ai gudun suke dansu sami sallar juma'a cikin jam'i.          Sam idonsa bai kula da abinda ke gabansaba sai da yazo gab. Yay ƙoƙarin taka birki yana salati kamar yanda suma fasinjoji keyi cike da tashin hankali da ruɗani, sai hakan ya gagara dan sun riga sunzo gab da ita. Gashi ita kuma sam batajin uban horn ɗin da drivern ke zabga mata da iyakar ƙarfinsa ba.      Ji kake wani ƙuuuuuuuu!!!!!! Motar ta bada sauti mai ban tsoro, yayinda razananniyar ƙarar da zinneerah ta ƙwalla saboda azaba ta danne ƙarar ƙugin da motar tayi.. Cikin tsananin tashin hankali kowa dake a cikin motar yake ƙoƙarin fitowa. Dan cikin amincin ALLAH babu abinda ya faru da kowa a cikinsu. Gaba ɗayansu kan Zinneerah dake kwance wanwar a ƙasa sukayi kowa na salati a rikice.............✍             *_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 _Na Safiyya Huguma_ *_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖 _Hafsat Rano_ *_★ DALAAL_*💝 _Na Miss xoxo_ *_★ UBAYD MALEEK_*💓 _Na Mamu gee_ *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 _Na Bilyn Abdull_ Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 *_08085405215_* IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   0903 234 5899 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 *_TYPING📲_* *_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_* *_Page 8_* ________________________ *ZAUREN GIRKI* Abinci na *gargajiya* ...Kuka,Taushe,Danbu, Sinasir,Waina Abinci na *zamani* ...Afang,Edikaikong, Coconut Rice, Ofada Rice *Garabasa* ...Salads,Pancakes, Plantain mosa, Gyaran nama/kifi kafin girki,Shirin/shinfida abinci kan table. • A kowane sati,in shaa ALLAAH, za a koyi miya/abinci daya da kuma wani abu ta karkashin *Garabasa* . • Duk ranar *Lahadi* za fito da sabobin *videos* guda biyu na miya/abinci da na wani abu daga karkashin *Garabasa* . • Kowacce daga cikin masu koya zasu bibiya video su kwaykwaya su gwada yin abincin bisa ga umurnin *video* • Kowane ranar *Asabar* za a yi *Q&A* a inda kowa zai samu yin tambayoyi akan *videos* din satin daya gabata, da inda suke neman karin bayani/gyara akan kokarinsu na gwada abincin *video* da kawunansu • Ga wace taga dama,daga ranar *Talata* za a iya fara turowan *video* ta kokarin da aka yi na kwoyon abincin da aka kwoyar ta *video* na ranar *Lahadi* . • Inda akwai me bukatan wani fanni na abinci,ana iya hada *aji(Special Personal Video Classes)* musamman domin wannan bukatan.Anan za a shirya live *video* sessions domin cimma wannan burin • Za a biya dubu biyu *(#2,000)* na watan farko,sannan za dinga biyan dari biyar *(#500)* ta kowane sati ga masu bukatan shiga group dinnan namu mai albarka • *Zen Commute,account number 0119343451 Union Bank* ,asusunmu • Duka lokacin da aka biya sai a turomana da hoton teller ko bank confirmation akan wannan number ta *WhatsApp 0817-541-7533* • Ana iya tuntubammu akan wannan number domin karin bayani; **0817-541-7533(WhatsApp kawai)*                                   ZA MU FARA ZAUREN GIRKI LAHADIN SATIN FARKO TA WATAR SEPTEMBER,IN SHAA ALLAAH! *MU TSARE MUTUNCINMU,MU KARE MAZAJENMU...MU KOYI GIRKI!!!* __________________ *Page 8* ..........Ko tsayawa fahimtar a ina taji ciwon direban baiyiba. Kasancewarsa mutum tamkar ruɗaɗɗe, abu kaɗan ke gigitashi. A yanzu hakanma jikinsa sai rawa yakeyi.      “Dan ALLAH ku taimaka a sata a mota muje asibiti karta rasa ranta”. Ya faɗa a gigice da rawar jiki saboda jinin dake zuba a jikinta da basusan ko daga ina bane.       Suma kansu yanda ya rikice ɗin sai hankalinsu ya ƙara tashi, ga yarinyar tunda tai ƙarar farko bata sake ko motsiba alamar numfashinta ya rabu da gangar jikinsa. Ga jinin dake fita a jikin natama tashin hankaline mai zaman kansa.      Wani abokinsa driver ne daya tsaya  a wajen kamar yanda yaga motoci nata tsayawane ya nufesu a rikice. “Ya ilahi, Naziru Accident kukayi haka?”. Cike da tashin hankali ya bashi amsa. “Wlhy bugeta nayi Malam Abubakar, sam banga yarinyarnan ba sai da mukazo gab da ita. Nayi ƙoƙarin kauce mata kuma hakan ya gagara”.         “Hasbinallahu wani'imal wakil. Inaga to kusata a mota, wasu ƴan motar taka saisu dawo nan wajena tunda ba mutane sosai”.      Kowa yayi na'am da wannan shawaran, dan haka a take sukayi hakan kuwa. Cikin kano suka ƙarasa shiga, inda kai tsaye suka nufi wani asibin kuɗi kamar yanda wani a motar ya bada shawran, dan sunsan yanzu idan sunje na gwamnati wani sabon turancine zai tashi na maganar ƴan sanda da sauransu. Cikin amincin ALLAH suna zuwa kuwa aka amshesu kasancewar ansan shi wanda ya bada shawaran. Ashema yana taɓa aiki a asibitin. Da taimakon wannan bawan ALLAH aka shiga bama Zinneerah da batasan ina kanta yakeba taimakon gaggawa.            Alhmdllh kusan awa ɗaya da rabi saurayin nan da likitan da suka taimaketa suka fito, fuskar saurayin da murmushi yace, “Alhmdllhi kowa ya kwantar da hankalinsa komai yazo da sauƙi, cikin ikon ALLAH ma bataji wasu ciwuka masu tsauriba, sai dai cikin jikinta da ƙyar aka samu ya tsaya, saboda shi ne ma zamu riƙeta dan tana buƙatar kasancewa a ƙarƙashin kulawar likita na kamar sati biyu zuwa uku haka”.          Ajiyar zuciya drivern ya sauke. Hakama sauran fasinjojin da sukai karar biyosu duk suka shiga ambaton Alhmdllhi. Sai dai kuma hankalin drivern a wani fanin a tashe yake. Da damuwa yace, “Amma zamanta sati uku a asibitin nan zan iya shiga wani hali ɗan uwa. Kuɗin gado kansu aikine babba a gareni”.         Murmushi saurayin yayi yana dafa kafaɗarsa, yace, “Karka damu za'asan yanda za'ai insha ALLAH. Idan kuma yarinyar ta farka ai dolene musan daga ina take? A nema iyayenta da mijinta ko”.         Ajiyar zuciya ya sauke yana gyaɗa kansa. Daga haka suka fita zuwa massallacin da basu tayar da sallaba su har yanzun.           Bayan an idar da salla daga can sauran fasinjojin kowa ya kama gabansa. Da ga shi Naziru direba sai abokinsa Abubakar da saurayin nan da ya faɗa musu sunansa Khalipha suka dawo asibitin. Sun sami damar shiga dubata yanzu kam. Tana kwance an saka mata ruwa. Sai hanunta dake ɗaure da bandage alamar taji ciwo a wajen, sai gefen kanta shima da sauran gurare jefi-jefi. Kasancewar an cire mata kayan dauɗar jikinta an saka mata na asibitin kalar green sai taɗan canja kamanni kaɗan. Duk da idanunta a rufe suke sun fahimci dai ta farfaɗo barci takeyi yanzun, dan haka sukaji daɗi har cikin ransu, a fili kuwa suna ambaton Alhmdllh tare da mata fatan samun lafiya. daga haka suka fita domin biyan kuɗi suma suɗanje gida kuma. *BAYAN KWANA UKU*          Kwana uku Zinneerah na samun kulawa a asibitin da taimakon Khalipha dake tsaye akan komai. Dan koda direba Naziru ya bada iya kuɗin da ALLAH ya hore masa Khalipha ɗinne ya ƙara wasu aka biya kuɗin gado harna kwana goma, yace idan da buƙatar tafi waɗanan kwanakin sai asan abinyi. Alhmdllh jikin nata da sauƙi, dan ƙananun ciwukan harsun fara nuna alamar warkewa saboda bata da ƙan jiki, sai dai hannun natane take kuka da shi dan ta samu tsagewar ƙashi ne. Amma shima Alhmdllh yau ta tashi da sauƙi.        Abu ɗaya ke tadama su Khalipha hankali, shine da zaran dare yayi babu zaman lafiya. Tata zabura kenan akan saita fita a asibitin. A daren farko sun ɗaukama tanada taɓin hankaline, hakan yasa suka danna mata allurar barci mai ƙarfi sosai, wadda ta jata har washe gari da rana tana barci. Sai da likita yay bincike kamar yanda Khalipha ya buƙata sannan suka fahimci lafiyar ƙwaƙwalwarta ƙalau sai dai kuma wani abu daban da basu saniba.       A dare na biyu kam tana farawa wani tunani yazoma Khalipha. Kafin azo ai mata allura ya shiga tofa mata addu'oi, tun tana ɗan fisge-fisgen kaɗan da faɗin ita a barta ta tafi har ta fara lafawa, sai kuma gashi kafinma ayi allurar barci mai nauyi yay gaba da ita. A ranar haka Khalipha ya kwana da abin nan a rai, dan ji yake a ransa tamkar ya santa ko yanada alaƙa da ita. Dare na uku ma tana farawa ya fara mata addu'oin nanma sai gashi ta lafa. To a yau Alhmdllh bayan an cire mata ruwan da aka saka mata Khalipha ya saka wata Nurse ta taimaka mata aka goge mata jiki da duk abinda zai taimaka mata.      Kusan ƙarfe bakwai sai ga Naziru direba da abincin karyawa kamar yanda ya jura kawowa kullum, da rana kuma almajiri yake kawo mata. Idan kuma ya dawo aiki yakan zo asibiti yay kamar awa guda sanann ya wuce gida. Hakan da yake yi nama Khalipha daɗi, shiyyasa baijin ƙyashin taimaka masa akan jinyar yarinyar dako sunanta har yanzun basu sani ba.         Sai da aka gama kimtsata sannan suka shigo ɗakin. Fuskar Naziru washe da fara'ar jin daɗin ganin jikin nata yaketa ambaton, “Alhmdllhi, Alhmdllhi. Kai naji daɗin ganinta haka Malam Khalipha, ALLAH ya saka maka da alkairi, nagode-nagode”.       Murmushi Khalipha yayi idanunsa akan Zinneerah shima yace, “Ai ƙoƙarin ka ne da adalcinka ya kaimu ga wannan nasarar Malam Naziru. Da ace guduwa kayi bayan kawota nan muma bazamu sami ƙwarin gwiwar taimakonta ba, dan direbobi da yawa idan irin haka ta faru guduwa suke subar majinyaci a asibiti koda kuwa ya zama gawa. Yanzu inaga jikin nata Alhmdllh gaskiya, ya kamata musan sunanta da inda ta fito dan mu nema iyayenta da mijinta kodan abinda ke a cikinta”.      Cikin washe haƙora Naziru yace, “Wannan gaskiya ne Malam Khalipha”.        Duk wannan magana dake fita tsakanin Khalipha da Naziru Zinneerah na zaune ne a gadon kanta a ƙasa tana saurarensu. amma ko sau ɗaya bata ɗago ta kallesu ba tanata faman wasa da yatsun hannunta ne kawai kamar bata a wajen ma.        Nurse ɗin dake a gefenta ta ƙarasa gyara mata abinda ya rage ta fice ta barsu. Sai a lokacin su Khalipha suka ƙarasa inda take suna mata sannu. Yanzunma bata ɗago ta kallesu ba. Sai dai cikin rawar murya tace, “Ina yini”. Daga haka tai tsit.      Wannan shine karon farko da sukaji muryarta tana cikin hayyacinta, dan haka sukaji daɗi har cikin ransu. Khalipha yace, “Masha ALLAH, yau dai naji muryar ƙanwata”.        Batace komaiba, kamar yanda bata ɗagoba. Bai damuba, dan ya fahimci akwai damuwa tattare da ita. Zama yay a bakin gadon daga can ƙarshe, dan haka tai saurin janye ƙafafunta data miƙe ta naɗesu. Baice komaiba, sai ma Naziru ne yaja kujerar roba shima ya zauna a kusa da shi. Su dukansu idanunsu a kanta suna kallonta cike da tausayi, dan shekarunta sunyi ƙanƙanta da fuskantar lalurar ciki irin haka a ganinsu.       “Ƙanwata!”. Khalipha ya kirata cike da kulawa..       A karon farko ta ɗago taɗan kallesu, sai kuma tai azamar maida kanta ta duƙar batare data amsa masaba. Ya ɗan murmusa da sake faɗin, “Ki saki jikinki munan duk yayunkine kinji, munason miki wasu tambayoyine, ko zaki taimakemu da amsa?”.       Kanta a ƙasa har yanzu ta gyaɗa masa kanta. Shima kan nasa ya gyaɗa cike dajin daɗin tana fahimtarsu. Ya cigaba da faɗin, “Minene sunanki?”. Shiru bata amsaba. Fahimtar bazata faɗaba ya sashi sake cewa, “A wane anguwa kike anan kano?”. Yanzu kam kanta ta girgiza masa.       Cikin rashin fahimta yace, “baki san anguwarba ko ba'a nan kikeba?”.     Kanta ta ɗaga masa. Naziru ya amshe da sake faɗin, “Ba'a nan kike ba?”.       Kanta yanzu ma ta kaɗa musu. Kallon junansu sukai da mamaki, kafin Khalipha yace, “A wane gari kike to?”.        “Nima ban saniba, na manta komai”.     Ta basu amsa a fisge tana ƙara ƙasa da kanta alamar gajiyawa. Nanma kallon juna sukai cike da mamaki da fargaba. Naziru zai sake magana Khalipha ya girgiza masa kai alamar su barta kawai.       Badan Naziru yasoba yay shiru, Khalipha ya miƙe yana faɗin, “Yauwa to bara na turo sister Salima ta baki abincin kici, dan nasan kina bukatarsa”. Daga haka ya kama hannun Naziru suka fice batare da ya jira amsawarta ba.          Bayansu tabi da kallo har suka fice, ta sauke nannauyan ajiyar zuciya tana lumshe ido. haka kawai take shiga takura da shiga wani yanayin da batasan dalilinsa ba a duk sanda Khalipha ya kasance a ɗakin.         “Malam Khalipha akwai matsala kenanfa idan yarinyarnan batasan wacece ita ba, gata da ciki”  Naziru ya faɗa cike da damuwa sanda suke fitowa.      Ajiyar zuciya Khalipha ya sauke yana furzar da iska. Yace, “Tabbas akwai matsala, amma ni tun daren farko da aka kawota na fahimci akwai wani ɓoyayyen al'amari tattare da ita. Dan yanda take zabura cikin dare da faɗin abarta ta tafi, da safe kuma taita barci yasa nake ganin kamar tana a wani hali. So yanzu dai sai munyi haƙuri munbi a hankali zamu kamo bakin zaren insha ALLAH”.         Numfashi Naziru ya sauke shima. ransa da damuwa yace, “Ni kuma yarinyar kama ma takemin da amaryar Yayana wlhy, sannan maganar ɗawainiyar asibin wani abune mai zaman kansa Khalipha, badan ka taimaka min ba ai bansan yaya zanyiba nikam”.      Murmushi kawai Khalipha yayi, cikin kauda maganar ƙarshe yace, “Kana nufin tana kamani da wadda kasani?”.      “Sosaima kuwa, tun jiya da aka ɗan goge mata jiki naga kamaninta da Maman Sadiq sosai wlhy. Amma dai yau zan kawo matata da yamma dan ina komawa gida da wuri irin yau ɗin, kasan mata sun fimu lura. Kaga sai muji abinda zatace itama”.       “Wannan shawaran yayi Malam Naziru, ALLAH ya jishemu alkairi”.      “Amin ya rabbi, bara nazo na wuce dan na samu damar dawowa da wuri, yau katsina zan nufa insha ALLAH. Kuma sahu ɗaya zanyi na dawo gida”.      “ALLAH ya bada nasara. Ya kuma maido mana daku lafiya”.     Godiya Naziru yayma Khalipha ya wuce. Shima Khalipha sai ya wuce nasa uzirin acikin asibitin. ★★★        Misalin ƙarfe huɗu na yamma Zinneerah na zaune a gadon jinyarta, idanunta tsaye ƙyam akan matashin cikinta, wanda yau ne karan farko data iya zaman masa wannan kallon. A duba guda da zakai mata zaka iya fahimtar ta lula duniyar tunanine. Dan har Naziru direba da matarsa sukai sallama biyu a ɗakin babu amsa.       Kallon juna sukai shi da matarsa, kafin su sake maida idanunsu ga Zinneerah wadda da'alama har yanzu batasan da shigowar tasu ba. Takowa matar Naziru tayi har inda take, ta kai hannu akan kafaɗarta tana sake rangaɗa wata sallamar. Zabura Zinneerah tayi dan kamar daga sama taji sallamar tata. Ganin Naziru tsaye a ƙofa ya saka sauke ajiyar zuciya. Ta janye hanunta data ɗora saman cikin nata tana maida dubanta ga matar Nazirun da tai tsaye ƙyam tana duban Zinneerah ɗin da alamun mamaki a fuskarta.       Kafin Zinneerah tai magana tai saurin faɗin, “Ikon ALLAH, Abban Nasiba kaga kuwa abinda nake gani?”.      Cikin nuna tamkar bai fahimceta ba yace, “Mi kika gani?”.      Ganin kallon da Zinneerah ke musu ne na alamar tsoro ya sakata wayancewa ta zauna kusa da Zinneerah ɗin tana faɗin, “Gani nai ƙanwar tawa ta lula tunani batama san da zuwan namu ba”.      A hankali Zinneerah ta sauke ɓoyayyar ajiyar zuciya da sake maida kanta ta duƙar a ƙasa.     Yayinda shi kuma Nasiru ya kasa ko motsi dan yayi zaton abinda ransa ke raya masa na kamannin yarinyar da Maman Sadiq matar tasa zata faɗa. Sai kuma yaji saɓanin hakan. Jin Zinneerah da matar tasa na gaisawa ne ya sakashi shima ƙarasowa gaban gadon ya ajiye ledan hannunsa yana dubanta da kulawa.         Itama batare data sake ɗagowa ta kallesaba ta shiga gaishesa kamar yanda ta saba. Da kulawa ya amsa mata da sake tambayarta ƙarfin jikinta. Tace taji sauƙi.      Sun jima a ɗakin tare da ita, sai dai su kaɗai suke ƴar hirarsu jefi-jefi. Zinneerah na zaune shiru tana saurarensu kanta a ƙasa. Sai da Naziru ya tambayeta ko Khalipha ya shigo? Ne ta girgiza masa akai alamar a'a kawai batare da tayi magana ba.       Fara kiraye-kirayen sallar magriba da akai ne yasa sukai mata sallama suka fito.       Suna fita ta sauke ajiyar zuciya, tare da zamewa a gadon ta kwanta ta lumshe idanunta da sake maida hannunta akan cikinta kamar ɗazun. Batasan wane tunani zatai akan wannan cikinba a rayuwarta. Dan yazo mata a yanayin MAKAUNIYAR ƘADDARA. shin tayaya wai aka samar da shi ne? Wanene ubansa? Kodai dama cikin basai mutum yayi aure ko ya aikata iskanci ba yake samunsa?.       Wannan tunanin shine a ranta. Dan harga ALLAH ita dai tasan duk masu haihuwar garinsu sai sunyi aure. sannan idan akaga wadda batai aureba da ciki akance mata ƴar iskace mai bin maza. A yanda kuma takejin ma'anar kalmar mai-bin maza a abaki manya shine mace mai zuwa ta aikata abu mara ƙyau da namiji. To amma ita yau gashi bata a cikin duk waɗancan kason mutanen amma gata da ciki. Bata taɓa aure ba. Bakuma ta taɓa iskanci irin na waɗancan matanba. To kenan bayan waɗanan dalilan mace zata iya samun ciki ta wata sigar kenan kamar yanda itama a yanzu take tsamanin ta hakan ta sameshi?.         Lokacin da Zinneerah ke wancan tunani a waje tsakanin Naziru da natarsa kam tattaunawa sukeyi suma akan abin al'ajabin da suka gani. Dan suna fitowa Matar tasa ke faɗin, “Abban Nasiba wlhy ɗazunfa waskewa nayi dan naga yarinyar nan ta tsorata. Kasan kuwa mina gani tattare da yarinyar nan?”.        Kansa ya girgiza mata kawai batare da yace komaiba. Itama batare data damu da hakan da yayinba tace, “Wai shin kai bakaga kamarta da Maman Sadiq ɗin gidan babban yaya bane?”.         A yanzu kam gaba ɗaya ya tattara hankakinsa gareta. Cike da zumuɗi yace, “Wannan dalilin yasa na kawoki nan Faɗima. Dan inata kokwanto, kinsan akan hakan jiya har gidan Yaya naje na sake ganin Maman Sadiq kuwa?”.        “Ikon ALLAH, to amma ita yanzu ai kaga yan uwanta ko?”.        “Inafa, bata iya faɗa mana komai akantaba wlhy, da alama akwai saka hannu a al'amarinta gaskiya, dan kamar bata da isashshiyar kafiya, kamar kuma mai tare da sammu ko jinnu. Amma ni yanzu kinsan wane tunani nayi?”.      Kanta ta girgiza masa. Ya sauke numfashi yana bin Khalipha dake fitowa daga wata baƙar mota data faka a kusa dasu da ido. Tinted glass ɗin motar yasa basuga wanda ke zaune matsayin driver ba. Sai Khalipha ɗin daketa faman ɗaga masa hannu yana murmushi har motar ta sake ficewa a harabar asibitin.       Inda su Nazirun suke ya ƙaraso yana faɗin, “A'a malam Naziru kune anan haka?”.          Cike da kallon alamar tambaya da Nazirun ke masa ya gyaɗa kansa. Dan mamakin wannan babbar motar da aka saukesa a ciki yakeyi. fahimtar hakan da Khalipha yasoyi ya sakashi yin murmushi da juyawa yana kallon motar da har ta gama ficewa a gate ɗin asibitin ta hau titi. Sake maido dubansa yay ga Naziru da shima motar ya koma kallo yanzun cike da basarwa.          “Yaya dai malam Nazir?”. Murmushi Naziru yayi a karon farko ƙasan zuciyarsa fal saƙe-sake akan tunanin da alama Khalipha ɗan masu da shi ne. Dan shi tunma randa suka ɗakkosa a Jigawa yaso fahimtar hakan. Amma shi Khalipha kamar bayason nuna shiɗin wanine.......        Gyaran muryar da Khalipha yayine ya katse tunaninsa. Shi kuma Khalipha ya maida dubansa ga matar Nazirun suka fara gaisawa. Bayan sun gama gaisawarne Naziru yay masa bayanin itama abinda matar tasa ta faɗa game da kamannin yarinyar da matar yayan nasa.        Khalipha yace, “To inaga mafita ɗayace damu kamar akan wannan tunain naku, mizai hana kubi hanyar data dace ita matar yayan naka tazo asibitin nan ko zamu sami wani bakin zaren, idan kuma babu damar yin hakan mu haƙura har yarinyar ta samu sauƙi sosai sai mu kaita gidan yayan naka mu da kanmu”.         “Lallai wannan shawaran taka yayi Khalipha, kuma na gamsu da shi. Insha ALLAH zanyi iya duk ƙoƙarina zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu Maman Sadiq tazo asibitin nan kafin yarinyar nan ta kammala kwanakinta inaga kamar zaifi sauƙi”.        Daga Khalipha har matarsa sun gamsu da hakan, dan haka sukai sallama yay cikin asibitin su kuma suka fito don tafiya gida. __________________★          A haka kwanaki suka cigaba da tafiya, Zinneerah na cigaba da jiyya da samun kulawa ga Khalipha, Naziru ma yana iya bakin ƙoƙarinsa ganin yazo dubata koda hidimar Khalipha ɗin da baya gajiyawa.      Sosai ta samu sauƙi, dan yanzu Alhmdllh ko zaburan daren nan nason a barta ta fita batayi saboda Khalipha bai barin asibitin da wuri saboda ita kawai. Kasancewar suna sakata barci da wuri dan ta sami hutu sosai yakan zauna yayta mata addu'oi yana tofa mata, itako bama tasan yanayiba dan tuni tayi barcinta.      Yawan kulawa da samun abinci mai inganci da takeyi yanzu ya sakata canjawa a zaman asibitin tamkar bamai zaman jinyaba. Tayi wani fresh da ita ga cikin nata nata sake nuna kansa. A duk sanda ta dubi cikin takan zauna taita kuka maiban tausayi. Dan takan rasa wane irin kalar tunani zatayi akan wannan MAKAUNIYAR ƘADDARA data riski rayuwarta?. Gaka da ciki amma bakasan ta hanyar daka samosaba balle ai tunanin wanene ubansa kuma. Ita yanzu ma da'an sallameta daga asibitin nan batasan indama ta dosaba kuma. Dan koda sha'awa bata son tunawa da Danya a ranta ma balle ai tunanin komawarta can.      Har yanzu su Khalipha basusan sunantaba, tun kuma waccan ranar basu sake neman jin wacece itaba. Tamaƙi yarda ta saki jiki dasu gaba ɗaya.        Yauma kamar kullum tana zaune a ɗakin da tab ɗin Khalipha dakan bata wai tayi game ko kallo haka danta rage kaɗaici. Game ɗin takeyi fuskarta na fidda murmushi mai ƙayatarwa, a kallo ɗaya zaka fahimci tana cikin nishaɗi, shiyyasa shi kansa Khaliphan yake ɗaukar Tab ɗin ya bata dazaran ya shigo cikin asibitin. Shekaran jiyama a wajenta ta kwana.       Ɗan harbawar da zuciyarta yayi yasata dakatawa dayin game ɗin, haka yau ta tashi da wannan tsinkewar zuciya da batasan dalili ba, jin abin na ƙara ƙarfi ne ya sakata ajiye tab ɗin ta Khalipha gefe ta zame ta kwanta tana ambaton ‘hazbunallahu wani'imal wakil’ a ranta ko zataji ɗan daɗi............✍ *_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 _Na Safiyya Huguma_ *_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖 _Hafsat Rano_ *_★ DALAAL_*💝 _Na Miss xoxo_ *_★ UBAYD MALEEK_*💓 _Na Mamu gee_ *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 _Na Bilyn Abdull_ Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 *_08085405215_* IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   0903 234 5899 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 *_TYPING📲_* *_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_* *Page 9* ________________________ *_Hummmmm!!. Wai wai wai, wani aiki sai: GIDAN ƘAMSHI💃🏻💃🏻💃🏻🥺_* *_INA MATA ƳAN ƘWALISA MA'ABOTA SON ƘAMSHIN GIDA DANA JIKI?_* *_INA MATAN DAKAN SO DUK INDA SUKA DOSA KO SUKA BARI SAI SUN BAR MUSU TARIHIN ƘAMSHINSU_* *_TO MATAN ƘWARAI KUZO GA WANI SIRRI DAZAN BAKU DAGA FITACCEN GIDAN ƘAMSHIN NAN DA BAIDA NA BIYU A KANON DABO😁_* _Ina magana ne akan GIDAN ƘAMSHI da ke a Jihar KANON DABO MAIDUGURI ROAD MARIRI_. *MUNA SIYAR DA TURARURRUKAN WUTA SET NA AMARE, MUNA KUMA BADA SARI.* *AKWAI KUMA SABULUN GYARAN JIKI MAIDA TSOHUWA YARINYA, BUDURWA TAURARUWA, MATAN ƘWARAI ANNURIN HASKAKA GIDA. SHIMA DAI AKAN SARI, DOZIN KO KATON* *AKWAI KUMA ZUMAR ƘARA ƘIBA GA MATAN DA KESON SU GANSU DUMURMUR SUNA JUYAMA OGA KAYAN...😉🙈💃🏻 kundai gane*. *_Mata ku garzaya GIDAN ƘAMSHI domin ƙamsasa kanku kuma kar aci kasuwar sama babu ku😁_* *ZAKU IYA SAMUN MU TA WANNAN LAMBAR WAYAR: 07033778564 DOMIN JIN ƘARIN BAYANI*. *KO A KANO MAIDUGIRI ROAD MARIRI*.💃🏻💃🏻👍🏻 _______________________ *Page 9* ..........Jin kamar ana nufo ɗakin ya sata miƙewa zumbur taja hijjab ɗinta da Khaliphan ya kawo mata saboda salla ta saka da sauri. Ƙirjinta ne ya sake ƙarfin bugawa fiye da ko yaushe lokacin da Khalipha yay sallama a ƙofar ɗakin. Haka yakeyi mata a duk sanda zai shigo sai yayi sallama ta amsa sannan yake shigowa.      Yanzu ma bai shigo ɗinba sai da ta amsa ya turo ƙofar ya shigo. Kallo guda tai masa tai saurin maida idanunta ƙasa saboda kwarjinin da yake mata da cika ido. Sai dai kuma luguden dakan da ƙirjinta ke mata ne ya tilastata sake ɗago kanta badan ta shirya ba. Naziru ne biye da bayansa. Sai matarsa. Sai wasu mata biyu da batasan daga inaba. Sai dai shigowar ta ƙarshen ya sakata wani irin zabura tana binta da kallon ƙurilla maiban mamaki.        Yanda take kallon matar da yanda itama matar take kallonta tana tafiya da ƴar sassarfa ne yaja hankalin su Khalipha garesu baki ɗaya. Kusan mini ɗaya matarnan da Zinneerah na kallon juna batare da sun saniba, sai can Zinneerah ta fara janye nata tana sauke wata irin nannauyar ajiyar zuciya a ɓoye. Kanta ta maida ƙasa tana ƙoƙarin haɗiye hawayen da suka cika mata ido da batasan na minene ba.          Jin yanda ɗakin yay shiru ɗayar matar da suke tare da itama al'ajabi ke neman halakawa ta katse shirun da faɗin, “Baiwar ALLAH sannu kinji, ALLAH ya kiyaye gaba, ya ƙara lafiya”.         Kusan a tare duk sukace amin, banda matarnan mai kama da Zinneerah da gaba ɗaya hankalinta bayama tare da ita. har yanzu kuma idonta nakan Zinneerahn. Sun ƙara jajanta mata da mata addu'ar samun lafiya mai ɗorewa sukai musu sallama suka fita bayan matan nan biyu sun ajema Zinneerah kuɗi. Koda zasu fitanma matarnan tana tafiya tana waigen Zinneerah har suka fice. Shi dai Khalipha yana tsayene yana kallonsu da nazari tun shigowarsu har suka fice.         Wayarsa da ke ring a aljihu ta sashi sauke numfashi da warware hannayensa daya harɗe a ƙirji ya cirota a aljihu. Wani lallausan murmushi ya saki wanda yay dai-dai da ɗagowar Zinneerah. Sai ko ga idanunsu cikin na juna. Tai azamar maida kanta ƙasa ƙirjinta na wani irin harbawa, dan ba ƙaramin dukan zuciyarta wannan murmushi nashi yayiba.         Shikam wayar ya kai a kunne yana ɗan lumshe idonu, cikin wata murya mai ɗunbin ladabi da girmamawa yace, “Assalamu alaika Yayanmu”.      Batajin mi ake faɗa acan ɗin, sai Khalipha ne taji ya wani sake narke murya da shagwaɓa yana faɗin, “Oh Yayanmu Please ka jirani gani nan zuwa, nifa nace zan kaika da kaina yau, nanda mintuna goma insha ALLAH ina gida”.          Bataji mi nacan ya sake cewaba. Sai Khalipha ne ya matso gaban gadon yaɗan bubbuga yana cigaba da sauraren abinda ake faɗa ɗin daga can. Ɗago kanta tayi ta kallesa dai-dai ya sake narke fuskar tamkar wani yaro ƙarami, kokuma yana a gaban wanda yake wayar. “ALLAH Yayanmu bazanyi gudu ba, kasan mashin bakamar motaba ai, kuma zanbi ta hanyan dazan samu sauƙine fa Please ”.         Ita dai Zinneerah ganin yana neman zauta mata kwanya taso sake maida kanta ƙasa sai yay saurin mata alama da hannu wai yana zuwa. Bai jira cewartaba ya fice da hanzari. Bin bayansa tai da kallo harya fice, tsigar jikinta na wani tashi batare da tasan daliliba. Sai kawai ta fashe da kuka.        Kuka sosai Zinneerah taci wanda yana alaƙa da wasu baƙin al'amura a gareta, sai dai ƙuruciya ta hanata fahimtar komai. Ta zame a hankali ta kwanta tana lumshe idanunta badan barciba, sai don son samun damar tunani da wassafo matar ɗazun da takesonyi harma da tuno halin data shiga a dalilin ganin nata da wanda ta lura itama matar ta shiga saboda ganinta.      A ɓangaren Maman Sadiq kam itama tunda suka fito daga asibitin tafiya kawai take tamkar bata cikin hayyacinta, jitake kamar ta dawo ta sake ganin Zinneerah ɗin saboda abinda takeji a ranta da dukkan magudanar jinin jikinta a dalilin tozali da yarinyar. Duk da wani ɓangare na zuciyarta na ƙwaɓarta da cewar ba haka bane ta kasa yarda sam.        Daga Naziru har matarsa hankulansu nakanta ne suna nazarin halin da take a ciki, sai dai basuce komaiba har ya maidasu gida shima ya wuce nasa gidan da matarsa. Inda sai anan suka sami damar tattaunawa akan yanayin maman Sadiq ɗin.         Tunda suka shiga cikin gida ta buɗe ɗakinta ta shige saita kasa zaune ta kasa tsaye, kaikawo taketa famanyi a ciki, duk da masifar kishiyarsu Saude da take jiyowa akan taƙi fita ta ɗora girkin rana ga lokacin kaima yara abincin rana makaranta ya kusa bata fito ɗinba. Sai Uwargidansu da sukaje asibiti tare ce ta jiyo tana bama Sauden amsa da “Haba dai Maman Sakina, kodan himma irinta Maman Sadiq ai yakamata ki fara tunanin anya lafiya kuwa? Amma sai ki ɓige da neman fitina daga shigowarmu gidan dai”.          A harzuƙe da masifar da dama Sauden jira take ta hayayyaƙoma Uwargidan nasu.....        “Yaya! Yaya! Ƴar ayi jikan nasaba”. Muryar mai-gidan dake shigowa ta katse masifar Sauden ta koma ƙunƙuni ciki-ciki. Baibi takantaba sai uwargidan tashi dake masa sannu ya duba. “Mike faruwa kuma daga dawowarku Binta?”.       “Babufa komai Alhaji, fitinace irin ta Saude da baƙarewa take a gidan nan ba. Kawai dan Maman Sadiq bata fito ba shine take tsogumin batazo ta ɗora abinciba wai lokacin kaima yara makaranta ya kusa”.        Ɗan tsaki yayi yana girgiza kansa. Yace, “Ina ita Hauwa'un take?”.       “Tana ɗakinta, inaga dai akwai abinda ke damuntane, dan tunda muka baro asibitin naga yanayinta ya canja, na bartane muzo gida taɗan huta dama ko wani abune ya tada hankalinta acan ɗin tunda wajene bana daɗin rai ba”.      Baice komaiba ya nufi ɗakin Maman Sadiq ɗin, wadda duk tanajin mi'ake a tsakar gidan amma taƙi yin ko tari dan abinda ya isheta ya girmi fitinar Saude. Labulen ya ɗaga yana dubanta daga bakin ƙofar, yitai kamar bata gansaba, hakanne yasa ya shigo ciki yana faɗin, “Hauwa'u lafiyarki kuwa”.        Juyowa tai ta kallesa tamkar yanzune tasan da zuwansa. Tace, “Ashe ka shigo? ALLAH yasa dai lafiya?”.         “Ai ke za'a tambaya ko lafiya Hauwa'u? Mike faruwa ne?”.     Tamkar jira take ya tambayeta sai ga hawaye sharrr. Zumbur ya miƙe daga ɗan zaman da yay a hannun kujera yace, “Subahanallahi, wai mike faruwa ne? Ko wani abun ya faru acan inda kukaje dubiyan?”.       Hawayen ta share, tace, “Lallai Alhaji akwai matsala wlhy, dan ALLAH inason na sake komawa asibitin nan yanzun”.       “Ki koma asibiti kuma? Akan wane dalili to?. Kimin bayanin dazan gane mana”.       Wasu hawayen ta sake sharewa. Muryarta na rawar tahowar sabon kuka tace, “Alhaji yarinyarnan da mukaje dubawa wadda Nazirun ya kaɗe wlhy kamar Zinneerah, kai inamji a jikina itace duk da kuwa rabon dana ganta tun tana ƙarama”.         Shima kansa da mamaki yace, “Zinneerah dai tamu dake a Danya?”.       Cike da ɗanjin nauyinsa ta gyaɗa kanta, dan shi mutumne mai kara, duk da ɗan uwantane dama can, auren zumincine akai musu bayan aurenta ya mutu, ya sota tun tana budurwa ALLAH baiyi zata zama matarsaba a lokacin sai da ta fito yace shifa yana sota har yanzun. Da farko taso ta tirje dangi sukai mata caa akan rashin dacewar hakan. Dan kowa yasan irin son da ya nuna mata. Haka dole ta haƙura akayi aka kawota nan Kano gidansa dan dama can anan yake zaune shi shekara da shekaru, to gashi yanzun har ALLAH ya azurtasu da ƴaƴa uku duk maza. Tana kuma samun kulawa da soyayyar mijinta mai tsafta da saka kwanciyar hankali, ga Uwargidanta mutuniyar kirki, Saude ce dai sai a hankali, dan dama tun farko fitinar Sauden tasata son zamewa daga auren nasa.....        “Wai tunanin mi kuma kika tafi haka ne?”.       Kallonsa tai da sauri tana sauke ajiyar zuciya. Ya ɗan girgiza kansa kawai yana miƙewa. “Kinga ki kwantar da hankalinki tunda dai tana asibitin babu inda zataje, bara na kira Nazirun anjima yazo sai mu koma insha ALLAH dan wannan ba al'amarin da za'ai wasa bane”.      Cikin jin daɗi tace, “To Yaya ALLAH ya saka da alkairi”.        “Saboda ƴarki ce ke kaɗai kikemin godiya kenan?”.        Ƙasa tai da kanta tana murmushi. “A'a kayi haƙuri bankai canba”.         Fita yay yana murmushin shima. Saude dake laɓe a jikin Window ɗinta tana irga mintunan shigarsa ɗakin taja tsaki ganin ya fito yana murmushi. Afili tace, “Shegiya munafika, zanyi maganinki a gidannan wlhy. Oho ita dai maman sadiq bama tasan tanaiba, dan bayar fitar maigidan fitowatai ta ƙara gawayi a wuta ta ɗora ruwan abinci, dan dama tunkan su fita tayi miya shiyyasa bata damu da tsegumin Sauden ba ashe. ★★★★           A asibiti kam shiru-shiru Khalipha bai dawoba har lokacin yin barcin ranar Zinneerah yayi tasha magani ta kwanta. Bata tashiq farkawaba sai bayan sallar la'asar. Ganin lokaci yaja ya sata miƙewa aɗan harzance ta shiga toilet ɗin dake a ɗakin. Alwala tayo ta fito, bayan idar da sallar ne Salima ta shigo dan bata abinci kamar yanda Khalipha ya rataya mata alhakin yin hakan ga Zinneerah. Itako bala'in son da takema Khalipha yasa bata iya ƙetare buƙatarsa a rayuwarta, shiyyasa take bama Zinneerah kulawa sosai dan duk zatonta yanada alaƙa da zinneerah ɗinne musamman dataga an kawo zinneerah ɗin ɗaki na musamman ita kaɗai an ajiye.         Zinneerah na tsaka dacin abincinne Salima na mata hira tana ɗan murmushi sukaji sallamar Khalipha bayan yayi ɗan knocking. Saurin jan hijjab Zinneerah tai ta saka, Salima ma ta gyara zamanta dana ƙaramin hijjab ɗinta tana amsawa.        Shine ya fara shigowa ɗakin tamkar ɗazun, sai Naziru biye da shi, wani da suke tsananin kama da Nazirun na bayansu, sai dai a kallo ɗaya zaka fahimci ya girmi Nasiru ɗin dan ba yaro bane.        Sai matan ɗazun biye da su a baya, amma banda matar Naziru. Matar ɗazun da taji suna kira da Maman Sadiq ta ƙaraso gaban gadon sosai batare da tama saniba. Hannu takai bisa kumatun Zinneerah jikinta na wata irin tsuma da karkarwa. Ko shekara dubu tai bataga wannan halittarba tayi imani da ALLAH randa suka haɗu saita gane abarta. Tunda tabar ƙauyen Danya cikin gushewar hankali dana tunani har zuwa yau ɗinnan bata daina kwana da mafarkintaba da tashi da tunaninta kuma. Ta kai ƙasa durƙushe hawaye na silalo mata a kumatu. Tabar ƴarta da ƙarancin shekaru hannun kishiya mai ƙarancin imani dana tausayi badan ranta yasoba, sai dan anfi ƙarfinta kawai. Yau kuma sai gata a inda bata taɓa zatoba ko tsammani a shekarun girma....        “Zinneerah!”. Ta ambata da wani irin rawar murya dana harshe.      Ganin Zinneerah ta kasa magana sai kallonta kawai da takeyine kamar ɗazun ya saka Naziru faɗin, “Maman Sadiq ki kwantar da hankalinki, insha ALLAHU itace ma”.          Idanunta da hawaye ke kwarara ta ɗago ta kallesa, taɗan saki murmushin ƙafin hali tana miƙewa tsaye sosai. “Nasiru indai har yanzu ba ƙwaƙwalwata ce bata gama dai-daitaba to wannan kam Zinneerah ce, dan naji hakan a jikina duk da kuwa bata amsa sunan dana kirata da shi ba”.         Maman Halima da sukazo tare yanzunma ta matso gaban gadon itama ta zauna kusa da Zinneerah da alamu suka nuna tamkar bata a cikin hayyacinta. Sai da ta riƙe mata hannune tai firgigit alamun ta dawo cikin hayyacinta. Ƙasa tai da kanta saboda wani irin bugu da ƙirjinta ke mata ainun, Maman Halima ta katse shirun ɗakin da faɗin, “Ƴammata minene sunanki?”.      Babu wanda yay tsammanin zata amsa. Sai ji sukai a bazata tace, “Zinneerah”.       Wata irin nannauyar ajiyar zuciya maman Sadiq ta sauke, yayinda ɗunbin mamaki ya kashe Khalipha da  Naziru, musamman da suka tuna randa sukaita ƙwaƙwar jin sunan nata amma tai musu shiru..      “Masha ALLAH Zinneerah daga ina kike? Ina nufin a wane anguwa iyayenki suke?”.      Shiru kamar bazata amsa ba yanzu. Sai kuma zuwa can tace, “Ba'anan nake ba”.         Cike da zumuɗi maman Sadiq tace, “Daga wane gari kike?”.       Ɗagowa tai tana kallonta na tsawon kusan mintuna biyu, sai kuma ta maida kanta ƙasa tana sauke ajiyar zuciya. Cikin suɓutar bakin da bata shiryaba tace, “Danya”.       Gani kawai sukai maman sadiq ta zube kan kujerar roban dake a gaban gadon ta fashe da kuka tana faɗin, “Wlhy itace, Zinneerah tace”.      A yanda tai maganarne ya sakasu jin wani irin tausayinta ya ɗarsu a rayukansu, cike da son jin ƙarin bayani Naziru yace, “Zinneerah kekam miya kawoki hanyar jigawa keda ke a jihar katsina?”.        Hawayen dake sakko mata ta share tana girgiza kanta. “Nima ban saniba, na samu kaina ne kawai a haka”.          Sai yanzu ne Alhaji yay magana. “Lallai da alama kamar bata cikin hayyacintane ta baro gida fa kenan”.       “Tabbas hakane Alhaji, kenan har yanzu Asabe bata canjaba ko kuma Zinneerah ma tayi gamo da abokiyar zama irin Asabe a gidan aure.” Maman Halima ta faɗa saboda ganin ciki a jikin Zinneerah duk da kuwa ta saka hijjab.       A karon farko shima Khalipha da tun ɗazun baice komaiba sai kallonsu ya sauke numfashi. Gyara tsaiwarsa yayi a jikin bangon daya jingina yana kallon Zinneerah da keta satar kallon maman Sadiq da suke tsananin kamanni. janye idanunsa yay ya maida ga Naziru yana faɗin, “Inaga tunda har an fahimci bakin zaren ayi haƙuri haka har zuwa lokacin da za'a sallameta daga nan ɗin insha ALLAH. Sai dai ya kamata ku sanar mata wacece ita a gareta dan na kula ba fahimtarku takeba kamar”.      Sosai duk suka gamsu da bayaninsa, suka zazzauna aka shiga gaisuwa da tambayar jikin Zinneerah ɗin, wanda Khalipha ya ƙara musu bayani game da matsalar dake tare da ita akan buƙatar hutu bisa ga lalurar cikin jikinta. Sun shiga mata addu'ar fatan sauka lafiya.       Maman Halima dai ce da har yanzu ke zaune a kusa da ita tana riƙe da hannunta ta nuna mata wadda aka kira maman Sadiq. “Zinneerah wannan ɗin mahaifiyarki ce, duk da nasan baki santaba kamanin dake a tsakaninku da duk bayan da mukeyi a wajennan zai tabbatar miki hakan, kai namasan zakiji a jikinki koda ba'a faɗaba dan mahaifiya tafi gaban wasa ai.”          Kafeta da kallo kawai Zinneerah tayi tamkar wadda ta suma a zaune. Sai da Maman Halima ɗin taɗan taɓatane ta kawo numfashi, sai kuma ga hawaye sharr. Batare datace komaiba tai ƙasa da kanta, daga haka bata sake ɗagowa ta kalli kowa a cikinsuba.      Sosai hakan da Zinneerah tayi ya taba zuciyar Maman Sadiq. Dan ta fahimci kamar Zinneerah ɗin fushi take da itane kokuma kalar nata murnar kenan oho. Kowa ma dake wajen da irin fahimtar da yayma shirun na Zinneerah. Murmushi Alhaji yayi, cike da sanin yakamata da hangen nesa irin na manya yace, “Kubata lokaci kamar yanda likitan nata ya faɗa ko”. Sai kuma ya juya ga Khalipha batare da ya jira amsarsuba. “Likita yaushene zaku sallameta?”.        Murmushi Khalipha yayi yanaɗan sosa gefen goshinsa. “Alhaji banine likitanba dai, amma insha ALLAH zuwa nan da kwana biyar haka akoda yaushe za'a iya bata sallama tunda jikin nata yana ƙyau, dama matsalar kamar daga cikin jikintane yasa aka riƙeta”.       “To masha ALLAH, ALLAH ya kaimu, ya kuma bata lafiya”.     A tare suka amsa da amin. Daga haka sukai musu sallama domin tafiya badan Maman Sadiq tasoba. Sai dai taji daɗin abinda Maman Halima ta faɗa akan cewar itace zata dawo ta cigaba da jinyar Zinneerah ɗin har a sallameta. Kowama yaji daɗin hakan har Khalipha.               ★★★        Tun daga wannan ranar jiyyar Zinneerah ya dawo hannun Maman Halima, Khalipha ma bai janye daga mata hidimaba, hakama Naziru, ga Alhaji ma ya ƙaru. Sai ga Zinneerah ta sake zama ƴar gata, sai dai abinda kebama kowa mamaki har yanzu taƙi barin damar da zasu fahimceta game da komanta. Hatta haɗuwarta da mahaifiyarta sun kasa gane mike a ranta. Dan taƙi cewa komai, ta kumaƙi nuna murnarta a fili ko damuwarta. A duk yanda Maman Halima ke janta a jiki dan son jin wani abu gameda rayuwarta da Inna taƙi sakin jiki da ita, duk da kuwa ta fahimci babu wata mummunar manufa ga Maman Halima ɗin. Sanin yakamatane kawai irin na matar.       Tun daga ranar Maman Sadiq bata sake zuwa asibitinba, sai dai ranta fal yake da damuwar yanayin Zinneerah a kanta. Tadai danne ne kamar yanda mijin nasu ya bata shawara akan ai haƙuri da komai har Zinneerah ɗin ta dawo gida.         Itakam Zinneerah bawai farin cikine batai da ganin Mahaifiyartaba. Har ranta ita kaɗai tasan daɗi da take a ciki, sai dai wani ɓangare na zuciyarta ya sakata jin ciwo da zargin mahaifiyar tata ta watsar da itane akan sani kenan. Dan duk wanda zai kalli Maman Sadiq ɗin yasan tana a cikin kwanciyar hankali a gidan aurenta na yanzu.        A ganinta idan ba tana saneba yaya za'ai ta watsar da ita tsahon shekaru batare data taɓa waiwayar inda take ba, hakama danginta. Wannan dalilinne ya saka yin kamar batai farin cikiba. Sai dai a randa abin ya faru tasha kuka a ɓoye, still rashin ganin kuma Maman Sadiq bata sake zuwa asibitinba ma ya ƙara taɓa mata zuciya.        Ana gobe za'a sallamesu Khalipha yazo mata da zancen da yasata tasha kuka sosai, dan har saida ta kaita da zazzaɓi mai zafin gaske. Ba komai yaja hakanba sai jin Khalipha ɗin zaiyi tafiya. Ashe dama yana karatune a wata ƙasa can daban, hutu yazoyi gida shine yake ɗan zuwa nan asibitin yana rage zaman banza saboda asibitin nada alaƙa da shi. Yanzu kuma hutunsa ya ƙare, yaso ace sai an sallami Zinneerah yaji cikakken labarinta sannan. Amma sai Yayansu yaƙi saurarensa da ɗaga masa ƙafar ƙarin kwana ukun daya buƙata. Ya tabbatar masa da dole-dole saiya koma makaranta gobe idan ALLAH ya kaimu. Shiko a duniya baya taɓa iya ƙetare maganar Yayan nasu saboda ƙauna da girmamansan da sukeyi akaf gidansu koma yace family ɗinsu.       Kuɗaɗe masu yawa da sayayya yayma Zinneerah ya kawo mata cike da damuwa. Bayan ya mata nasiha akan yanda zata kula da kanta yace ta bashi lambar mijinta koda ya tafine zai nemsa suyi magana ta waya. Shiru Zinneerah bata iya cemasa komaiba akan wannan magana. Ya sake mainaita mata, nanma shiru tai sai hawaye dake gudu a kumatunta.          Ƙyaleta Khalipha yayi, dan a tashi fahimtar kawai ta bashi cewar Zinneerah kodai rabuwa tai da mijin nata kokuma bata buƙatar ana alaƙantata da shi bisa wani dalili na ɓacin rai. Dan haka ya ƙyaleta kawai saboda ya amsa lambar Naziru. koma miye zai dinga ji daga garesa kawai.       Haka dai Khalipha yay mata sallama ya wuce ya batta da kukan zuci. Dan hatta Maman Halima da bata daɗe da saninsaba yaron da halayensa sun sakashi shiga ranta sosai.       Dalilin tafiyar Khalipha gaba ɗaya yinin ranar a rashin daɗin rai Zinneerah tayisa a asibitin, harma tanaji ta ƙagara a sallamesu gobe idan ALLAH ya kaimun, gara taje gidan maman tata taji nata dalilin itama na guje mata datai ta barta cikin wahalar rayuwa..          Haka dai a daddafe suka kai washe gari, inda ALLAH ya taimakesu aka basu sallama tunda safe. Dan haka Nasiru yazo ya kwashesu dan yakai gidan yayan nasa inda mahaifiyar Zinneerah ke rayuwa a yanzu matsayin gidan aurenta..............✍          *_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 _Na Safiyya Huguma_ *_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖 _Hafsat Rano_ *_★ DALAAL_*💝 _Na Miss xoxo_ *_★ UBAYD MALEEK_*💓 _Na Mamu gee_ *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 _Na Bilyn Abdull_ Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 *_08085405215_* IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   0903 234 5899 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 *_TYPING📲_* *_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_* *_Page 10_* ________________________ *_Hummmmm!!. Wai wai wai, wani aiki sai: GIDAN ƘAMSHI💃🏻💃🏻💃🏻🥺_* *_INA MATA ƳAN ƘWALISA MA'ABOTA SON ƘAMSHIN GIDA DANA JIKI?_* *_INA MATAN DAKAN SO DUK INDA SUKA DOSA KO SUKA BARI SAI SUN BAR MUSU TARIHIN ƘAMSHINSU_* *_TO MATAN ƘWARAI KUZO GA WANI SIRRI DAZAN BAKU DAGA FITACCEN GIDAN ƘAMSHIN NAN DA BAIDA NA BIYU A KANON DABO😁_* _Ina magana ne akan GIDAN ƘAMSHI da ke a Jihar KANON DABO MAIDUGURI ROAD MARIRI_. *MUNA SIYAR DA TURARURRUKAN WUTA SET NA AMARE, MUNA KUMA BADA SARI.* *AKWAI KUMA SABULUN GYARAN JIKI MAIDA TSOHUWA YARINYA, BUDURWA TAURARUWA, MATAN ƘWARAI ANNURIN HASKAKA GIDA. SHIMA DAI AKAN SARI, DOZIN KO KATON* *AKWAI KUMA ZUMAR ƘARA ƘIBA GA MATAN DA KESON SU GANSU DUMURMUR SUNA JUYAMA OGA KAYAN...😉🙈💃🏻 kundai gane*. *_Mata ku garzaya GIDAN ƘAMSHI domin ƙamsasa kanku kuma kar aci kasuwar sama babu ku😁_* *ZAKU IYA SAMUN MU TA WANNAN LAMBAR WAYAR: 07033778564 DOMIN JIN ƘARIN BAYANI*. *KO A KANO MAIDUGIRI ROAD MARIRI*.💃🏻💃🏻👍🏻 ______________________ *Page 10* ............Tunda suka iso gidan Zinneerah keta kalle-kalle. Basai an faɗaba a ganin gidanma kasan mahaifiyar tata yanzu kam tai gaba, kuma tana cikin jin daɗi da kwanciyar hankali. Bawai ƙaton gida baneba irin na masu kuɗi, babbane dai kam amma gini irin na mai rufin asirin ALLAH. Dan da Alhaji Bashir Ɗanmusa kam yayi kuɗi sosai, sai dai daga baya ya fuskanci ƙalubalen karayar arziƙi, tun daga nan ne dai har yanzu bai koma yanda yake daba, amma ko a hakan Alhmdllh dan yana iya ɗaukar nauyin komai na gidansa harma ya taimakawa ƴan uwa da maƙwafta. Hatta da motar da Nasiru keja a yanzu haka shine ya siya masa ita. Sannan duka ƴaƴansa suna karatu gwargwadon ƙarfinsa danshi mutumne maison ganin zuri'arsa ta samu ilimin addini dana zamani.         Zinneerah ta samu tarba maiba mamaki a gidan na kawunta, kuma mijin mamanta. Hakama yaran gidan duk da ba saninsu tayiba suma basu santaba sunzo sun zagayeta sunata kallo. Bata wani sake da kowa ba dan har yanzun damuwar tafiyar Khalipha bata saketa ba. Tanajin raɗaɗi da zafi a ranta wanda ita kanta batasan dalili ba.       Duk da a yanayin da take na rashin sakin jiki hakan bai hana Mama Sadiq nuna zumuɗin ganintaba, danma tana ɗan kawaicine wa Maman Halima kasancewar Zinneerah ƴar fari ce, sannan kuma yanda Maman Haliman ke nuna kara ma ta cancanci a ɗaga mata ƙafa ai. A yanzu hakama duk da tare suka dawo a ɗakinta ta sauketa. Sai dai an kawo kayan Zinneerah ɗakin Maman Sadiq ɗin alamar anan zata zauna.        Da ƙyar Maman Halima ta lallaɓa Zinneerah taci abincin da Maman Sadiq ɗin ta tarbesu da shi, bayan ta ɗan tsatstsakura aka kaita tai wanka, tare da bata kaya sabbi fil da Maman Sadiq ɗin ta ɗiɗɗinka mata a ƴan kwanakin nan gudun kar'a sallamosu tazo babu sitirar da zata saka, dan a yanzu haka gidan nasu ƴammatan dake sa'annin Zinneerah duk ƴaƴan Saude ne, Saude kam ba bari zatai su bama Zinneerah kayaba, ballema yaran suma sun rigada sun haddace karatun uwarsu suma kishi suke da su, danma sunajin tsoron ubanne, suma kansu su Maman Sadiq ɗin kuma basu basu fuskar rainiba suna ɗan shakkarsu.          A zahiri Maman Sadiq cike take da murnar kusantowar ɗiyar tata kusa da ita duk da batasan dalilin barowarta gidaba har yanzun. sai dai ƙasan ranta cike yake da fargabar yanda Zinneerah taƙi sakin jikinta ita. Haka dai ta daure ta danne damuwarta a ƙasan zuciyarta bayan sallar isha'i da Zinneerah ta dawo ɗakin nata bisa rakkiyar Maman Halima. Alhaji yayi tafiya, hakama Saude bata gidan, tana can gidansu bikin ƙanwarta akeyi, yaran natama suna dawowa Islamiyya da yamma yau suka bita can. Dan haka gidan ya kasance daga ita Maman Sadiq sai Maman Halima. Sai yaran Maman Sadiq uku duk maza ƙannen Zinneerah data haifa anan. Abubakar Sadiq, Abdul-Salam, sai Aliyu auta. Itako Maman Halima yaranta duk matane, huɗu sunyi aure ma, sai biyu yanzu a gabanta ƴan biyune sa'annin Sadiq. Sai itama Saude nada biyar, yanzu haka akwai ƴammata biyu da suka isa aure, sai ɗaya zasuyi kusan sa'a da Zinneerah, da ƙannensu biyu ƙanana suma kusan sa'annin su Sadiq ɗin dai.       Sosai Saude take kishi da Maman Sadiq saboda tazo gidan ta haifi ƴaƴa maza su basu haifaba, taso su haɗe kai da Uwargidan da suke kira maman Halima amma taƙi, dan dama itama ɗin can ba zaman lafiyarne a tsakaninsuba, to mizaisa ta yarda su haɗe su cuci wani bayan ALLAH shine mai badawa. Kuma koda Maman Sadiq tazo gidan batazo musu da raini ba, su duka girmamasu takeyi dan mace ce mai sanyin hali, sai dai idan ka ƙureta kam zaku kwasa da ita. Shiyyasa duk haukan da Saude zatai a gidan ko kallonta batayi, sai idan ta kaita maƙurane ta yaɓa mata maganar da zatai kwana da kwanaki tana damunta a rai.....          Numfashi Maman Sadiq taɗan sauke da duban Zinneerah dake a takure gefe tana magana dasu Sadiq  dake zagaye da ita a hankali. Tanajin misu Sadiq ɗin ke faɗa, amma batajin na ita Zinneerah ɗin. Gashi kuma ta duƙar da kai bata ko kallon sashen da take.       “Abdul!”. Ta kira sunan yaron nata na tsakkiya da yafi kowa ƙiriniya a yaran, dan a yanzu haka kusan rabin jikinsa na manne da na Zinneerah ne, gashi dama suna kamanni sosai da ita.      Kansa ya ɗago ya dubeta, “Na'am Mama”.       “Ku tashi aje ai shirin barci hakanan, duk kabi ka katantaneta bakaga halin da take ciki bane”.     Baki yaron yaɗan tura gaba da faɗin, “Ayya mama ki barmu muyi barci tare da ita, muna sonta sosai”.       A karon farko Maman Sadiq taga Zinneerah ta saki murmushi tana shafa kan yaron, sai dai bataji mita faɗaba sai da yaran suka haɗa baki wajen cewa, “Muma ai muna sonki sosai” ne ta gane cewa tai tana sonsu itama.       Murmushi tayi tana maijin daɗi da farin ciki a ranta, ta sake faɗin, “Karku damu ai tana nan tare da ku babu inda zata, kuje ku kwanta akwai islamiyya gobe idan ALLAH ya kaimu”.      Badan sunso ba sukaima Zinneerah sallama suka nufi ɗakin barcinsu. Shiru falon yayi na tsahon mintuna. Ita dai Maman Sadiq kallon Zinneerah ɗin takeyi cike da nazari, itako kanta a ƙasa tana wasa da zanen carpet ɗin dake shimfiɗe a falon.       “Zinneerah.” Ta kira sunanta cike da rauni.      Karon farko Zinneerah ta ɗago ta dubeta, sai kuma taɗan risinar da idonta. Murmushi mai ciwo Mama tayi, ta sake faɗin, “Taso ki dawo nan”.     Babu Musu Zinneerah ta miƙe zuwa gareta. Sai dai kamar bazata zauna inda ta nuna mata ɗinba, sai kuma mita tuna oho ta zauna a hankali gab da Maman nata. Mama dake cigaba da kallonta ta riƙo hannunta cikin nata tana gyara zama da fuskantarta sosai. Hakanne ya saka Zinneerah maida kanta ƙasa idanunta na cika da ƙwalla.       Itama Mama idanun nata cike suke da ƙwallan, cikin rawar murya tace, “Kiyi haƙuri Zinneerah, kiyi haƙuri kiyi haƙuri. Na fara da baki haƙuri ne saboda dalilai masu yawa. Nasan har ranki kina kallona ne matsayin uwa gareki mara adalci. wadda ta wofantar da ke ta manta da rayuwarki. Wlhy Zinneerah ba hakan baneba. Ni mahaifiyarki ban taɓa mantawa dakeba koda na daƙiƙa guda. A kowane sakanni kina maƙale a raina da zuciyata. Hawayena basu taɓa jinkirin fitowa ba a duk sanda na tunaki. Duk wanda ke tare dani yasan hakan Zinneerah. Nisantarki da nai itace babbar jarawar da har yanzu na kasa cimmawa wajen cinyeta, sai dai Alhmdllh, tunda yau gani gaki a yanda ban taɓa tsammataba ko tunani. Inason ki daure ki cire komai a ranki ki saki jiki dani ko hakan zai ragemin raɗaɗin ciwon gyanbon dake maƙale a zuciyata kinji”.         Hannu Zinneerah tasa ta share hawayen dake sakko mata daga idanu zuwa kumatu, cikin rawar harshe tace, “Amma miyasa baki taɓa zuwa gareniba mama”.      Murmushi Mama tayi itama tana sharar nata hawayen. “Zinneerah bana cikin hayyacinane, koda na baro ƙauyen Danya a yanayin ciwon hauka na barosa, sai dai Alhmdllh ALLAH ya taƙaitamin wahala maimakon na nufi wani waje saina nufi gida. Bayan isowata gida ƴan uwana sunje har Danya danjin miya faru dani amma mahaifinki yaƙi saurarensu, yama nuna bai sansuba baisan daga ina suka fitoba. Asabe kuma taci musu zarafi da musu korar kare. Duk da sunji zafin abinda akai musu sun buƙaci tahowa dake dan a gida na barki ni. amma mahaifinki ya hanasu, yama ɗora musu da cin zarafin dayafi na farko. Wannan shine dalilin yin fishinsu, amma basu haƙura akan wataran zasu amsoki ba. Ansha fama wajen nemamin magani sosai,  har takai mai gidannan dake a matsayin yayana yaje Ɗanmusa yaga halin da nake a ciki, shine ya fahimci sihiri ne tattare dani. Shine yasa aka kawoni nan kano wajen wani mutumi mai bada magungunan musulinci. Ya kashe kuɗi bana wasaba wajen ganin hankalina ya dawo tare dani, bayan wani tsahon lokaci aka dace na samu lafiya. Daga nanne ya nema aurena. Duk da banso hakanba aka tirsasani harna amince. Sosai kina maƙale a raina tunda na dawo hayyacina Zinneerah, sai dai bansan miyasaba ko sha'awar nufar hanyar Danya banayi, kai hasalima duk sanda nai yunƙurin son naje sai ciwona ya motsa min. Ƴan uwana kam bansan daliliba kowa ya bar zancen amsoki ko zuwama inda kike. Hakan na damuna a cikin rai, amma inajin kunyar yima wani magana ace na zaƙe da yawa, amma kiyi haƙuri Zinneerah ki yahe mani kinji”.         Kuka sosai Zinneerah keyi fiye da farko. tausayi da ƙaunar mahaifiyarta na sake shigarta cikin jiki da ɓargo. sun daɗe a haka kafin Mama ta koma lallashinta da tambayarta abubuwa game da rayuwarta da Inna Asabe.       Wani takan bata amsa, wani kuma takanyi murmushi ne kawai, hakan yasa Mama sake fahimtar ɗiyar tata tasha wahalar rayuwa kamar yanda tasani Asabe zama tayi fiye da haka. Dan ko ita ba daɗin zama taji da itaba a tsahon shekarun da sukayi tare na zaman kishi.       Yanda Mama bataima Zinneerah zancen ciki ba itama Zinneerah batace komai game da cikinba. Ganin dare yayi Maman tace ta taso taje ta kwanta haka nan.          Yau kam Mama da Zinneerah sunyi barci ne a gado ɗaya, hakan ba ƙaramin farin ciki da jin daɗi ya saka Zinneerah ba, har takaita da shagala dogon tunani akan abinda ke a cikinta itama. Mace ne ko namiji bata saniba. Wanene mahaifinsa yaya aka samar dashi bata saniba, wace amsa zata bashi taba mutane da mahaifiyarta game dashi bata saniba. Ta shafa cikin tana sakin wani murmushi mai ciwo da saka ƙunar zuciya, daga haka barci yay awon gaba da ita mai cike da mafarkin Khalipha. *WASHE GARI*           A yau kam Zinneerah ta sake tabbatarwa ashe itama mutum ce mai daraja kamar kowa, dan yanda ƴan uwanta da Mamanta suka kasance da ita ya jefa zuciyarta cikin matsanancin farin ciki. Kowa burinsa yaga dariyarta a gidan, ko yaya tai ɗan shiru sai ance mata mike damunta?. Abinci kam saita zaɓa wanda ranta keso ake bata taci.         Dawowar maigidan kuma aka sake ninka tattalin da ake mata, dan shima da aka kaita ta gaidashi bayan yaci abinci ya huta janta yay tayi da hira cikin kulawa, tun tana ɗan noƙewa bata iya amsawa harta saki jiki dashi ta fara amsa masa. Ta jima a wajensa tare da sauran ƙannenta kafin ta dawo sashen Maman Sadiq suka cigaba da shirmensu ita da ƙanen nata.       Haka rayuwa ta cigaba da yima Zinneerah daɗi a gidan mijin mamanta kuma kawunta, a hankali tana sakin jiki da kowa da komai nagidan. Har zuwa yau kuma da zata cika kwanaki uku babu wanda yay mata tambaya akan cikin jikinta balle jin ba'asin sanin inda ubansa yake. Itakuma bataima kowa maganaba dan addu'arta bai wucema ace kowa yaƙi tambayar tataba tunda batasan wace amsa zata basunba.         Yau ma duk suna zaune tsakar gida gab da magriba, tunda yaran suka dawo daga islamiyya anan suka yada zango inda suka sameta tana gurzama Maman Halima kuɓewa da zatai miyar tuwon dare. Anan suka shiririce bata labari tana musu dariya da biye musu kamar yanda ta saba.       Ƴammata ne biyu suka shigo gidan da sallama a bakinsu ciki-ciki. Sai ƙananu biyu dake biye dasu da ledoji a hannu. Idanu Zinneerah ta zuba musu kawai dan bata sansuba, hakama sauran yaran kallonsu kawai suke babu wanda yay magana. Sai Aliyu ne cikin tsalle yake faɗin, “Gasu Zainab gasu Luba”.           Ko kallon inda Aliyun yake basuyiba suka nufi ƙofar ɗakin uwarsu, dai-dai Maman Sadiq na fitowa ne uwar tasu ta shigo itama da ɗayar yarinyar da zasuyi sa'anni da Zinneerah. Cike da fara'a a fuskar Maman Sadiq ta shiga faɗin, “A'a ƴan bikine tafe. Sannunku da zuwa”.       A ɗan yatsine Saude da suke kira Maman Sakina ta amsa idanunta akan Zinneerah ko ƙyaftawa batayi. Ganin kallon ƙurillar da take matane ya saka Zinneerah faɗin, “Sannu da zuwa ina yini”.      “Lafiya” tace kawai tana nufar ƙofar ɗakin nata itama.      (Ashe tsugunne bata ƙareba kenan) Zinneerah ta ayyana a ranta zuciyarta fal tunanin waɗannan kuma daga ina?. Bata da mai bata amsa, dan haka ta miƙe dan ganin lokacin sallama yayi gashi wasu masallatan har an fara kira.        Alwala tace su Sadiq suje suyi su tafi massallaci, ita kuma suka shige sashen Maman Halima ita dasu ƴan biyu domin gabatar da tasu sallar. Daga haka bata sake jin ɗuriyar Saude da ƴaƴanta ba a gidan, bakuma ta tambayaba har suka gama hira ta miƙe ita dasu Abdul suka nufi sashen mahaifiarsu dansu kwanta.      Washe gari da safe bayan sallar asuba gari yay ɗan sha suka tafi gaida mutanen gidan kamar yanda Maman ta horesu. Sashen Alhaji suka fara zuwa wanda yaran gidan ke kira da Abba. Yana zaune a falonsa madaidaici da redio a hannunsa da alama kunnawa zaiyi, shigowar tasu ya sakashi ajewa yana dubansu da kulawa. Aliyu yaje jikinsa ya zauna, suko duk suka durƙusa a ƙasa suna gaidashi. Da fara'a yake amsa musu yana shafa kan Aliyu, ya ɗan duba Zinneerah da kanta ke a ƙasa, “Ɗiyata ya jiki-jikin?”.        Takanji kunya idan sukai mata tambaya akan jikinta, ta ƙara ƙasa da kanta da cemasa “Alhmdllh Abba”. “Masha ALLAH ai haka akeso, ALLAH ya saukeki lafiya”. Daga haka ya maida hankalinsa kan Aliyu.        Itace ta fara miƙewa, sauran yaranma duk suka miƙe suka fito a tare. Suna gab da shiga sashen Maman Halima Aliyu ma ya iso garesu da gudu yana faɗin, “Aunty! Kinga kuɗin makarantana Abba ya bani”. Juyowa Zinneerah tai tana murmushi, tace, “kace ka gode ko?”. Kansa ya kaɗa mata yana riƙo hannunta suka ƙarasa shiga sashen Maman Halima itama.          A falo suka isketa tanama Hussaina faɗa akan zubar da suga da tai ƙasa, ganinsu ya sata dubansu tana murmushi. Itama har ƙasa suka durƙusa gaisheta, ta amsa musu da fara'a da kulawa tana tambayar Zinneerah yaya jikinta. Nanma dai cike da kunya ta amsa kanta a ƙasa. Sunɗan jima anan fiye da sashen Abba. Daga haka suka shiga na Maman Sakina..         Suma dai a falon suka samesu sunata hayaniya, dan ɗakinta yafi na kowa yawan yara a gidan. Yanda suka wani watsoma Zinneerah idanu gaba ɗayansu har uwar sai duk taji ta muzanta. amma haka ta daure takai ƙasa tana gaida Maman Sakina ɗin. A ɗan yatsine ta amsa mata. Carab Luba dake kwance a kujera ta miƙe idonta akan Zinneerah. “Tab ɗi jan, jama'a wai kuna ganin abinda nake gani kuwa? Wai wannan ƴar yarinyarce da ciki”. Kusan a tare suka sheƙe da dariya, Sakina tace, “Kinsan ƴan ƙauyen nan sai a hankali, amma dubetafa sa'a tace, koma na girmeta kamar”. Cikin taɓe baki uwar tace inako sukaga hankali, ai kamar dabbobi suke basu banbance komai sai shirme. Nanma dariyar suka kwashe dashi su duka harsu Zainab ƙananu.        Tsam Zinneerah ta miƙe daga durƙuson da tai batare da tace komaiba ta kama hannun Aliyu suka fito zuwa sashen uwarsu.        Suna shigowa Abdul ke faɗama Mamansu abinda akaima Auntynsu a sashen Maman Sakina. Wai su Sakinar ne ke dariyar Zinneerah ƴar ƙarama da ita tanada ciki. Shine mamansu tace wai ai kusan mutanen ƙauye ba hankaline dasuba kamar tumaki suke. Ran maman Sadiq ya ɓaci, amma saita shanye bata nunaba. Hasalina batace komaiba ta cigaba da haɗa musu abin karin da takeyi. Itama Zinneerah komai bataceba tamayi kamar ba a gabanta akai abinba.      Bayan sun kammala karyawan ne Zinneerah tahau gyaran ɓangaren kamar yanda ta saba tun zuwanta gidan, su Sadiq kuma suka shiga shirin tafiya Islamiyya dan suna hutun boko. Tsaf ta gyara ko ina ta saka musu ƙamshi, ganin komai ya mata tsaf yanda takeso sai taje itama tayi wanka. Ta fito tana cikin shiryawa Mama ta shigo ɗakin.         Sai da ta ƙarasa abinda takeyine Mama tace, “Zauna magana nazo muyi”. Zama Zinneerah tayi inda Mama ta nuna mata babu musu, Mama taɗan sauke numfashi tana dubanta, itako kanta a ƙasa tamkar ko yaushe.        “Zinneerah!”. Maman ta kirayi sunanta a karo na farko. Batare data ɗagoba tace, “Na'am mama”..          “Zinneerah tun zuwanki gidannan nake jiran naji miya baroki da gida? Amma shiru bakice dani komaiba. Ya kamata nasani ai, sannan nasan kuma  ta yanda zamu nema mijinki shima dan yasan inda kike ko hankalinsa zai kwanta, tunda nasan duk inda yake kodan cikin dake jikinki basai samu nutsuwar zuciyaba”.        Yawu Zinneerah ta haɗiye da ƙyar wani abu na tattarowa a ƙirjinta. Ganin taƙi magana Mama tace, “Ke nake saurare”.        Maimakon amsa sai kawai Zinneerah ta saka mata kuka. Idanu kawai Mama ta zuba mata kamar yau ta fara ganinta, bata kawo komai a rantaba sai tunanin harda matsalar mijin ƙila ta barota da gidan.        “Abinda ya faru ya riga ya faru, dan haka kuka baida wani amfani a yanzu. Ki sanarmin nasan madafar kamawa wajen samo mafita”.        Yanda Mama tai maganar babu wasa ya saka Zinneerah bata amsa cikin dauriya da matsanancin tsoro. “Nima bansan ya akai na baro gida ba, nawayi garine kawai naga kaina a asibiti”            “Nikam ban fahimceki ba, sai kimin bayani dalla-dalla”. Mama ta faɗa tana tsareta da idanu.      Maimakon amsa sai hawaye Zinneerah ke faman sharewa. Shigowar Alhaji ya hana Mama sake cewa komai...........✍      *_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 _Na Safiyya Huguma_ *_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖 _Hafsat Rano_ *_★ DALAAL_*💝 _Na Miss xoxo_ *_★ UBAYD MALEEK_*💓 _Na Mamu gee_ *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 _Na Bilyn Abdull_ Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 *_08085405215_* IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   0903 234 5899 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍   *_TYPING📲_* *_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_* *page 11* ________________________ *_Hummmmm!!. Wai wai wai, wani aiki sai: GIDAN ƘAMSHI💃🏻💃🏻💃🏻🥺_* *_INA MATA ƳAN ƘWALISA MA'ABOTA SON ƘAMSHIN GIDA DANA JIKI?_* *_INA MATAN DAKAN SO DUK INDA SUKA DOSA KO SUKA BARI SAI SUN BAR MUSU TARIHIN ƘAMSHINSU_* *_TO MATAN ƘWARAI KUZO GA WANI SIRRI DAZAN BAKU DAGA FITACCEN GIDAN ƘAMSHIN NAN DA BAIDA NA BIYU A KANON DABO😁_* _Ina magana ne akan GIDAN ƘAMSHI da ke a Jihar KANON DABO MAIDUGURI ROAD MARIRI_. *MUNA SIYAR DA TURARURRUKAN WUTA SET NA AMARE, MUNA KUMA BADA SARI.* *AKWAI KUMA SABULUN GYARAN JIKI MAIDA TSOHUWA YARINYA, BUDURWA TAURARUWA, MATAN ƘWARAI ANNURIN HASKAKA GIDA. SHIMA DAI AKAN SARI, DOZIN KO KATON* *AKWAI KUMA ZUMAR ƘARA ƘIBA GA MATAN DA KESON SU GANSU DUMURMUR SUNA JUYAMA OGA KAYAN...😉🙈💃🏻 kundai gane*. *_Mata ku garzaya GIDAN ƘAMSHI domin ƙamsasa kanku kuma kar aci kasuwar sama babu ku😁_* *ZAKU IYA SAMUN MU TA WANNAN LAMBAR WAYAR: 07033778564 DOMIN JIN ƘARIN BAYANI*. *KO A KANO MAIDUGIRI ROAD MARIRI*.💃🏻💃🏻👍🏻 _______________________ *Page 11* ............Alhaji dake dubansu yace, “Lafiya kuwa naga tana kuka?”.        “Humm lafiya ƙalau wlhy, daga tambaya fa shine sai kukan nan. Gani nai ya kamata musan matsalar data barota daga gida. Idan ya dace mu nema mijinta saimu nemesa kuma”.        Murmushi Alhaji yayi yana zama a kujera, cike da nazarin Zinneerah yace, “Uhm inaga bata wannan hanyar ya kama mu saniba Hauwa'u, ki barta kawai ta huta dan yanzun farin ciki da kulawarmu tafi buƙata. Sauran maganar idan na dawo zamuyi ni da ke”. Bai jira amsar Maman Sadiq ba ya maida dubansa ga Zinneerah dake kuka har yanzu.      “Ɗiyata kinga share hawayenki kinji, banason na sake ganin kinyi kuka a gidan nan dan ALLAH. Ki fahimci mamanki kuma, batai miki wannan tambayar bane danta ƙuntataki. Wannan shine halin girma daya kamata kowacce uwa ta nuna ga matsala irin wanna. Ina fatan kin fahimceta”.      Kai Zinneerah ta ɗaga masa alamar eh.       Yace, “Alhmdllh, to share hawayenki kinji, ki kuma saki ranki a gidan nan dan baki da maraba da sauran yaran gidan, ALLAH yay miki albarka ya saukeku lafiya. Mikikeso na sayo miki idan zan dawo?”.      Ƙasa Zinneerah ta karayi da kanta cike da girmamawa da ƙaunar wannan bawan ALLAH.      Shima sai ya miƙe yana murmushi, “Shikenan tunda kin kasa faɗa, kafin dai na taso ki faɗama mamanki saita kirani a saya miki komi kikeso ɗin”.       “Nagode Abba, ALLAH ya tsare ya bada sa'a”.      Murmushi ya sakeyi cike dajin son yarinyar a ransa. Ya amsa idonsa akan matarsa. ___________________★          Tun daga wannan ranar babu wanda ya sakema Zinneerah magana akan sanin uban cikin jikinta da dalilin barowarta gida. saima kulawa ta musamman da Maman Sadiq, Abba, Maman Halima suka sake ninka mata. Koyaya aka ganta a damuwa sai anbi ba'asinta domin son kauda mata. Duk da Maman Sadiq na kawaici a kanta cikin hikima take jan abarta a jiki idan sun shige ɗaki, hakan yasa shaƙuwa mai ƙarfu ke sake shiga tsakaninsu, tana sake sakin jikinta sosai kuma. hakama ƙannenta idan ka gansu saika ɗauka dama can tare suka tashi.       A wajen ƴaƴan Maman Sakina (Saude) ne kawai Zinneerah batajin daɗi da ita kanta Sauden. Dan ko ranar girkinta bacin Maman Sadiq nakai zuciya nesa da sun dinga tafka rigima akan abincin da ake zubama Zinneerah ɗin. Amma sai bata cewa komai ta barta da halinta. Tadai gargaɗi Zinneerah ɗin akan koda wasa karta shiga hurimin Maman Sakina da ƴaƴanta inhar ya wuce gaisuwa da girmamawa. Sannan duk wanda zai sakata aiki a gidan tai masa indai ya girmeta.      Dayake Zinneerah ɗinma bamai kwaramniya bace sai tabi huɗubar mahaifiyarta aka zauna lafiya. Dan duk da cikin dake tare da ita da gadara Maman Sakina ke sakata aiki a gidan, itako babu musu takeyi koda batajin daɗin jikinta. Saima idan Maman Halima taga abin yayi yawane takanyi magana kota hana Zinneerah ɗin. Haka yakan saka Maman Sakina taita masifa a gidan da gori tana kiran Zinneerah da suna agola kinfi masu gida.           Maman Sadiq bata taɓa tankawaba, bakuma ta taɓa gayama mai gidanba. Ta kuma roƙi Maman Halima akan karta faɗa itama, dan tasan duk dai iya zaman Zinneerah a gidan naɗan lokacine kafin ta koma gidan mijinta.      Haka kwanaki suka cigaba da shuɗawa Zinneerah na rainon cikinta dake bata wahala. dan bata taɓa ƙulla kwana biyu babu ciwo. Sai dai yanda cikin ya fito ɗas a jikinta ba ƙaramin ƙyau yasa tayi ba. Gashi tana samun kulawa sosai yanzun.        Dan hatta da zuwanta asibiti Naziru ke zuwa ya kaita kamar yanda Khalipha ya bar masa sallaho. A ranar farko da suka fara komawa asibitin domin ganin likita Zinneerah ta samu damar ƙare masa kallon tsaf bayan ta karanta sunan asibitin tun daga waje. *_SHIRA HOSPITAL_*.        Sosai take jinjina ƙoƙarin maginin wannan asibiti, dan yayi ƙyau sosai kuma an zuba masa kayan aiki bana ƙaramin kuɗiba. Ga likitoci ƙwararru da basa wasa da aikinsu kuma babu wulaƙanci. Sai dai abinda ke matuƙar bata mamaki yanda asibitin yay matuƙar haɗuwa zaka ɗauka sai wane da wane ne masu iya shigarsa neman lafiya, amma saika shigo ciki kai gamo da masu karamin ƙarfi bila-adadin suna amsar magani hankalinsu kwance.      Samun damar ganin likita akan lokacine ya katse mata dukkanin tunaninta. Sai dai yanda aka karɓesunne ya sake bata mamaki, amma jin zancen Khalipha a bakin likitan kuma sai ta fahimci a dalilin shine ake mata wannan tattalin da kulawar. An bata magungunan da suka dace da ita, tare da sake gargaɗinta akan daina duk wani aiki dan cikin jikin nata yana buƙatar hakan saboda ƴar matsalar da suka hanga tattare da shi.     Ƙuruciya tasa batako damuba suka dawo gida. Sai dai bayanin da Naziru yayi na maganar kula da hutun nata a gaban Yayansa da bai kai ga fitaba yasa Abba gargaɗin kowa na gidan akan yasa ido kar Zinneerah ta sake wani aiki. Baki maman Sakina ta taɓe cikin ƙunƙuni take fadin, ‘Wayaga agola kinfi ƴaƴan gida’.         Babu wanda ya tanka sai shi Alhajin ne ya dubeta rai ɓace, “Saude mikike faɗa?”.        A zabure ta mike tana yarfar da hannaye da tafasu, “A'a kaga Alhaji bance komaiba nikam, karkuma a bugamin gangar ɗan bazakuɗa babu gaira babu sabar”.      Daga haka tabar wajen fuuu. Ƙwafa yay kawai batare da yace komaiba.        Tun daga wannan zuwan sai yazam Naziru kanzo ya kaita asibitin ganin likita kamar yanda akan rubuta musu.        A kwana a tashi babu wahala wajen UBANGIJI sai ga cikin Zinneerah ya shiga watanni na takwas. Zuwa yanzu ta saki jikinta sosai a gidan, musamman ma da mahifiyarta da kannenta dake faɗaɗa farin cikinta a koda yaushe. Idan ka ganta bazaka taɓa dauka ita bace, bakinta ya buɗe sosai alamar dama can rashin samun ƴancin kai ke sakata zama mai sanyi. Ita kanta maman Sadiq har mamaki take a ranta dama Zinneerah nada surutu haka? Ta tabbatar nan gaba idan ta sake warwarewa sai tafima haka kauɗi. Danma lalurar cikin kanɗan taƙaita mata wasu abubuwan.          Duk da waɗanan sauye-sauye da Zinneerah ta samu a rayuwarta hakan baisa ta manta da Khalipha a rantaba. Koda yaushe yana nan maƙale a ranta, wani lokacin har mafarkinsa takeyi, kota zauna zugum tana tunanin yaushene zai sake dawowa gareta ne ko dan ta masa godiya akan ɗawainiyar da yayi da ita?. Idan kuma Naziru yazo gidan har ALLAH ALLAH take taji yace Khalipha na gaisheta, dan yana kiransa lokaci-lokaci idan ya samu dama. Sai dai bai taɓa cewa a haɗasuba dan shi duk zatonsa tanada aure ne.        Yauma kamar kullum suna baje a falon Mamansu suna cin gyaɗa dafaffe da Zinneerah ta ƙwallafa rai sai da aka sayo aka dafa mata, kallo suke suna kwasar dariya. Maman Sadiq dake ciki tana shirin tafiya sashe Alhaji ta fito falon da kwalliyarta. Kallon yanda suke cikin nishaɗi tayi daɗi da farin ciki na ratsa ranta itama. Ta ɗauki tiren data shirya abincin Alhajin tana faɗin, “Zinneerah tashi ki tura muku ƙofar ni zanje na kaima Abbanku abinci, idan kunji barci kafin na dawo kimasu Aliyu addu'a karsu kwanta babu addu'a. Wannan sarkin fitsarin Abdull ki tabbatar ledan katifan bata zameba a inda zai kwanta. Ga kuma magungunanki nan kisha kema kafin ki kwanta”.        “To mama sai kin dawo”. Ta faɗa fuskarta washe da murmushi. Suma sauran yaran duk adawo lafiyar sukai mata ta ɗauki tiren ta fice. Yayinda Zinneerah ta saka Sadiq zuwa ya tura ƙofar suka cigaba da kallonsu.      A can ɓangaren maman Sadiq ko bayan Alhaji yaci abincinsa ya ƙoshi take dubansa da damuwa. “Yaya dan ALLAH karkace na takura, baka ganin kuwa ya dace mijin yarinyarnan yasan wani abu game da ita”.       Murmushi Alhaji yayi na manya. Ya gyara zamansa da cewa, “Eh kina kan gaskiyarki Hauwa'u, nima bawai hakan baya raina bane. Dama inason dai ta gama sakin jikintane sosai ta manta da duk wani ɓacin ran da yabarota daga gidan sannan. A yanda kuma nake tunani bata wajenta ya kamata muji komaiba. Nine zan shirya da kaina naje Danya ɗin domin ganawa da Baban nata da Mijinta. Kinga idan mun samu bakin zaren saimu yanke hukuncin daya dace. Dan indai ba rabuwa tai da mijin nataba tofa sai dai yasan mai yuwuwa”.         Murmushi kawai taɗanyi, “To duk hukuncin daka yanke ai shine dai-dai Yaya. ALLAH yay mana jagora”.      “Amin” ya faɗa yana maijin daɗi a ransa na yanda duk ta sakar masa ragamar rayuwarta batare da jin ko ɗarba garesa.        ★★★ Bayan sati ɗaya dayin wannan magana Alhaji ya shirya zuwa Kusada ƙauyen Danya batare da sanin Zinneerah ba.         Kasancewar a ranar yaje ya dawo kuma bata san komai akaiba tunda tasan yana fita kasuwa dama. Abinda dai kawai ta fahimta ranar Mamansu ta kwana cikin wani irin yanayi na tsantsar baƙin ciki. Dan harta kai washe gari ma sai da aka kwantar da ita asibiti. Kwananta ɗaya aka sallamota ta dawo gida. Zinneerah ta shiga damuwa da ganin yanayin na mamansu daya kaita ga kwanciya asibitin. Amma sai rashin wayo ya hanata tambaya koda suka dawo. Kallo ɗaya zakai mata itama dai ka fahimci tana cikin damuwar.       Kusan kwanaki goma tana ganin Maman tasu a wannan bahagon yanayin, kafin kuma taga ta warware ta cigaba da harkokinta a gidan cike da ƙarfin hali.         Abinda Zinneerah bata saniba shine mummunan labarin da Alhaji yaje ya samo a garinsune yakai ga mahaifiyarta kwantawa asibiti saboda motsawar hawan jininta. Sai dai kamar yanda Alhaji ya gargaɗeta yin gum da bakinta kar Zinneerah da abokan zamanta susan wani abu game da cikin Zinneerah ɗin yasata shanye komai a rai ta fawwalama UBANGIJI ikonsa da amsar ƙaddara. Musamman daya kasance duk wanda Alhaji ya jiyo labarin cikin Zinneerah a bakinsa saida ya yabi kyawawan halayyarta da wahalar data dinga sha ga matar ubanta. Harma takai wasu na ganin Inna ce silar komai akan cikin na Zinneerahn.            Hakan yaɗan sake girmama danganarta ta shanye komai ko a fuska basu taɓa nuna Zinneerah sunsan komaiba daga ita har Alhaji. matan gidan kuma sun sanar musu cewar ashe mijin Zinneerah ɗinne ya mutu kawai, ruɗanin rasuwarne ya sata baro gida cikin gushewar hankali. Maman halima ta tausaya mata, Maman Sakina kuwa ko'a jikinta. saima ƙorafi data dingayi akan kenan an ƙara ma mijin nasu nauyi tunda dai nan Zinneerah zata cigaba da zama ita da abinda zata haifa.      Babu wanda yabi takanta dan idan da sabo kowa ya rigada ya saba da halinta a gidan ai.          Zinneerah ta cigaba da rainon cikinta aɗan tsakanin nan cikin rashin jin daɗin jiki, dan tunda ya shiga wata na tara komai ya sake mata wahala. Harma takai randa suka koma asibiti dole Doctor ɗin ya riƙeta akan zata cigaba da zama anan har saita haihu.      Hakan baima Zinneerah daɗiba. Amma yaya zatiyi tunda ance wannan ne samun sauƙi a gareta. Yanzunma dai Maman Halima ce tare da ita, sai Mamanta dakanzo duk bayan kwana biyu ta amsheta ita kuma taje gida ta huta. Abba kam babu fashi kullum sai yazo safe da dare dubata. Ko'a fuska bai taɓa nuna ƙyamar cikin jikintaba balle bakinsa ya suɓuta wajen faɗama matansa dalilin samuwarsa.        A randa ta cika kwana tara a sibitinne da Naziru yazo dubata yake faɗa mata kwana biyu bayajin Khalipha kwata-kwata. Yayi ƙuru ya gwada kiransa ranar kuma bata shigaba. ya tura masa saƙo babu reply har yanzun.        Murmushi kawai Zinneerah tai na ƙarfin hali batare da tace komaiba. Hakan yasa shima bai sake cewa komaiba akan batun.         Washe gari data cika kwana goma cif a asibitin jikinta ya ƙwaɓe ta fara zubar jini (bleeding). Hankalin likitocin ya tashi harma da su Maman Sadiq dan sun fahimci naƙudace tazo mata a bahagon yanayi. Tun suna ganin zata iya haihuwa da kanta har al'amarin yasoyin tsamari suka yanke shawarar mata cs kawai.      Babu wani ja'inja Abba ya saka hannu matsayinsa na uba gareta. Daga haka suka shiga da ita ɗakin theatre su kuma suka koma gefe suna mata addu'ar rabuwa lafiya da abinda ke a cikin nata.         Awa kusan uku Doctor Mansura ta fito fuskarta da murmushi. Duk miƙewa sukai suna mai sauke ajiyar zuciya ganinta a yanayi mai daɗi. Ta sake faɗaɗa murmushin da faɗin, “Alhmdllhi, an ciro baby boy ƙyaƙyƙyawan gaske, mai kuma lafiya insha ALLAH”.         Basu gaza wajen ambaton Alhmdllh ɗinba suma, dan sunyi imani akan duk abinda kaga UBANGIJI ya jarabceka da samu ta hanyar da kai baka buƙatarsa ya fika sanin dalilin yin hakan. Basu isa canja ƙaddarar Zinneerah ba komai son hakan da zasuyi, sai dai su tayata da addu'ar ALLAH yasa haka shine mafi alkairi. Duk da har cikin ransu suna tsananin tausayin uwar da ɗan.        Abbane yace, “Yaya jikin ita Zinneerah ɗin kuma?”        “A Alhmdllh Alhaji. Itama dai insha ALLAH komai zai dai-daita zuwa nan gaba kaɗan. Kuyi haƙuri sai zuwa anjima zaku samu ganinsu koma da safe”.        Godiya sukai mata. Ta wuce su kuma suka koma suka zauna kowa da abinda yake saƙawa a ransa.     ★★★      Kamar yanda likita Mansura ta faɗa basu sami ganin Zinneerah ba a ranar dai kam, sai dai zuwa yamma an fiddo musu da jariri ƙaton gaske kuma ƙyaƙyƙyawa kamar yanda Dr Mansura ta faɗa ɗazun.      Abba ne ya fara amsarsa yana mai yin godiya ga ALLAH tare da jin tausayin yaron da baisan wanene shiba. Bayan ya masa addu'a ya miƙama Maman Halima daketa faman washe baki. Tace, “Masha ALLAHU mijin nawa kam dai-dai ni. ALLAH ya rayaka ya albarkaci rayuwarka. Ya jiƙan mahaifinka kaji”.         Da amin suka amsa. Kafin ta miƙama Maman Sadiq dake kukan zuci. Bata musaba ta amsa itama ranta fal tausayin yaron dabaijiba bai ganiba. Ta ƙura masa idanu na tsahon lokaci zuciyarta na suya akan samuwarsa ta hanyar da ba ita sukai fataba. Sai dai a gefen zuciyarta na gargaɗinta da ambaton Alhmdllh. Dan babu maima UBANGIJI dole akan abinda yaso. Babu kuma mai sakashi saɓanin hakan.      Itama dai addu'ar tai masa tamkar kowa ta sake miƙama Maman Halima dake kusa da ita. Ita kuma ta miƙama Matar Naziru. Bayan sun gama ganinsa da masa addu'a Nurse Salima tazo ta amshesa tana faɗin, “To waye zai zauna a wajenta? Dan an kaita ɗakin hutu yanzu haka. Sai dai likita tace wadda zata zauna da ita kawai za'a kai sai zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu zaku ganta”.         Dukansu sun gamsu da hakan, kafinma kowa yay magana Maman Halima tace ai bama sai anja zanceba itace zata cigaba da zama da ɗiyarta.     Wannan karamcin na Maman Halima kesa Maman Sadiq jin daɗi sosai da sake ganin girmanta da kimarta a koda yaushe, dan mace ce data cancanci girmamawa kodan ƙyawawan halayenta.          Sallama tai musu tabi bayan Nurse Salima. Su kuma suka fito domin komawa gida. ★★         Koda suka shigo gidan Maman Sakina batako leƙoba balle ta tambayesu yaya jikin Zinneerah ɗin tunda batabisu asibitinba. Duk da kuwa sanda Matar Nasiru tazo ta sanar musu ruɗewar jikin Zinneerah ɗin itama tana zaune a tsakar gidan. Amma taƙi bin Maman Sadiq. Bayan tafiyarta kuma bata kira waya taji halin da ake cikiba. Gashi yanzu sun dawo bataleƙo tajinba kuma.       Hakan bai dami Maman Sadiq ba. Dan halin da take ciki ya wuce na matsalar Saude a yanzun. Tana shiga ɗaki fashewa tai da kuka, kamar Alhaji yasan za'ai haka ya biyo bayanta kuwa. Ganinta tsaye gaban mirror kanta a ƙasa tana shashshekar kuka ya sashi ƙarasowa cikin ɗakin sosai.        “Haba Hauwa'u, minene kuma abin kuka anan dan ALLAH? Kenan bazaki iya karɓar ƙaddaraba? Ki tuna UBANGIJI ya fimu sanin abinda ke a ɓoye. Sannan yarinyar-nan mutane da yawa sun shaideta akan ba yarinyar banza bace. Kowa na ƙyautata mata zaton cewar tsautsayine kawai da ƙaddara da babu wanda ya isa kankaresu a rayuwarta. A ganina yanzu kamata yayi mu sake nutsuwa da janta a jiki wajen samun gaskiyar zance game da samuwar cikin, dan a yanda na fahimci zantukan jama'a a inda taje kwana da kwanaki ba'a saniba acan koma minene ya faru. Ina son ki kwantar da hankalinki ki karɓi komai a mashayin ƙaddara da jarabawa. Karki bari yarinyarnan ko wani a gidan nan yasan gaskiyar zance gameda yaron nan saboda gudun matsala, kokuma ita mu sakata  a wani halin da har zata iya tunanin sake sulalewa ta gudu daga nan kamar yanda ta baro can”.      Cike da gamsuwa da bayanin mijin nata ta share hawayenta. “Nagode Yaya, nagode sosai da rufa asirina dana yarinyarnan. Lallai kaiɗin masoyine na gaskiya abin alfaharin kowacce mace. Insha ALLAH zanyi kamar yanda kace, sai dai ka tayani addu'ar jurewa wannan al'amari”.        “Insha ALLAHU zan tayaki Hauwa'u. kema kuma kisa a ranki zaki iya ɗaukar komai kamar yanda kika ɗauki na baya da suka shuɗe. Kuma in ALLAH ya yarda inhar yarinyar nan bata da hakki duk inda uban yaron nan yake sai ya bayyana kansa watarana. ALLAH kuma zai wanketa ga idon kowa da izininsa”.       “ALLAH ya tabbatar da hakan Yaya”.       “Amin” ya amsa yana juyawa ya fita. Itama saita sake share hawayen da ke sake zubo mata. Zuwa tai ta leƙa yaranta taga harsun kwanta. Dama tasan Sadiq akwai ƙoƙarin kulawa kamar yanda ta horesa. Ɗan gyara musu abinda baiyiba tayi ta fito. Bayan tayi wanka itam ta kimtsa zuwa ɗakin maigidan dan girkintane.      Sosai ya sake mata nasiha da tausarta akan komai, ya kuma sakata sukai salla da mikama UBANGIJI kukansu da bukatunsu. Sai gashi Alhmdllh ta wayi gari zuciyarta sakayau. Harma da jin zumuɗin komawa a sibitin taga halin da ƴarta ke ciki da baƙon duniya da baisan wanene shi ba.             A asibiti kam da daddare ansha rikici, dan ɗan jinjiri dai kuka ya dinga tsula musu na yunwa gabannin asuba. Haka dai Maman Halima taita ƙoƙarin bashi ruwan zam-zam da aka haɗa da zuma a ciki. Zinneerah kam tanata faman barci batare da tasan wace wainar ake toyawaba.        Koda suka tashi aɗan barcin daya figesu bayan lafawa da kukan jaririn sai maman Halima ta samu sun makara. Lallaɓawa tayi domin gabatar da alwala. Tana kabbara salla tamkar jira yake ya fara raira kukansa da muryarsa dake cauy-cauy masha ALLAH.       Sosai maman halima ta rikice, tana a raka'ar ƙarshe taji shigowar mutum cikin ɗakin, ba'ayi maganaba dai, sai wani irin ƙamshin turare mai shegen daɗi daya gauraye ko ina na ɗakin. Tana ƙoƙarin sallamewa taji an fice da jaririn da har yanzu kukan yakeyi. Saurin sallamewa tai ta miƙe zaram ta biyo bayansu. Wayam babu kowa a wajen, sannan babu kukan yaron kuma. Hankalintane yay masifar tashi sanin duniyarnan fa babu gaskiya a cikinta. A cikin matuƙar ruɗani ta shiga leƙe-leƙe na neman inda aka nufa da yaron..............✍             *_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 _Na Safiyya Huguma_ *_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖 _Hafsat Rano_ *_★ DALAAL_*💝 _Na Miss xoxo_ *_★ UBAYD MALEEK_*💓 _Na Mamu gee_ *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 _Na Bilyn Abdull_ Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 *_08085405215_* IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   0903 234 5899 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 *_TYPING📲_* *_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_* *_Page 12_* ________________________ *_Hummmmm!!. Wai wai wai, wani aiki sai: GIDAN ƘAMSHI💃🏻💃🏻💃🏻🥺_* *_INA MATA ƳAN ƘWALISA MA'ABOTA SON ƘAMSHIN GIDA DANA JIKI?_* *_INA MATAN DAKAN SO DUK INDA SUKA DOSA KO SUKA BARI SAI SUN BAR MUSU TARIHIN ƘAMSHINSU_* *_TO MATAN ƘWARAI KUZO GA WANI SIRRI DAZAN BAKU DAGA FITACCEN GIDAN ƘAMSHIN NAN DA BAIDA NA BIYU A KANON DABO😁_* _Ina magana ne akan GIDAN ƘAMSHI da ke a Jihar KANON DABO MAIDUGURI ROAD MARIRI_. *MUNA SIYAR DA TURARURRUKAN WUTA SET NA AMARE, MUNA KUMA BADA SARI.* *AKWAI KUMA SABULUN GYARAN JIKI MAIDA TSOHUWA YARINYA, BUDURWA TAURARUWA, MATAN ƘWARAI ANNURIN HASKAKA GIDA. SHIMA DAI AKAN SARI, DOZIN KO KATON* *AKWAI KUMA ZUMAR ƘARA ƘIBA GA MATAN DA KESON SU GANSU DUMURMUR SUNA JUYAMA OGA KAYAN...😉🙈💃🏻 kundai gane*. *_Mata ku garzaya GIDAN ƘAMSHI domin ƙamsasa kanku kuma kar aci kasuwar sama babu ku😁_* *ZAKU IYA SAMUN MU TA WANNAN LAMBAR WAYAR: 07033778564 DOMIN JIN ƘARIN BAYANI*. *KO A KANO MAIDUGIRI ROAD MARIRI*.💃🏻💃🏻👍🏻 ________________________ *Page 12* .........Iya ruɗewa Maman Halima ta ruɗe. Tun tana leƙe-leƙe ita kaɗai harta nufi reception ta sanarma wanda ke zaune a wajen shi da wata budurwa. Ganin yanda take a rikice suka shiga tambayarta ko lafiya?.       “Inafa lafiya bayin ALLAH, ina salla wani ya shigo ya ɗauke jaririnmu. Dan ALLAH ku taimakeni na shiga uku”.         “Kinga mama kwantar da hankalinki, mu anan ba'a wannan dan asibitine dake tare da tsaro ta ko ina da kike gani” saurayin ya faɗa da sauri yana mikewa.        Katsesa Maman Halima tai, “Wane tsarofa anan yaro, inda da tsaro a shigo a ɗauki Jariri har cikin ɗaki? Ku taimakeni yaron nan ko uwarsa da tasha wahalar haihuwarsa bata dawo hayyacintaba, balle tasan mita haifa”.       Ganin bata cikin hayyacinta budurwar ta fito a inda suke a killace tana faɗin, “Mama dan ALLAH ki taimakemu ki nutsu, boss yana cikin asibitin nan karki ja mana matsala dan girman ALLAH”.      Sam Maman Halima ba saurarensu takeba, saima hankalin mutane data fara jawowa kansu saboda kwakwazonta. A wannan yanayi Maman Sadiq da Alhaji da Maman Sakina data biyosu yau saboda cin mutuncin da Alhajin ya mata suka iso. Jin abinda ya farune ya saka hankalinsu suma tashi, sai dai kafin suce wani abu sai ga Nurse Salima ɗauke da jaririn a hannu tana faɗin, “Wannan taron lafiya kuwa?”.      Yanda taɗanyi maganar da ƙarfine ya saka yawancin mutanen wajen juyawa suna dubanta. Kafinma wani ya bata amsa idon maman Halima ya sauka akan jinjirin, hakan yasata kwasa da gudu gaban Salima tana faɗin, “Ya ilahi, to aiga yaron ma anan”.        Kusan duk saida jama'ar wajen suka sauke numfashi. Saurayi da budurwar nan dake a reception sukace, “Mama abinda muke sanar miki kenan, amma kika gaza fahimta. Mudai munsan babu yanda za'ai mutum ya bata a asibitin nan”.       Salima data ɗan fahimci zancen tai ƙaramar dariya tana faɗin, “Kai mama wai kin ɗauka sacesa akai?. Asibitin nan yanada matuƙar tsaro fiye da yanda kike zato. Oga ne da kansa yazo gittawa zaije office ɗin Dr Mahmud yaji kukansa, shinefa ya shiga ɗakin danya duba. Sai ya samu kina salla shine ya ɗaukesa ya fita da shi. Yanzu na shiga wajen Dr Mahmud shine ya bani shi da faɗamin lambar ɗakin daya ɗakkosa. gashi ma yace a bashi wannan”. Ta ƙare maganar da miƙa ma mama wata ƴar takarda dake a linke da alamu suka nuna cheque ne na kuɗi.         Takardar Mama ta amsa batare data fahimci ta minene ba, yayinda su kuma mutanen wajen suka sami damar yin dariyar yanda ta ruɗe musu ɗazun.        Mama ma dasu Alhaji duk dariyar sukeyi, daga haka suka ɗunguma ɗakin da aka kwantar da Zinneerah. Mamaki ya kama Mama ganin ashema ta farka har likitan daya shigo ɗakin dubata yana ɗan musu faɗa akan fita su barta ita kaɗai haka.      Haƙuri mama ta bashi, tare da masa bayanin dalilin fitar tata. Ya ɗan murmusa yana faɗin, “A mama ai asibitin nan akwai tsaro sosai, motsin kowa dake ciki ana ganinsa ta cctv, dan haka ku kwantar da hankalinku babu abinda zai faru harku tafi insha ALLAH”.        “ALLAH yasa hakan” suka faɗa kusan a tare.        “Amin ya rabbi. Yanzu ga wannan, shine list ɗin komai na kuɗaɗen da zaku biya, sai kuma jini da zaku samo yanzu dan za'a ƙara mata. Dama jiran farkowarta muke mugani koda yuwuwar hakan, to yanzu kam naga alamar tana buƙatar jini leda ɗaya”.      Amsar takardar Alhaji yayi yana masa godiya, daga haka Doctor ya fice. Gaban gadon suma duk suka ƙarasa sunama Zinneerah sannu, da kai kawai take iya amsa musu batare data iya kallonsu ba. Sai faman haɗiyar zuciya take dan ita kaɗai tasan mitakeji a ranta. Ganin kamar batason hayaniyar ne ya saka Nurse Salima dake ɗauke da ɗan jinjirin daya gama shige mata rai har yanzu faɗin, “Inaga batason yawan hayaniya yanzu, idan kun gama dubata sai muɗan fita waje a bata waje”.      Gamsuwa da bayaninta ya sakasu amsa mata. Mama ta kalli Salimar tana faɗin, “Yauwa ƴarnan kinma sa na tuna. Ina dabinon da kika bada shawarar a tauna a bashi? Kinga yanzu tunda ga Alhaji sai ya bashi ɗin ko”.        Cikin ɗan nuna shakku Salima tace, “Aiko mama na muku laifi ko nace shishshigi, nazo da dabinon danna kawo mikine na biya office ɗin Dr Mahmud ɗin inda na sami Oga acan. To daya sanar min ɗakin da zan kawo yaron sai nake cewa dama can zani nakai dabino a bashi ko zai rage kukan yunwar da yakeyi. Jin hakan da kuma kukan da yaron keyi har lokacinne ya saka Oga ya amshi dabinon da kansa ya tauna ya bashi, har yana faɗin ALLAH yasa ya gaji sunansa”.        Alhaji dake saurarensu yace, “To masha ALLAH, ALLAH ya saka masa da alkairi duk da mu bamusan shi wanene ba”.       Salima tace, “Baba ai shine mai asibitin nan”.         Dukansu sai da suka ɗan ƙwalalo idanu waje. Mama tace, “Babbar magana, shima likitanne kenan?”.       “A'a mama, shi ba likita baneba, ɗan kasuwane. Nasan dai bazaku gaza sani kojin sunan *_AK SHIRA_* ba a garin nan ai”.          “Lallai kam sani bana wasaba, duk da dai ba sani na zahiri bane, amma wannan sunan ba ɓoyayyen suna bane, dan a Shira Family kowa yasan *AK SHIRA* ba ɓoyayye bane, kodan gidajen mansa kawai ai sun isa ka sanshi, balle kuma hidimar da yake ga bayin ALLAH mara iyaka”.        “To aiko Baba shine da kansa ya bama jaririn nan dabino yau, tare da wannan takarda da nake kautata zaton kuɗine rubuce a ciki”.      Sosai maganar ta sake girgizasu, mama ta mikama Alhaji takardar cheque ɗin. Amsa yay ya duba yana jinjina kansa. “Uhm lallai wani aiki kam sai manya. ALLAH ya saka masa da alkairi. ya azurtashi da duk alkairan duniya da lahira, ya kuma cigaba da karesa a duk inda ya saka ƙafa. Kuɗine zunzurutu harna dubu ɗari biyu ya rubuta anan”.      Sosai suka ƙara jin mamakinsa, ace lokaci guda mutum yay ƙyautar dubu ɗari biyu wa jariri kawai. Alhaji ya katse zantukan nasu da faɗin, “To lallai kam abokina dole kaci sunan AK Shira ai”.      Dariya duk sukayi banda Maman Sadiq datai ɗan murmushin kawaici. Hakama Zinneerah dake saurarensu kawai tana share hawayenta a ɓoye.      Alhaji ya buƙaci Salima ta rakashi yaymasa godiya, daga nan yaje wajen neman jinin da biyan kuɗaɗen da sukace. Bata musaba ta miƙama Mama jaririn suka fita. Office ɗin Dr Mahmud sukaje. Bayan Salima tai knocking ya basu izinin shiga suka shigo.          Shi kaɗaine a ciki, sai dai mayen ƙamshinsa na nan manne da office ɗin duk da babu shi a ciki. Dr Mahmud yace, “Salima lafiya dai?”.      “Laya ƙalau Doctor, dama Baba ne yace na rakosa yayma Oga godiya. Sune masu jinjirin nan na ɗazun”.       “Oh ALLAH sarki, Baba ina yini”. “Lafiya lau likita, ya aikin naku?”.      “Alhmdllh baba. Sai dai gashi kuma shi harya tafi, kasan shi uziri ba ƙaremasa yakeba. Dama yakan zo duk irin wannan ranar a tsakkiyar shekara da ƙarshenta ne ya bada jini inhar yana kano, yanzu hakama zaije Lagos ne ya biyo tanan ya bayar, ina ƙyautata zaton yanzu haka ya isa airport”.       Alhaji yace, “Ashsha. Naso kam na gansa nai masa godiya wlhy, sannan ya cika ladansa nama yaron nan huɗuba ya kuma saka masa sunan nasa dan ya cancanta”.        Cikin jin daɗin wannan karamci Mahmud yace masha ALLAH, shi da ya faɗa da wasa ashe ALLAH ya amsa mai sunan nasa aka samu, duk da nasan yanzu yayi nisan kiwo, amma bara na taɓasa a waya muji ko zamu samu ya ɗaga baba ka zauna”.       Zama Alhaji yayi yana murmushi. Dr Mahmud ya ɗauka wayarsa shima fuska ɗauke da murmushi ya shiga kiransa. Tana gab da tsinkewa aka ɗaga. Harma Mahmud ya fidda ran hakan. Cike da zumuɗi Mahmud yace, “Afuwan ranka ya daɗe kaga na kiraka”.      Basusan amsar da aka bashi daga canba. Cikin ƴar dariya yace, “Tona gode ranka ya daɗe. Dama masu jaririn daka ɗakko ɗin nan ne sukazo maka godiya, tare da sake kawosa ka cika ladanja ta masa huɗuba da saka masa sunan naka”.     Nanma basuji miya faɗaba, sai dai yanda fuskar Dr Mahmud ta ƙara washewa da fara'a zaka tabbatar da magana mai daɗi yake masa. Sai kuma ya saka wayar a amsa kuwwa (Hansfree) ya ajiye gaban Alhaji.          Wata tattausar murya mai cike da tarin nutsuwa kamar ta rowa sukaji tace, “Assalamu alaikum, baba barka da rana”.        Da sauri Alhaji yace, “Wa'alaikissalam, barka dai ranka ya daɗe, yaya ƙoƙari?”.      “Alhmdllhi baba. Yanzun nakejin daddaɗan albishir na samun takwara, gashi kuma nayi gaggawar tafiya”.      Yanda yake maganar cike da nutsuwa kamar bayasone ya saka Alhaji yin murmushi mai faɗi. “Alhaji ai kowa zaiso samun mai sunanka a gidansa kodan tarin alkairan dake tattare dakai. Munga hidima ALLAH ya saka da alkairi ya ƙara buɗi. Amma naso ace kaine da kanka kaima yaron nan huɗuba da sunan daka zaɓa masa”.       Kaɗan sukajiyo sautin murmushinsa daga can, cikin sake nutsar da muryar tasa mai sauti a tausashe yace. “Nima naso hakan Baba, dan kun bani abu mai daraja da bazan mantaba a tarihin rayuwata, amma duk da haka na bama Mahmud wakilcin yima takwarana huɗuba. ALLAH ya rayasa ya albarkaci rayuwarsa, ALLAH yasa ya zama mai tausayinmu da jin ƙanmu anan gaba”.           Atare suka amsa da amin kowa cikin jin daɗi. Musamman ma Alhaji dake mamakin yau shine ke magana da AK Shira baki da baki ta waya. Wata hikima sai UBANGIJI. Shikam dai har abada bazai taɓa mantawa da haihuwar wannan yaro ba a rayuwarsa.       Kamar yanda ya bada wakilci ga Dr Mahmud hakance ta faru, dan har ɗakin da aka kwantar da Zinneerah Dr Mahmud yaje yayma yaro huɗuba. Ya kuma ajiye kuɗi dubu hamsin shima yace asai rago a yankama takwaran abokinsa, kuma ogansa ranar suna.       Shima sun masa godiya sosai, kowa na jinjinawa a ransa yaro yazo da farin jini. yayinda Maman Sakina keta taɓe baki a kaikaice, a ranta kuwa tana ganin tsabar iya asirine na ƴan ƙauye kuma Katsinawa da kullum take ambata ga maman Sadiq.           Tare Alhaji suka fita da Dr Mahmud. Sai bayan kusan mintuna talatin ya dawo ɗauke da madaidaicin kwali da aka zubo masa magungunan da Doctor yace su sayo da drips, sai jini leda ɗaya. Kwalin Maman Sadiq ta amsa takai ɗakin dan sun fito waje. Tana fitowane yake faɗin, “Wani iko sai ALLAH, kunga jininma da naje nema a lab ɗin nasu saina samu bawan ALLAHn nan ya bada nasa a ajiye idan masu bukata sunzo nema. Cikin ikon ALLAH sai gashi ni na fara zuwa kuma. Gashi sun bada ƙyauta babu ko sule”.       Cikin riƙe haɓa Maman Sakina da hassada kecin ranta tace, “Oh har jini yake zuwa ya badar a asibitin kuma? Dan tsabar jin daɗi irin na masu arziƙi”.      Alhaji ya bata amsa da cewar, “Wlhy kin gani dai, dama likitan daya kira mani shi a waya yace jinin yazo badawa kawai shiyyasa bai jimaba ya tafi”.         Sudai su Maman Sadiq godiya suka sakeyi da jera masa addu'oin gamawa da rayuwa lafiya. ★★★          Sai yamma Zinneerah ta farka sosai cikin hayyacinta, bayan an cire mata jinin da aka gama ƙara mata. Bayan likita ya shigo ya fita suma su Maman Sadiq suka shiga. Zaune suka isketa jingine da filo ta zubama yaron dake gefenta yana barci ido. A zahiri shi take kallo, amma idan ka nutsu kaima a kallonta zaka fahimci sam batama tare da duniyar mutane gaba ɗaya. Dan yaron kuka yake iya iyawarsa amma da alama ba jinsa takeba.      Matar Naziru ce tasa hannu ta ɗauki yaron tana faɗin, “Haba Zinneerah, yaro na kuka ke kuma kin tsaya kallonsa kawai”.      Nan ɗinma ba jinta tai ba. Sai da Maman Halima ta taɓata sannan ta kawo numfashi. “Oh ni Binta, mi kike tunani haka Zinneerah?”.     Maman Halima ta faɗa tana tsatstsareta da idanu. Ƙasa kawai Zinneerah tai da kanta tana ƙoƙarin haɗiye kukan daya tokare mata ƙirji tun ɗazun. Matar Naziru dake jijjiga yaron dai yay shiru tace, “Haba Zinneerah ai yanzu ba lokacin kuka bane, lokacibe da zamu taru mugodema ALLAH ne. Jiya iyanzu muna nan cikin tsananin tashin hankali da fargabar rasaki, amma cikin amincin UBANGIJI yau gaki zaune da ƙyauta mai girma da wasu kecan suna bulayin nema da kuɗi amma ALLAH bai ƙaddara samuwarta garesuba. Kiyi haƙuri kibar kukan nan, mu yanzu babban fatanmu kuma ALLAH ya baki lafiya mu koma gida”.        “Maganarki kam gaskiyace Maman Abu. Zinneerah yanzu lokacine na godiya ga ALLAH kinji. ALLAH ya ƙara miki lafiya. Kinga yaron nanma ya kamata a bashi abincinsa dan wannan kukan bana komai bane sai na yunwa, tunda likita yace zaki iya ɗan gwada bashi yanzu sai a gwada ɗin ai ko”.        Sake fashewa da kuka Zinneerah tayi, dan ita kaɗai tasan yanda takeji a ranta akan wannan al'amari mai rikitarwa da matuƙar ruɗani. Tunda take bata taɓajin labari irin nataba. Tayaya zaka haifi ɗa na mutum batare da kasan yanda ka samu cikinsa ba. Anya kuwa yaron nan baɗan wani aljanin baneba?......       Shigowar Alhaji da Maman Sadiq da gayyar yaran gidan gaba ɗaya har da ƴaƴan Maman Sakina ya katse mata tunani. A take kuma ɗakin ya kaure da hayaniyar yaran. Dan bayan sun mata yaya jiki gaba ɗaya hankalinsu suka maida ga ɗan jinjirin suna yaba ƙyawun da ALLAH yay masa. Sai da Maman Halima taga kukansa na ƙara ƙarfine ta amsheshi cikin tilastawa suka saka Zinneerah bashi abincinsa tanata kuka.       Alhaji da Maman Sadiq ne kawai suka iya fahimtar kukan Zinneerah saboda sune sukasan labarin tushen samuwar yaron. Dan ita kanta maman Sadiq konawarsu gida tasha kuka, a yanzu hakanma kukan zuci takeyi. Su Maman Halima kuwa da basusan dawan garinba sai tunaninsu ke basu Zinneerah tana kukane saboda tunawa da mahaifin yaron da akace rasuwa yayi.      Da ƙyar aka samu ta bari yaɗan kama na wasu mintuna. Dan kuka take sosai tana yarfa hannu wai zafi. Maman Halima ta ɗaukesa tana mata faɗa akan karta sakama ranta fargabar tsotso dan yaron nan daga gani ba wasa zaiyi da cikinsaba. Ita dai Zinneerah zamewa ma tai ta kwanta a hankali tana matse baki dan inda aka yankata na mata ciwo sosai har yanzun.       Sun daɗe a asibitin yaran na cigaba da jagwalgwala yaron da aka samu yay shiru, yayinda Zinneerah ke kwance shiru bata sake kula kowa ba. Idonta a lumshe suke tana zirar da hawaye ta gefensu, yayinda hancinta ke shaƙar daddaɗan ƙamshin turaren dake manne da jikin showal ɗin yaron da batan a ina ya kwasoshi ba.        Ƴar hayaniyar yarance ta saka Doctor shigowa ɗakin yace suyi haƙuri a barta ta huta hakanan, ya kuma bada damar a bata abu mara nauyi tasha, kamar shayi ko kunu haka. Godiya sukai masa ya fice. Alhaji kuma ya tattara iyalansa shima sukai musu sai da safe suka tafi. Aka barta daga ita sai Maman Halina dake haɗa mata kunun da akace zata iya sha ɗin. _____________★         Haka Zinneerah ta cigaba da jiyya a asibiti. yayinda abokan arziƙin Maman Sadiq na anguwa da dangi ɗai-ɗai dake anan suke ɗan shigowa dubata. Kulawa da take samu na abinci ya saka komai yake tafiya kan tsari Alhmdllh. Dan jikinta yayi ƙyau sosai a kwanki shidan data ɗauka a asibitin. Idanma ba'a faɗa makaba bazaka taɓa ɗauka cs akai mataba. Sai dai sam babu mai ganin walwalarta, sannan ko kallo yaron bai ishetaba sai Maman Halima ta mata jan ido.      Matsalar da suke fuskanta da yaron kawai shine idan yasha nono cikinsa sai ya kumbura yayta kuka. Da farko basu fahimci hakanba sai suke ɗauka cibiyarsa ne ke ciwon. Sai daga baya Doctor ya gane inda matsalar take. Dan haka ya dakatar da Zinneerah daga bama yaron nonon gudun kar a cutar da yaron kuma. Sai dai sun ɗorata akan magani zuwa wani lokaci sai ta cigaba da shayar da shi. shi kuma yaron suka bada shawarar a ringa bashi madara.       Hakan yama Zinneerah daɗi, dan a shirementa ayyanawa take a ranta ta huta da ciyar da ɗan aljanu, dan har cikin ranta ta yarda aljanune sukai mata ajiyar yaron kawai a cikinta.      Babu wanda yasan da wannan shirmen nata, sai dai ranar tsabar jin daɗi har ɗan sakin jikinta tai sukai hira da Maman halima da ada take danganta rashin walwalar Zinneerah ɗin da rashin ƙarfin jiki.        Washe gari Alhaji ya sayi raguna biyu aka raɗama yaro suna Abdul-Mutallaf a masallaci, wato dai takwaran AK Shira kenan kamar yanda akai masa huɗuba. Ba ayi wani shagaliba kasancewar mai jego na asibiti, sai dai maman Sadiq tayi abinci ta bada sadaka ko zata samu sassauci a ranta da nutsuwar rugumar wannan ƙaddara a garesu.         Da yamma da sukazo dubasu a asibiti Alhaji yake sanarma Maman Halima cewar yaro yaci suna Abdul-Mutallaf.      Cike da murnarta da farinciki taita jera addu'a ga jariri tana tsokanarsa. Zinneerah kam ko motsi bataiba balle ta nuna taji sunan da yaron yaci. Sai dai tausayinsu da takeyi akan sunatama ɗan aljanu hidima batare da sun saniba. Ta tabbata wataran sai aljanin daya ajiye mata ɗan yazo ya ɗauke ɗansa batarema dasun saniba zasu gane wahalar banza sukayi. Babu wanda ya damu da rashin tankawar tata. Garama maman halima taɗan mata faɗa kamar yanda ta saba idan taga tana share yaron. Shiru dai tai batace komaiba kamar kullum, sai hawayen data share a ɓoye duk da ita Maman Sadiq na lure da ita.          Ganin komai normal ta samu lafiya Alhmdllh washe gari aka basu sallama. tare da basu ranakun da zasu dawo domin duba lafiyarta. Daɗi sosai Zinneerah taji da wannan sallama. dama ba ƙaramin gundura tayi da zaman asibitinba.         Koda suka dawo gida sun sami ƙyaƙyƙyawar tarba daga yaran gidan, dan harda ƴaƴan Maman Halima na ma'auri duk sunzo gidan tarbarsu, dama duk sai da sukaje asibiti anan nema Zinneerah ta fara saninsu. Amma yanda suka karɓeta saika ɗauka a cikinsu ta tashi itama.      Yau ɗinma tararwa sukai sun haɗa wata ƴar ƙwarya-ƙwaryar liyafa iya su kawai ƴan cikin gidan, sai ƴaƴan Naziru da matarsa da maƙwafta na kusa da ake gaiswar mutunci. Kowa yayi mamaki dan babu wanda yasan da wannan shirin nasu. Maman Sadiq zata hana Alhaji ya hanata akan kartace komai, dan sudai basusan komaiba akan wannan haihuwa ba. Sannan kosu ɗin da suka sani ai Zinneerah batasan sun saniba. Su daure su ƙarfafa farincikinta har lokacin da za'aje gaɓar da tuhumarta zatai musu amfani, kuma dalilin hanyar samuwar ɗan bazaisa su toshe hanyoyin karɓar ƙaddarar da yazo a cikintaba, da har zasu ƙi farinciki ko nuna godiyarsu ga ALLAH.       Badan tasoba ta haƙura ta zuba idanu itama.      Ita dai Zinneerah bata nuna wani alamun damuwa da hakanba, dan tunda suka shigo gidan Maman Halima tai mata gashi na musamman a jikinta sai ta samu nutsuwa sosai, aka kawo mata abinci kuma taci ta ƙoshi tasha magani sai barci. Sai gashi har suka gama walinarsu ita bama tasan wace waina suke toyawaba, sai bayan ta tashine su Aunty Halima suka shigo sukai mata sallama zasy wuce gida dan lokacin anyi sallar isha'i.        Yanda suke nuna mata so da ƙauna su da mahaifiyarsu yasa itama take sakin jiki dasu sosai, kuma tanajinsu tamkar yayunta, dansun maye mata gurbin su Yaya Gajejen ta.............✍       *_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 _Na Safiyya Huguma_ *_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖 _Hafsat Rano_ *_★ DALAAL_*💝 _Na Miss xoxo_ *_★ UBAYD MALEEK_*💓 _Na Mamu gee_ *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 _Na Bilyn Abdull_ Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 *_08085405215_* IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   0903 234 5899 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 *_TYPING📲_* *_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_* *Page 13* ________________________ *_Hummmmm!!. Wai wai wai, wani aiki sai: GIDAN ƘAMSHI💃🏻💃🏻💃🏻🥺_* *_INA MATA ƳAN ƘWALISA MA'ABOTA SON ƘAMSHIN GIDA DANA JIKI?_* *_INA MATAN DAKAN SO DUK INDA SUKA DOSA KO SUKA BARI SAI SUN BAR MUSU TARIHIN ƘAMSHINSU_* *_TO MATAN ƘWARAI KUZO GA WANI SIRRI DAZAN BAKU DAGA FITACCEN GIDAN ƘAMSHIN NAN DA BAIDA NA BIYU A KANON DABO😁_* _Ina magana ne akan GIDAN ƘAMSHI da ke a Jihar KANON DABO MAIDUGURI ROAD MARIRI_. *MUNA SIYAR DA TURARURRUKAN WUTA SET NA AMARE, MUNA KUMA BADA SARI.* *AKWAI KUMA SABULUN GYARAN JIKI MAIDA TSOHUWA YARINYA, BUDURWA TAURARUWA, MATAN ƘWARAI ANNURIN HASKAKA GIDA. SHIMA DAI AKAN SARI, DOZIN KO KATON* *AKWAI KUMA ZUMAR ƘARA ƘIBA GA MATAN DA KESON SU GANSU DUMURMUR SUNA JUYAMA OGA KAYAN...😉🙈💃🏻 kundai gane*. *_Mata ku garzaya GIDAN ƘAMSHI domin ƙamsasa kanku kuma kar aci kasuwar sama babu ku😁_* *ZAKU IYA SAMUN MU TA WANNAN LAMBAR WAYAR: 07033778564 DOMIN JIN ƘARIN BAYANI*. *KO A KANO MAIDUGIRI ROAD MARIRI*.💃🏻💃🏻👍🏻 _______________________ *Page 13* ............A zahiri dai Zinneerah ce ta haifi Abdul-Mutallaf. Amma dukkanin abinda ya shafi yaron ƙiri da muzu ta sakarma Maman Sadiq. Musamman daya kasance ba abincinsa yake sha ba yanzu sai madara. Idan ka gansa a hannunta ko tana masa wata hidima to Mama Sadiq na wajen Abba ne ko tana aiki, yaran kuma basa gida.       Wanda bai saniba ma idan yazo gidan saiya ɗauka Maman Sadiq ɗince ta haifi yaron. Tsabar ƙwarewa a shahara wani lokacin idan tace Zinneerah tai masa wani abu tata kumbura baki kenan. Ita maman Sadiq ma abin har dariya yake bata.         Itako Zinneerah ba komai ke ɗawainiya da itaba sai tsabar shirme da ƙuruciya, sannan har cikin ranta ta rigada ta saka cewar yaron ɗan aljanune suka ajiye mata. Bawai bata sonsa bane, sosai take son abinta kasancewarta mai son yara dama can, dan a hankanma wani lokacin haka zata zauna taita satar kallonsa, idan kuma Mama ta fita a ɗakin takan ɗaukesa kota zauna tana kallonsa tana murmushi da shafar kansa, kai har kiss idan ALLAH ya cidashi yimasa akeyi ko rawa.       A yau kusan shine ma ya tadasu da asubahi da kukansa, dan a daren jiya tsautsayi ya saka Maman Sadiq tsare Zinneerah ta shayar dashi akan ko za'a dace yanzun tunda tana shan maganin. Sai gashi a cikin rashin dacewar cikin yaron ya kumbura kamar yanda ya ringayi a asibiti. Abba daya dawo daga masallaci ya shigo yana faɗin, “Yaya dai wai nikam?. Mi akaima abokina ne yau a gidan nan?”.       Maman Sadiq dake bashi maganin da aka dinga bashi sanda suna asibiti idan hakan ta faru ta ɗago tana dubansa. “Wlhy Yaya tsautsayi yasa na sakata ta shayar da shi jiya da daddare dan tausayi yake bani, ace jinjiri kamar wannan babu abincinsa sai madarar banzar nan. Tofa shine kaga cikin dai ya kumbura kamar yanda yakeyi”.       Amsarsa yayi a hannunta bayan ta goge masa maganin daya ɗan ɗisa masa a wuya. Ya sakashi a kafaɗa yana hura masa kunne da shafar bayansa. sassauta kukan ya farayi kaɗan-kaɗan, kafin ya koma ajiyar zuciya. Kusan mintuna biyar suna a haka yaron ya saki gyatsa mai ƙarfi. Su dukansu sai da suka sauke numfashi. Su Sadiq dake zaune duk cikin damuwa Abdul yace, “Abba Little yaji sauƙi (dan haka suke kiransa saboda Abdul ɗin).        Fuskar Abba da murmushi yace, “Insha ALLAH yaji sauƙi gashi yayi gyatsa. Da alama kuma barci ma zaiyi, sai a goyashi”. Ya ƙare maganar da kallon Maman Sadiq.        Miƙewa tai tana faɗin, “Tazo ta goyashi ɗakinka zanje na gyara, dan sakarci duk wannan ihun da yaron nan keyi tana ciki tana jinmu amma ko leƙe, tun a ɗakinma luf tayi ita a dole barci take bata jimuba”.      Dariya kawai Abba yayi batare da yace komaiba. Maman Sadiq kuma ta shiga kwalama Zinneerah da duk tana jiyosu daga ɗakin kira. Fitowa tai sum-sum-sum kamar wata munafuka. Abba yace, “Koma ki ɗakko zani kizo ki goyashi akwai sanyin safiya”.        Cike da kunya ta juya ta koma. babu jimawa ta dawo da zanin goyon a hannu. Maman Sadiq ce ta amshesa ta saka mata a baya dan har yanzu ba wani iya goyon tayi da ƙyauba. Kusanma wannan shine karo na uku kacal da zata goyashi. Dan mafi yawancin lokuta su ƴan biyune ke goyashi ko Maman Halima ko ita Maman Sadiq ɗin. Har Sadiq da Abdull goyamusu akeyi, ƴaƴan maman sakina ma sukan faki ido suzo su ɗaukesa saboda kusan shine ɗan ƙaramin yaro yanzu a gidan, sai yazan abin sha'awa ga kowa banda maman sakina da ko sau ɗaya bata taɓa ɗaukarsaba ma ita.      Da ƙyar Maman Sadiq ta samu goyon yayi dai-dai tanata ma Zinneerah ɗin faɗa. Ita dai batace komaiba sai dariya takema a ranta wai mama ta dage da masifa akan ɗan aljanu, sai randa sukazo suka ɗauke abinsu taga yanda kowa zaiyi a gidan ai.           Bayan fitar Abba da Maman Sadiq Zinneerah ta hau gyaran ɓangaren nasu kamar yanda ta saba, Sadiq kuma suka shige suna shirin makaranta dan an koma hutu. ★★★★        Haka rainon Little Abdull ya cigaba da gudana kusan kaso biyu a hannun Maman Sadiq da maman Halima ne. Kaso ɗaya kuwa Zinneerah na rabawa dasu Sadiq. A haka sukai arba'in yaron yay ɓulɓul masha ALLAH, ga ƙyawunsa na sake fitowa. Yaro gaba ɗaya bai ɗakko kamannin Zinneerah ba ta fuska sai halittar yatsunsa na ƙafa da hannu da abinda ba'a rasaba. Amma daga basuba kamanninsa daban da nata. Takan zauna ta dinga kallonsa da shiga dogon nazarin ko zata iya gano da wanda yake kamar. Amma sam bata iya hasaso komai ga kamannin nasa.         Sosai jikinta ya warke, idanma baka saniba bazaka taɓa ɗauka cs akai mataba. Musamman da yazam bayan dawowarsu gida maman Sadiq da Maman Halima kulawa da gyara na musamman suke mata wanda ita bawani gane inda suka dosa take ba. Abinda kawai ta sani tanajin daɗin jikinta sosai balle yanzu barci take sosai tamkar kasa. Ga lafiyayyen abinci da take samu kuma ga kwanciyar hankali. Sam bata wani tunawa da Inna. Garama Babanta da Yaya Sa'a da Yaya Gajeje. Takanyi kuka a duk sanda sukazo mata ranta koda a boyene. Sai ko Khalipha da har yanzu yake maƙale a zuciyarta. Gashi yanzu Naziru ko gidan yazo baya mata maganarsa ma. Itako kunya ta hanata sake tambayarsa ko yanzu yana samunsa.       Bayan tayi arba'in da kusan wata ɗaya Maman Sadiq taga zaman nata baida wani amfani. sai dai taci ta ɗanyi aikin gida ta kwanta barci. Samun Abba tai da shawara akan Zinneerah ɗin ta shiga wata islamiyya dake anan kusa da su ta ƴanmata, inda su Sakina ke zuwa da yamma. To sunayi da safe kuma zuwa ƙarfe ɗaya ga yaran da basa zuwa boko.       “Eh shawaranki mai ƙyau ce Hauwa'u, nima kuma maganar fara karatunta dama yana raina. Na bartane kawai Abdul-Mutallaf ɗin ya ƙara ƙwari sannan. To amma tunda dai naga bama itace ke rainonsa ba gara ta fara islamiyyar kawai itama bokon sai a nema mata inda zai dace da ita dan nasan da wuya ace acan tayi karatunma”.        Cikin gamsuwa da bayaninsa Maman Sadiq tace, “ALLAH ya saka da alkairi yaya, sai dai duk da bamu taɓa maganar karatu da itaba sai naga kamar taɗanyi acan, dan naga wasu lokutan idan su Abdull na Assignment haka takan saka musu baki harma tayi gyara a wani wajen”.      “A'a ikon ALLAH, to kinga kiramin ita dai muji ta bakinta, kinga ai sai mu sami madafar kamawa ko”.      Miƙewa tai tana amasa masa da to. Babu jimawa kuwa sai gasu sun dawo tare da Zinneerah. Bayan ta gaida Abba sai yake tambayarta ajinta nawa a makaranta?.        Duk da a bazata tambayar tazo mata sai gashi ta saki murmushin da ya basu mamaki. Kanta tsaye cike da zumuɗi tace, “Abba nayi jsce ma ai”.       “Ikon ALLAH, to to Alhmdllh. Ashe ɗiyar tawama ƴar boko ce bamu da labari. Amma gaskiya naji daɗin hakan sosai, kuma na yaba ƙoƙarin babanki anan....”      Cikin suɓutar baki tace, “Lah Abba ai bama shine ya sakaniba. Inagama Baba fa baisan ina zuwa makarantaba, dan shifa babu ruwansa dani a gidan. Ni saima nayi kwana hudu biyar ban gansaba wani lokacin”.       Duk idanu suka zuba mata, a ransu kuma cike suke da zumudi da jin daɗin yanda ta fara sakin jiki da faɗa musu abinda ke ranta.      Maman Sadiq ce tace, “To wani guri yake zuwa da har kike kwanaki baki gansaba?”.       “A'a mama, yana nan a gidan, kawai dai bansan miyasaba shi bayason ganina ne wani lokacin, wani lokacin kuma daga sallar asuba idan ya fita bai dawowa sai munyi barci”.         Babu wanda ya iya magana tsakanin Maman Sadiq da Alhaji. Maman Sadiq dai rayawa take a ranta yaushe al'amarin baban ya taɓarɓare haka kuma?. Dan tasanshi a da mutumne tsayayye akan iyalansa da gidansa. Dan ko talla wannan bai yarda yaronsa ya fita ba. Duk inda akai sallar isha'i kuwa yana gidansa, bazai sake fitaba sai asuba. Da an idar da salla zai dawo gida ya karya sai rana ta haska zai fita kasuwa wajen sana'ar sai da dankalinsa ɗanye da makani.......          Tambayar da Alhaji ya jefama zinneerah ce ta katse tunanin Maman Sadiq ɗin ta maida hankalinta garesu.        “Karki damu yarinyata, haka rayuwa take kullum cikin tsere-tsere da jarabawa. To amma wanene ya kaiki makarantar?”.        Kunyar wanda zata ambata ɗin ya sakata jan lokaci kafin ta bashi amsa. “Abba Babawo ne ya kaini kafin ya koma yace Yaya Karima yake so”.        Duk da a dunƙule tai maganar kasancewarsu manya masu hangen nesa sai duk suka gano inda ta dosa kai tsaye.      “ALLAH ya saka masa da alkairi”. Abba ya faɗa dajin daɗi. Amin sukace ita da maman Sadiq. Daga haka Abba ya sallameta suka cigaba da tattaunawa shi da matarsa.        “Hauwa'u kinga fa'idar shiru da mukai mata akan son sanin bayanta ko? Ina mai tabbatar miki inhar zamu cigaba da binta a haka harma abinda bamuyi zatoba sai munji daga gareta wataran. Kinsan shi yaro tamkar dabba yake, mai kula dashi da mai sake masa shi yake sakewa da shi shima. Dan haka ki sake nutsuwa wajen fahimtarta a hankaki komai da muke buƙata zai fito. Domin a fahimtar danai mata rashin samun sake a inda ta baro ya sakata kasancewa shiru-shiru kamar mara wayo. Amma ras take kuma tanada kwaramniya, sai a hankali zakiga ta hau bisa hanya da ƙyau”.      Murmushi maman Sadiq tayi har haƙoranta na bayyana. “Maganarka haka yake Yaya. Dan yanda ma zakaji tana faman shagali dasu Sadiq idan na barsu su kaɗai ya isa tabbatarwa. Idan kaji bakinta cauy-cauy baka taɓa cewa itace ke zuba zance”.      Dariya shima Abban ya sakeyi. “Ahaf kaɗanma kenan. Bayan takurar data taso a can harda cikin yaron nan ya sake dankwafe dukkannin kuzarinta da karsashi. Amma zata ware tsaf ta bama kowa mamaki. Naga alamar kuma tanason karatu ma sosai, dan jin daɗinsa ya sakata bamu labarin abinda bamu tambayetaba ma”.       Haka suka cigaba da hirarsu cike da fahimta dajin daɗi. Yayinda Zinneerah kecan tana tsallen murna zata koma makaranta. Harda ɗaukar Little dake barcinsa ta hau masa rawa. Aiko ya farka ya birkuce mata kuma. Da ƙyar ta lallashesa tana dungure kansa da goyasa wai karya tona mata asiri Mama tazo tai mata faɗa ta tada ɗan aljanu kuma.        Kwana uku dayin maganarnan aka saka Zinneerah islamiyyar safe zuwa 2 sun taso. Kusan dai-dai da yaran gidan kenan amma ƴammatan kawai dake shirin gama secondary. Su Sadiq kam sai shidda suke tasowa makarantarsu haɗe take da islamiyya.       Faɗa muku irin kalar farinciki da Zinneerah tayi ɓata lokacine. Sai da akaje makarantar kuma ta raina kanta dan batasan komaiba. Amma tayi alwashin nutsuwa sosai ta fahimci komai ɗin kodan ta ribantu a duniya da lahirarta                         _________________★        A kwana a tashi babu wahala wajen UBANGIJI. Yau ga Abdul-Mutallaf (Little) da wattani bakwai a duniya. Yaro ƙyawunsa nata ƙara fitowa fili da lafiya ingantacciya. Bazaka taɓa cewa ba abincinsa yake samu daga mahaifiyarsa ba. Dan ma zazzaɓin haƙora kan girgiza kuzarin nasa wasu lokutan.         Amma da yake zuwa yanzun cin abubuwa yake sosai, dan su Aliyu komai suka yayo kimsa masa suke shiko ya cinye abunsa sai hakan ya ƙara taimaka masa aynun. Rarrafe yake ko ina ga ɓarna, inda yana waje kowa kaye-kayen kayansa yake inba hakaba yazo ya tarar an canja musu sabon tsari.       Babu ruwansa da Zinneerah, hasalima ƙyuya yake mata wani lokacin. ba komai ya jawo hakanba sai itama rashin kulashin da takeyi sosai. Dan komansa Maman Sadiq ce sai kace itace uwarsa. Shi da su Sadiq kuwa ai da kuka ake rabuwa idan zasu makaranta. Dasun dawo kuwa zakaga walwalarsa ta daɗu.        Zinneerah nata karatun islamiyyarta wanda a yanzu tayi matuƙar yin nisa dai-dai gwargwado, dan ko a Alkur'ani ta kusa kai izifi biyu, ta saka himma sosai. Hakama sauran littatafai bata wasa. Bokon dai ce ba'a kai ga sakataba har yanzu saboda wasu ƴan dalilai da suka riƙe Abba. Amma yanata shirin hakan batarema da sanintaba.          ★★★★★★    Little nada shekara ɗaya cif a duniya da ƴan kwanaki ALLAH ya bashi ikon fara takawa. Ranar zokaga murna wajen su Aliyu. Zinneerah na zaune a falon ita da Mama suka dinga ihunsu na murna mama na tayasu da dariya. Zinneerah dai ta murmusa ta kauda kanta ga abinda takeyi, sai dai a kallo ɗaya zakai mata ka fahimci kawaicine kawai takema mahaifiyarta, amma har cikin ranta tanason ɗanta da jin daɗin duk cigaban da zaizo masa a rayuwa. Duk da kuwa har yanzu tunaninta na nan akan aljanu suka saka matashi a ciki ta haifa musu. Wataran kuma zasuzo su sace abinsu.     Maman Halima dake tsakar gida tana girki ta leƙo tana tambayar lafiya su Sadiq ke ihu haka?. Cike da murna Abdull yace, “Mama little ya fara tafiya”.      Dariyar itama tayi, tare da shigowa ɗakin sosai ta ɗauka Little tana juyi dashi. Dariya su Sadiq suka sake sakawa. Amma banda Little da kowa ya fahimci miskilancin yaron tunda ya fara wayo. Sam baida yawan fara'a, akan daɗe ba'aga yana dariya ba. Garama idan su Aliyu ke masa wasa zakaji har ƙyalƙyalewa yanayi abunsa. Zinneerah ma catai ita daya rainama ko dariyar yake idan ya ganta dainawa yakeyi.    Duk sanda ta faɗi haka mama kan girgiza kai kawai da faɗin, “ALLAH ya kaimu randa zakiyi hankali dai, harshi Abdul-Mutallaf ɗin miya sani da sai ya zaɓa wanda zaima dariyar? Kawai dai zuciya nason mai ƙyautata mata, keko ko wasa bayimasa kikeba”.       Idan mama ta faɗi hakan Zinneerah bata ƙara cewa komai kuma, dan dai kam da gaskiyar mama. Idan kaga tama yaron wasa sai inba idon Mama a wajen. To kafin hakan ta faru kuwa akan jima musamman daya kasance yanzu itama ta fara makarantar boko a sukul ɗin su Sakina.     Duk da Sakina nashan zubar mata da mutunci ga abokan karatunsu na cewar ai bazawarace ta taɓa aure harda ɗa. Da farko ƴan ajinsu kan ƙaryata ta sukeyi, dan a ganinsu nawa Zinneerah ɗin take da za'ace ta haihu, a yanzunefa suke shekaru sha biyar suna farkon shiga sha shida. Tsabar son ƙara wulaƙanta Zinneerah saita ƙirƙiri dinga gayyatarsu gidansu dan aga little. Wasu ko sunje sun gansa basa yarda, amma yau da gobe sai suka fara amincewa da Sakina ɗin har suna tsokanar Zinneerah.      A farko takansha kuka. Amma zuwa yanzu da take neman watanni kusan biyar a makarantar sai hakan ya bar ɓata mata rai. Tama sake ɗammarar maida hankali akan karatunta kamar yanda a kullum Mama ke jaddada mata ta dage wannan karatun sai ya zame mata ado mai ƙawata tarihinta watarana.      Ba fahimtar Mama takeba kai tsaye akan furucin, dan ita a shirmenta har yanzu Mama batasan yaya aka samu Little ba. Bayan sun gama darerakunsu akan fara tafiyar little ɗin Mama ta fice. Su kuma suka cigaba da hidimarsu a ɗakin kasancewar lahadice yau islamiyya kawai yaran zasuje da yamma.      Ganin Little ya ɓingire ƙasa alamar barci zaiyi yasa Zinneerah ajiye buk ɗin hannunta da take Assignment ta ɗaukesa ta goyashi, dan Mama ma ta shige ciki kanta na ciwo. Fita tai tsakar gida dan ta taya Maman Halima aiki kasancewar yau ranar girkintace.         Maman Sakina kawai ta samu zaune dasu Luba dake wanki a bakin rijiya. Ba wani shiga sabgarta suke a gidanba shiyyasa itama bata matsawa kanta na shiga tasu. Dan wasa-wasa Zinneerah ma akwai miskilanci da tsiwa idan taso. Sai dai yanayin rayuwar data tashi a cikine ya sakata komawa sanyi-sanyi.      Yanzu ɗinma Maman kawai ta gaida taja kujera ta zauna a bakin rijiyar itama inda aka tara wanke-wanke. Cikin neman tsokana Luba ta dubeta taɗan taɓe baki, sai kuma a bazata ta bushe da dariya. Kallonta Aliya tayi, hakama Mamansu. “Luba lafiyarki kuwa da wannan dariya kamar wata mara hankali?”.      Cikin dariyar tace, “Mama bazaki ganeba. Wlhy wannan agolance take bani dariya. Idan ta fita waje samarin anguwarnan suyita wani rawan kai a kanta su sun sami budurwa, shashashun basusan harda surƙumemen ɗa gareta a gidaba. Jiyafa Faisal ɗin gidan Alhaji Zubair bakiga yanda ya nacemin da tambaya akan wacece ita ba? Niko na ce masa bazawarar agolan gidanmuce”.        Dariya suka bushe dashi su duka har Maman. Maman Halima dake kicin ta fito a fusace tana kallon Luba mai zancen. “Haba Luba wane shirmene haka da girmanki. Zinneerah ba ƙanwarki bace amma kike wannan sakarcin?”.      Da kunƙunin rashin tarbiyya Luban tace, “A'a Umma nikam ba ƙanwata bace, dan bamu haɗa komaiba banda agolanci datazo gidanmu cin arziƙi”.        “To sannu mara kunya, yanda kikejin nan gidankune itama haka gidansu ne. Dakike aibantata wajen mutane cewar bazawara kuma agola kina tunanin hakan zai hana wanda ALLAH yasa ya zama mijinta zuwa har gidan nan neman aurenta. Kubar wannan banzan halin dan baida ƙyau, ku matane gidan wani zakuje wataran kuma.......”      A fusace Maman Sakina ta tare zancen. “A'a Maman Halima kinga, miye na wannan dogon alkaba'in bayan gaskiya yarinyar ta faɗa. Daga ni har ke kowa yasan ai ita agolarce a gidan. Kuma bazawara. Luban ai taimakonta takeyi wajan faɗar gaskiya dan kar bayin ALLAH suzo a rufesu a basu budurwa bayan gata harda ƙurmusheshen ɗa a baya”.        Maman halima zata sake magana Maman Sadiq da hayaniyarsu ta sakata fitowa dole tai saurin faɗin, “Yaya dan ALLAH abar maganar dan bata da amfani. K kuma Luba ki kwantar da hankalinki ko baki faɗa musu ba dama idan sunzo ɗin zasu sani ai. Cin arziƙi kuma da tazoyi gidanku naɗan lokacine insha ALLAH ”. Daga haka ta juya ta koma ɗaki idanunta na cika da ƙwallar tausayin ɗiyar tata da babu ranar da zata fito ta koma ga ALLAH Saude da ɗiyanta basu yadda habaici akanta ba a gidan. Sai dai suna musu shirune daga ita har Zinneerah ɗin saboda tana ƙwaɓarta akan karta kulasu komai mai wucewane. Sai dai na yau ya mata zafi har tanajin kamar tasa Zinneerah tabar gidan ko itama ta huta da wannan gorin.        Maganar Maman Sadiq sai gashi tabar baya da hazo. dan dama irin wannan damar Maman Sakina ke jira ta dirje Maman Sadiq ɗin akan haushin zaman Zinneerah da ɗanta a gidan. Aiko ta zauna ta fara zuba tijara har su Luba na iƙirarin dukan Zinneerah wai.      Shiru Zinneerah dai bata kulaba, tamkarma batasan anaiba tanata wanke-wankenta. Sai da cikin suɓutar baki Aliya ta zagi Maman Sadiq ne Zinneerah ta miƙe batare da kowa ya luraba. Sai saukar sautin mari kawai sukaji akan fuskar Aliya a bazata..........✍ *_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 _Na Safiyya Huguma_ *_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖 _Hafsat Rano_ *_★ DALAAL_*💝 _Na Miss xoxo_ *_★ UBAYD MALEEK_*💓 _Na Mamu gee_ *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 _Na Bilyn Abdull_ Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 *_08085405215_* IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   0903 234 5899 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 *_TYPING📲_* *_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_* *Page 14* ____________________ *_INA MATA ƳAN ƘWALISA BA'ABOTA SON GYARA JIKI DA FATA SUYI ƘWANAS TAMKAR WATA ƊAN DAREN SHABIYAR?!_* _Ku marmatso kusa maza na kaiku kantin sauƙi na UMMU DUFAIL gidan sauƙi da biyan buƙatar MATA SARAKAN ado harma da MAZA ƴan ƘWALISA._ *_MATA da yawa kanso su koma Taurari ababen kallo da burgewa ga ma'abota kallo sai dai basusan ina zasu sami sinadarin kankaro wannan ƙyawu da mutuncinba._* _To maza kuzo kusa dan Bilyn Abdull ta lalubo muku kantin sauƙi na Umm Dufail dakeda kaya masu sauƙi da gamsar da maison afani dasu_. *_UMMU DUFAIL nada kayan gyaran jiki masu rahusa da inganci da gamsar da mai saya cikin ƙanƙanin lokaci kamar haka👇🏻😁_* *Customers price list By Ummu Dufail FACE AND BODY* SCRUB=2500(300ml) Face and body mango butter=3k (250ml) Face cream= 1800 Corretor oil/vitamin C oil=2k Fairness skin lotion= 2500 Hot chocolate skin lotion 2500 Serum (for Nuckles )2k Nuckles cream (stubborn)3500 Mix fruits Arabian black =soap 1800 Mix fruit glycerine soap =1900 Beetroot=1900 Coconut, milk,egg..face soap=1200 Lavender mix fruit soap =1800 Body wash =1500 cleanser=1600 Hair spray =700 Hair oil =1500 Hair relaxer =700 Hair butter 1700 Shampoo =1500 Breast=oil 2k powder 2k Strech marks cream= 2k Beetroot pink lips =700 Baby care soap glycerine=1k Baby care butter =1500 Shea butter baby soap =700 Tsumin tula =2200 Tsumin zinariya =1200 Sliming tea =1500 Amarya set =25k Liquid Arabian black soap =1900 Cleansing water =1500 *_Zaku iya bibiyarta domin gani da ido ta Handle ɗinta na istagram da facebook kamar haka_* Ummu Dufail @ Facebook Ummu Dufail @ instagram Phone no: 07067943479. _Ƴammata harma da masu auren karku bari ayi babuku. Dan gyara shine mace a wannan ƙarnin😉👍🏻_. _____________________ *Page 14* ............Tsitt gidan yay na wucin gadi kowa na duban Zinneerah da mamaki. Cikin fushin da basusan ta iyaba ta nuna Aliya idonta na cikowa da ƙwalla. “Ki kama harshenki a duk lokacin da zuciya ke ingizaki wajen kuskuren suɓucewarsa. Zaki iya mani ni baki isheni ko kalloba. Amma idan kikace ƙarancin tarbiyyarki zai cigaba da rufe idanunki wajen raina waɗannan lallai zan maidaki cikin hayyacinki!!”.            A yanda tai maganar babu tsoro ko alama a cikin idanunta ne yay matuƙar saka shakkarta a zuciyar Aliya. Dan haka ta kasa komai sai kallonta da take hannunta riƙe da kuncinta.      A fusace Luba tayo kan Zinneerah, wani wawuyan cakuma tai mata wadda tai sanadin suɓucewar zanin goyon datake goye da little. A take yaron yay baya gaba dayansa. Ita kuma Luba ta cakumi Zinneerah ɗin sukai gaba.     Kusan a tare Maman Sadiq da Maman Halima suka iso wajen daf da Little daya tsage da wani gigitaccen kuka zai kai ƙasa. Cikin amincin ALLAH ya faɗa cikin hannunsu da suka tara a tare.         A can kuwa tsakanin Luba da Zinneerah dambe ne sosai ya harƙume. A tunanin Luba zata iya dukan Zinneerah ne dan tana ganin ta fita girman jiki. Sai gashi Zinneerah ɗin na tumurmusar hancinta a ƙasan sumintin gidan. Ganin irin dukan da Zinneerah kema Luba yasa Aliya da Maman Sakina rufe Zinneerah da duka suma.     Masu iya magana sunce sarkin yawa yafi sarkin ƙarfi, da wannan damar suka sami galaba akan Zinneerah duk da dai ta more sosai itama akan Luba ai. Ganinfa abin zai zama hauka Maman Halima ta sakarma Maman Sadiq Little dake kuka saboda tsoratan da yayi ta nufesu tana ƙoƙarin janye Maman Sakina da Aliya amma ta kasa. Sai faman kaima Zinneerah duka suke suna ɗura mata zagi, har takai Maman Halima ɗinma na samun rabonta.         Ana cikin wannan rikici ALLAH ya kawo sallamar wata baƙuwa mai tsananin kama da Maman Sadiq. Ganin abinda ke faruwa duk da batasan wa suke duka ba ta ajiye jakka itama ta shiga cikin masu rabo. Da ƙyar suka iya yakice Zinneerah a tsakkiyar su Maman Sakina daketa zage-zage tamkar dangin maguzawan farkon ƙarni.        “Innalillahi, mike faruwa kukuwa haka a gidan naku Yaya Hauwa? Maman Halima miya kaiki shiga wannan shirmen?”. Baƙuwar ta faɗa tana duban Maman Sadiq dake jijjiga Little, sai kuma ta maida kan maman halima. Kafin ta dubi Zinneerah data nufi ɗaki abinta kamar bada ita aka gama kicimilliba yanzun.          Cikin baƙin ciki Maman Halima tace, “Sannu da zuwa Maryama. Dolene ta kaini ga hakan ai, taya zasu tararma yarinya haka bayan ta fisu gaskiya. Sam Saude batason a zauna lafiya a gidan nan wlhy Maryama”.       Ganin yanda su Maman Sakina ke ƙara hayayyaƙowa yasa baƙuwa Maryama cewa, “Kunga naga wata sabuwar fitinar ke neman tashi kuma. Maman Luba dan ALLAH kuyi haƙuri haka ya isa. Yaya shige muje, Maman Halima dan ALLAH kema shiga ɗaki kawai”.      Shawarar Maryama Maman Halima da Maman Sadiq sukabi kowa ya shige aka barsu sunata haushi kamar karnuka. Sai da suka shiga ne Maryama taga Zinneerah da ƙyau. Cikin ɗaurewar kai tace, “Wai nikam wa nake gani anan haka Yaya?”.        “Hummm Maryama bar wannan batun zauna ki huta. Sannu da zuwa kinsha hanya. Bansan kina tafeba ai”.         “Tafiyar bata shiri bace ba ai Yaya. Kuma nama nema wayarki amma sam bana samu, shiyyasa kawai nai ƙuru nace bara na biyo ɗin dai kar nai rashin hankali”.       “Tofa, ALLAH yasa badai wani abune ya faruba kuma?”. Mama ta faɗa tana mikama Zinneerah da kanta ke duƙe a ƙasa alamar kuka take little. “Ki tashi ki masa wanka a bashi abinci tunda yayi shiru”.        Sai lokacin Zinneerah ta ɗago tana share hawayenta. Ta amshi little ɗin kafin ta gaida Maryama. Amsa mata tai tana binta da kallo, hakan yasa Zinneerah miƙewa ta shige ɗaki da Little a hannu. Ajiyar zuciya Maryama ta sauke bayan shigewar Zinneerah ɗin, duk maman sadiq dake ƙoƙarin kawo mata ruwa na kallonsu. Sai da ta ajiye ruwanne ta sake maimaita mata tambayar ɗazun.        Maryama tace, “Lafiya ƙalau, sai dai lafiyar mai rauni. Inno ce jikin nata babu daɗi, dan sunce shekaran jiya da daddare kamarma bazata kwana duniya ba”.        “Innalillahi wa'inna ilairraji'un. Yanzu nan har jikin Inno yakai tsanani haka amma baza'a sanarminba Maryama, har ke dake a Minna kiji”.       “Kiyi haƙuri Yaya Hauwa, wlhy ba laifinsu bane. Buba yace tunda ciwonta ya fara motsawa a cikin satin nan suke neman wayarki data Yaya amma basa samunku. Ni kaina Baban su Atiku suka samu tunda kinsan dai ba wani muhimmanci wayata kedashi ba”.         “Eh kuma sun fini gaskiya, dan layin nawane ya samu matsala wlhy, Yaya kuwa bansan yaya akai suka gaza samun nasaba, kokuma matsalar network ne. UBANGIJI ALLAH ya ƙara mata lafiya. Jikine na tsufa sai dai Alhmdllh”.        “Wlhy jiki kam na tsufa. Dama na biyo ne idan babu matsala sai mu wuce Baucin tare mu dubata, to saima ina shirin tahowa danai waya da Buba yake sanarmin ai Hajiya Iya taje garin taga halin da take ciki ta ɗakkota suna anan kano wajenta”.          “Tofa, ita Hajiya Iya ɗin dama suna anan kano ɗin har yanzu?”.      “A'a yaya yakike wannan magana haka. Handa Hajiya Iya da iyalanta sukai ƙarfi a garin nan kina ganin zasu iya barinsa kuwa? Kenan baki cikama Inno alƙawarin da kikai mata na neman inda suke ɗinba?”.          “Humm Maryama bazaki ganeba. Ni wlhy kin ganni nan harka da masu kuɗin nan ba sonta nakeba sam. Bani ƙaunar shiga inda akafi ƙarfina a wulaƙantani”.       “Kai Yaya kenan har kin sani dariya. Aiko kinga Hajiya Iya bata da wannan, mace ce maison zuminci sosai. Danni kinga mun taɓa haɗuwa da ita kusan sau biyu kuma duk banga wani nuna ƙyama daga garetaba. Saima jana da taitayi a jiki tana min faɗa da cewar Baba ya rabamu da dangi bamusan kowaba sai Inno”.          “To kinsan abinne da wuya wlhy Maryama. ALLAH ya ƙaddara bazanje ɗinba sai ta silar zuwan Inno ɗin. Dan yanzu hakama ni nama manta yanda adireshin gidan yake”.        “Wannan mai sauƙine ai Yaya sai a kira Baban su Atiku ya kira Buba muji. Nidai na kasa haƙuri, dan ALLAH wai wacece wannan mai kamanni damu haka? Inaji a raina jininmuce yarinyarnan”.      Murmushi Maman Sadiq tai tana mata harar wasa. “Rashin haƙurinki na nan dai Maryama. to ƴarki ce ta Danya ƙaddarar rayuwa ta kawota nan”.      Da matuƙar mamaki Maryama tace, “Wai Yaya kina nufin Zinneerah?”.      Kai kawai Mama ta gyaɗa mata tana amsa sallanar Maman Halima.       Shigowar Maman Haliman ta saka Maryama yin shiru, Maman Halima ta ajiye mata kular abinci tare da zama suka gaisa cikin mutunta juna da tambayar lafiyar iyalai. ta mike zata fita Maman Sadiq ke sanar mata dalilin zuwan Maryama ɗin.           Jajanta musu Maman Halima tai cike da alhini, tare da addu'ar samun lafiya ga Inno ɗin kakarsu data haifi mahaifiyarsu. Bayan sun mata godiya ta fice. Maman sadiq kuma ta ƙwalama Zinneerah kira.      Koda Zinneerah ta fito sai Maryama dake sharar hawaye ta miƙa mata hannu tana faɗin, “Zonan ɗiyata dan ALLAH, zo naji ɗuminki”.     Babu musu Zinneerah ta nufeta duk da batasan wacece itaɗin ba. Sai dai kamaninta da mahaifiyarta ya tabbatar mata jininta ce. Haɗata tai ita da Little da yasha wanka duk ta rungume kukanta na ƙara ƙarfi. Maman sadiq ta miƙe tana ƴar dariyar ƙarfin hali da faɗin. “Oh halin naki dai bai canzuwa kenan har sai ƴar taki ta ganoki itama. Nikam bara kiga na miƙe, kema idan kin gama kukan kizo kiyi sallar la'asar kiɗan watsa ruwa sai ki zaman cin abincin ƙyafi jin daɗi”.        “Yaya dole nai kuka kodan kunya da takaicin kammu akan yarinyarnan. Zinneerah ki gafarcemu dan ALLAH, munsan bamu ƙyauta mikiba, bamuyi miki adalciba a rayuwa. Dan ALLAH ki mana afuwa”.        Zinneerah bata iya cewa komaiba. Sai murmushi kawai da take famanyi da ƙoƙarin danne nata kukan dake neman kufcewa. Sai da Maman Sadiq data sake fitowa mata maganar tazo tai wankan ne ta lallaɓeta da ƙyar ta share hawayenta da sakin Zinneerah da itama zuwa yanzun hawayen take sharewa. ★★★       Bayan Gwaggo Maryama tayi wanka da salla sukai zaman cin abincin zuminci da ƴar uwarta. Yayinda little kenan tare dasu a falo nata wasansa konace ɓarna. Zinneerah kam tuni ta shige ɗaki dan zazzaɓi nema ke neman rufe mata jiki.       Gwaggo Maryama ƙanwa ce ga Maman Sadiq. Uwarsu ɗaya ubansu ɗaya. Sukaɗai mahaifiyarsu ta haifa a duniya ALLAH yay mata rasuwa, dan haka akwai shaƙuwa mai ƙarfi da ƙaunar juna tsakaninta da ƴar uwartata wadda ƙaddarar aure takai can Minna jihar Niger. A yanzu haka itama ta zuba iyalai acan Alhmdllh.          Kaf labarin Zinneerah da dalilin zuwanta nan wajensu da samuwar Little Maman Sadiq sai da ta zayyanema ƴar uwarta dakeshan kukan tausayin Zinneerah har cikin ranta. Tare da ɗaukar dukan laifi ta ɗora akansu suda sukai wasarere da lamarin Zinneerah ɗin bayan sunsan rashin imani irin na Asabe. Tunda har ta iya rabo Maman Sadiq da mijinta itama Zinneerah ɗin ba barinta zataiba.         Murmushi mama tayi, cikin son kwantarma da ƴar uwarta hankali ta shiga nuna mata komai ƙaddara ne. Tunda UBANGIJI ya hukunta sai Zinneerah tai irin wannan rayuwar babu wani daya isa hana hakan a cikinsu ai. Sai dai su cigaba da mata fatan alkairi kuma a rayiwarta ta gaba. Wannan kam ta rigada ta faru kuma.          “Hakane Yaya Hauwa. Amma wannan tabon bazai taɓa goguwa a zuciyar yarinyarnanba dangane da watsi da mukai da ita bayan duk munsan a inda take”.       “To yadai wuce yanzu dan ALLAH. Muci abinci koma kimtsa kafin Yaya ya shigo gidan muji yanda za'ai tafiya inda Inno take. Dan da san samune mu tafi yau duk da naga garinma dai yana haɗe fuska alamar hadari”.         Da wannan maganar ta Maman Sadiq bakin Gwaggo Maryama yayi shiru. Suka ƙarasa cin abincin da saida ta matsa mata. Daga haka suka zauna zaman hirar zuminci da jiran dawowar Abba gidan.      Kamar yanda su Maman Sadiq ke jiran dawowar Abba iyalan Maman Sakina ma zaman jiran dawowar tasa gidan suke cike da alwashin sai Zinneerah tabar gidan yau ɗin nan. Duk da sun shige ɗaki basubar zage-zage ba da aibanta Maman Sadiq da Maman Halima. Dan ko abincin rana yau sunƙi zuwa su ɗakko na ɗakinsu har yamma tayi yara suka dawo daga makarantar islamiyya.          Tunda su Abdull sukaga Gwaggo Maryama suka rikice da murna sosai. Itama taji daɗin ganinsu. Ta haɗasu a jikinta ta rungume harda Little daketa walwalar ganinsu.         Bayan an idar da Sallar Magriba Sadiq yazo yana sanarma Mama Auntynsu bata da lafiya. Kafin tace wani abu sallamar Abba ta shigo kunnuwansu alamar ya dawo gidan kenan.        Duk da suna a cikin ɗaki ba kuma nan ya shigoba kai tsaye sai da suka amsa. Su Sadiq duk suka fice yima Abban sannu da zuwa kamar yanda suka saba idan ya shigo suna gida.      Wuff Maman Sakina ta fito daga ɗakinta tunda taji sallamar mijin nasu. Kusan a tare suka shiga falonsa da ita da yaran. Sama-sama ta gaidashi, zata fara kumfar baki ya ɗaga mata hannu dan dama tun a yanayin data shigo yasan gidan babu lafiya. Ga kuma Aliyu na faɗa masa Auntynsu bata da lafiya tana ɗaki kwance.       “Salla zanyi, sannan kinsan dokata a gidan nan bana buƙatar yin maganar da duk bata shafi alkairiba a gaban yarana. Dan haka ki koma sai anjima idan na nutsu kizo miyi magana ba yanzu ba”.      Wani irin baƙin cikine ya turnuƙe zuciyar Maman Sakina. Ta fito fuuu kamar zata tashi sama. Da kallo kawai ya iya binta yana mai girgiza kansa.      A ɗaki kuma Gwaggo Maryama ce da kanta ta miƙe zuwa wajen Zinneerah da Sadiq yace bata da lafiya. Ƙudundune ta sameta cikin bargo tana rawar sanyi. Saurin ƙarasawa tai gareta tana faɗin “Subahanalillahi Zinneerah dama baki da lafiya amma kikayi shiru?”.     Kafin Zinneerah ta bata amsa Maman Sadiq ta shigo ɗakin itama. Duban inda take kwancan tayi tana bama Gwaggo Maryama amsar zancenta. “Tunda ta iya cin dambe ba dole tai zazzaɓi ba. Ki tashi kiyi wanka da ruwan zafi kici abinci kisha magani, dan wannan dai zazzaɓin bai wuce sanadin hayaniyar nan ba”.     Cike da takaici Gwaggo Maryama tai tsaki. “Shi dai yaya ya auroma kansa masifa wlhy. Ayi mace bata son zaman lafiya kamar dangin yahudawa”.       “Humm ai kaɗanma kenan Maryama, dan wannan fitinar ba mutuwa taiba rufa tai, na tabbata jiran dawowar maigidan take, bara kuma kiji zakice nina faɗa miki”.       “Fitinanniyar banza. Gashi nan duk tabi ta koyama ƴaƴa hali mara amfani, aini Zinneerah ta birgeni sosai data nuna musu ƙyalesu dama kawai take ba tsoro bane. Shi kuma yayan tunda yasan halinta dama ai kinga sai yay musu iyaka yanzun”.       “To ALLAH yasa. Dan da kike ganinta a haka son matarsa yakeyi”.        Kiran sallar magriba da aka kirane ya katse hirar tasu. Zinneerah kam dama harta shige bayi tuni.        Bayan idar da sallar magriba Gwaggo Maryama ta tsare Zinneerah taci abinci tasha magani sannan ta kwanta. Maman Halima ma ta kawoma Gwaggo Maryama nata abincin yaɗan zauna sukai hira bayan ta shiga ta duba Zinneerah data sanu barci. Kiran sallar isha'i yasata komawa nata sashen.         Alhaji da yara kam basu shigo gidanba sai da aka idar da sallar isha'i. Harda Little da yay barci. Gwaggo Maryama ta amshesa ta goya tana maijin tausayin yaron a ranta.         Sai da Maman Sadiq ta tabbatar Alhaji yaci abinci ya huta sannan suka fita ta raka ƴar uwarta danta gaidashi. Sai da sukai sallama ya amsa shi da Maman Halima dake tare da shi  sannan suka shiga. Sosai fara'ar fuskarsa ta daɗu yanama Gwaggo Maryama lale da zuwa dan dama yara sun sanar masa zuwanta.        Suna kaiwa zaune sai ga Maman Sakina tamkar an jehota falon dan ko sallama basa tunanin tayi. Kallonta Alhaji yayi kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa ya maida hankalinsa ga Gwaggo Maryama. Hakan da yayine ya saka Maman Halima da Maman Sadiq suma yin kamar basusan da shigowar tataba.        “An haɗa kai an shigo dan a ƙulla mana sheri ni da ƴaƴana. To ta ALLAH bata mutumba”.      Babu wanda ya tanka mata. Sai da Alhaji ya gama gaisuwarsa ta zuminci da Gwaggo Maryama sannan ya dubeta fuska a tsuke. “Saude yaushe ne zakisan inda ke miki ciwo ne wai kekam?”.         “Taya kuwa zansan ciwon kaina agola ta haɗani da ƴayana ta doka saboda an gina mata jiki da tuwon gero dana dawa Abban Luba”.       Kallonta kawai yake batare daya tankaba. sanin baya son jan rai a magana ya sata fara zayyane masa abinda ya faru, sai dai tanayi tana haɗowa da ƙarya da sheri. Tsam Gwaggo Maryam ta miƙe zata fice ya dakatar da ita. “Maryam kina gidan duk akai wannan?”.       “A'a gaskiya Yaya kafin nazone. Nadai iske kawai suna rikicin faɗa nashiga na taya Maman Halima rabawa”.       Komai baiceba sai kallonsa daya maida ga Maman Sadiq. “Ina Zinneerah ɗin take?”.      “Tana can kwance babu lafiya”. “A dalilin shi wannan rikicin kenan?”. Ya tambaya yana cigaba da dubanta.     Kafin ta amsa masa Maman Sakina ta karɓe da faɗin, “Andai shirya munafunci kawai za'ace, yo inba munafun........”      “Saude!”. Ya katseta a tsawace. Badan tasoba dole tai shiru. Yaja tsaki da faɗin, “Da safe inason ganinku dukanku har yaran”. Ya faɗa yana miƙewa ya fice.     Ganin haka ya saka su Maman Sadiq miƙewa suma duk suka fito. Sai dai a mamakinsu sai hangarsa sukai ya nufi sashenta da alama duba Zinneerah zaijeyi.      Hakan yama Gwaggo Maryama daɗi sosai, duk da dama tasan halin ɗan uwan nasu baya wasa sam da lamarin gidansa. Amma batai tunanin Zinneerah ta samu matsayi na musamman haka a garesaba.       Bayan ya shiga ya dubata tana barci dan haka ya fito falo. Batare da dubansuba ya nufi hanyar fita yana faɗin, “A tada ita muje ko nan kyamis ɗin Umar ne tunda dare yayi”.      Halinsa da Maman Sadiq ta sani yasa bataja zancenba taje ta tado Zinneerah suka tafi kyamis ɗin. Itako Saude nacan tana tijara a sashenta kamar zata haɗiye haƙoranta, musamman ma dataga Alhajin ya fita tare da Zinneerah da Sadiq. WASHE GARI         Washe gari da safe Zinneerah ta tashi Alhmdllh babu zazzaɓin dan tasha allura jiya. Bayan idar da salla suka zauna zaman hira ita da Gwaggo Maryama dake janta a jiki cikin hikima. Sai da gari yay ɗan haske suna shirin fita gaida Alhaji sai gashima ya shigo duba Zinneerah ɗin. Kanta a ƙasa ta gaidashi. Ya amsa mata da kulawa kamar yanda ya saba da tambayarta kuma jikinta.      “Alhmdllh Abba naji sauki”.. “Haka akeso ai, ALLAH ya ƙara lafiya”.     “Amin” suka amsa gaba ɗaya. Sai da ya koma sashensa da kusan mintuna biyar sai ga Hussaina tazo kiransu. Maman Sadiq tasan Maman Sakina ce zata matsa da fitinar sai an zauna. Dan haka ta mike ita da Zinneerah ɗin suka tafi, aka bar Gwaggo Maryama na ƙarasa aikin da Zinneerah ta fara.        Kowa ya hallara su kaɗai ake jira, dan haka suka sami wajen zama suma su Luba nata harar Zinneerah. Alhaji daya gama nazarin kowa a ƴan sakanni ya basu damar bayani ɗaya bayan ɗaya.     Ya ɗan murmusa yana girgiza kansa. Sai kuma ya haɗe fuska ya balbalesu da bala'i su duka. Kafin ya dawo kan Aliya da Luba da sukaima su Maman Sadiq rashin kunya harda zagi. Ganinfa reshe zai juye da mujiya Maman Sakina ta miƙe da bala'i zata taresa ya daka nata tsawa itama. Cikin jan dogon gargaɗi yace, “Wlhy daga yau ya sakejin makamancin haka akan matansa saiya musu dukan mutuwa a gidan”. Ya kuma sakasu bama su Maman Sadiq haƙuri da ita kanta Zinneerah ɗin. Sannan itama yay mata faɗa akan marin Aliya da tayi tunda yayartace. Yayi hakanne dan kawai kar ace yayi son kai dan yasan dai Zinneerah ta fisu gaskiya. Daga haka ya sallami kowa suka fito Maman Sakina da ƴaƴanta ransu fal baƙin ciki da alwashin hana Zinneerah zaman lafiya a gidan cikin hanya mai sauƙi da Abban bazai gane komaiba.            Maman Sadiq kam ko a jikinta dan bataji komai ga abinda Abban yayiba. Sai ma shirin zuwa inda Inno take suka farayi dan Abban yace su shirya sai ya kaisu da kansa idan zai wuce kasuwa shima ya dubba Innon daga nan. Hakan yasa Maman Sadiq amso wayarsa suka kira mijin Gwaggo Maryama ya turo musu lambar Buba dazai kwatanta musu gidan Hajiya Iya ɗin ko asibitin da Inno ke kwance.............✍ *_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 _Na Safiyya Huguma_ *_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖 _Hafsat Rano_ *_★ DALAAL_*💝 _Na Miss xoxo_ *_★ UBAYD MALEEK_*💓 _Na Mamu gee_ *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 _Na Bilyn Abdull_ Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 *_08085405215_* IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   0903 234 5899 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 *_TYPING📲_* *_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_* *Page 15* ____________________ *_INA MATA ƳAN ƘWALISA BA'ABOTA SON GYARA JIKI DA FATA SUYI ƘWANAS TAMKAR WATA ƊAN DAREN SHABIYAR?!_* _Ku marmatso kusa maza na kaiku kantin sauƙi na UMMU DUFAIL gidan sauƙi da biyan buƙatar MATA SARAKAN ado harma da MAZA ƴan ƘWALISA._ *_MATA da yawa kanso su koma Taurari ababen kallo da burgewa ga ma'abota kallo sai dai basusan ina zasu sami sinadarin kankaro wannan ƙyawu da mutuncinba._* _To maza kuzo kusa dan Bilyn Abdull ta lalubo muku kantin sauƙi na Umm Dufail dakeda kaya masu sauƙi da gamsar da maison afani dasu_. *_UMMU DUFAIL nada kayan gyaran jiki masu rahusa da inganci da gamsar da mai saya cikin ƙanƙanin lokaci kamar haka👇🏻😁_* *Customers price list By Ummu Dufail FACE AND BODY* SCRUB=2500(300ml) Face and body mango butter=3k (250ml) Face cream= 1800 Corretor oil/vitamin C oil=2k Fairness skin lotion= 2500 Hot chocolate skin lotion 2500 Serum (for Nuckles )2k Nuckles cream (stubborn)3500 Mix fruits Arabian black =soap 1800 Mix fruit glycerine soap =1900 Beetroot=1900 Coconut, milk,egg..face soap=1200 Lavender mix fruit soap =1800 Body wash =1500 cleanser=1600 Hair spray =700 Hair oil =1500 Hair relaxer =700 Hair butter 1700 Shampoo =1500 Breast=oil 2k powder 2k Strech marks cream= 2k Beetroot pink lips =700 Baby care soap glycerine=1k Baby care butter =1500 Shea butter baby soap =700 Tsumin tula =2200 Tsumin zinariya =1200 Sliming tea =1500 Amarya set =25k Liquid Arabian black soap =1900 Cleansing water =1500 *_Zaku iya bibiyarta domin gani da ido ta Handle ɗinta na istagram da facebook kamar haka_* Ummu Dufail @ Facebook Ummu Dufail @ instagram Phone no: 07067943479. _Ƴammata harma da masu auren karku bari ayi babuku. Dan gyara shine mace a wannan ƙarnin😉👍🏻_. ___________________ *Page 15* ...........Tunanin basusan mi zasu tarar a inda zasujeba Maman Sadiq ta yanke shawarar barma Zinneerah little a gida tunda yau bazataje Islamiyya ba, Alhaji yace saita warke. Su Abdul kam duk sun wuce makaranta dama. Sai da Mama ta jama Zinneerah dogon gargaɗi akan su Maman sakina sannan sukai mata sallama suka tafi. A tsakar gidanma sallama sukaima Maman Halima harma da Maman Sakinar duk da ba kulasu tai da ƙyau ba.       Sai da Alhaji ya ɗauka hanyar barin anguwar tasu sannan ya kira wayar buba dazai musu kwatancen asibitin da Inno ke kwance a yanzu haka. Bayan sun gama wayarne ya ɗan duba Maman Sadiq dake a gefensa yana ajiye wayar. “To ashema asibitin da aka kwantar da ƴata Innon take”.           Batare da kawo komai a raiba Maman Sadiq tai murmushi da bashi amsa, “Oh to abin yazo da sauƙi Alhmdllh. Dama inata tunanin karmu baka wahala musaka makarar zuwa kasuwa”.       “Kenan saboda Inno takuce ku kaɗai?”.      Yanda yay maganar cikin raha ya sakasu suma fara dariya suna faɗin, “A'a Yaya harda kai ai mana afuwa”.        Sun iso *_SHIRA HOSPITAL_*. Alhaji ya kira Buba ya fito ya shiga dasu har ɗakin da aka kwantar da Inno ɗin. Wajene na musamman a cikin asibitin da iyalan family ɗin Shira ne kawai keda hurumin shigarsa koyin jiyya a wajen idan hakan ta kama. Wajen tsitt yake sosai babu wata hayaniyar komai. Gashi a gare tsaf duk da kuwa sun tadda mutane kusan shidda tare da Inno ɗin.      Ɗakin da take ɗakine babba da komai na kulawar marasa lafiya wanda ko ƙasar ka bari iya abinda zaka iya zuwa ka tarar kenan acan ɗinma.        Inno ta tsufa sosai, sai dai ba irin tsufan nan da za'ace ta fita hayyacintaba. Dan tana gani ras tana kuma magana. Matsalarta kawai ciwon ƙafa dake damunta kasancewar ta mace mai jiki a da can. A yanzu hakanma bawai ramammiya baceba.         Tunda sukai sallama a ɗakin kusan duk waɗanda ke a ciki suka zubo musu idanu suna mai amsa musu sallamar tasu. Tsohuwa mai ɗan yanayin kamanni da Inno, sai dai bata kaita tsufaba, sannan alamar jin daɗi fiye dana Inno ɗin ya bayyana a gareta ta tsaresu da idanu tamkar maison gano wani abu.     Ganin duk sun tsargu da kallon da take musunne ya sata sakin murmushi da faɗin, “Wannan dai kamar Maryama idan idanun nawa na gani da ƙyau?”.      Murmushi Gwaggo Maryama tayi a karo na farko, dan sai yanzune ta gane Hajiya Iya. Cike da girmamawa tace, “Nice Gwaggo. Tare da Yaya Hauwa da mijinta”.            “Eh to naganki dai ke da na sani, sai kuma mijin nata zan masa na baƙunta, amma ita kam idona bai gantaba tunda itama nasan bason ganin nawa takeba kamar yanda bana tunanin tama sanni. Mutuniyar da aka sanarmin an bata adireshin inda nake a garin nan kusan shekara huɗu kenan amma bata nemeniba sai yau dalilin zuwan Inno, ai nikam banace nama santaba tunda dama canɗin ba sanin nata nayiba”.         Sanin halin Hajiya Iya ya saka sauran mutanen ɗakin kowa yin murmushi harda Alhaji da Gwaggo Maryama. Maman Sadiq ma kanta a ƙasa take murmushin. Inda Hajiya Iya ke zaune kusa da Inno ta ƙara ta durƙusa akan gwiwoyinta tana faɗin, “A gafarceni Gwaggo. Nasan ni mai laifice amma dan ALLAH ina mai neman afuwarki”.        “To zanɗan haƙura kaɗan idan mijinki ya sanarmin bashi da laifi wajen hanaki neman inda nake. Shi zuminci ai daɗine dashi koda na zaman anguwane balle ace na ɗan uwanka na jini. Uwa ɗaya uba ɗaya fa mahaifiyata suke da Inno, hasalima itace ta riƙe mahaifiyar tawa harta aurar da ita, dan itace ƴar zaman ɗakinta. Da hannunta ta raini mahaifiyarku har tsahon shekara huɗu kafin a aurar da ita. Amma ace yau ƴaƴan Hafsat na gudunmu saboda mahaifinku ya nisantamu daku a dalilin Hafsat bata raye a duniya”.     Yanda ta ƙare maganar tana sharar hawaye ya saka ɗakin yin tsitt, itama Maman Sadiq sai hawayen suka shiga silalo mata saboda tinawa da mahifiyarsu da ALLAH yayma rasuwa tun suna yara.       “Kiyi haƙuri Gwaggo munyi kuskure. amma insha ALLAH zamu gyara, na tabbatar miki zamu gyara”. Alhaji ya faɗa cike da girmamawa.      Gyalenta tasa ta sake share hawayen nata, sai kuma ta kalli Alhajin tana murmushi. “Shike nan ɗana ALLAH ya tabbatar da hakan. Tunda harkun gane kunyi kuskure na haƙura. Amma dan ALLAH ku gyara dan shi zuminci babban abune mai girma da ta silarsama za'a iya zuwa aljanna. Mu daina biyema sharrin sheɗan dana zamani zukatanmu nayin nisa da juna. Ina daɗi ace ƴaƴan Hafsat basusan inda nakeba saboda iyayenmu basa raye. Wajen gwaggo kawai kuke zuwa”.         “Tabbas ba'a ƙyautaba Gwaggo. Amma dan ALLAH ayi haƙuri. Kamar yanda ya faɗa insha ALLAH zamu gyara. Wlhy zuwanma da kikaga banyiba nima rasa takardar da aka rubutamin adireshin da lambar wayar nayi. ALLAH kuma bai ƙaddara duk sanda na shigo bauchi na sake amsar wani adireshin ba a wajen Buba”.         Hannu Hajiya Iya tasa ta kamo na Mman sadiq mai maganar, sai kuma ta kamo na Gwaggo Maryama duk ta haɗa cikin nata tana murmushi. “Ya wuce insha ALLAH, nima namuku hakane danku ƙara sanin muhimmancin zuminci, mu kuma sake dunƙulewa tsintsiya naɗaurinki ɗaya. ALLAH yayi muku albarka kuda zuri'arku damu baki ɗaya”.      Cikin jin daɗi su mmn Sadiq suka amsa mata. Daga haka aka koma gaishe-gaishe kamar ba yanzu Hajiya Iya ta gama sharar ƙwalla ba.      Sai da aka gama gaishe-gaishe da tambayar jikin Inno daketa kallonsu kawai dan ko magana bata iyayi amma tana jinsu. Hajiya Iya ta koma nuna musu sauran jama'ar ɗakin.        “To ga ƴan uwanku nan nasan duk baku sansuba. Waɗan nan biyun matan yayanku ne. Waɗan nan kuma ƴaƴanku ne dukansu gasu nan. Badai zaku gane lissafinba anan sai munje gida”.        Su mmn Sadiq dai murmushi sukeyi cike dajin ƙaunar ƴar tsohuwar, suka sake gaisawa da waɗanda ta nuna musun. Yanda suma babu alamun wulaƙanci a garesu yasaka jin farin ciki a zukatansu Mmn sadiq ɗin.     Hajiya Iya ta nuna su mmn sadiq kuma garesu suma tana faɗin, “Ku kuma waɗannan ƙannenku za'ace kenan ko. Dan ƴaƴan Yaya Hafsat ne da ALLAH yayma rasuwa babbar ƴar Gwaggo da aure ya kai can Katsina, nasan dai bazaku gaza jin sunantaba a hirata ma. mahaifinsu ne bai barsu sakewa a cikinmuba tun suna kananu shiyyasa baku sansuba basu sankuba kuma. Amma insha ALLAH daga yau kowama zai sansu ɗin”.      Duk suma amsa mata sukai da girmamawa dan babu mai jayayya da ita a kaf family ɗin harsu matan ƴaƴan nata. Sallama Alhaji yay musu ya tafi saboda ganin lokaci zai ƙure masa na kasuwa. ya wuce akan zai dawo anjima ya ɗaukesu idan ya taso.       Sosai su Mmn Sadiq suka tsinci kansu cikin farin cikin kasancewa da dangin mahaifiyar tasu da suka gaza samun kusanta a lokacin ƙuruciya yanda ya kamata. Dan mahaifinsu baison kaisu su sake a cikinsu gudun karsu ƙwace masa su. Sukan dai je suga Inno naƴan kwanaki su dawo. Hakan yasa ko lokacin aurensu dangin mahaifiyarsu ba kowa yazoba dan haushin babansu. Su kuma bayan duk sunyi aure rashin sabon tun farko ya hanasu sakewa dasu, dan Inno kawai suka sani da wasu tsuraru a ciki.         Babban abinda ya basu mamaki bai wuce yanda zuri'ar Hajiya Iya ke tururuwar zuwa asibitin duba jikin Inno ba. Saika rantse Hajiya Iya ɗince kwance ke jiyya. duk wanda yazo kuma saita masa bayaninsu suma sai ta musu bayaninsa. Alhmdllh kuma basuga raini ko wulaƙanci ga kowaba dukda kuwa sun shaida akwai kuɗi a wannan zuri'a kodan manya-manyan kulolin abincin da ake shigowa dasu na dubiya.      Har dare suna a asibitin Inno bata wani san da zuwansuba saboda zafin ciwo, sai dai binsu da take da ido da kuma surarensu. Gashi kuma ɗiyar ƴar uwarta nata kaf-kaf da abunta gwanin sha'awa.        Rigimar Hajiya Iya bata basu mamakiba sai da Alhaji ya dawo ɗaukarsu bayan ya taso kasuwa. Ta tubure akan babu inda zasuje gidanta zata wuce dasu su kwana dan asibitin Nurses ke kwana da Inno. Ana cikin wannan kicimilli babban ɗan Hajiya Iyan ya iso asibitin. Dawowarsa kenan daga tafiya ko gida bai shigaba ya wuto nan dan duba Gwaggo mahaifiyar tashi, shi kuma kakarsa.        Tunda yay sallama cikin ɗakin Alhaji yay suman zaune. Akan laɓɓansa ya ambaci *_“Alhaji Kabir Abdul-Mutallab Shira_* babbar magana”.      Alhaji Kabir Shira da baisan da zancen zucin Alhaji ba ya ƙarasa gaban mahaifiyarsa duk da shekarunsa na girma ya kai har ƙasa duƙe yana gaisheta da tambayar mai jiki.       Amsa masa take da kulawa tare da tambayarsa yaya hanya?.       “Alhamdulillahi innata. Ina fatan ana samun cigaban sauƙi a jikin Inno ɗin?. Dan tunda kika sanarmin halin da kuka sameta jiya da ƙyar nai barci. Inagama zuwa Laraba insha ALLAH kawai za'a wuce da ita India”.       Cike dajin daɗi Hajiya iya ke jinjina kanta. “Wannan tunanin shine dai-dai Babangida. ALLAH yay maka albarka. jikin kam Alhmdllh dan bakamar jiya da muka baro Bauchi da ita ba. Amma dai nima nafi yarda da maganar zuwa india ɗinma a duba wannan ƙafar tata da ƙyau”.        “Karki damu Innata, insha ALLAHU harma nayi magana da Bashir zai fara shirye-shiyen tafiyar daga daren yau ɗin nan”.      Sai da ta jero masa addu'a sosai, sannan ta nuna masa su maman Sadiq dake gaisheshi. Bayan ya gama amsa gaisuwar yaransa da suma ke cike da ɗakin mazansu da matansu. Dan dolene kazo duba Inno saboda muhimmancinta ga Hajiya Iya.        Da kulawa ya amsa musu yana sauraren bayanin mahaifiyar tasa. bayan ta gama ya miƙe tsaye yana bama Alhaji hannu da faɗin, “Lallai yau ina cike da farin ciki gani ga ƙannena da ban saniba suma basu sanniba kuma. Idonku kenan a gabanmu?”.        Cike dajin kunya da mamakin sauƙin kansa tamkar mahaifiyarsa suka shiga bashi amsa. shiko kasancewarsa mutum ɗan boko kansa tsaye yake masu magana har Alhajin dake mamaki da al'ajabin dama Alhaji Kabir Shiran haka yake da sauƙin kai ashe? Bazaka taɓa cewa shahararren ɗan kasuwar nan bane mai faɗa aji a cikin kano da wajenta a gabansu haka ba. Dan ya saki jiki dasu sosai babu wani alamun girman kai ko raini duk da ya gansu talakawa kuma yaune ya fara sanin nasu.       Sai da suka fito zasu tafi ne dan itama ashe isowarsa take jira su tafi gida tare yakejin zancen cewar ta hana su maman sadiq bin alhaji gida.      Murmushi yayi mai ƙayatarwa yana duban mahaifiyar tasa da jinjina rigimarta dason zuminci.        “Innata ai ba'ayi hakaba. Nasan dai ƙannena bazasu rasa yara a gidaba. Dan haka kiyi haƙuri suje yau ɗaya su shiryo kamar zaifi”.         “Uhm-uhm Babangida banyardaba. Salon suje suƙi dawowa tunda dama gudunmu sukeyi”.       “A'a Inna baza'ayi hakaba insha ALLAH”. Mmn Sadiq ta faɗa da sauri.      Sudai sauran jikokinta da suke asibitin dariya suketa kwasa a gefe sanin halin kakar tasu. Itafa indai akan zumincine bata da wasa. Shiyyasa su kansu suka tashi da wanan trianing ɗin nata kansu ke a haɗe bakajin wani fitina sai wadda ke a ɓoye dan ba'a rasataba musamman a tsakanin iyayensu mata.      Da ƙyar dai Alhaji Kabir ya lallaɓa Hajiya Iya ta yarda akan su mmn sadiq su taho da shirinsu gobe idan ALLAH ya kaimu. Daga haka Alhaji Kabir ya buɗe mata motar da aka kawosa da kansa ta shiga, shima ƴaƴansu suka buɗe masa yana ma su Alhaji sallama da jaddada ma su mmn sadiq su taho da ƙatuwar jakka dan sai Iya tasha ziyararsu ta more zasu koma gidajensu.        d sukai masa dajin daɗin wannan karamci da suka samu daga manyan mutane da ada basu taɓa tunanin ganiba ido da ido sai gashi sun kasance jininsune ma ashe. _______★★          Sai da suka ɗauki hanyar gida ne cikin mamakin daya kasa sakin Abba har yanzun yace, “Nifa kaina a ɗaure yake har yanzu Hauwa'u. Wai dama kunsan familyn Alhaji Kabir Abdul-Mutallab Shira sune ƴan uwanku ɗinnan da kika taɓa bani labari?”.         Saurin kallonsa Mmn sadiq tai da mamaki itama tace, “Kabir Shira kuma yaya? Muko a ina zamu san Shira? Bashi baneba”.        Ƙaramar dariya yayi saboda fahimtar itama dai da gaske batasan hakanba, ya kalli Maryama ta mirror “Maryama kema baki saniba kenan?”.      “Wlhy Yaya ban saniba. Nadai san Gwaggo Aminan na anan cikin kano da iyalanta, kuma sunda arziƙi suma, sai dai bansan sune ake kira Shira ba koda wasa”.        “Ikon ALLAH kenan. To aiko waɗanan dai sune Shira Family da ake faɗa a cikin kano da wajenta. Kuma kenan wanda yayma Abdull-Mutallab alkairi har yaci sunansa shima jininsu ne. Wata hikima sai UBANGIJI kenan”.       “Gaskiya kam Yaya. Dan wannan UBANGIJI ne kawai mai kusanta abinda suka kasance makusanta batare da su kansu sun saniba. Amma wlhy ni harma na tsorata. Sai dai sun bani mamaki yanda sukasan darajar mutane”.        “Ai babu wani abin tsoro Hauwa'u, sanin darajar mutane kam tarbiyyarsuce hakan daga mahaifiyarsu. ALLAH ya ƙara mana zuminci da sanin darajarsa”.     Sun amsa da “Amin ya rabbi” dai-dai suna isowa gida. Bayan Alhaji yayi fakin a inda yake ajiye motarsa anan ƙofar gidan duk suka fito suka shiga dan ba'akai ga rufe gidanba da alama su ake jira.     Ilai kuwa a tsakar gida suka iske Maman Halima zaune baiwar ALLAH. Ta tarbesu da sannu da zuwa tare da tambayar mai jikin?. Saida suka tsaya wajenta suma suka gaisa da sakejin lafiyar gidan sannan suka shige dan duk a gajiye suke.      Yaran duk sunyi barci kamar yanda Maman Halima dama ta sanar musu. Sai Little ne kawai kecan wajenta shima bayan tafiyar tasu zazzaɓi ya rufesa ashe. Itama dai Zinneerah wuni tayi kwance sai yamma zazzaɓin ya saketa harta ɗan fita tsakar gida ta zauna dan Maman Sakina da yaranta basu yini a gidanba.       Wanka kawai sukai suka nema makwanci tunda a ƙoshe suke.         Washe gari tunda safe Alhaji ya samu kira daga Alhaji Kabir Shira daya amsa lambar hannun Buba. Da farkoma bai gane mai maganaba sai da yay masa bayani. Cikin ɗan rikicewa Abban ya shiga gaishesa dan zai iya girmarsa ma ko'a shekaru. Sai kuma yanda yaji muryarsa ya sake rikitashi.       Daga can Alhaji Kabir ya sanarma Abba ALLAH yayma Inno rasuwa tun asubahin yau, yanzu haka ga gawarta zasu ɗauka zuwa can gidan, sai suyi ƙoƙari suzo ayi jana'izarta dasu.       “Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un” Abba keta faman ambata dukkan gaɓɓansa na saki lokaci guda. Da ƙyar ya iya fitowa zuwa sashen Mmn Sadiq ɗin yace musu su shirya zasuje asibiti. Sosai hakan ya basu mamaki, sai dai ganin bai basu fuskar da zasu tambaya ba ya sakasu yin shiru gabansu na faɗuwa. Dan sunaji a jikinsu lallai babu lafiya.      Yau ɗinma dai haka suka shirya suka tafi su biyu kawai ko little ba'aje da shiba sabboda baijin daɗi. Zinneerah dai gara ita da sauƙi jikinta ba kamar jiyaba.     Kasancewar gidan Alhaji Kabir Abdul-Mutallab Shira ba ɓoyayye bane a birnin na kano kai tsaye Abba ya nufi can dasu bayan ya kira Buba kawai ya tambayi anguwar.      Gidane katafare sosai, duk da kuwa gidajen anguwar ma babu ƙaramin gida. Kasancewar Buba ya fito gate ya saka suka samu damar shiga babu wani gargada dan mutane basu kai ga fara isowaba. Ruɗanin mutuwar da suka samu ya hanasu damuwa ko tsayawa duban yaya gidan yake, balle tsarinsa.       Kukan Hajiya Iya ya matuƙar sake tada hankalin kowa dake a gidan matuƙa. Su Mmn Sadiq kam ai ba'a magana dan suna tsananin so da ƙaunar kakar tasu, musamman daya kasance ita suka tashi suke gani tamkar mahaifiya a garesu tunda sun rasa tasu tun basusan kansuba.        Cikin ƙanƙanin lokaci gidan ya cika da ƴan uwa da abokan arziƙi, dan ba'a binne Inno ba sai da tawagar ƴan bauchi ta iso. Inno uwace kuma kaka da wannan family bazasu taɓa mantawa da alkairan data ginasu a kaiba. To yau dai gashi ta tafi ta barsu da kewa da kuma alkairin data bari baya garesu. Dama ita kaɗai ta rage musu cikin iyaye. To ya rage nasu subi bayan nata da addu'a batare da gazawa ko ƙosawaba.      (Ya rabbi kasa mu kasance cikin bayinka masu barinma bayanmu tarin alkairi ba sharriba. ALLAH yasa ranar barinmu duniya ta zama ranar farin ciki a garemu😭🙏🏻, ALLAH ka gafartama iyayenmu da bayin ALLAHn da suka rigamu tafiya badan sunyi gaggawaba🙏🏻😭).     A ranar dai dole su Maman Sadiq anan gidan suka kwana. Yanda manyan mutane keta shigowa gaisuwa sai kasha mamaki da tabbatar da lallai Inno nada matuƙar daraja ga Hajiya Iya. Dan dukkan ahalinta suna ɗaukartane kakarsune uwa ga Hajaiya Iya, hakan yasa dukan harkokinsu suka tsaya cak harna tsahon kwanaki uku da aka amshi gaisuwa. Sai a ranar cikon ta huɗu ne ƴan Bauchi da suka rage suka koma gida, hakama sauran dangi dake wasu garuruwa kowa ya kama gabansa.     Suma su mmn sadiq shirin komawa gidan sukeyi yau dan harma sunyi waya da Abba akan zuwa anjima zaizo ya ɗaukesu insha ALLAH. Shima dai kwanakin nan uku kullum sai yazo gidan wajen amsar gaisuwa, hakama mijin Gwaggo Maryama yazo harda ƴaƴanta biyu maza duk da ƙananune, amma a ranar suka koma.       Da ƙyar Hajiya Iya ta aminta da komawar tasu, sai dai ta musu dogon sharaɗi da gargaɗin wannan karon bazata yarda da sakaci da zuminciba. dan su kaɗaine jinin inno mafi kusanci da suka rage a yanzu. Dama Inno bata wani haihu da yawaba. Yaranta biyune kacal a duniya, mahaifiyarsu sai mahaifin Buba. Kuma duk ALLAH yay musu rasuwa, shima Buba shi kaɗaine namiji a wajen mahaifinsa sai ƙannensa mata biyu duk sunyi aure anan Bauchi. Suma kuma sai da Hajiya Iya taja musu dogon gargaɗin kafin su wuce da safe. Sai su kuma su Mmn Sadiq ɗin da suka kasance suma su biyu kawai.      Sun mata alƙawarin kulawa insha ALLAH a wannan karon. Da wannan yasa ta amince su koma gida ɗin dan Gwaggo Maryama ma da anyi bakwai zata wuce duk da ba taro zasuyiba, amma tace zata sake dawowa nan gidan taima Hajiya Iya sallama.      Sai kusan biyar na yamma Abba ya iso tare da su Sadiq da Mama batasan dasu zaizo ba. Amma hakan da yay ya sakata jin daɗi matuƙa kamar yanda Hajiya Iya ma ta nuna jin daɗinta sosai.      Har ƙasa su Zinneerah suka kai suna gaisheta da mata gaisuwa. Cikin jin daɗi ta kamo hannun Zinneerah ta zaunar kusa da ita tare da Aliyu. Suma su Sadiq tace su matso gareta.       “Ikon ALLAH, nan ai Inno ce kamar an tsaga kara an karya”. Hajiya Iya tai maganar tana nuna Zinneerah da kanta ke a ƙasa.      Sauran dake ɗakin suma suka shiga faɗin albarkacin bakinsu akan tsananin kamanni da Zinneerah ɗin keyi da marigayiya Inno. Dan duk wanda yasan Inno yaga Zinneerah yasan jinintace. Gashima ita Zinneerah ɗin ba saninta tayiba.      Hajiya Iya ta ƙara damƙe hannun Zinneerah dake cikin nata tana faɗin, “Lallai akwaiki da karambani, duk iyayenki damu kakanni kika tsallake sai kammanin Inno kika kwaso. Inno ta tafi ta barni ga ALLAH ya sake bani Inno a kusa dani dan na ƙwace”.       Kusan kowa dake falon sai da murmushi ya suɓuce masa. Yayinda kuma duk suka fahimci Hajiya Iya na nufin zata amshe Zinneerah kenan ta dawo hannunta. Hakan yasaka gaban Mmn Sadiq faɗuwa, amma sai ta dake dan ba wajen da zata iya jayayya bane balle musu............✍ 🤣😂Tofa, yau naga ƙarfin hali wajen wagga tsohuwa.      *_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 _Na Safiyya Huguma_ *_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖 _Hafsat Rano_ *_★ DALAAL_*💝 _Na Miss xoxo_ *_★ UBAYD MALEEK_*💓 _Na Mamu gee_ *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 _Na Bilyn Abdull_ Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 *_08085405215_* IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   0903 234 5899 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 *_TYPING📲_* *_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_* *Page 16* ____________________ *_INA MATA ƳAN ƘWALISA BA'ABOTA SON GYARA JIKI DA FATA SUYI ƘWANAS TAMKAR WATA ƊAN DAREN SHABIYAR?!_* _Ku marmatso kusa maza na kaiku kantin sauƙi na UMMU DUFAIL gidan sauƙi da biyan buƙatar MATA SARAKAN ado harma da MAZA ƴan ƘWALISA._ *_MATA da yawa kanso su koma Taurari ababen kallo da burgewa ga ma'abota kallo sai dai basusan ina zasu sami sinadarin kankaro wannan ƙyawu da mutuncinba._* _To maza kuzo kusa dan Bilyn Abdull ta lalubo muku kantin sauƙi na Umm Dufail dakeda kaya masu sauƙi da gamsar da maison afani dasu_. *_UMMU DUFAIL nada kayan gyaran jiki masu rahusa da inganci da gamsar da mai saya cikin ƙanƙanin lokaci kamar haka👇🏻😁_* *Customers price list By Ummu Dufail FACE AND BODY* SCRUB=2500(300ml) Face and body mango butter=3k (250ml) Face cream= 1800 Corretor oil/vitamin C oil=2k Fairness skin lotion= 2500 Hot chocolate skin lotion 2500 Serum (for Nuckles )2k Nuckles cream (stubborn)3500 Mix fruits Arabian black =soap 1800 Mix fruit glycerine soap =1900 Beetroot=1900 Coconut, milk,egg..face soap=1200 Lavender mix fruit soap =1800 Body wash =1500 cleanser=1600 Hair spray =700 Hair oil =1500 Hair relaxer =700 Hair butter 1700 Shampoo =1500 Breast=oil 2k powder 2k Strech marks cream= 2k Beetroot pink lips =700 Baby care soap glycerine=1k Baby care butter =1500 Shea butter baby soap =700 Tsumin tula =2200 Tsumin zinariya =1200 Sliming tea =1500 Amarya set =25k Liquid Arabian black soap =1900 Cleansing water =1500 *_Zaku iya bibiyarta domin gani da ido ta Handle ɗinta na istagram da facebook kamar haka_* Ummu Dufail @ Facebook Ummu Dufail @ instagram Phone no: 07067943479. _Ƴammata harma da masu auren karku bari ayi babuku. Dan gyara shine mace a wannan ƙarnin😉👍🏻_. ______________________ *Page 16* ............Kamar da wasa sai ga ƙaramar magana ta zama babba. Dan kuwa dai Hajiya Iya da gaske take akan amshe Zinneerah daga hannun su Mama. Dan take a wajen ta ɗaga waya tai kiran Alhaji Kabir da dukkan ahalin gidan ke kira da suna Baffah.      A rayuwa Alhaji Kabir bai haɗa uzirin mahaifiyarsa dana kowaba. Kai bama shi kaɗaiba har sauran ƴan uwansa da jikokin familyn babu mai sakaci da buƙatar Hajiya Iya. Dan ita ko wasan jika da kaka sai taso takeyinsa.     A cikin ƙanƙanin lokaci sai gashi a sashen nata. Hannu ya bama Abba suka gaisa yana faɗin, “Ai bansan ka shigo gidanba Alhaji Isma'il, dana fito mun gaisa”.        Abba yace, “Wlhy yanzuma na shigo Yayanmu, nazo wucewa da ƙannenka ne, sai kuma ƴayanka dana kawo suma suyi gaisuwa su kuma gaida Gwaggo”.        “Kai kai masha ALLAHU, lallai yau ka farantamin sosai sosai. Kuzo-kuzo ƴaƴan albarka ga babanku da baku saniba ko”.      A nutse su Sadiq duk suka nufesa harda Zinneerah. Sai dai ita ta durƙusane daga gefensa kaɗan. Saɓanin su Abdul daya jawo jikinsa ya rungime. Sai da su Sadiq suka gama haishesa ya amsa da kulawa da tambayarsu sunyaensu da ajinsu nawa a makaranta kafin ya maida dubansa ga Zinneerah itama.      “Ikon ALLAH, Inna wannan ai saikace Inno ta haifeta dan kamanninsu. Ɗiyata yaya sunanki?”.        Zinneerah da kanta ke duƙe tana wasa da yatsun hannuna tace, “Zinneerah”. “Masha ALLAHU suna mai daɗi kamar yanda kike ƙyaƙyƙyawa ɗiyata. ALLAH yay muku albarka. Ke ajinki nawa a makarantan?”.      A take murmushi ya subucema Zinneerah tace, “Abba ss1”.       “Kai-kai, kice Maman nawa bata wasa bace ƴar boko ce”.       Barkwancin nasa ya saka dariya suɓucema Zinneerah. Yayinda hakan kuma ya sake saka ƙaunarta a zuciyar Alhaji Kabir dan nutsuwar yaran da tarbiyyarsu ya matuƙar birgesa, musamman Zinneerah ɗin da take mace.     Kallonsa ya maida gasu Mmn Sadiq yana fadin, “You see. Gashi kun fara tara zuri'a amma basusan kowaba suma. Sai dai ko a hanya naci karo da Zinneerah ai nasan jini nace. Idan akaimin gaddama kuma har kotu zan kai dole a bani abata”.       Sosai maganar tasa ta saka kowa dariya. Hajiya Iya tace, “Aini kiranma danai maka kenan. Dan nikam dai babu mai rabani da mai kama da Inno tazo gida kenan”.       “Ina bayanki Innata. Dan haka Alhaji Isma'il dan ALLAH a taimakemu badan halinmuba a bamu Zinneerah, bamason a kalli hakan kuma fin ƙarfi roƙo muke gwiwoyinmu a ƙasa. Ƙila hakan ya zama sanadin gyaruwar zumincin dake neman kufce mana. Amma kuje dai kuyi shawara. Idan kuma akwai matsala dan ALLAH karkuji kunya ku sanar mana kanku tsaye zamu fahimceku insha ALLAH. Kunga ko ba'a bamuba sai take zuwa mana hutu ita da sauran ƴan uwanta lokaci-lokaci”.         Cike da jin kunyar wannan roƙo nasa Abba yace, “Ai kunfi ƙarfin hakan a garemu”. Yay maganar yana duban Mmn Sadiq data duƙar da kai.        Daga Hajiya Iya har Alhaji Kabir suma idonsu na kanta. Dan haka Alhaji Kabir yay saurin fadin. “To Alhmdllh, yanzu dai kuje kuyi shawaran nan da kwana uku sai muji yaya ake ciki kamar zaifi”.       Sam Hajiya Iya bataso jin hakan daga bakin ɗan nata ba, dan sotai take yanke su tafi su barta da Zinneerah, saboda wata irin ƙaunar yarinyarce ta musamman ta shigeta lokaci guda. Amma sai tai shiru dan itama taga cancantar barinsu suje su shawarta ɗin. Amma kuma komai zasuyi tasa a ranta sai Zinneerah ta dawo hannunta da zama dan yarinyar ba karamin shiga mata rai tayiba lokaci guda. shi kansa Alhaji Kabir wani irin kaunar yarinyar yaji a ransa batare da yasan dalilin hakanba.       Alkairi mai tsoka Alhaji Kabir yayma su Aliyu. kamar yadda aka koyar dasu tarbiyyar godiya haka suka shiga masa godiya da addu'ar fatan alkairi a rayuwa. Sosai hakan yay masa daɗi har cikin rai. Ya kuma kara jin girma da darajar su mmn sadiq sosai. Dan a wannan zamanin bama yaro tarbiyya shine mai matuƙar wahala ga iyaye aynun. ★★★★        Tunda suka baro gidan babu wanda ya iya yin magana, sai da suna gab da shiga anguwarsune ma Gwaggo Maryama tai ƙarfin halin tambayarsu ina suka baro little kuma?.       “Gwaggo ai baida lafiya an kwantar dasu a asibiti shida Umma”. Abdull ya bata amsa da damuwa a fuskarsa.       Saurin juyowa Mmn Sadiq tai ta kalli yaron, kamar zatai magana sai kuma tai shiru ta maida kanta. Fahimtar hakan da Abba yayi ya sakashi faɗin, “Ban faɗa muku bane dan banason raba muku hankali biyu, amma jikin nasama Alhmdllh dan yanzu haka sun koma gida ta kirani cewar an sallamesu ga Naziru yaje zai maidasu gida. Bakomai ke damunsaba kuma sai zazzaɓin haƙora”.      Addu'ar samun ingattacciyar lafiya sukai masa ita da Gwaggo Maryama. Daga haka suka ƙarasa gidan.         Sai da sukayi sallar magriba suka huta Maman Halima ta shigo gaishesu ɗauke da Little daya rame sosai saboda yasha jiki. danma ALLAH yayisa mai kwaramniya ga karfin hali da akasan duk yaro da shi.     Ƙiri-ƙiri sai gashi yana musu ƙyuya. Yaƙi yarda da kowa sai Zinneerah da kunya ta rufe kamar ƙasa ta tsage ta shige. Badan tasoba dole ta amshesa. Aiko ya wani lafe a jikinta yana kallon su Gwaggo Maryama dake jan kafarsa cikin tsokana tana fadin, “Aiko yaro nama fasa auren. Na maka saki goma sha biyu ni da kai baram-baram”.      Dariya Mman halima tai tana tare masa. Ana cikin haka Maman Sakina ta shigo da yaranta wai zatai musu gaisuwa. duk da bataje can gidanba sai mmn sadiq bata nuna mata komaiba ta amsheta hannu bibbiyu suka gaisa tai musu godiya.    ______________,★       Har washe gari babu wanda ya sake tada maganar komawar Zinneerah gidan hajiya Iya. Dan shi Abba ma ya fice kasuwa abinsa tun safe.        Sai bayan sallar la'asar ne Mmn Sadiq da abin keta cin ranta dai ta tunkari ƴar uwarta da maganar. “Maryama nifa inaga kodan matsalar gidan nan zanbar yarinyarnan ta koma wajen Gwaggo, sai dai kuma idan na tuna kar ace dansu masu arziƙi ne mukai haka abin na damuna. Sannan shi kansa Yaya na fahimci baison maganarnan”.      Murmushi Gwaggo Maryama tayi tana gyara zamanta sosai. “Yaya Hauwa nifa kin ganninan babu abinda ya dameni da cewa ta mutane. Abinda duk ra'ayina ya bani na kuma ji raina ya aminta da shi kuma bai saɓama addinina ko al'adata ba to tabbas yinsa nake dan bama kaina farin ciki. Shi ɗan adam babu wani abu da zakayi a rayuwa ƙyaƙyƙyawa ko mummuna da zai iya gani bakinsa bai tankaba koda kuwa shi a tare dashi akwai abinda yafi naka muni ɗin da ƙyau. Dan haka ajiye batun cewa na mutane muyi abinda ya cancanta. Tun jiya nima cikin nazarin maganar nakeyi da shi Yaya kansa. Shi kawai abinda na fahimta da shi gani yake kamar za'a nuna gazawarsa akan riƙon Zinneerah tunda ba shine ya haifetaba. To amma abinda bai tunaba kuma shine sufa mutanen nan bawai sunsan bama shine ya haifitaba. Sai dai ni har cikin raina na yarda da komawar Zinneerah can gidan kodan wannan fitinanniyar matar tasa dake ganin Yayan ne kawai keda arziƙin da ake zuwa a ci”.         “Maganganunki duk suna a kan hanya Maryama. Harga ALLAH inason basu ita domin ALLAH da suka roƙa da kuma darajar zumincin da suma sukayi dan shi. sai dai inason tai nesa da su Saude kodan ɓata mata suna da suke a anguwatnan miji zaima Zinneerah wahalar samu. Dan damafa ni ko wannan bata tasoba nayi niyyar ta biki can ku zauna har muga abinda ALLAH zaiyi”.       “A to tunda hakane a bani abata mu tafi”. Gwaggo Maryama tai saurin faɗa tana dariya. Itama Mmn sadiq dariyar tayi. Haka suka cigaba da tattaunawa har tsawon wani lokaci kafin subar maganar da nufin jiran dawowar Abba yau su tunkaresa da batun.        Zinneerah da batasan mike faruwaba tana can ɗaki da Little wanda a yanzu yake maƙale mata baya yarda da kowa a gidan sai ita da Gwaggo Halima. Sai su Sadiq idan yaso. Makarantama yau da zata tafi kuka yayta zabgawa sai daga baya ya haƙura bayan yayi barci ya tashi. Wauta da ƙuruciyar dake tattare da ita kuma yasa bata ɗauki hakan komaiba saima tausayin yaron da ƙaunarsa dake ƙara ratsata. Maganar komawa gidan Hajiya Iya kuwa bata damuba ba kuma ta mantaba. Sai dai bata wani ɗaukesa da muhimmanci ba balle taji wani abu a ranta game da hakan. _________________★         Koda Abba ya dawo gidan sai da Mmn Sadiq ta bari yaci ya ƙoshi ya nutsu sosai sannan ta tunkaresa da zancen kasancewar yau itace dashi dama. Shiru yay mata tamkar baijitaba. Ita kuma tunanin baiji ɗin bane ya sata sake maimaitawa kai tsaye. Sai dai yanda ya sake tsuke fuska ya saka tasha jinin jikinta kuma.         Bai kulataba sai da ya mula dan kansa sannan ya fara magana a ƙufule. “Hauwa'u kun shirya hakanne dama saboda abinda ya faru a gidan nan kwanaki shida da suka wuce komi? Shin halin Saude ne baki saniba a gidan nan ne? Da har zaki yanke hukuncin rabani da Zinneerah bayan ni har cikin raina ɗaya na ɗauketa da duk wani yaro dake a gidan nan”.       “Yaya kayi haƙuri dan ALLAH, sam ba yanda kake tunani baneba. Ni abinda yasama kaji namaka magana saboda mu toshe ɓarakar da dangin mahaifiyarmu ke ganin mahaifinmu ne ya assasata. Su daina ganin tamkar muna gudunsune. Sannan baiwar ALLAHn nan ka duba yanda suka ɗauka Inno, wandama bai saniba zai ɗauka itace ta haifi Hajiya Iyan ai. Wlhy na tabbata da ace banan ta kawo Inno har ALLAH ya ƙaddara rasuwarta ananba da sai munyi kuka bana wasaba akan wannan rasuwar. Yanda zuminci ya taɓarɓare kowa zagayewa zaiyi yabar Buba da gawar Inno, da kuma sun bizneta su kama gabansu su barmu. Amma yanzu kaga yanda suke tururuwar zuwa nan hardama waɗanda bakai zaton ganiban. Amma kayi haƙuri nayi kuskure, dan babu yanda za'ai Zinneerah ta koma can bada yardarkaba”.       Numfashi Abba ya sauke yana ɗan jinjina kansa. “Maganarki akan hanya take Hauwa'u, ni kaina naji daɗin wannan karamci da suka nuna akan marigayiyar, dan sun nunama sauran dagi su basu manta alkairin Inno ɗinba garesu har yanzun. Badanma ALLAH bai ƙaddaraba kinjifa maganar kaita india da suka fara. Da ace masu kuɗi haka suke daraja zuminci fiye da dukiyarsu dake tsone idonsu lallai da bamu lalace hakaba. Ace dan ALLAH ya baka wani abin jin daɗin duniya kakoma ƙyamar ɗan uwanka baka ƙaunar ya raɓeka. shiko yana gudun raɓar takane saboda karka wulakantashi. Kaiconmu da fifita abinda zai halakamu sama da abinda zai kaimu aljanna”.        “Amin ya rabbi Yaya. Al'amuran kam sai dai addu'a. Ni kaina halayyar mutanen nan ta zaburar dani wani muhimmin abu insha ALLAH”.       “Ai haka akeso dama. idan kaga wani ya aikata alkairi kayi ƙoƙarin koyi da shi, ka kuma nisanta kanka ga mai aikata mummuna. Dan masu iya magana kance zama da maɗaukin kanwa shike kawo farin kai”.          “Sosai kuwa Yaya, ALLAH kai riƙo da hannayenmu”.     “Amin. To amma nima kuma sai a duba ni dan har cikin raina inason zaman Zinneerah tare damu kodan kansu ya haɗu da sauran ƴan uwanta. Gashi kuma inajin matuƙar kunyar mutanen nan wlhy, yanzu hakamafa ɗazun sai da Alhaji Kabir ɗin ya kirani da kansa akan suna nan dai suna jira”.        Cike da mamaki Mama tace, “Wai kirafa Yaya?”.        “Wlhy kuwa, mutanen nanfa mutanen kirkine masu ban mamaki. Toni banda dalilinki ta inama zan ishesu kallo koda a haɗuwar hanyane. Amma ki duba yanda suke da sauƙin kai. Yanzu da wani zaiji nace Alhaji Kabir Shira na kirana a waya ai cazai na zuga ƙarya ko”..      Dariya ta kufcewa Mmn Sadiq, shima Abban ya shiga tayata. “ALLAH kuwa Hauwa'u koni kallon abun nake tamkar mafarki. Ku riƙe bayin ALLAHn da ƙyau bawai dan arziƙin da ALLAH yay musuba, sai don sanin darajar ɗan adam da zuminci da ALLAH ya azurta zukatansu da shi”.      “Insha ALLAHU Yaya. ALLAH ya bamu ikon gina zuri'armu bisa ƙyaƙyƙyawar tarbiyya muma. Koda sun zama wanu abu a rayuwa sukasance masu sanin mutunci da darajar ɗan adam”.       “Amin ya rabbi Hauwa'u. To ammafa zan basu Zinneerah ne kawai banda Abdul-Mutallab. Tunda ba wani shayar dashi takeba tabar mana abummu anan. Itama dai su tausaya mana ta dinga ziyararmu akai-akai. dan ɗazun namasa maganar karatunta dan shine babban burina a gareta. Inason rayuwarta ta inganta sosai kodan kaddarar data ziyarci rayuwarta tun tana ƙanƙanuwarta. To shine yake cewa indai karatune sai Zinneerah tace ya isheta da kanta insha ALLAH”.        “Yaya ALLAH ya saka da alkairi. Dama nima damuwata akan Abdul ɗinne. To amma kana ganin mu sanar dasu gaskiyar al'amari game da haihuwar tata kenan?”.       “Eh to, bazance miki a'a ba, bakuma zance e ba. amma inaga muɗan bada lokaci taje gidan muga yanayin zaman nata tukunna, duk da har cikin raina bana tunanin wani abu saɓanin ƙyaƙyƙyawa”.        Cike da gamsuwa Mmn Sadiq ta gyaɗa masa kai. ___________________★         Washe gari Gwaggo Maryama ta shirya taje yoma Hajiya Iya sallama dan zata wuce itama. Shatara ta arziƙi aka haɗota dashi, tare da driver na ɗaukar Zinneerah, dan Hajiya Iya tace ta gaji da gafarasa bataga ƙaho ba. Da tarema zasu zo da kanta ta ɗauka Zinneerah ɗin sai akai rashin sa'a tai baƙi. Hakan yasa ta haɗo Gwaggo Maryama da driver tace kafin itama tazo, dan tayi alƙawarin dukkan zuri'arta sai sun tako har gidajensu suma insha ALLAH.        Wannan al'amari ya bama su Mmn Sadiq Mamaki da dariya. Babu shiri tai kiran Abba ta sanar masa. Dole ya baro kasuwa yazo sukai magana. Gashi su kofa Zinneerah basu zaunar akan batunba dan sun yanke da saita samu hutun makarantane.        Ganin kar Hajiya Iya taga kamar suna mata yawo da hankali suka yanke shawarar barin Zinneerah taje kamar da nufin yin kwana biyu haka. Dan karsu mata gatsau takuma shiga wani hali musamman akan Little.       Ilai kuwa da suka kirata aka sanar mata zataje wajen Hajiya Iya ta zauna da ita na kwana biyu saboda batajin daɗi sai bata wani damuba. Hasalima taɗanji daɗin tafiyar kodan taje ta huta daga izgili da ƴaƴan mmn sakina da ita kanta maman sakinar kemata a kwanakin nan musamman a makaranta. Shiru kawai takeyi dan karta tada hankalin mahaifiyarta. Amma abin na damunta, dan takai yau har ihu Sakina ta saka akai mata a aji ana kiranta agola ƴar cin arziƙi. Damuwarta ɗaya karatunta da kuma Little dake nane da ita a kwanakin nan duk da ya ƙara samun sauƙi bakamar daba.      Bayan Mama da Abba sun mata nasiha akan ta kula da kanta da kuma girmama kowa yanda zasuyi alfahari da ita ta ɗauka kaya kala uku kawai abinta tai musu salama cikin dabara ta fito saboda little. Su Sadiq kuwa suna makaranta sai dai su dawo suga wayam bata nan.       Motane lafiyayya kuma ƙosashshiya. Dan ƙamshin dake a cikintama kansa na musamman ne. (Abinda bata saniba wannan mota ta mai gayyace mai aiki ce. dan Alhaji Kabir motarsa ya bada musamman domin ɗakkota. Haka kawai yarinyar ta shiga ransa yakejinta tamkar ƴaƴansa daya haifa. Ga kuma son daya fahimci mahaifiyarsa na mata itama). Tana a baya driver na gaba yana tuƙinsa a nutse, tai tagumi kawai tana kallon waje da zurfafa a tunanin yanda rayuwarta keta walagigi. Anya kuwa ita tanada farin jini ga mutane? Duk inda zata rayu bata taɓa samun salama hundred percent sai da matsaloli. A Danya matsalarta Inna, Yaya Karima, Tinene. Bayan ƙaddara ta haɗata da mahaifiyarta gakuma su Maman Sakina da ƴaƴanta yanzu suna neman hanata shan ruwa a gidan data samu gata da kulawa. Anya kuwa idan ta dawo daga inda zata yanzu bazata shawarci mamansu akan a maidata boarding school ba ko zata samu nutsuwar yin karatunta cikin salama?.       Wannan tunanin yasata jin nutsuwa a ranta taketa sakin murmushi batare data saniba har suka iso gaban katafaren milk color ɗin gate ɗin gidan. Sai da driver yay horn maigadi ya wangale gate ɗin ta dawo hayyacinta. Nannauyan numfashi ta sauke zuciyarta na wani irin tsargawa tamkar waccan ranar da Abba ya kawosu. Addu'a ta shiga karantowa a ranta har driver ya buɗe mata ta fito. Godiya tai masa cikin risinawa. Hakan ya sakashi jin daɗi har cikin ransa. Ya miƙa hannu zai amshi jakkar hannunta amma sai ta hanashi. “Haba Yayana, jakkarma kai zan ba ka ɗauka min, ai babu dacewa a cikin hakan, kaine zan ganka da kaya na amsa bakai zaka ganni dasu ka amsa ba”.      Murmushi ya mata cike da jin ta kuma birgeshi. Shine da kansa yay mata rakkiya har sashen Hajiya Iya. Inda a tafiyar tasu take samun damar yima gidan mai sassa da yawa kallon tsaf. A ranta kuwa raya irin jin daɗi ta masu hannu da manda takeyi. Shiyyasa akace wasu tun a duniya suke cinye rabonsu na lahira. Wasu kuma sai kaga ALLAH ya haɗa musu duniyar da lahirar duka. Ya ALLAH kasa muna cikin masu samun dukan gaba ɗaya.............✍                            *_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 _Na Safiyya Huguma_ *_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖 _Hafsat Rano_ *_★ DALAAL_*💝 _Na Miss xoxo_ *_★ UBAYD MALEEK_*💓 _Na Mamu gee_ *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 _Na Bilyn Abdull_ Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 *_08085405215_* IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   0903 234 5899 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 *_TYPING📲_* *_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_* *Page 17* ____________________ *_INA MATA ƳAN ƘWALISA BA'ABOTA SON GYARA JIKI DA FATA SUYI ƘWANAS TAMKAR WATA ƊAN DAREN SHABIYAR?!_* _Ku marmatso kusa maza na kaiku kantin sauƙi na UMMU DUFAIL gidan sauƙi da biyan buƙatar MATA SARAKAN ado harma da MAZA ƴan ƘWALISA._ *_MATA da yawa kanso su koma Taurari ababen kallo da burgewa ga ma'abota kallo sai dai basusan ina zasu sami sinadarin kankaro wannan ƙyawu da mutuncinba._* _To maza kuzo kusa dan Bilyn Abdull ta lalubo muku kantin sauƙi na Umm Dufail dakeda kaya masu sauƙi da gamsar da maison afani dasu_. *_UMMU DUFAIL nada kayan gyaran jiki masu rahusa da inganci da gamsar da mai saya cikin ƙanƙanin lokaci kamar haka👇🏻😁_* *Customers price list By Ummu Dufail FACE AND BODY* SCRUB=2500(300ml) Face and body mango butter=3k (250ml) Face cream= 1800 Corretor oil/vitamin C oil=2k Fairness skin lotion= 2500 Hot chocolate skin lotion 2500 Serum (for Nuckles )2k Nuckles cream (stubborn)3500 Mix fruits Arabian black =soap 1800 Mix fruit glycerine soap =1900 Beetroot=1900 Coconut, milk,egg..face soap=1200 Lavender mix fruit soap =1800 Body wash =1500 cleanser=1600 Hair spray =700 Hair oil =1500 Hair relaxer =700 Hair butter 1700 Shampoo =1500 Breast=oil 2k powder 2k Strech marks cream= 2k Beetroot pink lips =700 Baby care soap glycerine=1k Baby care butter =1500 Shea butter baby soap =700 Tsumin tula =2200 Tsumin zinariya =1200 Sliming tea =1500 Amarya set =25k Liquid Arabian black soap =1900 Cleansing water =1500 *_Zaku iya bibiyarta domin gani da ido ta Handle ɗinta na istagram da facebook kamar haka_* Ummu Dufail @ Facebook Ummu Dufail @ instagram Phone no: 07067943479. _Ƴammata harma da masu auren karku bari ayi babuku. Dan gyara shine mace a wannan ƙarnin😉👍🏻_. ________________________ *Page 17* ...........Tarba mai ban mamaki da tu'ajjibi Zinneerah ta samu daga hajiya iya, harma da wasu daga cikin jikokinta dake gida ta iske a sashen. Duk yanda taso ta takura kanta saboda baƙunta da rashin sabo sunƙi bata damar hakan. Dan sai faman jera mata tambayoyi suke tamkar ƴan jaridu.       Dolenta ta saki jiki dasu dan su biyun duk sa'anninta ne. Biyu mata, Bahijja da Meenal wadda taci sunan Hajiya Iya kenan. Sai ɗaya Namiji mai suna Jamal.     Harga ALLAH Zinneerah taji daɗin kasancewa dasu, dan ta fahimci sunada tarbiyya da sauƙin kai sosai, sannan son ɗan uwansu ko yaya yake wannan trianing da akai musu ne tun asali.       Cikin katsesu Hajiya Iya dake shafa man zafi a ƙafarta tace, “Niko kun isheni da subaɗi Bahijja. Kuma barni nai hira da Innon tawa kunbi kun hana. Sai ku tashi ku kaita wancan ɗakin kuɗan ƙara gyarawa duk da dai ko jiya Rahi ta garasa ta samu taɗan watsa ruwa ta huta dan shine zai zama ɗakinta”.        Wani irin waro idanu Jamal yayi tare da zabura. Haka Meenal da Bahijja ma duk sai da suka zaro idanun. Jamal yace, “Granny kina nufin ɗakin Yayanmu fa kenan?”.       Harara sosai Hajiya iya ta watso musu tana ƙyaɓe fuska. “Eh shi dinfa nake nufi ba waniba. Zuwa yake ƙasar ne da har za'a wani cigaba da faman barin ɗaki haka aljanu na dubulwa a cikinsa? Ubansama dana haifa bai tuna inda nakeba shekara guda balleshi da ke neman haɗa kusan uku”.        Yanda ta ƙare maganar cikin ɗacin rai ya saka jikinsu duk yay sanyi. A sanyaye Meenal tace, “Kiyi haƙuri Granny, mu dama zaki yarda sai mu tafi da ita sashenmu, kinga saita zauna a ɗakinmu dan ALLAH”.         “Hakan zaifimin daɗi kuwa Amina. Sai dai kuyi haƙuri nafison zamanta kusa dani akoda yaushe. Koba komai zanga fuskar Innota naji sanyi”.       Kansu kawai suka iya kaɗa mata, dan tunda ta faɗi haka basu isa jayayya da ita ba. Ko min roƙon da zasu mata kuma bazata canja ra'ayintaba. Zinneerah dai najinsu kanta a ƙasa, sai dai babu abinda ta fahimta a zancen nasu kuma. Amma ganin yanda fara'ar fuskar Hajiya iyan ta ɓace tun daga maganar ne ya saka jikinta yin sanyi itama......       “Taso muje kiga ɗakinki Sister”. Bahijja ta katse tunanin Zinneerah tana kama hannunta cikin nata. Babu musu ta miƙe tabi bayanta, Meenal da Jamal ma suka mike suka biyosu.      Kallo Hajiya Iya ta bisu dashi idanunta na cika da ƙwalla. Dan maganar nan ta tado mata da wani babban miki dake zuciyarta tsahon shekaru, wanda a shekarin can da suka shuɗe kusan biyar sun fara ganin haske, amma a wannan karon al'amarin na neman komawa baya. Dan inhar lissafinta bai ƙwace mataba kusan shekararsa ɗaya kenan rabonsa da Nigeria. A take wasu hawaye masu zafi suka fara gangaro mata. Saurin saka hannu tai ta sharesu tare da miƙewa ta nufi hanyar ɗakinta tana ɗan ɗingisa ƙafarta dake mata ciwo tinda safe.         “Sister Zinneerah lallai keɗin mai sa'a ce”. Meenal ta faɗa tana tura ƙofar ɗakin da suka iso a ɗan lungun corridor ɗin dake facing jikin ɗakin Hajiya Iya. Kafin Zinneerah ta iya cewa wani abu Jamal ya karɓe da cewa “Mai sa'a kuwa ta gasken gaske. Dan kece ta farko a tarihin gidannan kaf da zaki rayu a wannan ɗakin na Yayanmu bayan shi kaɗai dake rayuwa a cikin kayansa idan yazo ƙasar”.       Haka kawai gaban Zinneerah ya faɗi batare da tasan daliliba. Har suka shige ɗakin ita tama kasa motsawa balle ɗaga ƙafarta. Ganin hakan yasa Jamal dawowa da baya yaja hannunta suka shige ciki, duk da taso ƙoƙarin ƙwace hannun nata amma yaƙi bata dama sai da suka shigo tsakkiyar ƙaton ɗakin da batamasan yanda zata fasaltashi ba a fahimceta.            Sakin hannunta da Jamal yayi ya bata damar ɗago idanu tanabin ɗakin da kallo. Yayinda hancinta ke shaƙar mata wani irin mayataccen ƙamshi mai sanya zuciya salama. Wani irin saki gaɓɓanta sukai a lokaci ɗaya, ta zubama su Bahijja daketa yaye fararan ƙyallayen da aka lulluɓe komai na cikin ɗakin dasu saboda gudun ƙura ta hausu.          Sai da suka gama yaye komai ya bayyana Meenal ke faɗin, “Bara na ɗakko kayan shara mu tayaki ɗan ƙara gyarawan baƙunta. Kuma mufa kibar mana wannan ɗari-ɗarin Madam”.      Cikin tsokana Jamal yace, “Barta sotake mu kirata baƙauya maybe. Gwarama ki sake damu kafin su Yah Haneef su dawo gidannan gobe idan ALLAH ya kaimu, dan zasu cinyeki da bakine”.        “Kaji munafiki, saina faɗa musu yasin”. Bahijja dake hararsa ta faɗa.     Yanda Jamal yay da fuskane ya saka dariya kufcema Zinneerah batare data shiryaba. Hakan yay dai-dai da dawowar Meenal ɗauke da kayan shara ɗakin. “Oh ALLAH, kokefa ƴar uwa. Ni kuwa an taɓa faɗa miki keɗin ƙyaƙyƙyawa ce musamman idan kina dariya?”.           Kasa bata amsa Zinneerah tayi, sai dariyar tatace ta koma murmushi kawai. Hakan datai ya saka su Jamal kwashewa da dariya a tare. Bahijja tace, “Kinga kinsatama ta haɗiye abinta da wannan bakin naki da bai gani ya ƙyale”.......        “Wai nikan sharar zakuyi ko damuna da shegen surutu?”. Suka jiyo muryar Hajiya Iya dake tunkaro ɗakin.        A take kowa ya nutsu suka fara ƙoƙarin sharar. Shigowa tai har yanzu fuskarta a dagule da ɓacin ran ɗazun. Tabi ɗakin da kallo da ƙyau kamar mai nazari. A ƙarshe ta sauke idonta akan Zinneerah dake ƙoƙarin tayasu itama. Haka kawai kuma sai taji ɓacin ran nata ya sassauta. Ta sauke ajiyar zuciya da juyawa ta fice a ɗakin.       Tsaf suka gyara komai dan an horar dasu aiki tuni. Cikin kanƙanin lokaci ƙyawu da tsaruwar ɗakin ya ƙara bayyana a idon mai kallo. Musamman da suka cire labulayen ɗakin duk suka sake canja wasu fararen tas dan dama fararen suka cire. Kaso mafi yawa dake a ɗakin kalar blue and white ne. Sai wasu colors ɗin ɗai-ɗai da ba'a rasaba. Da yawansu kuma an ɓaɓɓoyesu ma.       Idanu ta lumshe a hankali tana maijin wani abu mai nauyi dake a ƙirjinta yana narkewa sannu-sannu zuwa cikinta. Nannauyar ajiyar zuciyar da bata shirya fitartaba ta kufce mata a karon farko. Kusan a tare Meenal, Bahijja, Jamal suka dubeta. Sai dai babu wanda ya iya cewa komai a cikinsu, dan sun fahimci Zinneerah bata da sakewa da mutane, gata kuma da alama akwai miskilanci tattare da ita. ★★        Ƙarfe bakwai da wasu mintuna Alhaji Kabir ya iso katafaren family House ɗin nasu. Bayan samun wajen fakin da direba yayi ya tsaya aka buɗe masa ya fito riƙe da leda a hannunsa wadda kowa yasan mai ita. Dan babu fashi kullum sai ya shigo da irin wannan ledar domin mahaifiyarsa koda iyalansa basu samu hakanba. Sanin baya bama kowa dakon ɗaukarta, shi yasa babu wanda ya tunkaresa domin karɓa. Sai dai sauran kayansa da ɗallami driver ya kwasa zuwa sashensa shi da iyalansa. Shi kuma ya nufi sashen Hajiya Iya kansa tsaye.         Ɗauke da cikkakkiyar sallama a bakinsa ya shigo falon duk da yasan a irin wannan lokacin Hajiya iya na ƙuryar ɗakinta. dan idan tai sallar magriba bata fitowa sai isha'i. Amma yanada tabbacin baza'a rasa wasu daga cikin ƴaƴansaba da basa rabo da sashen a koda yaushe.     Ilai kuwa yana shiga da fuskar Zinneerah da Meenal ya fara tozali dan sune ke facing ƙofa. A take falon yay tsit kowa ya ƙara nutsuwa. Sai Meenal ce datai saurin miƙewa ta nufesa domin amsar ledar hannun nasa. “Baffah sannu da zuwa?”.       “Yauwa uwata kune anan?”. “Eh Baffah, munzo tarbar Sister Zinneerah ne tun ɗazun”.      Murmushi Alhaji Kabir yayi yana maida kallonsa ga Zinneerah data risinar da kanta ƙasa tun bayan amsa sallamarsa. Ya ƙaraso cikin falon sosai su Bahijja ma na masa barka da dawowa. A hankali Zinneerah ta zamo ƙasa tana faɗin, “Sannu da zuwa Baffah. Ina wuni”.      Murmushinsa ya sake faɗaɗawa da faɗin, “Yauwa ɗiyata. Welcome to Shira's family”.        “Thanks you Baffah”. Ta faɗa a hankali cike dajin kunya.        Ya cigaba da faɗin, “Yaya kika barmin ƙanwata da ƙannanki da Abbanki?”.       “Lafiya lau Baffah, sunce suna gaisheka”.      “Ina amsawa. Alkairin ALLAH yakai garesu. Tashi ki zauna”.     Babu musu Zinneerah ta miƙe ta koma kusa da Meenal data kaima Hajiya Iya leda ta dawo ta zauna. Shikuma ya wuce bedroom ɗin Hajiya iyan domin gaisheta.        Tunda yay sallama a yanda ta amsa masa ya saka gabansa faɗuwa. Cikin ƴar ruɗewa ya ƙaraso ƙaton ɗakin nata itama da sassarfa. Gabanta ya zube jikinsa na rawa. “Innata mike faruwa naji muryarki tamkar baƙyajin daɗi?”.        Ɗago kyawawan idanunta da mafi yawan ƴaƴa da jikokin gidan suka gada a wajenta tai tana kallonsa. A take hawayen da taketa maƙalewa tun ɗazun suka silalo mata tare da murmushi a lokaci guda. Sake ruɗewa Alhaji Kabir yayi idanunsa shima na kawo ruwan hawaye.      Kanta ta girgiza masa a hankali tana share nata. “Hawayena basu zuba domin kai ba Kabir. Dan kai ɗa ne tamkar da dubu ga kowaɗanne irin iyaye. Nagodema ALLAH domin yayimin ni'imomi masu yawa a rayuwa da har wanda ke a nesa dani bazai ɗauka inada wata damuwa ko jarabawa nima tattare dani ba, kuma har da samunka matsayin ɗa a cikin ni'imomin. Kabir tabbas ɗan uwanka shine jarabawata. Dan ALLAH ka tayani addu'a ALLAH ya bani ikon cinyewa. A lissafin danai yau shekarar Ahmad ɗaya da watanni biyu kenan rabonsa da ƙasarnan. Yanzu ace Kabir har Inno ta rasu Ahmad ya gagara ɗakko iyalansa suzo sumin ta'aziyya. Idanma ita data nisantani dashi bazatazo ba shi bazai iya zuwaba koda shi da Modibbo ne?. Moddibo fa kansa shekararsa uku kenan rabonsa da ƙasarnan. Tunda nai maganar yay auren nan bai sake zuwaba, uwarsa kuma ta hana wannan ƙoɗaɗɗiyar yarinyar zuwa nan ɗin koda ta haihunma. To kosai na mutune zata barsu suzo su raɓi gawata......”       Ta kasa ƙarasa maganarta saboda kuka daya kufce mata.       “Innata dan girman ALLAH ki daina kuka. Kiyi haƙuri dan ALLAH, addu'arki da tamu Ahmad yafi buƙata. Kuma insha ALLAH namiki alƙawarin a wannan karon zanbi duk hanyar data dace domin maido ɗan uwana gida. Har ita ɗin da shaiɗancinta dole ta biyosa. inko taƙi wlhy sai dai ta kama gabanta inda ta fito. Amma dan ALLAH kibar kuka Inna”.       “Kayya Kabir. A baya fa kayi irin wannan namijin ƙoƙarin amma kaga ta sake sabon shiri, harshi Moddibo ɗinma da ada bayabin ra'ayinta yanzu ta sake janyesa. A zatonmu kusancin da Khalipha ya samu dasu zai kawo wani canjin sai gashi ba hakaba”.        “Insha ALLAH Inna komai zai wuce. Ai duk abinda ya saka kuka wataran zai saka dariya. Duk kuma abinda ya saka dariya wataran sai ya saka kuka. Itama ai gasunan ta haifa indai ƴaƴane ko. kuma Alhmdllh sai ya bata mafi rinjayensu maza. Itama kukan da zatayi akansu sai ya ninka naki sau dubu. Amma dan ALLAH ki daina masa kuka Inna dan shima ba laifinsa bane, anfi ƙarfinsa ne kawai”.       “Humm ko anfi ƙarfinsa kam da halima. Dan shima kaidin macen yana iske haline. Kai miyasa matan naka basu rabani da kai ba”.      Kasa cemata komai yayi sai ban haƙuri dai. Sai da yaga hankalinta ya kwanta sanann ya miƙe ya fice domin zuwa gabatar da sallar isha'i tunda ya cinye lokacin zuwa yay wankan anan.      Bai iske su Zinneerah a falonba yanzu. Da alama sun shige gabatar da sallar suma. ______________★       Duk yanda Alhaji Kabir yaso rintsawa a daren yau hakan ya gagara. Ba komai ke masa kai kawoba a rai sai tattanawarsa da Mahaifiyarsu akan ɗan uwansa.        Su uku kacal mahaifiyarsu Hajiya Iya ta haifa a duniya. Shine babba, sai ƙaninsa Ahmad, sai autarsu Bilkisu da ayanzu haka tana Lagos tana aure. Rana ɗaya aka ɗaura masa aure da ɗan uwansa Ahmad, wanda mafi yawan mutane sukafi sani da suna AK Shira. Ba komai yasa ake kiransa da suna AK ba sai tsanain soyayyar da sukema juna tun ƙuruciya. Kasancewar boarding school sukayi acan ake kiransa da suna Ahmad ɗin Kabir. A hankali kuma sai abokai suka koma kiransa a takaice da suna AK Shira. Mai makon Ahmad Abdul-Mutallab Shira kamar yanda shi ake kiransa Kabir Abdul-Mutallab Shira. Bayan sun kammala secondary tare suka wuce ƙasar Turkey ƙaro karatu. Cikin amincin ALLAH suka haɗa digiri ɗinsu na farko dana biyu duk a tare. Tun suna farkon fara digiri na biyu Ahmad ya haɗu da matarsa ta yanzu mai suna Hindatu. Asalin Hindatu ƴar ƙasan Nigeria yace. dan mahaifinta ɗan nanne. Sai dai mahaifiyarta ƴar asalin ƙasar Morocco ce. Amma suna zaune a ƙasar Turkey tun tanada ƙuruciya, acan ta girma tamafi sanin can matsayin ƙasarta fiye da Nigeria dan sukan jima basuzoba. Ƙyaƙyƙyawa ce itaɗin sosai kasancewarta halfcast ce. Sai ALLAH ya bata wani irin usilin ƙyau mai ɗaukar hankalin mai kallonta.      Duk da yasan ba wannan ƙyawun bane ya ruɗi ɗan uwansa ga sonta, amma shima ya taka rawar gani wajen jan hankalinsa gareta. Bayan sun kammala digirinsu na biyu suka dawo Nigeria kamar yanda mahaifinsu ya buƙata. Dan yana bukatar suzo suyi aure. Koda suka iso suka huta babu wani jan rai iyayensu suka gabatar musu da matan aure. Shi Alhaji Kabir ya amsa da hannu biyu yay godiya dan dama baida ko budurwar. Amma Ahmad ƙiri-ƙiri yace shifa yanada matar aure. Hajiya iya ce ta fara nuna rashin yardarta akan hakan amma ya nuna bamai rabasa da Hindatu dan yana mata so mai zafin gaske. Gudun samun ɓaraka yasa Marigayi Alhaji Abdul-Mutallab zaunar da Hajiya Iya yaymata nasiha harta amince badan ranta yasoba.        A take aka hau shirin biki, cikin kanƙanin lokaci komai ya kammala dan ana zuwa nemawa Ahmad auren Haindatu babu wani ja'inja aka bashi. Ansha biki na nunawa sa'a lokacin, dan Alhaji Abdul-Mutallab ya tara musu. Bayan biki duk aka kai amare garin Bauchi, harda Hindatu. Ƙyawawan halin Hindatu yasa Hajiya Iya ta fara sonta, sai kuma akazo dandanan ta samu ciki. Duk da Hindatu na karatu a jami'ar Turkey bata taɓa nuna ƙorafinta nason komawa makarantaba. Tai shiru abinta har ALLAH ya sauketa lafiya ta haihu ɗanta namiji da yaci suna Abdul-Mutallab. Amma saboda alkunya suke masa laƙani da suna Adnan, Hajiya Iya kuma na kiransa Moddibo.      Bayan haihuwarsa da kusan  watanni huɗu Ahmad ya buƙaci sake komawa ƙasar Turkey dan cigaba da karatunsa. Sai dai a baɗini wannan shirin Hindatu ne. Basu kawo komai a ransuba suka amince Ahmad ya ɗauka Hindatu da dansu suka tafi Turkey saboda kowa yasanshi da matuƙar son zurfi a karatu, shi kuma a lokacin matar Kabir ta fara laulayin nata cikin ita.         Kamar wasa tun daga wannan tafiyar ganin Ahmad ya fara musu wahala. Dan ya samu aiki acanma ta dalilin mahaifin Hindatu. Sannu-sannu ƴaƴa suka fara yawaita a wannan family, yayinda ALLAH yayma Alhaji Abdul-Mutallab rasuwa. Akan wannan rasuwa kuwa saida sukai yaƙi na gaske Ahmad yazo Nigeria. Inda a wannan zuwan nasane Hajiya Iya ta amshe Moddibo ko hakan zaisa Ahmad ya ringa tunawa dasu.       Hakan kuwa yaso fara tasiri akan Ahmad ɗin, saboda tsananin so da sukema Moddibo daga shi har Hindatu. Sai dai kuma yana kammala secondary daga tafiya karatu ƙasar London aka sake samun matsala suka sake ƙwace abinsu. Ɗan dawowa da Ahmad ɗin ya farayi garesu ta ƙara lalacewa. Sai dai Alhmdllh duk hutun duniya a Nigeria Moddibo keyinsa. Wannan ne ya ɗan sanyaya ran Hajiya Iya. Amma duk da haka basu daina yaƙin son maido Ahmad jikinsu ba. A dalilin Adnan da shima rashin zuwan mahaifin nasa gida ke cin ransa suka sake dawo dashi cikinsu a shekarun nan, sai dai kuma suna murna an samu waraka shima sai Adnan ɗin ya ɗauke tasa ƙafar gaba ɗaya a dalilin aure da Hajiya iya ta matsa masayi.......          Nannauyan numfashi Baffah ya sauke mai haɗe da ajiyar zuciya saboda fahimtar da yay tunaninsa yayi zurfi. A yanzu haka kuma ba tunanin abinda ya shuɗe bane mai muhimmanci garesa, a'a abinda zaizo shi ya kamata yay tunanin gyarawa kodan farin cikin mahaifiyarsa ma dasu kansu shi da ƴar uwarsa da zuri'arsu. Dan haka ya sake zurfafa a wani dogon tunanin da bai dawo hayyacinsaba sai a wani tsahon lokaci daya samo mafitar da yaji har a cikin ransa ya gamsu da ita sannan.          ★★★★    Washe gari daga sallar asuba ya zarto sashen Hajiya iya. Bayan ya zauna sun gaisa ya zayyane mata shawarar da ya yanke a wannan karon. Cikin jimami tace, “Amma Kabiru baka gani wannan shawarar tana kamanceceniya data baya kuwa?”.         “Eh to Inna tana kama da ita. Sai dai akwai ɗan banbanci da waccan ɗin. Ki dai tayani addu'a, kuma ki ƙara nazari kema akan hakan mugani”.       “To shilenan. Ai ba'aƙi ta mutumba inji masu iya magana. ALLAH ya shige mana gaba”.       “Amin ya rabbi Inna nagode. Ina mutuniyar takine banji motsintaba?”.       “Oh kana maganar Zinneerah ne? Tana ɗakin Moddibo tunda ba zuwa yakeba ita ai saita zauna. Dan nace ja'iran nan suzo su rinƙa tayata kwana harta saba wai tsoro sukeji sudai. taya zasu iya kwana ɗakin Yayansu bayan kowa yasan dokarsa ba'a shigar masa ɗaki sai da dalili mai ƙarfi”.        Dariya Baffah yayi yana faɗin, “Inna sunsan halinsa ba wasa yake dasuba ai Babana. Itama Zinneerah ɗin dai gara a gyara mata wani karki haɗa rikici Inna”.        “Oh to nima tsoron nasa nakeji kenanma ashe?. To yaci ƙaniyarsa shida dokar tasa babu inda zataje. Idan yazo ni basai ya dakeniba mai bauɗaɗɗen halin tsiya irin na uwarsa”.       Dariya Baffah ya mike yanayi shidai da faɗin, “Ai kunfi kusa Innata.  Wazai yarda ya shiga tsakaninki da Adnan da Khalipha a gidan nan”.        “Aikam ni yanzu bana yayin wani Moddibo can. Garama Khalipha ɗin duk da shima ja'irin kansane, daka ɗakko laifin takwaran nasa zai fara karewa da yayansu kaza-kaza, saikace akansa aka fara ɗan uwa”.      Shi dai Baffah dariyarsa yaketa sha harya samu ya gudu domin zuwa yay shirin fita kasuwa.        Lokacin da Hajiya iya kenan suna maganarsu da Baffah Zinneerah datai kwanan baƙunta a ɗakin data fahinci mai shi mutum ne mai matuƙar daraja da girma ga jama'ar gidan, dan su Meenal ƙiri-ƙiri sunƙi zaman ko mintuna goma a ciki, nacan ta shige cikin masu aikin Hajiya Iya tana tayasu aikin gyaran sashen. Lokacin da Baffah ya fito ya fice suna Kitchen domin haɗa breakfast kasancewar kullum anan Baffah ke karin kumallon safe tare da mahaifiyar tasa.     Masu aikin sunso hanatayi amma taƙi. Dole suka barta saboda sunsan yaran gidan dama kan shiga ai aiki dasu suma bisa dokar Hajiya Iya. Amma da dan ta iyayensu matane kam da ba hakaba. Itako Hajiya Iya ta tsaya tsayin dakane domin taimakonsu tunda tasan gidan wani zasuje.      Bayan sun kammala komai tsaf Baba Rahi tace taje tai wanka kafin Hajiya Iya ta fito dan batason ƙazanta ko kaɗan. Shiyyasa kosu kansu idan baka saniba bazaka taɓa ɗauka ƴan aiki bane a gidanma sai an faɗa.............✍       *_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 _Na Safiyya Huguma_ *_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖 _Hafsat Rano_ *_★ DALAAL_*💝 _Na Miss xoxo_ *_★ UBAYD MALEEK_*💓 _Na Mamu gee_ *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 _Na Bilyn Abdull_ Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 *_08085405215_* IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   0903 234 5899 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 *_TYPING📲_* *_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_* *Page 18* ____________________ *_INA MATA ƳAN ƘWALISA BA'ABOTA SON GYARA JIKI DA FATA SUYI ƘWANAS TAMKAR WATA ƊAN DAREN SHABIYAR?!_* _Ku marmatso kusa maza na kaiku kantin sauƙi na UMMU DUFAIL gidan sauƙi da biyan buƙatar MATA SARAKAN ado harma da MAZA ƴan ƘWALISA._ *_MATA da yawa kanso su koma Taurari ababen kallo da burgewa ga ma'abota kallo sai dai basusan ina zasu sami sinadarin kankaro wannan ƙyawu da mutuncinba._* _To maza kuzo kusa dan Bilyn Abdull ta lalubo muku kantin sauƙi na Umm Dufail dakeda kaya masu sauƙi da gamsar da maison afani dasu_. *_UMMU DUFAIL nada kayan gyaran jiki masu rahusa da inganci da gamsar da mai saya cikin ƙanƙanin lokaci kamar haka👇🏻😁_* *Customers price list By Ummu Dufail FACE AND BODY* SCRUB=2500(300ml) Face and body mango butter=3k (250ml) Face cream= 1800 Corretor oil/vitamin C oil=2k Fairness skin lotion= 2500 Hot chocolate skin lotion 2500 Serum (for Nuckles )2k Nuckles cream (stubborn)3500 Mix fruits Arabian black =soap 1800 Mix fruit glycerine soap =1900 Beetroot=1900 Coconut, milk,egg..face soap=1200 Lavender mix fruit soap =1800 Body wash =1500 cleanser=1600 Hair spray =700 Hair oil =1500 Hair relaxer =700 Hair butter 1700 Shampoo =1500 Breast=oil 2k powder 2k Strech marks cream= 2k Beetroot pink lips =700 Baby care soap glycerine=1k Baby care butter =1500 Shea butter baby soap =700 Tsumin tula =2200 Tsumin zinariya =1200 Sliming tea =1500 Amarya set =25k Liquid Arabian black soap =1900 Cleansing water =1500 *_Zaku iya bibiyarta domin gani da ido ta Handle ɗinta na istagram da facebook kamar haka_* Ummu Dufail @ Facebook Ummu Dufail @ instagram Phone no: 07067943479. _Ƴammata harma da masu auren karku bari ayi babuku. Dan gyara shine mace a wannan ƙarnin😉👍🏻_. ______________________ *Page 18* ...........Washe gari daga sallar asuba Baffah ya zarto sashen Hajiya iya. Bayan ya zauna sun gaisa ya zayyane mata shawarar da ya yanke a wannan karon. Cikin jimami tace, “Amma Kabiru baka gani wannan shawarar tana kamanceceniya data baya kuwa?”.         “Eh to Inna tana kama da ita. Sai dai akwai ɗan banbanci da waccan ɗin. Ki dai tayani addu'a, kuma ki ƙara nazari kema akan hakan mugani”.       “To shilenan. Ai ba'aƙi ta mutumba inji masu iya magana. ALLAH ya shige mana gaba”.       “Amin ya rabbi Inna nagode. Ina mutuniyar takine banji motsintaba?”.       “Oh kana maganar Zinneerah ne? Tana ɗakin Moddibo tunda ba zuwa yakeba ita ai saita zauna. Dan nace ja'iran nan suzo su rinƙa tayata kwana harta saba wai tsoro sukeji sudai. taya zasu iya kwana ɗakin Yayansu bayan kowa yasan dokarsa ba'a shigar masa ɗaki sai da dalili mai ƙarfi”.        Dariya Baffah yayi yana faɗin, “Inna sunsan halinsa ba wasa yake dasuba ai. Itama Zinneerah ɗin dai gara a gyara mata wani karki haɗa rikici Inna”.        “Oh to nima tsoron nasa nakeji kenanma ashe?. To yaci ƙaniyarsa shida dokar tasa babu inda zataje. Idan yazo ni basai ya dakeniba mai bauɗaɗɗen halin tsiya irin na uwarsa”.       Dariya Baffah ya mike yanayi shidai da faɗin, “Ai kunfi kusa Innata.  Wazai yarda ya shiga tsakaninki da Adnan da Khalipha a gidan nan”.        “Aikam ni yanzu bana yayin wani Moddibo can. Garama Khalipha ɗin duk da shima ja'irin kansane, daka ɗakko laifin takwaran nasa zai fara karewa da yayansu kaza-kaza, saikace akansa aka fara ɗan uwa”.      Shi dai Baffah dariyarsa yaketa sha harya samu ya gudu domin zuwa yay shirin fita kasuwa.        Lokacin da Hajiya iya kenan suna maganarsu da Baffah Zinneerah datai kwanan baƙunta a ɗakin data fahinci mai shi mutum ne mai matuƙar daraja da girma ga jama'ar gidan, dan su Meenal ƙiri-ƙiri sunƙi zaman ko mintuna goma a ciki, tana can ta shige cikin masu aikin Hajiya Iya tana tayasu aikin gyaran sashen. Lokacin da Baffah ya fito ya fice suna Kitchen domin haɗa breakfast kasancewar kullum anan Baffah ke karin kumallon safe tare da mahaifiyar tasa, weekend ne kawai bayayi anan.     Masu aikin sunso hanatayi amma taƙi. Dole suka barta saboda sunsan yaran gidan dama kan shiga ai aiki dasu suma bisa dokar Hajiya Iya. Amma da dan ta iyayensu matane kam da ba hakaba. Itako Hajiya Iya ta tsaya tsayin dakane domin taimakonsu tunda tasan gidan wani zasuje.      Bayan sun kammala komai tsaf Baba Rahi tace taje tai wanka kafin Hajiya Iya ta fito dan batason ƙazanta ko kaɗan. Shiyyasa kosu kansu idan baka saniba bazaka taɓa ɗauka ƴan aiki bane a gidan ma, sai an faɗa.          Babu musu ta nufi komawa ɗakin data kwana. Ɗakin da kallonsa kawai saka mata wani shakkar zama a cikinsa take shiga. Dan har cikin ranta tanaji cewar matsayinta bai kai na ta zauna wannan ɗakinba da take ƙyautata zaton na musamman ne.        Kamar yanda ta kasance a ɗarare daren jiya yanzunma a ɗararen tai komai. ALLAH ya taimaketa ma hatta da soson wanka da kayan shafarta ta taho da abinta. Komai na ɗakin bata yarda tai amfani da shiba bayan ruwa, sai bargo data saka a ƙasa ta kwanta a daren jiya.      Tsaf ta kammala shirinta cikin riga da skirt na atanfa ruwan bula da ratsin fari, sai ɗan baƙi-baƙi kaɗan. Hijjab ƙarami data taho dashi saboda zaman gida ta ɗauka ta saka sannan ta fita. karo suka kusanci da Jamal tai baya da sauri.      “Oh sorry Sister, dama Granny tace ki fito ke kaɗai ake jira cin abinci”.  Kallonsa tai kamar zatai magana sai kuma tai shiru saboda tinawa da nasihar mahaifiyarta data tuno akan zaman gidan. Tai ɗan murmushi da faɗin, “Ina kwana”.       Dariya yayi yana susan kai. “Uhm su Jamal an girma. Wai ni kike gaidawa ma kowa?”.      Karon farko tai dariya da fara tafiya, har cikin rai yanda suke da barkwanci na birgeta. Shima sai ya biyota yana rawa wai an gaishesa, bayan kaf gidan shike gaida kowa. Koda suka iso ƙaton dining ɗin karaɗinsane ya saka kowa maido hankalinsa kansu. Ya ƙaraso garesu yana basu labarin yau an gaisheshi shima ya tashi daga autan gidan nan yanada ƙanwa.         Babu wandama yaji miya faɗa dan duk hankalinsu nakan Zinneerah da duk ta daburce saboda idanunsu. Ƙasa takai tsugunne dai-dai tana isowa gabansu tace, “Hajiya ina kwana?”.        Fuskar Hajiya Iya ɗauke da fara'a da kulawa ta amsa mata, tare da tambayarta baƙunta. Kan Zinneerah a ƙasa take amsawa. kafin ta juya ga Baffah shima ta gaidashi da girmamawa. Amsa mata yay shima cikin kulawa da faɗin, “Kinga taso ga abinci, ga kuma ƴan uwanki nan dake gida duka”.        Kanta ta jinjina masa jikinta na ƙara saki saboda jin idanunsu duk a kanta. batare data miƙe ɗinba tace, “Ina kwanan ku?”.      Moos'ab ne ya fara sauke numfashi da amsa mata. “Lafiya lau ƴar ƙyaƙyƙyawa, Granny ina kika samo mai kama da Inno haka?”.       Kafin Hajiya Iya ta bashi amsa Haneef ya amshe da cewa, “Masha ALLAH ko itace ƙanwar tamune?”. Saifudden zaiyi magana shima Baffah da ke shirin fara cin abincin da Abidah ta haɗa masa yace, “Wai ni gidan nan halan duk ƴan jarida muka tarane? Indai kune yanzu sai kowa yace sai ya mata tambaya anan. Ɗiyata taso kinji”.        Cikin jin kunya ta taso ta zauna kujerar da Ni'ima ta gyara mata. Kallonsu Baffah yayi su duka, danya fahimci har yanzu duk hankulansu naga Zinneerah musamman ƴan samarin ƴaƴan nasa. Yay ɗan murmushin manya yana lumshe ido da buɗewa. “Wannan itace Zinneerah ƙanwarku. Wadda tun kafin zuwanta an sanarma kowa dake gidan nan. Muna fatan zaku karɓeta da hannu biyu ku kuma ɗauke babu wani banbanci daku”.       Insha ALLAHU Baffah. Suka haɗa baki wajen faɗa su duka.     Kansa ya jinjina cike da gamsuwa yana maida dubansa ga Zinneerah da kanta ke ƙasa. “Ɗiyata Zinneerah ɗago ki kalli kowa danki haddace fuskokinsu da sunayensu”.        Duk da tana cikin yanayin jin nauyi bin umarnin Baffah dolene a gareta. Hakan yasa ta ɗago a hankali. Da wanda ke kusa da Hajiya Iya ya fara. “Wannan sunansa Mas'ood, ƴan biyu ne shi da Moos'ab gashinan. Wannan kuma Saifudden, wannan Haneef, wannan Abidah, wannan Safiyya, wannan Ni'ima. Sai Jamal, Meenal, Bahijja. Akwai yayunki kusan goma da babusu anan. Koda yake ba duka bane yayun naki a cikinsu dan kin girma wasu. Insha ALLAH duk zaki sansu su sanki suma a hankali. Waɗan nan dai sune yanzu tare dake anan gida, zaki kuma kasance da kusan dukansu yanzu a gida insha ALLAH”.         Fuskarta daɗan murmushi tace, “Nagode Baffah”.       Murmushin shima yay mata yana jinjina kansa. Yayinda su Haneef suka haɗa baki wajen, “Welcome to Shira's family ƙanwarmu”.        “Na gode Yayuna”. Ta faɗa ita cikin son aro jarumtar son sakewa da su. Dan taji daɗin yanda duk suka nuna jin daɗin kasancewarta a cikinsu.     Ƴar gajeruwar nasiha Hajiya iya tai musu akan zuminci kafin su fara cin abincinsu a tsanake. Wajen yayi shiru bakajin ko ƙwaƙwƙwaran tarin wani saboda dokace a garesu ba'acin abinci ana magana musamman idan Hajiya Iya da Baffah na waje. Uwa uba kuma Babban Yaya mai gayya mai aiki dashi ko ƙara cokalinka ya cikayi sai kasha uwar harara.          Koda duk suka kammala duk ficewa sukai, dan dukansu karatu sukeyi a mabanbanta makarantu jami'oi. Wasunsu na gab da kammalawa, wasu kuma yanzu suka fara musamman ƴammatan. Wasu kuma na tsakkiya. Sai su Bahijja dake secondary sun wuce Zinneerah da aji daya, dan suna ss2. Sai dai yau bazasujeba dan suna wani ɗan hutun kwana biyu a gida.       Bayan wucewar kowa ita dasu Meenal ɗin ne suka gyara dining ɗin. Hajiya Iya kuma ta nufi ɗaki gabatar da sallarta ta walha tana bar musu saƙon raka Zinneerah wajen iyayensu ta gaishesu.      Suna kuwa kammala gyara wajen suka jata. Meenal ce taja birki lokacin da suke gab da kaiwa tsakkiyar ƙaton harabar gidan nasu. “Kunga ku tsaya a fara da nunama sister kowanne sashe first”.        “To uwar tsari”. Cewar Jamal da shaƙiyanci.      Hararsa Meenal tayi sai dai batace komaiba. Bahijja tace, “Da gaskiyar sister ai, a fara da waje”.       “Naji karku cinyeni da baki malamai. Sister Zinneerah nan inda muka fito shine sashen Granny nasan kin sani ai?”.     Jamal ya faɗa idonsa a kanta. Batare da jiran amsarta ba ya cigaba. “Wannan na kusa da shi shine sashen Daddy Ahmad ne. Sai dai basa nan suna ƙasar Turkey lokaci-lokaci suke zuwa. Yaransa biyar shima. Yah Ibrahim, Yah Sadiq, Yah Hafeez. Aunty Zuhrah. Sai Aneesa dan bazance mata Aunty ba, kwana tara kawai ta bani a duniya kamar wannan yarinyar”. Ya nuna Meenal.       “Shashasha ai dai na girmekan ko?”.         “Oho a banza dai tunda kammu ɗaya”. Ya bata amsa yana mata gwalo.     Dariya abin nasu keba Zinneerah. Dan haka yanzuma tai murmushi mai faɗi.        “Yauwa sai nan kuma Sashen Gwaggo Bilkisu ne idan tazo nan take sauka itama. Tana Lagos da yaranta huɗu itama, kada lissafin yay miki yawa zakisan sunayensu suma nan gaba. Sai nan shine sashen su Yah Saifudden. Nan kuma sashen baƙine. Wannan da zamu shiga shine sashenmu, iyalan Baffah kenan”.     Murmushi Zinneerah tai cike da gamsuwa dajin birgewar tsarin nasu. Batare da tayi maganaba suka nufi sashen Baffah ɗin da yafi na kowa girma a gidan kasancewar yafi kowa yawan iyalai.       Sun fara shiga katafaren falo da yaji kayan more rayuwa da ƙawa, wanda har suka fice daga cikinsa Zinneerah bata gama kammala kallon daular dake shimfiɗe a cikinsaba. Basu tsaya anan ba suka isa falo na biyu wanda shima ƙatone na gaske harma zai iya ɗara na farko kayan alatu. A tunaninta an gama kenan, sai taga sun shigo wani falon a hannunsu na dama, sai dai shikam madaidaicine bakai na baya girmaba amma ya fisu tsaruwa.       Hamshaƙiyar mace ƙyaƙyƙyawa dake zaune da waya a kunne ta ɗago tana kallonsu. Fuskarta a sake take sai dai ba murmushi takeba. Zama su Bahijja sukai a kujera suna faɗin, “Barka da safiya Momie”.       Kasancewar waya take bata amsa musu ba. Tadai ɗaga musu hannu kawai idonta akan Zinneerah data kai zaune ƙasa zuciyarta na harbawa da ganin kamanin matar da Khalipha sosai. Bayan ta kammala ta ajiye wayar tana faɗin, “Masha ALLAH ɗiyata sai yanzu muke ganinki?”.        “Kuyi haƙuri Momie”. Zinneerah ta faɗa kamar yanda taji su Meenal na kiranta.       Cikin ƴar dariya tace, “A'a aiba laifi kikaiba ƴata. muna miki maraba da shigowa cikinmu”.        Gaba ɗaya kan Zinneerah a kulle yake. Tadai daure ta amsa mata da godiya tana gaisheta cikin girmamawa. Hakan yasaka Hajiya Nafisa jin daɗi har ranta dajin ƙaunar Zinneerah. Sun ɗanja lokaci a sashen Hajiya Nafisa da suke kira Momie nata mata ƴan tambayiyi jefi-jefi da janta da hira.        Hajiya Nafisa itace Baffah ya aura bayan rabuwarsa da Hindatu. Itace mahaifiyar Khadija da a yanzu haka tayi aure itada ƴar uwarta Hafsat. Sai Khalifa, Saifudden, da auta Bahijja. Sunɗan jima Kafin su miƙe su fito dan itama wajen aiki zata fita.     Daga nan sai sashen Hajiya Halima mahaifiyar su Meenal. Wadda suke kira Ummi. Itace ta haifi Mas'ood, Moos'ab, Ni'ima, Meenal auta. Itama ɗin dai ta tarbesu da kulawa da sakewa. Dan tamafi Momie fara'a gata da barkwanci. Yanda Zinneerah ta lura su Jamal sunfi sakewa sosai anan. Nanma sun jima sosai kafin su fito zuwa sashen Hajiya Ai'sha amaryar Baffan da suke kira da suna Ammi. Itace mahaifiyar su Haneef Safiyya, Abidah Jamal auta.        Mahaifiyar su Jamal ba mace bace mai yawan fara'a. Amma tanada son mutane itama. Dan ta tarbi Zinneerah ɗin da kulawa sosai, harma takai hirarsu tafiyin tsaho anan fiye da kowanne sashe. Basu fitoba sai da akai kiran sallar zuhur suka koma sashen Hajiya Iya data gaji da zuba idon dawowar tasu ma. ★★★         Lallai da gaske Shira's Family yayma Zinneerah daɗi. A cikin kwanaki huɗu kacal sai gashi ta saki jikinta da kowa, musamman ma su Bahijja dake ɗorata a hanya waɗanda bata da aminai sama dasu a gidan. Zata iya cewa shine gidan zama na farko data shigo bata fuskanci ƙiyayyar waniba a zahiri. Dan inma akwai masu ƙin nata sun danne a zukatansu basu taɓa nuna mataba.        Daɗin zama cikinsu ya matar da ita batun kwana biyu da akace zatayi ta koma. Abinda kawai ta kasa sakewa da shi shine kwana ɗakin da aka bata matsayin nata. Komai take a cikinsa a ɗararene. Gashi su Meenal basa shiga ɗakin sam. Ko zuwa sukai tana ciki sunfi yarda su jirata a falo harta fito..          A randa ta cika kwana na biyar suka koma makaranta. Ranar duk sai taji kuma babu daɗi. Amma janta a jiki da Hajiya iya keyi yay matuƙar ɗebe mata kewar su Little da ke damunta a rai tun zuwanta gidan. Tamkar kuma Hajiya iya ta shiga ranta sai gashima ta kira mata Mama a waya suka gaisa. sai dai su Sadiq duk sun wuce makaranta. Gwarancin Little dake wasa kawai take jiyowa. Tanason tambayar lafiyarsa tanajin kunyar maman Sadiq. Dan haka tai shiru tunda dai ALLAH yasa ta jisa ɗin.          Zinneerah na zuba ido taji ance ta shirya ta koma gida kodan karatunta sai taji tsit. A ranada ta cika kwanaki tara a gidanma Baffah yasa ta shirya Yah Saifudden ya kaita makarantar su Meenal da sunan sabuwar ɗaliba. Hakan ya bata mamaki dan babu wanda yay mata bayanin za'a canja mata makarantane. Garama Hajiya iya ta mata nasiha akan ta dage sosai karta bari su maidata baya. Tafi son karatunta da nasu Bahijja ya tafi dai-dai.      Zinneerah ba ƙoƙarine da itaba. Sai dai tanada naci akan abinda takeso. wannan ne ya taimaka mata matuƙa wajen amsa interview da akai mata duk da dai karatun da tayi a gidan Abba ya matuƙar taimaka mata. Da ace sanda ta baro Danya ne to lallai wannan haɗaɗɗiyar makarantar babu fashi aji ɗaya zasu maidata kuwa.       A yanzunma sunyi batun sai da ta koma js3. Saifudden ne ya roƙa alfarmar barinta a ss2 ɗin da alƙawarin zata dage insha ALLAH. Da yake maganace ta kuɗi kuma su ɗin sunada babban matsayi a makarantar yasa suka bar Zinneerah ɗin Ss2. cikin amincin ALLAH kuma aka kaita ajinsu Meenal. Zokaga farin ciki da murna lokacin da aka rakata ajin a zuwan sabuwar ɗaliba. Malamin na fita Jamal ya fita gaban aji ya sake gabatar musu da Zinneerah matsayin sister ɗinsu ce. Hakan yasa ta samu tarba mai ƙyau daga ƴan ajin dansu Jamal ƙurayene sosai akan ƙoƙari.       A ranar kam dai babu abinda Zinneerah ta fahimta a wannan aji. Sai ma neman ruɗewa da tsorata da tayi ganin yanda tsarin karatun nasu yake. Sam babu maganar hausa a ajin ma balle ga malami. Turancine da larabci kawai ke tashi.     Fahimtar yanda ta shiga ruɗanine ya saka su Bahijja kwantar mata da hankali akan karta damu zata iya itama ai wataran. Badan ta yarda da hakanba tai shiru, amma har cikin ranta a tsorace take kam. Sai dai kuma tana fatan iyawar kodan wasu abubuwa masu yawa dake cimata rai da zuciya a tarihin rayuwarta. Itama tanason ta zama wani abu kodan wani dalili nata dake ɓoye mata a cikin rai game da samuwar ɗan da batasan wanene ubansa ko yanda aka samar da shi ba.      Bayan tasowarsu ne Hajiya iya ta kira mata Mama a waya suka gaisa. A take ta labartama Maman komai har tana hawayen farin ciki dana kewarsu. Dan tasan dai tunda har aka sakata a makaranta da wahala ace zata koma zama wajen Mamanta sai dai idan anyi hutu. To koba komai dai ai tamayi nesa dasu Sakina iyayen gorin gida dana arziƙi. Kuma karatunta zaifi inganci anan fiye dacan duk da shima Abba bazata taɓa gajiya da yaba masaba a rayuwarta har ƙarahen numfashinta kuwa. ★★★      Kamar da wasa sai ga rayuwa ta fara canjama Zinneerah alƙibla. Dan kuwa dai da alama *_MAKAUNIYAR ƘADDARA_* data barota da Danya na neman zame mata ƙyaƙyƙyawar nasara mai abubuwan fata ga duk wanda ya tsinci kansa koda a makamancin irin tata rayuwarne. Yau ita Zinneerah mai tallar riɗi da gyaɗa da ɗanwake ce a wanann matsayin. Ita da kashin gidansu ma ya fita matsayi da daraja wajen Inna dasu Yaya Karima. Lallai ta yarda da yawan ƙaddara tsanine na nasara gamai haƙuri insha ALLAH. Sai dai ya danganta ga yanda ƙaddarar tazo maka da kuma yanda kai ka amsheta kai haƙuri da ita.      Sosai a kallo ɗaya zakaga ɗumbin canjin data samu. Jikinta ya murje matuƙa, ƙyawunta da nutsuwarta na sake fitowa gareta. Yayinda cikakken budurci ke sake huda gaɓɓanta da surarta. Ta kuma dage da naci akan karatu da taimakon su Bahijja duk da sukan sha wahala wani lokacin kafin ta gane abu daƙyau.      Zuwa yanzu a hankali su Meenal na jan ra'ayinta kwana sashensu fiye da ɗakinta. Wani lokacin kuma wajen Hajiya Iyama take kwana musamman idan ta tashi batajin daɗin ƙafarta haka ko jikinta. Tsakaninta da ɗakin nata bai wuce shiga tai wanka sai kuma gyarawa. Sai randa ALLAH kuma ya ƙaddara zata kwana a cikinsa.                 A kwana a tashi babu wahala wajen UBANGIJI sai gasu Zinneerah an cinye hutun zangon farko a tsadajjiyar majaranta. Kwanansu biyar dayin hutu Baffah ya haɗa mata shatara ta arziƙi Yaya Haneef ya kaita gida wajen mahaifiyarta. Da dasu Jamal zasu tafi Baffah yace su bari sai ta tashi dawowa sai suje su ɗakkota tunta dai kwanaki goma zatai kacal ai.      Haneef ya shiga sun gaisa. Sai dai bai jimaba ya fito ya tafi, dan makaranta zaije kuma yace yanada jarabawane. Amma daɗin tarbar daya samu ga Mama yace zai dawo. Bai iske su Sadiq gidaba suna islamiyya. Little kuma yana barci abinsa.        Kwatanta irin farin cikin da Zinneerah ta tsinci kanta a ciki ɓata lokacine. Amma tsabar kewar Mama da tayi harda rungumeta. Little kuwa data shiga ta samu yana barci yasha kisses, harda hawayenta ganin yanda ya ƙara girma a watanni uku kacal data ɗauka bata ganshiba. Wani irin son yaron da ƙaunarsa na ƙara tasiri a ranta alamun hankali ya fara game jikinta a yanzun fiye da da.      Lokacin kuwa data shiga gaida Maman Sakina ai baki ta saki tana kallonta tamkar sokuwa. Hakama dasu Luban suka dawo gidan daga makaranta dan suna jarabawa sai da ƴaƴan cikinsu suka hautsina da ganin canjawar Zinneerah ɗin a ƙanƙanin lokaci. Duk da sunsan dama ƙyaƙyƙyawa ce a yanzu kam ƙyan nata yafi fitowa da armashin gani gamai kallonta.      Itako sosai ta nuna murnar ganinsu cike da sakewa alamar yanzu akwai banbanci da da kenan. Dan babu wannan yawan duƙar dakan da ɗari-ɗari tattare da ita. Miskilancin nedai kam akwaishi saima abinda yay gaba.      Sai da suka shiga ɗaki sukaita gulma da zaginta wai dan taje gidan masu kuɗi kanta ke rawa tana musu shan ƙamshi. Duk da har yanzu basusan taka maimain a inda takeba. Har uwarsu ba sani taiba duk bin ƙwaƙwƙaafinta. Koda ta tambayi Abba cayay mata dangin mahaifanta ne suka ɗauketa dama basusan ta baro gida baneba zuwa nan shiyyasa. Daga haka kota masa maganar sai yace taje ta tambayi maman sadiq ɗin mana. Daga haka yake kashe bakin son gulma da tsugudidi.       Maman halima kuwa taji matuƙar daɗi da canjin da Zinneerah ta samu. Koba komai itama ta samu ingantacciyar rayuwa bisa ga zaluncin Asabe ai.      Dawowar su Sadiq aka sake kafa sabuwar murna da bidiri har takai ga tashin Little. Sosai girman nasa ya sake bama Zinneerah mamaki dan bakace ɗan shekara ɗaya da rabi bane. Da alama akwaishi da garin jiki kam. Yanda yaga su Aliyu nane da ita shima sai ya nane natan yana gwarancinsa dan maganar tasa bawani ganewa sosai akeba garama maman sadiq.      Ganin ƴan uwanta yay mata daɗi duk da bata mance dasu Jamal ba suma. Kullum ma babu fashi sai tayi waya dasu ta wayar Hajiya Iya ko cikin wayar ƴammatan gidan............✍       *_1~UBAYD MALEEK_* _By MamuhGee_ *_2~ MAKAUNIYAR QADDARA_* _By Billyn Abdul_ *_3~ DALAAL_* _By Miss Xoxo_ *_4~ MABUDIN ZUCIYA_* _By Hafsat Rano_ *_5~ ALKIBLA_* _By Safiyya Huguma_ Zaku samu wainnan duka biyar din akan farashin 700, Guda 5👉700 Guda 4👉500 Guda 3👉450 Guda 2👉400 Guda 1👉300 Zakiyi payment dinku cikin account dinmu dake rubuce na👇👇👇👇 *_0225878823 HAFSAT KABIR UMAR GTBANK_* Saika tura shedar biyanka ta wannan numbern👇👇 *08085405215* Idan kuma katin wayane zaka turo da MTN card ta  wannan numbern👇👇👇 *09032345899* Mungode *_TM ZAFAFABIYAR🔥_* *_TYPING📲_* *_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_* *Page 19* _________________________ *Assalamu alaikum warahmatullah, shin kinaba amfani da turaren gashi a matsayinki na mace data amsa sunanta idan amsarki aa toga dama tasamu *awwaba scent* *tazomaku* *da turaren fesawa a gashi natural 100% organic *wanda akahada rose water da essential oils tripped action gashi yy kamshi yay kyali kuma moisturiser at *the same time ba anan abun yatsayaba duk wanda yy order zaahada masa da freshener kala hudu ta daki *ta bandaki ta Mopping da turaren wanka a kan kudi 3,000 kacal indai q cikin watan September dinnna ne daganan kuma zasukoma *normal price dinsu, hakanan turarukqn wuta da humra dinmu anyi masu ragi duk me bukata se nememu a 08034236800 ta what's app kokuma ya ziyarci shafinmu a instagram* @turare_by_awwaba mungode* ______________________ *Page 19* ...........Sosai zaman hutun nan yayama Zinneerah daɗi. Dan koba komai shaƙuwa sosai ta sake shiga tsakaninta da Little, dan yanzun taɗan rage yin kawaici akansa. Hakama ƙannenta koda yaushe suna nane da ita.       A randa ta cika kwanaki goma sai ga su Jamal babu zato wajen sha ɗaya na safe. Lokacin suna shirin fita gidan sunan ƙanwar Maman Halima. Duk da taso taje gidan sunan sai zuwan nasu ya kauda son fitar, ta shiga murnar ganinsu. Su maman Halima kam dake goye da Little suka tafi bayan sun gaisa dasu Bahijja iyayen rawar kai.     Sukam babu ruwansu da wata baƙunta. Dan sakin jikinsu sukai tamkar a gidansu. Sai hakan yayma maman sadiq daɗi sosai, dan koba komai hakan girmamawace suka nuna mata. Maman Sakina da yaranta kam sai suka shige ɗaki suna leƙensu ta Window da gulmar a ina su mmn sadiq ɗin suka samo yaran ƴan gayu haka?. Basu da mai basu amsa, dan haka suka cigaba da habaice-habaice da sukar mmn sadiq ɗin harma dasu Meenal da basusan da zamansu a gidanba. Harda cewa kodai a gidansu Zinneerah ke zaune aikin wanke-wanke yanzun?. Sai suka yarda a haka duk da suma sun san faɗane kawai danjin daɗi. Dan Zinneerah batai kama da wadda taje aikatauba. Su Jamal ma sun sami rabon nasu zagin sosai, dan koda sukazo suka iske Maman sakina a tsakar gida dasu Luba ko kallo basu ishesuba. Sai mmn halima data tarbesu da fara'a suka gaida cike da girmamawa. Hakanne ya sake baƙanta ran mmn sakina taja ƴaƴanta suka shige ɗaki.       Wainar filawa Zinneerah tai musu kamar yanda sukace suna buƙata, sai da sukaci suka ƙoshi Abba ya dawo gidan bayan la'asar suka gaisa sanan driver yazo ya kwashesu harda Zinneerah da taso yin sallama da Little da sauran yaran, dan sanda maman halima ta wucene da shi yana barci, ko ganinsu su Bahijja ma bayi sukaiba. To da yakema ba sanin labarinsa sukaiba basu kawo komai a ransuba sun zatama ɗan mmn halima ɗinne duk da dai basuga fuskarsaba.        Sosai Hajiya iya dasu Yah Moos'ab suka nuna farin cikinsu na dawowarta. Tare da faɗi mata sunyi kewarta kowa a gidan. Cikin ƴar dariyarta tace, “Nima nayi kewarku ai, wani lokacin har mafarkinku nakeyi”.        Sunji daɗin maganarta har cikin ransu, dan itama suna mata kallone na ɗaya daga cikinsu bawai wadda tazo cin arziƙi gidansu ba. Moos'ab da bai cika yawan maganaba shi dama yaɗan ɗage gira yana gyara kishingiɗar da yay a kujera da faɗin, “Ni ba yarda nai dakeba fa yarinya”.      A hankali Zinneerah ta ɗago manyan idanunta farare tas ta zuba a kansa, irin kallon da yake matane ya sakata saurin maida nata ƙasa tsigar jikinta na tashi, ba yaune karan farko da Yah Moos'ab ɗin ke mata irin wannan kallonba, shiyyasa a mafi yawan lokuta bata wani cika sakewa da shiba sosai. Kasa bashi amsa tayi, hakan yasa Saifudden kwashewa da dariya yana faɗin, “Wataran dai zata fashe”.        “Minene zai fashe?”. Cewar Haneef dake a kusa dashi yana latsa waya.      Saifudden yace, “No jaridar mai tsadace, duk maiso ya tanaji kuɗi akwai ranar da zan saida muku”.      Abidah ce tai dariya tanama Saifudden alamar jinjina. “Ai Yah Saif nima na daɗe da harbo jirgin, kasanfa idanuna sun iya gane-gane nima, duk randa suka tashi saya ka nemoni zan ƙara da nawa rahoton”.      Tsam Zinneerah ta miƙe zata bar wajen, dan haka kawai ta tsargu da zancen nasu, tanaji a ranta kenan suma duk suna sane da Yah Moos'ab ɗin komi?.       “A'a, auta ina zuwa?”. Cewar Safiyya da sauri.       “Im ihm Aunty Safiyya zanje cikine nayi wanka”.      Da sauri Ni'ima tace, “Wankafa? Ba shigowata Granny ke faɗin kina ciki kina wankaba Auta (Mafi yawan lokaci haka suke kiranta auta).       Kasa magana tai, hakan yasa Saifudden kwashewa da dariya yana raira waƙa. Duka Moos'ab ya kai masa. Yay saurin wuntsilowa a kujerar yana cigaba da dariyarsa. Da sauri Zinneerah tabar wajen ranta fal tsoro. Ɗakin da har yanzu ta kasa sakin jiki da zamansa ta shige tare da faɗawa saman gadon a karo na farko. Tai ɗan murmushi dajan filo ta cusa kanta a ciki. A ranta kuwa rayawa take itakam karsu Yah Saifudden su jawo mata rigima. Ina ita ina soyayya da waninsu bayanma duk kallon yayu take musu itakam. Wannan zance ai da girma yake idan har yazo a yanda zuciyarta ke hankaltar da ita game da take-taken Yah Moos'ab ɗin.       Haka ta kasance cikin dogon tunanin da har barci mai nauyi yay awon gaba da ita batare data saniba. Harsuka gama hiratsu kowa ya miƙe zuwa makwancinsa basu sake ganintaba. Hajiya Iya kam dama ta kwanta tuni saboda maganin mura da tasha, kuma dama ita ba'a doguwar hira da ita, tanada saurin barci. Wani lokacinma sai jikokin nata suzo su ƙaraci shirmensu a sashen bata saniba. Dan kullum nanne wajen hiratsu sai dai idan yayansu na gari kam babu sakewa, duk da suna zuwa a hakan.              Sosai Zinneerah taji daɗi barci akan wannan gado da yau ya zame mata na farko, dan ko fitsari bata farka yiba yau saboda daɗin barci. Sai kiran sallar farko na asuba ta buɗe idanunta da ƙyar tana karanto ɗaya daga cikin addu'ar tashi daga barci. "الحَمْدُ لله الذِي أَحْيَانَا بَعْدَ مَا أَمَاتَنَا وَإِلَيْهِ النُّشُور" Alhamdu lillahil-lazee ahyana ba'ada ma amatana wa-ilayhin-nushoor.        Sai da ta bada ratar kusan mintuna uku bata motsaba dan idanunta su ƙara saki sosai sannan ta tashi zaune tare da zuro ƙafarta ta sauka a gadon. Tayi mamakin ganin an kashe mata wuta da lulluɓa mata bargo, sai dai tasan bazai wuce ɗaya daga cikin su Aunty Safiyya ba. Wanka ta farayi da ɗauro alwala ta fito. Bayan ta gabatar da nafila raka'a biyu ta ɗakko AL-QUR'ANI ta fara duba inda akai mata ƙari jiya a islamiyyasu data koma zuwa ta anguwar su mmn sadiq.     Tana zaune a wajen har akai salla. Bayan an idar tai Azkar kamar yanda Hajiya Iya ke maimaita mata muhimmancin yinta a kowacce safiya da maraicen duniya. Sai da ta kammala gari yay haske ta miƙe ta gyara ɗakin tsaf kamar yanda ta saba, ta saka kayan ƙamshi ta fice zuwa taya su baba Rahi aiki. Amma sai da ta fara shiga ta gaida Hajiya Iya da mura sannan.         Sai da suka kammala komai tsaf suka shirya tebir sannan ta koma ɗakin domin yin wanka.        Sanin ba kowa ke shigowa ɗakinba sai Hajiya iya yasata fitowa kanta tsaye da towel. Sai ƙarami da take ƙoƙarin naɗe kanta data wanke a ciki. Wani irin mugun tsargawa zuciyarta tayi dai-dai lokacin da take fitowa daga ɗan lungun da toilet ɗin yake. Tsabar ruɗani da firgici batama san ta saki towel ɗin da take ƙoƙarin ɗaurawa kantaba a ƙasa....      Ƙyaƙyƙyawan matashin dake zaune hakimce a bakin gadon ƙafa ɗaya kan ɗaya waya manne da kunnensa ya ɗago dara-daran idanunsa masu cikar gashi da haske yana kallonta da alamun tsantsar mamaki a cikinsu. Hannunsa yakai bisa kwantaccen sajen fuskarsa da babu yawan fara'a a kanta ya shafa ɗan guntun sakewar dake kanta na ƙoƙarin gushewa gaba ɗaya. Sauke hannun daya shafa fuskar yay yana gyara ɗayan dake riƙe da wayar da yakeyi har yanzun yana janye idanun nasa daga kanta yana furzar da wani irin huci daya saka Zinneerah dawowa hayyacinta ta ƙwalla ƙara dan duk zatonta aljanine kawai ya shigo mata, shiyyasa tai sumar wicin gadi.       Gaba ɗaya ya saki wayar a ƙasa, yay saurin saka tattausan hannunsa ya toshe kunnuwansa yana runtse idanunsa da ƙarfi.            Kusan rige-rigen shigowa ɗakin akai tsakanin Hajiya Iya da Baba Rahi.  Su duka kan Zinneerah sukayi dan babu wanda ma hankalinsa ya kai kansa. Hajiya Iya ta kamo Zinneerah da alamu suka nuna bata cikin hayyacinta jikinta. “Ya ALLAHU, Zinneerah! Zinneerah kinga buɗe idonki gani tare dake. Miya faru? Ko wani abune ya tsorataki?. Rahi kawo ruwa a bata dan ALLAH da sauri”.        Fita Baba Rahi tayi da sauri sai gata da ruwa ta dawo. Amsa Hajiya iya tai ta bama Zinneerah daketa faman ɓoye fuskarta a jikin Hajiya Iya nata jikin na rawa dan ta tsora sosai musamman data sake kallon fuskarsa yanzu hankalinta ya sake tashi. Kaɗan ta sha dan bata tare da nutsuwar shansa. Hannunta na karkarwa ta sake ƙanƙame Hajiya Iya  ta nuna inda yake zaune kunnensa toshe, hakama idanunsa a rufe har yanzu.        “Aljani, wlhy Aljanine Granny”. Tana maganar hawaye na ziraro mata kamar an buɗe fanfo.        Daga Hajiya iya har Baba Rahi turus sukayi suna kallonsa suma fuskokinsu ɗauke da mamaki musamman Baba Rahi da sam bataga shigowarsaba duk da tana kitchen tana wanke-wanke. Sai dai tabbas taji baƙon ƙamshin turare datai tunanin ko cikin samarin gidanne suka fara shigowa yin breakfast.          Fuska hajiya iya ta haɗe da kamo hannun Zinneerah dake nunashi har yanzun ta riƙe, ta sake kwantar da ita a jikinta tana shafa mata baya da sauke ajiyar zuciya. “Kinga Zinneerah kwantar da hankalinki ba aljani bane mutumne”.      “Wlhy ba mutum bane Granny, aljanine, dan aljanine kawai zai iya buɗe ɗakin dana rufe kuma na cire key ɗin kingansa acan na ajiye......”        “Shiii, ya isa kiyi shiru, Yayankune ba aljaniba, yanada key a hannunsa shiyyasa ya shigo”.        Kafin Zinneerah ta samu damar cewa wani abu Baffah ya shigo ɗakin saboda jiyo muryar Zinneerah ɗin dake magana tana kuka, sai kuma ya jiyo hajiya Iya itama.       “Lafiya kuw....” ya kasa ƙarasawa saboda sauka da idanunsa sukayi akansa shima. A take fara'ar fuskar Baffah ta ɓace ɓat. Saurin duƙawa Baba Rahi tai tana gaishesa. Bai iya amsa mataba sai hannu kawai ya ɗaga mata. hakanne ya sakata tashi da ta fice a ɗakin.            Hijjabin Zinneerah na salla hajiya iya ta jawo ta saka mata, batare da tace komaiba ta kama hannunta suka fice daga ɗakin. Bayansu Baffah yabi shima batare da yace uffanba.         Kansa dake a duƙe tun haɗa ido da sukai da baffa ya ɗago a hankali yabisu da kallo har suka fice gaba ɗaya. Sake lumahe idanun yay da furzar da huci mai ƙarfi tare da kai hannunsa ya dafe kansa.               Tsaye cirko-cirko suka iske yaran gidan da suka fara shigowa sashen. Dan har sunji labarin zuwan Yayan nasu gidan a bakin Yaya Khalipha da sukazo tare.       Wucesu Hajiya Iya tayi riƙe da hannun Zinneerah dake sharar hawaye ɗakinta. Baffah kuma ya nifi dining shima fuska a ɗaure.      Baffa mutum ne mai barkwanci ga yaransa, amma idan ransa ya ɓaci dolene kowa ya shiga hankalinsa. Da sauri Safiyya ta taso inda yake ta fara ƙoƙarin haɗa masa abincin gabansa. Hakan yasa suma sauran yaran nufo dining ɗin duk suka zauna. Hajiya Iya ce ta fito daga ɗakinta tana ƙwalama Jamal kira. Dai-dai yana ƙoƙarin zama danshi shigowarsa ma kenan sashen baisan mike faruwa ba.       “Na'am Granny ”. Ya amsa yana maida kujerar daya jawo tare da juyawa gareta.      “Ka shiga ɗakin can ka ɗakkoma Zinneerah Uniform ɗinta da jikkarta”.       Cikin rashin damuwa da abinda tace ɗin, yace, “Okay maa”.      Yanda ya nufi ɗakin kansa tsayene ya saka sauran ƴan uwansa binsa da kallo. Bahijja ta saka hannun ta rufe bakinta jin dariya na neman kufce mata. Meenal kam ƙasa tai ƙarƙashin tebir tamkar zata gyara wani abu tayi tata.        “Oh ni Jamal ni za'a saka na ɗakkoma ƙanwata abu. yau yarinyarnan zatasha ƙwanƙwashe a kai kuwa a class na rantse”. Yay maganar yana tura ƙofar ɗakin da shiga kansa tsaye.      Wani wawan birki yaja yana waro idanu waje ganin wanda baiyi zatoba tsaye yana ƙoƙarin zame rigar saman suit ɗinsa. Cikin rawar baki yace, “Bar... Ba.. Barka da zuwa Yayanmu. Kazo lafiya? An barosu lafiya? Ya hanya?”.      Yanda ya jero gaisuwar kawai zaka fahimci a kiɗime yake. Shiko da ake gaidawar kallo ɗaya yay masa ya janye idanunsa batare daya amsa ko ɗayaba a ciki, dan gaba ɗaya ransa a dagule yake. Yasan shiɗin mai laifine ga mahaifinsa da kakarsa. Amma yayi zaton Baffa ya yafe masa kamar yanda ya roƙesa tun a waya kafin ya taho....      Da sauri Jamal ya juya zai fice a ɗakin....           “Mi kake buƙata?”.    Nutsatstsiyar muryarsa mai kama data rowa ta bayyana cikin kunnuwan Jamal. Tamkar zai fasa kuka ya juyo garesa. “Yayanmu Granny tace nazo na ɗaukama Zinneerah Uniform ɗinta zamu wuce school”.       Uffan baice da shi ba, sai ma towel daya ɗauka a akwatin da yazo dashi ya nufi toilet abinsa. Jamal na ganin ya shige ya sauke nannauyar ajiyar zuciya, tare da nufar Uniform ɗin Zinneerah dake ajiye a bakin gado ya ɗauka sauri-sauri tare da schoolbag ɗinta da takalma ya fita da gudu.         Shikam koda ya shiga toilet ɗin kallon tsaf ya shiga masa, dan a rayuwa ya tsani ƙazanta. Jin ƙamshin toilet ɗin gaba ɗaya ya canja daga nashi ya sakashi cije baki a ransa yana raya hukunci da zaima yarinyar nan da har idonta yay tsaurin shigo masa ɗaki tai wanka. Gamsuwa da tsaftar bayin ya sakashi ƙoƙarin ajiye towel ɗin hannunsa a bazata idonsa ya sauka akan B&P ɗin Zinneerah data shanya. Kauda ido yay yana wani cizar baki da rinmtse idanu da ƙarfi, a fusace ya rataye towel ɗin ya fito yana ƙwala kiran sunan Jamal.        Wayam babu Jamal a ɗakin alamar ya gudu, ya riƙe ƙugunsa da hannaye duka biyu idanunsa na canja launi saboda haushi. Ƙofa ya nufa kamar zai fita sai kuma ya fasa ya dawo da baya yanayin ƙwafa. Haka ya haƙura ya gudanar da dukan uzirinsa, sai dai sau goma idonsa yakai ga kayan sai sun sami tsarabar harara talatin da tsaki. Sai wani faman yamutsa fuska yake tamkar yau ya fara ganin irinsu.      Oho ita mai kayanma batasan yanayiba. Dan tanacan tayi shirin makaranta bisa umarnin Hajiya iya. Sai dai ranta cike yake da ruɗani. a kuma matuƙar kiɗime take da ganin wannan fuskar. Tasata gaba Hajiya Iya tai suka fito dining domin karyawa. Baffa ta fara gaidawa sannan su Haneef dasu Ni'ima. Ta bama Meenal da bahijja hannu sukai musabaha sannan ta zauna.      Hajiya iya kam da suka fito tare abinci ta fara shiryawa. wanda kowa yasan na yayan nasune, shiyyasa duk suke addu'a a ransu kar mutum yazam shi za'a aika yakai masa.     Ganin Hajiya iya ta zauna bayan tagama yasa kowa ke ƙoƙarin ganin ya gama ya fita, Jamal ne ya fara miƙewa yana kallonsu Zinneerah. Guys kutashi muje kunsan yau Sir Mansur ne damu a period ɗin farko”.       Daga Meenal har Bahijja sun ramfo saurin nasa. Dan haka suka miƙe da hanzarinsu suna faɗin, “Hakanefa ka tuna mana”.       Miƙewa Baffah yayi yana goge bakinsa da tissue. Ya ɗan kallesu ya kauda kansa. “Kumuje sai mu saukeku dan zan shiga makarantar taku ne”.       Sosai daɗi ya kamasu. Duk suka washe bakuna suna kashema juna ido najin daɗi yau tare da Baffahnsu zasuje school. Duk da dama yakan musu haka lokaci zuwa lokaci dan kawai ya sakasu farin ciki.        Zinneerah dai duk jikinta a sanyaye yake har yanzu. Babu abinda ke mata gizo a zuciya sai ƙyaƙyƙyawar fuskarsa mai cike da kwarjini da kamalar cikar haiba. Sallama sukaima Hajiya iya sukai waje suna ɗagama sauran yayyensu hannu.              Cikin raɗa-raɗa Saifudden yake cema Moos'ab mumafa mu tashi mu fece dan yau gidanan akwai ƙura tsakanin Granny da Yayanmu. Wannan faɗan kuwa yafi ƙarfin ganinmu koda ta bayan katanga ne”.     Miƙewar kuwa duk sukayi sunama Hajiya Iya dake kicin-kicin da rai sallama. A dai-dai wannan lokacin Khalipha ya shigo falon da sallama. Kansa ƴammatan sukai cike da ihun murna ƙasa-ƙasa dan gudun kar Yayansu yajiyosu. Fuskarsa washe da murmushi kuwa ya buɗe musu hannayensa. Sai dai harar da Hajiya iya ta balla masa ce ta sakashi maida hannun ya naɗe a ƙirjinsa yana dariya. Duk da haka sai da sukaje suka ɗan fabu da jikinsa suna jera masa kalaman kewarsa da sukayi.      Gudun samun matsala yasa sukai masa sallama suka fice su dukansu. Shi kuma ya ƙarasa ga Hajiya iya. Ɗan rungumeta yayi ta gefe yana faɗin, “Oh my sweetheart, i miss you so much”.        “Oh ai nazata kaima ka koyo halin turawanne ka fara ƙyama da gudun danginka”.        “Kai! Granny ni na isa. Babu wani ɗaukaka da ALLAH zai mana a duniya mu kyamaceku ai. Dan kune kuka nunamu ga duniyar harta san da zamanmu”.      Cikin taɓe baki tace, “Kai kasan wannan ai. Banda wasu bauɗaɗɗu masu bahaguwar rayuwa”. Ta ƙare maganar da harar gefenta tana ƙara ɗaure fuska.       Juyawa Khalipha yay da sauri saboda jin ƙamshinsa, ya kuma tabbatar da shi Hajiya iya ke wannan zancen. Ilai kuwa shine ke takowa inda suke, kuma komai da Hajiya Iyan ta faɗa ya shiga cikin kunnuwansa. Amma yay tamkar bai jiba sai ma kujerar daya ja ta dining ɗin ya zauna.      Murmushi Khalipha yay yana dubansa. “Barka da fitowa Yayanmu. Yanzu nake batun zuwa na fiddoka kayi breakfast dan nasan kana jin yunwa sosai”.        Wani ɗan murmushi yayma Khalipha ɗin yana lumshe idanunsa masu yalwar gashi da cikar gira. Khalipha yasan halin kayansa. Dan haka cike da rashin damuwa yace, “Mi za'a haɗa maka?”.      Kafin ya bashi amsa Hajiya iya ta amshe da faɗin, “Ni ban girka abincina da shi ba. Sai yayi waya su ƴan can London ɗin ko Morocco su kawo masa yaci”.        Ƙaramar dariya Khalipha yayi da kai hannu ya fara buɗe kwanikan dake shirye akan tray wanda ya tabbatar nasu ne. Shiko gogan hannayensa kawai ya harɗe a ƙirji yana kafe Hajiya iya da kallo.       “Bar kallona malam karka cinyeni da waɗanan shu'uman idanun naka  lokacin mutuwata baiyiba”.        A karo na biyu ya sake sakin lallausan murmushi yana kauda kansa gefe. Cikin magana ƙasa-ƙasa yace, “Bazata canjaba kullum”.       “Anƙi canjawar dan ubanka”. Hajiya iya ta faɗa tana zabga masa harara da masa daƙuwa.      Bakinsa yaɗan taɓe da ɗaukar wayarsa ya hau latsawa kamar bashine ya takalo rigimarba. Khalipha dai abinci yake haɗa masa yana dariya, dan inhar Yayansu na gidan nan irin wannan rigimar shi da kakar tasu ba sabon abu bane. Sai suyi sau goma a rana su shirya. Hakan kuma bazai hana gobe su ɗora daga inda suka tsayaba.      Masifa Hajiya Iya ta cigaba dayi, inda take shiga ba nan take fitaba. Shi dai yay mata shiru yanata cin abincinsa hankali kwance. Danshi mutum ne da baya wasa da abinci. Cinsa yake bil haƙƙi da gaskiya a duk lokacin daya samesa. Musamman daya kasance mutum mai tsananin son abincin Nigeria ma.        Hajiya iya dai batai shiruba sai da tayi mai isarta sanann ta mike tabar wajen. Dan Khalipha ne keta faman bata haƙuri, shiko yayi kamar babu shi a wajen sai cin abinsa yakeyi.      Bayanta yabi da kallo harta shige. Ya maido idonsa kan Khalipha, “Besty matarnan bazata taɓa canjawaba da wannan faɗan nata?”.         Dariya Khalipha yake sosai. “Yayanmu kaimafa mai laifine, bai kamata kai mata shiruba, amma ka barni da bada haƙuri”.       “Bazaka gane bane, itafa idan kana bata haƙuri kamar tunzurata kakeyi. Bakinta ko gajiya bayayi”.        “Munafiki, ai inajinka”. Suka jiyo muryar Hajiya Iya da basuji fitowartaba a bayansu.       Dariyace taso kufce masa. Dan haka ya miƙe da sauri yana goge bakinsa da tissue yabar falon gaba ɗaya. Da alama gaida matan gidan zaijeyi.           Harya gama ficewa bai daina jiyo masifar Hajiya iya da dariyar Khalipha ba. Ya ɗan dafe kansa yana furzar da huci da faɗin, “Madam Problem”............✍        *_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 _Na Safiyya Huguma_ *_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖 _Hafsat Rano_ *_★ DALAAL_*💝 _Na Miss xoxo_ *_★ UBAYD MALEEK_*💓 _Na Mamu gee_ *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 _Na Bilyn Abdull_ Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 *_08085405215_* IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   0903 234 5899 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 *_TYPING📲_* *_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_* *Page 20* ______________________ *Mg's herbal whitening black soap* Duk wacce batayi anfani da sabulunnan ba anbarta abaya acan karshen bayama kuwa duk Mai tantama akan sabulai nagyaranjiki cewa basa Aiki toh yacire mg's domin kankat ne insha Allah babu Wanda yayi anfani dasabulunmu yace baiyi ba koyaushe mg's sai sanbarka amare da uwargidaye hardama yanmata kuhanzarta kusamu naku ba karya domin bama cika Baki kugwada kubada labari da bakunanku sabulu daya tamkar dubu wadandama basasan using cream sabulun mg's herbal whitening black soap yawadacemuku jikinku zaiyi kyau koyaushe kukasance clean cikin kamshi Kuna glowing koda bakusa turare ba🤗 Kayanmu bana bleaching bn organic ne sunagyarajiki fiye da tsammaninku zaifiddomuku da ainihin natural beauty dinkine Wanda yagwada shi zaitabbar amare kuyi kokari kumallaki mg's domin baruwanku da zuwa adirjemuku jiki zakuga yanda fatarku zata dinga walwali Ina masu pimples Tabo(spot) Sunburn dama dukwani matsalar fata kuyi kokari kunemi soap dinnan before 2weeks zaisharemuku hawaye kuzama abun kwatance Sister's masu nankarwa kuma kunemi soap dinnan Yana rage nankarwa sosai🧖🏻‍♀️duk me shakku tayi kokari tagwada mg's insha Allah bazakiso rabuwa dashi ba Akwai maisa haske Amma kayanmu nafada bana bleaching bn zaifiddomiki d ainihin halittarkine yagoge dukkan dattin jiki Akwai Kuma Wanda zaimiki maintaining skin dinki yasaki fresh fatanki tazama kalar hutu Pls bamacika Baki you HV to try it and see for yourself 100%tested nd trusted Soap price:3k Location:kaduna buh munaturawa ko Ina Amma delivery is not free Maiso kindly message 08062991549 Call 08064532391 Note:Babu inda zakusami mg's herbal whitening black soap sai a number dinnan bairiga yakai market b inyakai we will let you know buh as for now wnn numbern ne kawai🙏 Maiso yahanzarta before yaji sold out akwaisu available now insunkare you HV to wait akawo so maiso yahanzarta🙏adade anayi sai gsky🤭🤝 Mg's skincare _____________________ *Page 20* ..........Ƙarfe biyar da rabi motar dake ɗakko su Zinneerah makaranta ta shigo harabar gidan. Kamar yanda ta fita gidan da damuwar baƙon dasu Jamal ke kira Yayansu haka ta dawo da ita a rai. Babban damuwarta ya ganta daga ita sai guntun towel a jiki. Gashi yanda taga fuskarsa da yanda su Meenal ke labarinsa tasan ba kirki zaiyiba sam, sai kuma wani abu mai kama da almara da take hangowa, wanda ƙwaƙwalwarta sam ta kasa ɗauka.         Kamar kazar da ƙwai ya fashema a ciki haka ta nufi sashen Hajiya iya tana mai addu'a a ranta ALLAH yasa baya nan. Koda tazo ƙofar falon sai da ta tsaya tai addu'a sannan ta shigo bakinta da sallama. Da sauri taja birki a taku huɗu, dan tun sakko ƙafarta ciki hancinta ya shaƙo mata mayataccen ƙamshin turare. Bata kawo a ranta falon yakeba idanma shine, sai da ta ƙarasa shigowa sosai idanunta sukai gamo maiban ruɗani, dan a yanzune ta sake samun damar yimasa kallo mai ƙyau.       Zaune yake bisa kujera 1seater dake facing kofar, ƙafarsa ɗaya kan ɗaya. Hajiya Iya na zaune kujerar gefensa tana dama fura. Sai wanda bataga fuskarba saboda juya mata baya da yayi. Har cikin ranta taji daɗin samunsa bashi kaɗaiba duk da bataso ganin nasaba ma gaba ɗaya.        Sallamarta Hajiya iya ta amsa fuska ɗauke da murmushi take faɗin, “Ƴan makaranta an dawo?”.        Cike da ƙarfin hali Zinneerah ta sakima Hajiya Iya murmushi da faɗin, “Eh Granny barka da yamma”.        “Barka dai Inno na, da alama yau kam an dawo da yunwa naga kinyi zuru-zuru?”.        Murmushi tayi batare da tace komaiba. Ta ɗan saci kallon inda yake zaune idonsa a wayarsa dake hannunsa yana latsawa tamkar baisan da shigowartaba. Sai dai abinda bata saniba cikin abinda baifi sakkani ashirinba ya gama ƙarema shigar Uniform ɗin jikinta kallo. Skirt ne iyakar ƙwauri pink color. Sai farar shirt dataji guga da baby hijjab fari daya tsaya mata iya ƙirjinta shima dai a gogen yake. Sai farar safa data rufe ƙwaurin nata da farin takalmi. Bayanta goye da school bag ɗinta data saki hannunta guda. Babu mai cewa Zinneerahn danya ce data taɓa rainon ciki harta haifesa yake gudu ko ina da kafarsa a halin yanzun. Baka iya hango komai tattare da ita sai zallar ƙuruciya da jin daɗin rayuwa na canjin data samu cikin ƙanƙanin lokaci.          “Yayanmu barka da yamma”. Ta faɗa ciki-ciki tsabar fargaba da tsoron dake mamaye da ita. Harta fidda rai zai amsa sai taga ya ɗaga mata hannu alamar amsawar kenan.      Gaba tai zata wuce, batare da ta gaida ɗayan wanda bata ganin fuskar tasa ba. A tunaninta ko shi baisan da shigowarta ba. Sai da taɗan gitta su taji ashe waya yake amsawa. Numfashi ta sauke da nufar ɗakin Hajiya Iya da saurinta, dan bata fatan abinda zai sake tsaidata a wajen. Ajiyar zuciya ta sauke a hankali dai-dai tana saɓule school bag ɗinta da zubewa akan sofar ɗakin. Zamewa tai ta kwanta ko jininta daya ɗauke na wucin gadi zai dawo aiki jikinta yanda ya kamata.         “Kina lafiya kuwa Zinneerah?”. Hajiya iya data shigo ta faɗa tana kai hannunta saman goshin Zinneerah dake kwance rigingine. Buɗe idanu tai a hankali tana kallon Hajiya Iyan, ta yunƙura zata tashi Hajiya iya tace, “Kinga yi kwanciyarki abunki. Amma kina lafiya dai ko?”.        “Lafiyata ƙalau Granny, na gajine sosai yau shiyyasa”.      “Tofa, halan tsalle-tsallen wofin nan naku kukayi a makarantar ko?”.     Ƙaramar dariya Zinneerah tayi tana tashi zaune saboda ganin a yanda Hajiya Iya tai magana fuska a yatsine. “Granny yanzu yaya zanyi kayana nacan ɗakin fa. Ni kuma wlhy wannan mutumun tsoro fuskarsama take bani. ALLAH yasa dai baiyi faɗan ganina a ɗakinsaba”.        “Idan yayi tsoronsa zanjine Zinneerah? Indai Moddibo ne ma bar wahalar da kanki wajen tsoron wani faɗansa na wofi. Shi haka yake baida fara'a dason hayaniya. Harkar kowa kuma ba shiga yakeba sai idan yaso hakan dan kansa. Tashi kije ki ɗakko kayan da zaki saka, zuwa weekend idan ALLAH ya kaimu sai ki tattaro kayan da zakiyi amfani dasu harya tafi kafin ki koma”.      Cikin waro idanu Zinneerah tace, “Granny kina nufin sake koma masa ɗaki zanyi da zama?”.        “Oh to kajimin ja'ira bakison ɗakinne?”.       “Nidai zan zauna dake anan. Ɗazu ɗinnan da ace babu kowa a gidannan da yazo ya sameni a ɗakinsa ai kakkaryani zaiyi yasin”.      Yanda take maganar da iya gaskiyarta yasa Hajiya Iya yin dariya. “Idan bazaki takuraba anan ɗin nima zanfi jin daɗin ganinki kusa dani. Dama danki sake yasa nace kije ɗakinsa ki zauna a binki ai. Yanzu tashi ki watsa ruwa sai kizo kici abinci duk kinmin zuru-zuru a idanuna”.        Miƙewa Zinneerah tai tana ƙoƙarin cire baby hijjab ɗinta. Hajiya iya kuma ta fice a ɗakin.        “Granny wai keda wa naji kuna magana ɗazun ina waya?”.     Khalipha ya faɗa dai-dai Hajiya iya data fito tana kaiwa zaune. Sai da ta zauna ta bashi amsa da, “Ƙanwarku ce mai kama da Inno. Yanzu zata fito sai ku gaisa”. Cikin rashin damuwa da sonjin daga ina yace, “Okay. Bara naje nan waje ga Sadam yana jirana zamu ɗan fita. Yayanmu baka buƙatar komai?”.          Har yanzu idanunsa nakan wayarsa tun yanda Zinneerah ta barshi. Ya ɗan ɗago kansa ya duba Khalipha ɗin ya maida. “No jeka abunka. Nima zuwa 6:30 Mahmud zai shigo muɗanyi magana”.      “Okay bye, insha ALLAH zan dawo nima kafin ya tafi. Dan nasan yau tare zakuci abincin dare. Granny bye”.        “A dawo lafiya”. Ta faɗa dai-dai yana ɗaga mata hannu zai fice.      Koda Zinneerah tai wankan ƙin yarda ta fito ɗaukar kayan tayi, duk da tanajin yunwa ta gwammaci ɗaukar sauran biscuit ɗinta dake cikin jakka taci, a ranta addu'a take ALLAH ya kawo wani acikin su Jamal ya taimaketa ya ɗakko mata kayan. Sai dai addu'arta bataciba. Dan muryar Hajiya Iya ta tsinkayo tana ƙwala mata kira. Hijjab ta ɗauka ta fito badan tasoba. Hajiya iya dake kallonta tunda ta fito tace, “Wai nikam bazakizo kici abinciba kika maƙale a ɗaki kamar wata sabuwar amarya?”.         “A'a Granny dama yanzu zan fito”. Ta faɗa tana satar kallonsa ta gefen ido. Yanzu kam waya yake a kishingiɗe saɓanin ɗazun. Saurin nufar kitchen tayi ɗebo abincin a bazata ta tsinkayi nutsatstsiyar muryarsa mai kama data rowa cikin kunnenta a karon farko. “Ki kwashe tarkacen da kika barmin a toilet”.        Duk da ba ita yake kalloba ta tabbatar da ita yake. Tuna abinda ta bari ɗinne ya saka kunya mai tsanani lulluɓeta. da sauri tabar wajen.      Gaba ɗaya turarensa mai ƙarfi ya danne nata daya fara zama a ɗakin cikin wuni ɗaya. Toilet ta wuce sum-sum tamkar yana a cikin ɗaki. Ganin alamar yayi amfani da toilet ya ƙara saka zuciyarya shiga cikin wani irin matsananciyar kunya. Ta kwaso kayan tana rintse ido kamar ta fasa ihu. shikenan ya gama gane mata sirrinta wayyo ita Zinne. Koda ta fito sum-sum ta wuce bata yarda ko sashen da suke ta kallaba.               Fitar da yay da daddaren saboda zuwan abokinsa Dr Mahmud ta bama yaran gidan damar shan sharafin hirarsu yanda suka saba. Sai dai anayi ana leƙen waje wai karya shigo. Sai ma ALLAH ya taimakesu har suka tashi bai shigo ɗinba.      Washe gari da safe ma har suka gama breakfast kowa ya fice yana ɗaki bai fitoba. Kasancewar juma'a ce da wuri su Zinneerah suka dawo gidan.               A bedroom ta iske hajiya iya zaune tana karatun AL-QUR'ANI. Bata zaunaba ta ajiye school bag ɗinta da cire hijjab ɗinta ta fice zuwa kitchen dan yunwa takeji, yau bata wani zauna tayi karin kirkiba suka fita makaranta. Gaba ɗaya ta shafa'a da kasancewar sa a gidan. dan haka ta fito kanta tsaye ko ɗan kwali babu akan nata. Sai gashinta data wanke dan zuwa kitso dake ɗaure a tsakkiya. Tanada gashi duk da bamai wani uban tsaho bane, dan yakanzo mata dai har kafaɗa musamman idan ta wankosa a saloon.         A yanda take tafiyar yasa sam bataga mutum dake tahowa a gabantaba. Gab sukai karo da juna. Ta ɗago a firgice tana murza goshinta zatai magana, amma sai maganar tata ta maƙale a maƙoshi ta tsaya kawai tana kallomsa. Shima ɗin dai kallo yake mata irin na sani, sai dai ya kasa tunano a inda yasan fuskar.         Baki ta buɗe da nufin ambaton sunansa ya katseta yana murmushi. “Sorry Beauty. Ko kece Sister ɗin tamune?”.         Saurin haɗiye maganar tata tai itama mamaki na neman kasheta a tsaye. Kenan bai ganetaba komi? Kokuwa basarwace irinta masu hannu da manda. Aiko inhar hakane itama ta iya ai, musamman a yanzu da take ƙara samun wayewar rayuwa da zamantakewa wajen malamta su Jamal.        Kanta ta kaɗa masa tana ƙaƙaro murmushi. Tace, “Eh nice Yayanmu, kunzo kafiya?”.         “Alhmdllh, amma kinma sanni kenan?”.       “Eh mana. Na sanka a bakinsu Bahijja”.       “Kai-kai a bakin magulmatan gidannan kenan. to ALLAH yasa dai basu koyama ƙanwar tawa gulma ba?”.          Ƙayataccen murmushi ta saki har haƙoranta na bayyana fili. Hakan yayi dai-dai da isowarsa wajen. Ta buɗe baki da nufin bama Khalipha amsa idanunta suka faɗa cikin nashi. Wani irin yarrr tsigar jikinta ta tashi, tai azamar maida kanta ta duƙar ƙirjinta na bugawa saboda abinda zuciyarta ta hasko mata a yanzunma kamar jiya data fara ganinsa, koma wanda yafi na jiyan, idanunsu iri daya hatta da kwayoyin ciki.       Juyawa Khalipha yayi domin son ganin abinda ya hanata maganar, yay murmushi a dai-dai sanda yayan nasu ke ƙoƙarin gittasu tamkar baima gansuba. Da sauri Khalipha yace, “Barka Yayanmu”.      Hannu ya ɗaga masa kawai yawuce abinsa. Hakan yasa Khalipha ƙara matsawa gaban Zinneerah da kanta ke a ƙasa. Cikin raɗa-raɗan magana yace, Beauty bara muje massallaci, idan na dawo zakizo ki tayani hira”. Daga haka yabi bayan Yayan nasu ɗakin Hajiya Iya daya shiga.         Nannauyan numfashi Zinneerah ta sauke tare da lumshe idanu ta dafe kirjinta. Zuciyarta na gargaɗinta akan abinda ƙwaƙwalwata ke hasko mata maiban tsoro da ruɗani. jiki a saɓule ta wuce kitchen dan neman abinda zata sakama cikinta ko taji dama.       Sosai ran Zinneerah yake a jagule da tunani mai tarin ruɗani kala-kala. Ba komai ya janyo hakanba sai ganin da taima Khalipha. Wanda zuciyarta taƙi aminece mata cewar bai ganetaba. Amma har a ranta tana shiga ruɗani da al'ajabin yanda ya nuna ɗin. Itako tayi imani da ALLAH ko shekaru fiye da haka sukai bata gansaba duk randa suka haɗu saita ganesa. Kenan itace keta shirmenta shi baimasan tanayiba, koda yake alkairinsa garetane yasa ta kasa mantawa dashi bawai wani abuba. A take ƙwalla suka cika mata idanu, sai dai tai ƙoƙarin hanasu su zubo dan ba wannan matsalar kaɗai bace matsalarta, hadda wadda take tsoron bayyanar tabbatuwarta saboda ɗimuwa.      Duk yunwar da take iƙirarin ji sai gashi ba wani abincin kirki taciba  bakuma ta yarda ta fitoba har saida ta tabbatar a ranta sunbar gidan.     Koda ta koma ɗakin Hajiya iya wanka ta farayi itama tai salla sannan tai zaman karanta suratul kahfi. Bayan ta kammala suka gaisa da Hajiya iya take sanar mata “Af Inno na kinga ina neman shafa'a. Idan kin idar da addu'arnan jeki ki gyara Moddibo ɗakinsa”.       Cikin dauriya da danne damuwoyinta tace, “To Granny”. Daga haka ta miƙe zuwa ɗakin nasa datai zaman watanni kusan uku a ciki. Cikin ƙanƙanin lokaci ta gyara komai ta baza ƙamshi. dan ita bama taga wani datti da ɗakin yayiba. Rufo ɗakin tai ta fito. Hakan yayi dai-dai da fara shigowar samarin gidan falon alamar yanzu suke dawowa daga massallaci. A ƙa'ida kuma duk irin wannan ranar anan suke lunch saɓanin breakfast kawai da sukeyi anan kowacce safiya.        Ƙasa tai da kanta cike da jin kunyar kallon da Moos'ab ke mata tunda suka haɗa ido. Batare da tayi tunanin hardasu Khalipha ɗin suke tareba itama ta zauna a falon saboda harda Jamal daya ja hannunta suka zauna a centre table ɗin falon yana miƙa mata ledar hannunsa da faɗin, “Surprise sweet sisi”..          Murmushi tayi tana ƙoƙarin buɗe ledar. Ganin abinda ke a ciki ya sata waro manyan idanu waje ta ɗago da niyyar yin magana taja birki wajen ganin ta haɗiye abinda ke a bakin nata saboda idanunta da suka sauka akan wanda batai fatan ganiba....       Ledar hannun nata Khalipha ya zare yana faɗin, “Ƙanwata mi muka samu haka?”.       Kasa amsa masa tai saboda wani kallo data kasa fassara inda ya dosa da Yah Adnan ya watso mata. Sai dai zata iya fassarashi da kamanni dana gargaɗi ko takaici.     Tsam ta miƙe batare data iya amsa Khalipha daya fiddo agwaluma ɗaya dake a ledarba yana faɗin, “Lallai kayan daɗin nan dani za'a shashi ƙanwata”.       Tana ƙoƙarin gittashi tace, “Na bakama Yah Khalipha kasha ma duka kawai”.         Saurin bin bayanta yay dan shima yaga kallon da Yayan nasu yay mata, wanda ya tabbatar shine ya hanata zama wajen. “No. Kinga tsaya Beauty guda ɗaya ma ya isheni karɓa kayanki”. Badan tasoba dole ta tsaya ta amsa. Shi kuma yace, “Thanks” cike da wani salo daya sanya Moos'ab dake binsu da kallo cike da kishi yay azamar kauda kansa garesu.       Koda ta samu ta shige bataso sake fitowaba Hajiya Iya ta korota domin zaman yin Lunch. Badan tasoba dole ta biyota, dan ko tace taci ba barinta zataiba sai dai ma tai mata faɗa. Duk sun hallara a dining har Baffa dasu aunty Ni'ima. Baffah ta fara gaidawa da juma'a, sannan ta zauna a kujerar data rage kusa da Khalipha da Meenal. Hajiya Iya kuma ta zauna a mazauninta da kowa ya sani.           Sai da Ni'ima ta fara miƙewa ta zubama Hajiya iya abincin sannan Baffah. Sanin halin Yayansu itama Safiyya ta miƙe ta zuba masa dukkan abinda tasan yana buƙata a wajen. Daga haka kowa ya fara ƙoƙarin zubama kansa abinda yafi buƙata.        Zinneerah dai duk jinta take a matuƙar takure. Kaɗan ta zuba dambun cus-cus a filet ɗin gabanta. Tana ƙoƙarin ɗaukar Mango juice ta zuba Khalipha ya rigata azamar ɗauka jug ɗin ya zuba mata a ƙaramin cup yana murmushi. “Thanks you Yaya” ta faɗa a hankali tana ƙoƙarin kai hannu ta ɗauka aka rigata..        Da azama ta ɗago fararen idanunta tana tsuke baki dan duk zatonta Jamal ne, kasancewar sun saba irin wannan wasan. “Malami kafa raina min....” ta haɗiye sauran maganar tata da sauri har tana sarƙewa saboda a hannun data hango juice ɗin.        Kowa dake wajen sai da ya ɗago ya dubeta tare da kallon abinda taima kallo guda ɗin ta duƙar da kanta. Jamal ya ɗan harareta batare da yace komaiba.        Duk kansu suka maida ƙasa kowa na mamaki a ransa ganin Yayansune da aikin, harma ya kai juice ɗin bakinsa tamkar bashi ya aikataba. Baffah da Hajiya iya kam da basu fahimci ainahin abinda ya faruba har haɗa baki suke wajen faɗin, “Kubata ruwa mana kuna ganin ta sarƙe”.      Saurin miƙa mata ruwan Meenal tayi a baki. Babu musu Zinneerah ta buɗe baki ta hau sha. Hajiya iya tace, “Maganin mai cin abinci yana magana ai kenan”.        Shiru Zinneerah tayi, dan bata da bakin yin bayanin gaskiyar zance. Khalipha dai mamakin abinda Yayan nasu yayi yake a zuciyarsa. Dan shi da kansa yasan baya shan mango juice. Hasalima daga shi sai Baffah suke matuƙar sonsa. Zinneerah ɗinma dan yaga ta nuna tanaso ne ya zuba mata. kauda tunanin yayi a ransa ganin yanda Yayan nasu ya sake cin mur tamkar bai aikata komaiba, sannan kuma yafi kowa sannin halinsa, shiyyasama bai kawo komai a ransa ba.          Kowa nama Zinneerah sannu shi banda shi, abincinsa ma yaketa faman ci hankali kwance tamkar baya jinsu.        Tsakurar abincin kawai Zinneerah keyi a takure matuƙa. Sosai zamnsa a wajen yay masifar cika mata ido. Hakama idanun Yah Moos'ab suma sun takura mata. Ga kuma wani irin yanayi mai kama da shauƙi da takeji game da ganin Khalipha, duk da yanda ya nuna bai ganetaba yana damunta cikin rai. Ganin batacin abincin sai juya cokali yasa Baffah yimata magana.          “Baffah na ƙoshine”. “Ƙoshi kuma ɗiyata? Haba yaushema kika fara cin abincin, bayanma kaɗan dama naga kin zuba. Kodai baki da lafiyane?”.      Kai ta girgiza masa da sauri. “A'a Baffah lafiyata ƙalau, barci nakeji”.         “Barci kuma? A to tashi kije ki kwanta kafin la'asar tayi dan yau lokacin gudu yake ga mai yawan rai...”      Zaram ta miƙe kafinma Baffah ya rufe baki. Ta nufi ɗakin Hajiya iya tanaji kamar ta runtse ido ta ganta a kwance ko zataji sassauci daga abinda takeji na ruɗani akan mutanen nan uku da sukazo mata da mabanbanta tunani.        Washe gari weekend suka tashi kowa yana a gida. Sai sune zasu fita islamiyya zuwa yamma. Tunda Zinneerah ta gama taya su Baba Rahi aikin safe ta gudu ɗaki ta sake kwanciya. Har Hajiya iya na mata ƙorafin anya wannan yawan kwanciyar tata ba shawara bace ke damunta?.       Luf tayi tamkar tai barcin, dan batason Hajiya iya tace yau saita fita dining yin breakfast. Batare da tunanin komaiba hajiya iya tace, “Oh harma kinyi barcin kenan? Dolene nazo na nema miki maganin shawara kuwa”. Daga haka ta cigaba da duba littafin hannunta, Zinneerah kuwa ta ƙara lafewa a bargo.       Tun tana barcin ƙarya harma na gaskiyar yay gaba da ita. Kasancewar weekend basu zauna breakfast ba sai wajen tara. Iya su yaranne kawai babu Baffah.       Shine ƙarshen fitowa sanye cikin wando 3quarter fari da yellow ɗin t-shirt. Gaishesa ƴammatan suka farayi yana ɗaga musu hannu saboda waya dake manne a kunnensa yana magana. Ni'ima ta fara haɗa masa abinci gabansa. Kamar an tsikari Moos'ab ya ɗan wawwaiga yana faɗin. “Wai ina Zinneerah ne?”.        Saurin ɗagowa Khalipha dake zuba kunu a kofi yay yana kallon Moos'ud saboda jin sunan daya ambata. “Dama sunanta kenan?”. Yay tambayar ga Moos'ab ɗin kansa tsaye. Wani ɗan murmushi Moos'ab yay yana sosa gefen wuyansa alamar dai akwai wata a ƙasa. “Sunanta kenan Yah Khalipha, ya haɗu ko?”. Ya ƙare maganar da ɗage gira.      Dariya su Haneef sukayi suna masa daƙƙuwa.          Ɗan jimm Khalipha yayi yana tunani a ransa. sai dai kafin yace wani abu Moos'ab ɗin ya sake faɗin, “Bahijja dubata a ɗakin Granny tazo ta karya”.       “To Yaya”. Bahijja ta faɗa tana miƙewa. Sai dai babu shiri ta koma ta sake zama saboda wani malalacin kallo da Yayansu ya watso mata a kaikaice, ya kuma ɗauke kansa tamkar bashi yayiba.        “A'a yaya kika koma kika zauna kuma? Nace kije ki duba Zinneerah ne fa”. Fuska ta narke tamkar zata fasa kuka tana duban sashen Yayan nasu da yay tamkar baisan abinda akeba a wajen. Dan dama dai duk a hankali suke magana gudun yin laifi a garesa.      Kallonsa shima Moos'ub ɗin yayi, mamaki ya kamashi ganin hankalinsa bama a garesu yake ba. Cikin faɗa yace, “Bazakije bane komi?”.        Da sauri ta girgizama Moos'ab ɗin kanta, da idanu ta nuna masa Yayan nasu tana ɗan noƙe kafaɗa. Baki ya sake buɗewa zaiyi magana suka tsinkayi fitar siririn tsakinsa. yaɗan watsama sashin da Moos'ab ɗin yake  kallo. A yanayin maganarsa na rashin son sakewa yace, “Kun isheni da surutu fa”.         Tsit wajen yay suna satar kallonsa ta ƙasan idanu da mamakin ganin yanda yay maganar tamkar a hasale..........✍ *_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 *_★ MADUBIN ZUCIYA_*💖 *_★ DALAAL_*💝 *_★ UBAYD MALEEK_*💓 *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 *_08085405215_* IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   0903 234 5899 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 *_ALLAH ka gafarma iyayenmu🙏🏻😭_*    *_TYPING📲_* *_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_* ________________________ *_OUMMAHMAD COLLECTIONS_* _(WE’VE GOT YOU&YOUR HOME COVERED)_ _MUNA SAYAR DA KAYAYYAKI MASU KYAU, INGANCI, DA KUMA RAHUSA👏🏻KAYAYYAKIN MU TUNDAGA NAHIYAR KETARE AKE KAWO MANA SU, DAGA RASSA DA DAMA._ _KAMAR SU: Kitchen utensils_ _Fabrics_ _Shoes nd bag_ _Phones_ _Veils_ _Children's wears_ _Furnitures_ _Dubai, china, India, turkey, Malaysia_ _MUNA GARIN: Kano, Unguwar hotoro_ _Facebook handle d’inmu: Maryam muhd_ _Lambar tarhon mu: 07014488636_ _________________ *Page 21* ...........Khalipha kam da zuciyarsa tayi matuƙar nisa a cikin tunani sam baiji mi yayan nasuma ya faɗaba. Yaɗan ɗago ya dubi Moos'ab ɗin kamar zaiyi magana sai kuma yayi shiru yana binsu da kallon mamaki su duka ganin yanda duk suka sake nutsuwa. Sashen da yayansu yake ya maida kallonsa, sai yaga hankalinsama baya kan kowannensu.       Maida kansa kawai yayi ga abincinsa shima, sai dai gaba ɗaya hankalinsa ya tafine ga tunanin sake son ganin yarinyar ɗazu da sukace sunanta Zinneerah.       Har aka kammala breakfast ɗin babu wanda ya ƙara ƙwaƙwaran motsi. Shine ya fara tashi a dining ɗin, suka bishi da kallo harya shige ɗakinsa. Tamkar jira suke yabar wajen suka fara ƙus-ƙus na gulma.         “ALLAH ya baku sa'a ya fito ya jiku”. Khalipha ya faɗa yana miƙewa shima ɗauke da kofin shayi ya nufi ɗakin Hajiya Iya. Zaune take a gaban gadon saman carpet ɗin dake a malale, ta mimmiƙe ƙafafunta dake mata zugi, dan ciwon da suke matannema ya hanata zama cin abinci a dining ɗin yau.        Fuska ɗauke da murmushi take duban Khalipha. Ya zauna a kusa da ita yana ajiye kofin ya amshi man zafin ya fara shafa mata. “Moddibo fa?”. Hajiya iya ta tambaya tana kallon Khalipha.     Ya buɗe baki zai bata amsa sallamarsa ta katsesa. Duk suka kalli ƙofar dai-dai yana ziro ƙafarsa ciki. Kallonsu yay ya kauda kai, sai da ya shigo ciki sosai yakai zaune a bakin gadon dai-dai ƙafafun Zinneerah dake ƙudindine a bargo sannan yace, “Ciwo ƙafan yake ne?”.         “Ba wani da yawa bane ai. Yanzuma zakaga ta saki tunda Khalipha ya daddana min ita”.       Kansa ya maida ga wayarsa dake haske alamar kira ake batare da yace komaiba.      “Fita zakayine Yayanmu?”. Khalipha ya faɗa yana kallonsa.          Kansa ya girgiza masa da faɗin, “No, Phones ɗin yaran nan ne”.        “Woow, autoci an shigo gari kenan”. Khalipha yay maganar yana jawo ƙyaƙyƙyawar ledar gabansa. Kwalayen wayoyi masu ƙyau da tsada guda shidda ya fiddo a ciki. Ya miƙama Hajiya Iya. “Granny ga wayoyin jikokinki Yayanmu ya cika alƙawari”.       Murmushi tayi a karan farko da miƙa hannu ta amsa ɗaya tana kallo. “A to lallai munyi rabin shiri da ja'irin nan yau. ALLAH ya saka da alkairi ya bada ladan zuminci”.      Da amin suka amsa shi da Khalipha. Hajiya iya tace, “To ga kuma Zinneerah ta ƙaru, sai itama kasan yanda zakai da ita, dan ba'a basu wayoyiba ita batada ita”.       Kamar bazai tankaba sai kuma ya ɗan dubi Hajiya Iyan. “Tunda bansan tana a gidanba sai tai haƙuri sai wani karon”.       “A'a bazai yuwuba gaskiya Moddibo. A duba mata dai ko anan ita sai a saya mata”.      Shiru yay bai sake tankawaba duk da sarai yaji mi Hajiya iyan ta faɗa. Sanin halinsa yasa Khalipha saurin faɗin, “A'a Granny a bar Yayanmu ya huta. insha ALLAH ni saina saya mata kawai”.         Hajiya Iya tace, “To shikenan hakanma yayi ALLAH ya saka muku da alkairi. ya ƙara haɗemin kanku”.       Khalipha ne kawai ya amsa da amin. Shiko laɓɓansa kawai yaɗan motsa kaɗan alamar ya amsa ɗin.         Daga Haka Khalipha da Hajiya Iya suka cigaba da hira, shiko yana saurarensune kawai amma baya saka baki sai yaso, yama maida hankalinsa gaba ɗaya akan latsa waya.                Zinneerah da tun shigowar Khalipha ɗakin ta farka taɗan motsa kafarta, jin ta dunguri abu yasata saurin matsarwa baya tana rintse ido. Hakanne ya sakashi ɗan juyawa ya kalli abinda ke bayan nasa duk da tun shigowarsa yaga alamar mutumne kwance. Kamar zaiyi magana sai kuma ya miƙe yana tura wayarsa a aljihun wandon 3quarter ɗinsa. “Ni bara naje zanyi magana da Baffah, zuwa anjima inason zuwa Jigawa”.       “Jigawa kuma? Yin me?”. Duban Hajiya iya mai maganar yayi, yaɗan kai yatsa gefen idonsa ya sosa kaɗan da cewar, “Akwai wani gona ne da nakeson yin noman shinkafa. So mun gama magana da Mahmud shine nakeson dubawa”.        “Tofa, bana kuma nan aka tsallaka kenan? Kai dai duk hanyar neman kuɗi kasanta Moddibo. Kana gudunmu kuma kana son zuwa kaci arziƙin ƙasarmu”.       “Tunda ni ba ƙasata baceba ko. Idan wannan mai barcin ta tashi taje ta gyaramin ɗaki”. Ya faɗa yana ficewa daga ɗakin abinsa.        Harara Hajiya iya ta raka bayansa da shi tana yamutsa fuska. “Bauɗaɗen banza jikan ƴan Morocco”.     A yanda tai maganarne ya tilasta Khalipha ƙyalƙyalewa da dariya shima yana miƙewar. “Granny rigima. show ɗinki da Yayanmu nada matuƙar ƙayatarwa ga mai kallo. ALLAH ya ƙara miki lafiya da tsahon rai mai amfani uwargida kuma amaryar Abdul-Mutallab Shira”.          “Oh to, ko kanamin baƙin cikine ba'a taɓamin kishiyaba?”.     “Wah? Ni?  Rufamin asiri Granny karkisa Baffah yaji ya zagemin uwa. Kinga nayinan raba tsaraba na samo tukuyci. Itama  ya kamata ta tashi ta karya”. Ya nuna Zinneerah da duk tana jinsu amma ta lafe.        “Eh nima yanzu nake tunanin nan a raina. Barama naji jikin nata kodai batajin daɗine, dan bata saba irin wannan barcinba sam”.        “Okay to bara naje na dawo sai naji wane hali take ciki”. Daga haka ya fice a ɗakin.        Ihun murnar waya da su Meenal suka shigo ɗakin sunayi ya tilasta Zinneerah tashi. A take suka kaure ɗakin da sabon ihu. Koda Hajiya iya data shiga bayi ta fito tana musu maganar su fice sun dameta a guje suka fita kuwa suna cigaba da ihunsu. Acan harabar gidan suka iske su Abidah suma suna nasu tsallen murnar dan da gaske yayan nasu ya shigo dasu gari da masu zafi kam.         Duk da babu Zinneerah a cikin masu wayar babu damuwa ko ɗigon sisi tattare da ita, hasalima itace mai farke wayoyin su Bahijja daga cikin kwalinsun. Da ƙyar hajiya iya ta tilastata zama cin abinci. tana gamawa kuma taje tai gyaran ɗakin nasa daya faɗa kamar yanda Hajiya iya ta sanar mata saƙon duk da itama taji da kunnenta.     Koda ta kammala taje tai wanka fitowa tai suka ɗora shirmensu daga inda suka tsaya ita da su Jamal. A haka Khalipha ya shigo ya samesu, daga asibiti yake yin bincike akan Zinneerah da suka haɗu wancan karon, dan gaba ɗaya zuciyarsa ta kasa yarda cewa wannan ɗin itace waccan Zinneerah ɗin. Gadai satar kammani sunayi da juna. Amma kuma wayewar kai da wasu abubuwa da yawa ya banbantasu. Babbar matsalar daya samu na rasa Number Naziru da yayi sakamakon wani tsautsayi daya samesa acan London. Yanzu kuma yaje asibitinma a iya binciken da yayi bai samu wani bakin zaren da zai iya nemansu ba. Amma an tabbatar masa ta haihu baby boy.            Gida ya dawo da sabon tunani akan tunkarar wannan Zinneerah ɗin yaji daga gareta ita kuma, dan a tunaninsa da ace waccan ɗince data ganesa. To waccanma ai matar aurece miyasa zaiyi tunanin itace anan?.       Ruwa Meenal ta kawo masa ya sha. Ya kumace ta haɗa masa abinci a dining zaije yay wanka ya dawo. Binsa Zinneerah tai da kallo a cikin wani irin bahagon yanayi. Cikin dabara takai hannu ta share ƙwallar da suka ciko mata idanu. A yanzu haka babu abinda kecin ranta da damuwarta sai yanda Khalipha ya nuna tamkar baima taɓa sanintaba. Bayan ita tunda ya barta bata taɓa hutawa da tunaninsaba a ranta. har mafarkinsa tasha yi ma. Amma insha ALLAH zata daure itama ta kama kanta gareshi, idan ya ganota fine. idan ya cigaba da pretending ɗin rashin sanin nata itama saita samawa kanta lafiya ai. Da wannan tunani ta cigaba da hidimarta har lokacin Islamiyya yayi suka fita. *_DANYA_*             Tafe take buguzun-buguzin cikin uwar ranar dake ƙwalle ga zafi da take da shi. Ga wanda baisan halin ruɗanin da take ciki a ƴan watannin nan ba sai ya ɗauka ko mahaukaciya ce. Duk ta fige ta fita hayyacinta tun barin Baba garin Danya. Duk dukiyar datake taƙama ta tara ta dabbobi da buhunan kayan masarufi sun ƙare tas wajen bin gidajen malamai dake mata aiki akan yima Baba kiranye ya dawo gida duk inda yake.        Aikin ake kamar ba gobe amma babu alamar yanaci dan har yau ko inda Baba yake babu wanda yazo yace yaji. Gashi kullum malam nata ƙarya suke mata Zinneerah nacan tama zama karuwa a binnin ikko. Sosai wannan labarin ke mata daɗi akan Zinneerah. dan bata da burin daya wuce taga yarinyar ta tagayyara ta wulaƙanta a duniya, saboda kawai tazo matsayin ƴar kishiyarta.      (Ƴan uwana mata dan ALLAH mu canja, mu daina saka yara a kishinmu. sannan kishinma mu dinga sassautama zukatanmu. Nasan kishi dolene domin kamar jininmune. To amma suma mazan idan suka fahimci kana musu kishi na hauka duk da sonsu ne yake jawo hakan saisu maidaka wawa mahaukaci. ka kuma fita a cikin ransu ma baki ɗaya su koma ganin baƙinka maimakon hasken da kake dashi a garesu. Babu amfani kai burin lalacewar ɗan wani ko shigarsa wani bala'in rayuwa. Dan kaima ba tsira naka zaiyiba wlhy. dan ba'a taɓa shuka dawa a girbi shinkafa. Sai ka ƙyautata zato da addu'a ga ɗan wani kaima ALLAH zaiji ƙanka ya ƙyautata rayuwar naka ƴaƴan insha ALLAH. ALLAH yasa mufi ƙarfin zukatanmu😭🙏🏻).        Yanzunma wani ƙauye can nesa dasu sosai akai mata kwatancen wani malami shine taje. A yanzu haka dai ya mata alƙawarin dawowar Baba nanda kwanaki bakwai, idan har bai dawo ɗinba zai biyata kuɗin daya karɓa a wajenta. Hakkane ya sata tahowa gida cike da ƙwarin Gwiwa ko ranar dake dukanta da azabar tafi bataji.         Shiru ta iske gidan babu kowa. ta zube ƙarƙashin bishiyar tsakar gidan nasu tana maida numfashi da ƙyar. Ta kusa mintuna biyar a haka kafin ta miƙe zuwa randunansu dan tasha ruwa. Wayam ta samu tabbacin dai Tinene data barma sallahon ɗebo musu ruwan bata ɗebo ɗinba kenan. A take ranta ya ɓaci taja ƙafafunta da ƙyar ta koma ta zauna dan har juwa takeji saboda yunwa. Ko karyawa bataiba ta fita, ɗan hatsin da baba ya bari a rumbu duk sun cinye ta salwantar da wani kuma wajen bin malamanta na tsiya. Hakan yasa abincima sau uku a gidan wataran gagararsu yakeyi. sai idan Yaya Gajeje taji tausayinsu ta ɗakko ta kawo musu. Koda yake mafi yawancin lokacima itace ke zama da yunwar, dan Tinene sai dai ta ganta da kayan ciye-ciye ta shigo. bata isa tambayarta kuma ina ta samosuba saita hayayyaƙo mata da rashin kunya. Wani lokacinma bata tambayar tata amsa take itama taci saboda wahala. Sa'a kuwa yanzu takan jera kwana huɗu biyar bata kwana a gidanba. Tuni ta koma gidan Baba Rabilu abinta, dan ɗansa ya maidata makaranta tana zuwa. da Inna ta nuna bata yarda bane yasa Sa'a tattara inata-inata ta kona can gidan. Sai randa ta bushi iska take zuwa ta kwana anan tunda yanzu babu talla Malamai sun cinye jarin Inna Asaben.        Miƙewa Inna tai tana tsinar Tinene a cikin ranta, dan yunwa da wahalar tafiya tasa koma magana mai ƙarfi bata iyayi. Ɗakinta ta shige ta faɗa saman gado da fatan ALLAH ya kawo wani a cikinsu Sa'a ɗin ya taimaketa da ko kunu ne taɗan kurɓama cikinta ko taji dama-damar tashi ta bizne aykin malam.        ALLAH kuwa ya taimaketa babu jimawa ta farajin motsi a tsakar gidan da ƙarar taunar chewing gum. ko ba'a faɗaba tasan dai Tinene ce. Dan itace mai ɗabi'ar cin cingam ɗin a koda yaushe. Idan tai mata magana tace mata ƙoshi ya sakata ci danta rage nauyin cikinta. Dole Innar keyin shiru dan Tinene kam ta fara fin ƙarfinta. Gashi kuma wani lokacin tana ɗan samun mai daɗi a wajenta taci.      Bankaɗa labilen da akaine ya sakata ɗago idonta ta kalli ƙofar. Tinene dake tsaye a bakin ƙofa tana cakal-cakal da cingam a baki cikin rashin ladabi tace, “Oh oh, wai se yanzu kike dawowa gida Innarmu? Ke dai baki gajiya da mikama maluma kuɗi suna cinyewa mu baki anhwana mana da ko taro ba a ciki. Naga dai Baban da ƙahwarsa yabar gidan ba saceshi akaiba halan”.      Kasa cemata uffan Inna tai, sai kanta data girgiza kawai. Hakan datai ya bana Tinene haushi, harta saki labulen da niyyar barin wajen Inna ta ƙwala mata kira cikin ƙarfin hali. “Tinene wai nikan yaushene zaki natsune? Ni yanzu duk bama wanga ba. Dan ALLAH idan da goma hannunki ko murtala kije nan gidan dije ki sayo mani kunu koba suga nasha”.     Baki Tinene ta zunɓura gaba. kanar zatai magana sai kuma taja tsaki fuuu ta fice tana ƙunƙuni. “K kuɗinki na wajen bokaye da malamai ni kuma kin sakama nawa ido mu ramtsesu tare. Bayan duk kece kika jehwamu a wagga rayuwa ta yunwa da talauci wajen neman baƙin asirinki mtsoww”.       Da wanan mitar taje ta sayo kunun na goma ta kawo mata dukda ba wani na kirki bane. Da rawar jiki kuwa Inna ta amsa tahau sha duk da zafin da yake da shi. Ta saki gyatsa tana ajiye kofin duk da bata ƙoshi bane yanda take buƙata. Daga haka ta zame ta koma kwance tana zufa. Tinene ta taɓe baki da nufar hanyar ficewa gidan tanama Innar tasu baƙar magana. (Hhhh yanzu aka fara wasan Hajja Asabe😂😂😜). ________________________★★            Washe gari lahadi ma duk suna a gidan, sai dai banga Khalipha da Yah Adnan da suka tafi jigawa. Dan jiya bai samu damar zuwanba saboda wani uziri. Bayan sallar la'asar duk suna zaune a falo suna ɗan hira iyasu ƴammatan sai ga Safiyya da ita kaɗaice bata gidan. Momie ta aiketa can wajen yayarta kai saƙo.         A yanda ta shigo falon kamar wadda aka koro ya sakasu duk suka zuba mata ido. “Ke lafiyarki kuwa?”. Hajiya iya data kasa haƙuri ta faɗa tana duban Safiyyan.           “Humm Granny inafa lafiya, wlhy wani abun al'ajabi da ruɗani nai gamo dashi a yanzun nan hanyata ta dawowa daga gidan Umma”.        Duka falon maida hankalinsu sukai a kanta, kowa nason jin dami tai gamon?. Wayarta ta lalubo a jakka tai ƴan danne-danne sannan ta miƙama Hajiya iya. “Granny dan ALLAH kikalli yaron nan dawa yay miki kama?”.       Cikin rashin damuwa Hajiya Iya ta amshi wayar. Yanda tai kasare tana kallon wayar ya saka su Meenal duk suka zuba mata ido suma. Itama da alamun makamancin irin ruɗanin da Safiyyar ta shigo da shi tace, “Keko Safiyya a ina kikaga wannan yaron haka?”.         “Wlhy Granny a Napep. Mun taho da driver motar ta mutu a hanya. Shinefa nace masa bara na tare napep na ƙaraso gida. Mun daɗe tsaye yanason taremin ba'a samuba sai da ƙyar ya tsaida wanda ke ɗauke da maman yaron nan.      Hajiya iya daketa faman jinjina kanta tace, “Amma wannan kamanni da mamaki a cikinsa. Koda yake hakan kan faru koda baka haɗa komai da mutumba. Amma ita matar a ina take?”.        “Wlhy ban tambayetaba Granny, amma da alama wani waje zatajema. Bama tasan na ɗauki hoton yaronba dan cikin dabara nayi”.       Wani irin nannauyan numfashi hajiya iya ta sauƙe. Sai kuma ta miƙama Abidah wayar ganin duk sun zaƙu su gani. A haka samarin gidan dake shigowa a tare sukazo suka samesu. Ganin yanda aketa ƴar bayayya da waya ya sakasu tambayar ko lafiya?. Safiyya ce tai musu bayani. Amsar wayar suma sukai duk suka gani. Duk wanda ya kalli hoton sai ga mamaki ya bayyana a fuskarsa da ruɗani.         Duk wannan al'amari dake faruwa Zinneerah nacan ɗaki tana shirya kayanta data kwaso a ɗakin Yah Adnan cikin wadrobe ɗin Hajiya iya. Hakan yasa batasan hidimar da akeyiba. Dan so take ta gama shiryasu a daren yau tunda gobe idan ALLAH ya kaimu monday akwai makaranta.         Kasancewar dama bata fara aikin da wuriba sai gashi har Hajiya iya ta shigo domin sallar magrib bata kammalaba. Sai kusan sha ɗaya ta gama lokacin hajiya iya ta jima dayin barci mai cike da mafarkin yaron da Safiyya ta kawo musu a hoto, takan dai tashi tai salla idan lokaci yayi. Su meenal kuma sunɗan lekota, sanin hajiya iya idan ta kwanta batason surutu yasa suka fice suka barta ita kaɗai ta cigaba da aikinta.           A falo kuwa hirarsu suka cigaba dayi bayan tasowar hajiya iya. Dan duk sun barma kansu cewar kamannine kawai da akan samu a rayuwa tsakanin wani da wani koda babu alaƙar jini saboda hikimar UBANGIJI. Basu wani jimaba suka fice duk da Moos'ab yaso ganin Zinneerah kafin ya wuce ɗin. Rashin samuwar hakan ya sakashi haƙura kawai.         Tun daga wannan ranar babu wanda ya sake tada zance akan hoton yaro, sai dai abin na nan maƙale a zuciyar Hajiya Iya ta kasa mantawa. Tanason yin maganar kuma wata zuciya na kwaɓarta akan kamannine kawai. Idan kuma tace zata kawoma zuciyarta wani tunani daban ya zata alaƙanta al'amarin ma to. Hakan yasata tsuke bakinta ta barma ranta komai kawai.      kwanaki sun cigaba da shurawa a hankali sai ga Khalipha da Adnan na cika kwanaki goma da zuwa. Ko kaɗan Zinneerah ta kasa sabawa da kasancewar sa a gidan duk da a kwanakin nan bai cika zamaba kullum suna hanyar Jigawa gonar da zaiyi noman shinkafa. Sukan fitama kafin su su fito, wani lokacin kuma sai sunyi barci suke dawowa. Wannan dalilin yasa takanyi kwanaki uku biyu ma bata sakashi a idontaba har Khalipha ɗin da take marmarin gani a ko yaushe.       A kwanakin nan daya ɗauka gaba ɗaya hidimar gyaran ɗakinsa ta dawo kan Zinneerah. Kullum ita yake cewa taje ta gyara masa ɗaki. Bata damuba dan dama ta rigada ta saba. Idan ta ganshi tsoro na matuƙar kamata, dan kullum abubuwan daya dangancesa suna sake danganta kansu da abinda sam ta kasa gaskatawa.         A randa suka cika kwanaki goma sha uku a gidan basuje gona ba, amma duk da haka babu wanda ya sakashi a ido sai yamma. Yana ɗakinsa yana harkokinsa na business a lap-top.         Zinneerah, Meenal, Bahijja sai Jamal na zaune a falon hajiya iya Yah Khalipha ya shigo. duk sannu sukai masa ya amsa yana zama kujerar dake facing ɗin Zinneerah da Bahijja. Cikin kafe Zinneerah ɗin da idanu ya miƙa mata ledar hannunsa yana murmushi.         “Ƙanwata yau dai ga wayarki na cika alƙawari”. Kafinma ta kai ga yunƙurawa amsar wayar Jamal yay azamar zuwa ya amsa yana washe baki. A take suka rufi akan wayar suna tayata murna duk da ba irin tasu Meenal ɗin bace ba, amma itama ta haɗu. Tasowa Zinneerah tai tsam inda yake takai tsigunne kanta a ƙasa tana faɗin, “Nagode sosai Yah Khalipha, ALLAH ya ƙara buɗi mai albarka”.       Kansa ya jinjina mata yana sake faɗaɗa murmushinsa. Sai kuma ya miƙe ya fice zuciyarsa na bashi ƙwarin gwiwa akan yau ya tunkareta da zancen nan. Dan yauɗin kawai ke garesa Yah Adnan yace nanda kwanaki huɗu idan ALLAH ya kaimu maybe zasu wuce Abuja. Daga can kuma bazasu dawo Kano ba London zasu koma zaiyi wasu uzirinsa kafin ya dawo akan zancen auren su Ni'ima da ayanzu haka an tsaida rana da kuma maganar Company da yake tunanin buɗew na shinkafa.      Binsa da Kallo Zinneerah tayi ƙwalla na cika mata idanu, sai kuma ta miƙe tsaye tana murmushi saboda wani abu data tuna. Idanuntane suka sauka akan Yah Adnan dake tsaye bakin ƙofarsa da waya a kunne yayi wani kicin-kicin da fuska............✍ *_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 *_★ MADUBIN ZUCIYA_*💖 *_★ DALAAL_*💝 *_★ UBAYD MALEEK_*💓 *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 *_08085405215_* IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   0903 234 5899 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 *_ALLAH ka gafarma iyayenmu🙏🏻😭_* *_TYPING📲_* *_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_* __________________________ *_ina 'yan uwa musulmai masu kishin addinin islama???_* *_maza ku matso ga wani aikin lada ya samu_* *_Ɗanku kuma dan uwanku kuma qaninku wato ABDURRAHMAN, yaro mai hazaqa, ƙwazo da tarin baiwa, gami da kwadayin haddace littafin Allah mai tsarki, ya bude YOUTUBE CHANNEL nashi na qashin kansa, ku tallafa masa ta hanyar shiga wannan shudin rubutun ku danna masa subscribe, ba abunda xai rageku dashi saima samun dimbin lada dalilin KARFAFA MASA GWIWA, MUN GODE 🙏🏽🙏🏽🙏🏽_* 👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽 https://youtu.be/WWIGq5Jbtb0 _______________________ *Page 22* .........Cikin sauri ta haɗe murmushinta dayin diri-diri na alamar rikicewa. Dan wani irin kallo da take kasa fassarawa a duk sanda yay matashi ya watso mata yanzuma ya ɗauke kansa fuskarsa na ƙara tsukewa fiye da yanda ya fito. Sum-sum ta juya gasu Bahijja da suma sukai tsitt daga ihun da sukeyi na murnar wayarta zata zauna yace, “Haɗomin black tea yanzun nan”. Daga haka ya juya ya koma ɗakinsa.        Da sauri duk suka kalli Zinneerah da itama kallonsu take. Meenal tace, “Wlhy ki tashi kafin yace kin ɓata masa lokaci”. A take idon Zinneerah ya fara tara ƙwalla. Dan wannan shine karo na farko da ya sakata irin wannan aikin bayan gyaran ɗakinsa.      Bahijja tace, “Kinsan mi zakiyi?” Zinneerah ta girgiza mata kai da sauri. “Kije kima Baba Rahi magana ta haɗa miki, dan tafi kowa sanin abinda yakeso a nan gidan bayan Granny. ALLAH yasa basu tafi ba, tunda ba gani yayba ki fiske abinki ki kai masa kawai a rabu lafiya. Dan shi inhar ya sakaka abu bakayi dai-dai yanda ya buƙataba ka shiga uku”.        Jin abinda Bahijjan ta faɗa ɗinne ya sake tsurar mata da ciki, amma shawarar saka Baba Rahi ta haɗa matan ya sata jin sassauci. Da sauri ta miƙe zuwa kitchen, sai dai wayam babu baba Rahi a ciki. Tai saurin kallon agogon dake a kitchen ɗin wanda ya bata tabbacin Baba Rahi ta wuce gida dan ba'a nan take kwanaba daman.      A take ƙwallan da take maƙalewa suka silalo mata. Jiki a sanyaye ta ɗiba kayan ƙamshi tasa a turmin ƙarfensu ɗan ƙarami ta hau dakawa. Cikin ƙanƙanin lokaci ta gama dafa shayin daketa uban ƙamshi a kicin ɗin, sai dai duk wannan ƙamshin nasa dazai iya saka mai kallo buƙatar sha ita a tsorace take. Ƙaramin flask ta samu ta juye tare da ɗorawa a tire ta saka kofuna biyu da mitsilin bowl data zuba suga a ciki ta ɗakko ta fito tana karanto addu'ar nasara a cikin ranta.        Bata iske kowa a falonba su Jamal sun gudu, hakanne ya sake ɗarsa mata tsoro a cikin rai ta nufi ɗakin tamkar an daddoke mata gwiyawu. Sai da tai sallama kusan sau huɗu sannan ya amsa mata da bata izinin shiga. Ta tura ƙofar ta shigo ƙamshinsa na rige-rigen shiga mata hanci. Tsaye yake a gaban mirror sanye cikin farar jallabiya ruwan madara yana ƙoƙarin ɗaukar wayarsa dake vibration.      Tai saurin kauda kanta ƙasa murya na ɗan rawa tace, “Yayanmu ga tea ɗin”.         Juyowa yay dai-dai yana ɗora wayar tasa a kunne ya kalleta da fararen idanunsa da suka nema ruɗata. Dan itama yayi dai-dai da ɗago nata zata saci kallonsa. Ƙasa tai da kanta shima ya janye nasa yana zama kan sofa. Ƙafa ɗaya ya ɗora kan ɗaya yana kai bayansa ya jingina da kujerar ya sake dubanta ya ɗauke kai. “Zaki cigaba da tsayamin a kaine?”.          A sanyaye Zinneerah ta ƙaraso ta ajiye tiren saman table ɗin gabansa, dai-dai yana faɗin, “Ina ruwanki da ko wacece. Ki cigaba da maganarki kona kashe wayata”. Ya ƙare maganar dajan guntun tsaki.         Zinneerah dai dake saurarensa haka kawai ranta ya bata matarsace. maganar su Meenal data tuna yasata kaiwa tsuggunne ta fara ƙoƙarin zuba masa a kofin. Sai dai jin kamar ana kallonta ya sata ɗan daburcewa, kamar zata ɗago sai kuma ta fasa.      Kamar ya fahimci ta gane kallonta yake sai ya miƙe gaba ɗaya yana bama matarsa dake tambayar ya bata hajiya iya amsar da cewar “Bama tare”.            Tabbas Zinneerah taji kalmar “Bama tare” daya faɗa, sai dai batajin mi matar tasa ke faɗa dagacan, a bazata taji saukar wata gigitacciyar tsawarsa cikin kunnuwanta. Ai batama san sanda ta zube ƙasa daɓar ba tana cusa kanta a ƙafafunta jikinta na rawa. Shiko da baisan tanayiba ya cigaba dayin magana a hasale matuƙa.         “Farah! Ki shiga hankalinki, ke miyasa a kullum tunaninki baya a layin na masu hankali? To kije hakaɗinne ma, ai dai nima namijine ko? Wawuya kawai mtsoww”. Ya ƙare maganar dajan wawan tsaki yana yanke wayar ya jefa saman gado. Wadrobe ya nufa ya finciki murfin da ƙarfi ransa na nasa suya, ya rasa wane irin hukunci zai fara yima Farah akan yawan furta kalmar zargi gareshi a duk lokacin da yay nesa da ita zuwa wani waje. Inhar zaiyi tafiya ta dinga bin ƙwaƙwƙwafinsa kenan tamkar wani ɗanta saboda shegen kishinta na tsiya.           “Zan koya miki hankali” Ya fada zuciyarsa na sake kumbura. Ɓacin ran da yake a ciki ya sakashi mantawa da Zinneerah a ɗakin ya fara ƙoƙarin fara shiryawa.         Shirun da tajine ya sakata ɗago kanta a tunaninta fita yayi. Babu shiri ta miƙe ta fita da gudu ganin ya fiddo kaya alamar sanyawa zaiyi.        Shikam baimasan tanayiba, Sai da ya gama saka kayan ya nufo mirror dan saka turare idonsa ya sauka a kan kayan data ajiye, sai dai babu ita a wajen. Wani sabon takaicine ya sake lulluɓesa tuna abinda Farah ta faɗa akanta. Ya cije baki da rumtse idanunsa da ƙarfi yana raya wannan karon sai tasan shi take dangantawa da Zina wlhy.....        Yana ƙoƙarin zaman shan shayin da Zinneerah ta zuba kira ya shigo masa. Sanin mai wannan ringtone ɗin yasashi miƙewa ya ɗauka wayar yana ƙoƙarin sassauta fushinsa.        “Barka Mammah”. Ya faɗa cikin nuna girmamawa a gareta. A take zuciyarsa ta kara rinewa da ɓacin rai dan dama yasan bai wuce Farah takai ƙararsa wajentaba kamar yanda ta saba. Uffan baiceba har Mammah dake zuba faɗa daga can tayi ta gama. Sai daga ƙarshe da tace Farah ɗin zata biyowa Nigeria itama sannan yay magana.        “Mammah abinda nazoyi nanfa important ne, karki biyema shirmen.......”     “Saurara min Abdul-Mutallab!!” Ta katsesa a tsawace. “Kana nufin bansan abinda ubanka da kakarka suke shiryawa a kanka bane?, to wlhy su sani ƙwatarka a hannuna wannan karon sunyi kaɗan. Idan har bakaso Farah ta biyoka ka dawo London yau yau ɗin nan tunda kasan tanada lalura a jikinta. Inba hakaba bayan itama tazo nima zanzo dan ina dai-dai da kowa cikinku”.        “No, Mammah Please, nafa faɗa miki abinda zanzoyi tukan na taho”.       “Amma baka sanarmin zaka daɗe haka a nanba, dama an manna maka harkar noman ne saboda munafunci ai. Sannan wannan munafikin yaron dake nane da kai ko yaushe idan kun dawo ya wuce hostel da zama, inba hakaba Abdul-Mutallab sainayi bala'i bala'in ɓata ranka, wlhy ubanka ma sai yayi dan.........”        “Mammah Pleaseeee!”. Ya faɗa cikin zafin rai, dan ya mugun tsanar yaji tana zagar masa mahaifinsa da ƴan uwansa.          Ƙitt ta yanke wayar batare data sauraresa ba.        Kansa ya dafe saboda wani jiri-jiri dake neman kwasarsa. Shin wai wace irin rayuwace wannan mahaifiyarsu kesan taga sunyi? Gaba ɗaya ta tsani taga sun raɓi mahaifinsu da ƴan uwansu. Ta yaya kuwa hakan zata kasance bayan hausawa sunce da uba ake ado. Duk ƙoƙarin da yake wajen fuskantar da ita muhimmancin family ɗinsa bata fahimta. nata ƴan uwan kawai takeso su girmama su raɓa. Anya kuwa idan ya cigaba da biye mata bazai halaka ba. Tunda suke da Baffah bai taɓa nuna masa matsanancin ɓacin ransa akan abinda Mammah takeyi na katangesu daga garesaba irin wannan karon. Har a yanzu haka ya kasa tarosa gaba ɗaya. A da kam idan yayi masa faɗan yakan sakko ya koma nasiha. Amma wannan karon yaƙi sakkowa. Ya dage akan sai yabi umarnin hajiya iya ya ƙara aure yabar matar anan Nigeria idan ita waccan tafi ƙarfin dawowa cikin family ɗinsa ta zauna.      Zazzafan huci ya furzar yana zamewa ya kwanta a sofar da dafe kansa kawai ya lumshe idanunsa.        Lokaci mai tsaho ya ɗauka a haka batare da ya saniba. Dan har saida Hajiya Iya ta shigo ɗakin dubashi dan taga har anyi magrib bai gitoba.        “Moddibo kana lafiya kuwa?”. Ta faɗa tana kai hannu ta cire nasa daya dafe kansa. Idanunsa ya buɗe a hankali yana kallonta, ta sake maimaita tambayar tana taɓa goshinsa.      “Lafiya kuwa kake yau har anyi salla baka fito kaje massallaci ba Moddibo?”.        Zaune ya tashi sosai, Sai kuma ya girgiza mata kansa, “Kaina ke ciwo kawai Granny, bamma san anyi sallanba ai”.      Tsura masa idanunta tai cike da nazarinsa. Dan ta riga ta gama karance halayyarsa tun ƙuruciya. Duk da ta hango damuwa tattare da shi sai batace komai a kai ba. ta nufi hanyar fita kawai tana cemasa ya tashi to yay sallar”.       Goshinsa ya murza yana cige laɓensa na ƙasa, har yanzu yana takaicin da mamakin yanda Mammah ke biyema Farah a kowanne lokaci. Duk da yasan akwai nata halin itama ya fahimci akwai zuga mai ƙarfi da akai mata a yau ɗin, a bazata wani guntun murmushi ya suɓuce masa, ya miƙe yana abinsa harya shiga toilet dan shi kaɗan yasan muguntar daya shiryama Farah da mai zuga Mammah ɗin dan ya tabbatar itace taje London ɗin kokuma sunyi waya akan tahowar tata.      Alwala yayo yazo ya gabatar da sallar magrib data wucesa. Daga haka ya fito zuwa massallaci samun jam'in isha'i. Koda aka idar tare da samarin ƙannensa suka shigo gidan abin sha'awa, su sukai sashensu shi kuma yanufo sashen Hajiya iya. Kamar yanda ya fita bai samu kowa a falonba yanzuma haka ya dawo bai samu kowaba.      Ɗakin Hajiya iya ya shiga da sallama. Tana zaune a inda tai salla Zinneerah dake fashin salla na kan kujera kwance tana latsa waya, lokaci-lokaci takan matse idanu da baki saboda mararta dake ɗan mata ciwo can ƙasa. Saurin miƙewa tai zaune saboda jin sallamarsa. Sai dai kafin tace zata tashi harya rigada ya shigo. Akanta ya fara sauke idanunsa ya janye. Batare da damuwar ganinta zaune a Sofa ɗinba yakai zaune yana cema hajiya iya “Barka da dare”.       Zaram Zinneerah ta miƙe a sofar har tana neman faɗuwa. “A hankali mana Zinneerah. Koma saman gado ki kwanta, jira nake wani ya shigo cikin su Mas'ood su nema miki magani”.      Da sauri Zinneerah tace, “Granny yama daina ai, bara naje wajensu Bahijja”     Kafin Hajiya Iya tace wani abu harta nufi hanya da sauri. Tana gab da fita yace, “Zonan”.         Tamkar ta fasa ihu taji. babu yanda ta iya dole ta dawo kanta a ƙasa. Batare da shima ya ɗago daga latsa wayar da yakeba yace, “Ki ɗauka min lap-top a ɗaki da abinda kika kai ɗazun”.          Amsa masa tai da to tana fita cika umarninsa. Harga ALLAH yana burgeta saboda baida hargowa. Banda ɗazun bata taɓa ganin yayi faɗaba ko tsawa ma wani a gidan. Shi dai kawai baida sakewane, idan kaga fuskarsa a sake yana tare da Yah Khalipha ne ko Hajiya Iya. A zatonta yanda yasan ita ba komai bace a gidan face mai cin arziƙinsu zaita karta mata wulaƙancine. Amma sai taga saɓanin hakan.      Da wannan tunanin ta ɗakko duk abinda ya sakata ta dawo ɗakin. Magana ta samu yanayi da Hajiya iya. Amma ko a cikin ɗakin kake da wahala ka jisa.        Wani shayin ta sake zuba masa zata saka suga uku yace, “two is ok”.     Maida ɗaya tay ta saka masa biyun, daga haka ta ɗauki ƙaramin hijjab ɗinta da waya ta fice ta barsu       koda taje sashensu Bahijja da suka tambayeta labarin yanda ta ƙare da kai shayi catai musu ai babu abinda ya faru, dama takai masa shayin yana wanka ajiyewa kawai tayi ta fito abinta. Mararta ke mata ciwo kaɗan-kaɗan shiyyasa taje ɗaki ta kwanta ganin sun fito.        Meenal tace, “Yo tsoro mukaji kar wani abu ya faru yazo ya haɗa damu. dan laifinmu sai yafi naki. cazaiyi mune bamu nuna mikiba yasin”.      Ƙaramar dariya kawai Zinneerah tai ta zame ta kwanta. Daga haka suka cigaba da hirarsu. Daga ƙarshe ranar anan ta kwana abinta. _____________________★     *DANYA*      Ta daɗe kwance tana maida numfashin gajiya dana yunwa daya jigatata. Kafin ta miƙe dan ɗan kunun da tasha ya taimaketa. Ledar data shigo da ita ta jawo, ta buɗe tana fiddo kayan da malam ya haɗa mata da ƙara bitarsu yanda bazata mantaba. Baki ta washe na farin ciki tunawa da baba ya kusa dawowa gareta. Ta ɗaga wata ƴar kwalbar turare tana jujjuyawa.         “Yanda ka bani wahala akan ƴarka Sule, sai na sakaka mantawa da ita na har abada acikin jerin ƴaƴanka. Duk dukiyata data salwanta dan ganin ka dawo saina fansheta a jikinka ko sisi bazanyi asaraba. Ƴan uwanka kuwa dake aibantani a gari cewar ta sanadina kabar Danya zan koyar dasu hankali a sannu, duk sai kunsan kunyi da Asabe wlhy”. Ta ajiye kwalbar tana cigana da dariyarta. Maida komai tai a ledar bayan ta ɗauka wasu layu guda biyu ta fice a ɗakin.         Inda murhun girkinsu yake ta nufo. kasancewar jiyama ba girki sukai a gidanba yasa ta turbuɗa hannunta tsakkiyar tokar hankali kwance ta fara tonawa. Sai da ta ƙwakule tokar duka tasa icce ta fara tona ƙasar sannan ta saka layun nan guda biyu ta maida ƙasar da tokar ta rufesu ruf tamkar komai bai faruba. Duk da basu da isashen hatsin yin tuwon dare a gidan haka ta tattare ɗan wanda Yaya gajeje ta kawo musu daya rage ta wanke ta fita kai niƙa da kanta. Tasan ko jiran Tinene tace zatayi tayi a banza, baizama lallaima ta sake ganinta gidan a yanzuba kuma.        Da ƙyar ta samu Malam Mati yay mata niƙan akan bashi zata kawo masa kuɗin. Rai ɓace ta baro injin saboda yarfin da malam mati ɗin yay mata a gaban yara. Tai ƙwafa kawai da ayyana rashin mutuncin da zatai masa shima.          Sa'a ta iske a gidan tana shara, da alama ganin gidan datai kaca-kaca yasata takaici tana shigowa tahau aikinsa. “Sannu innarmu. Tun ɗazu nazo ai gida babu kowa ga ko ina kaca-kaca kamar ba mutane ke rayuwaba. Shiyyasa na hau aikin nan”.         Baki innar ta taɓe tana ajiye ƙwaryar da tayo niƙan dawa a ciki. “Kin san dai Tinene ba moriya takesoba, ke kuma tunda kin zaɓi dangin ubanki sama dani wazai gyara mani”.         “Kiyi haƙuri dan ALLAH Innarmu”.      Banza tai mata. saima ƙoƙarin fara haɗa wuta a murhun data saka layun nan ta farayi, itama Sa'a sai ta cigaba da sharar tsakar gidan ranta duk babu daɗin. Bayan ta gama sharar ta tattara duka kwanika ta hau wanke-wanke da ruwan data fita ta roƙo a maƙwaftansu dan gidan ko ruwa babu. Itama Inna shita samu ta ɗiba tasa ruwan tuwo. Tsaf ta gama wanke-wanken shima ta ɗauki botiki ta fita dan dama ta gyaro ɗakunan.        Sa'a na fita Inna ta miƙe ta ɗakko sauran kayan da malam ya bata ta ƙarasa yin yadda yace, sannan ta cigaba da hidimar girka tuwonta.        Haka Sa'a taita kai kawon ɗibar ruwa har sai da ta cika ko ina na gidan sannan tai zaman hutawa. Sai a lokacin Tinene ta dawo gidan niƙi-niƙi da ledar kayan ƙwalam da maƙulashe. Yanda tayi tamkar bataga Sa'a bane ya bata haushi tahau zaginta, a take suka harƙume faɗa. Inna najinsu da kallonsu taƙi ta tanka sai da ta gaji da hayaniyarsu ta kora Sa'a wai ta tashi ta koma inda ta fito ita batason fitina.        Da haushi Sa'a taja hijjabinta ta fice a gidan tana sharar hawaye...... __________________________★ *_SHIRA'S FAMILY_*          Washe gari a bazata suka tashi da baƙuncin matar Yah Adnan. Lokacin duk suna dining suna karyawa saboda masu fita makaranta. Sai dai shi bandashi, amma yana zaune a falon shi da Khalipha suna magana akan wasu takardu dake baje a centre table ɗin falon, shi yanata danna lap-top Khalipha na gefensa yana masa magana da takarda ɗaya a hannunsa.      Kasancewarsa a falon yasa babu yawan hayaniyarsu, dan Baffah ma bayanan yayi tafiya tun shekaran jiya. Iyakar sune kawai a falon suna taya Zinneerah murnar wayarta kowa na ƙoƙarin saka mata Number ɗinsa.        Hajiya iya ce ta fito daga kitchen ɗin ita da baba Rahi tana faɗin, “Oh ALLAHU ni Amina. Yanzu dan ALLAH zaman latsa wayoyi zakuyi ko karin kuyi ku tafi makaranta. Sai kuma kun makara ku ishi mutane da mitar an saku makara”.       Alamar roƙon tayi shiru suke mata wai dan kar Yayansu yaji. Basu sanma duk abinda suke tun ɗazun yana jiyosun ba. Ya sharesune kawai saboda aikin dake gabansa mai matuƙar muhimmanci ne. Suna fidda kuɗaɗen da zasuyi ginin company shinkafa ne da waken suya. Shiyyasa tun jiya yake busy. Da niyyar yin noman shinkafar kawai yazo Nigeria, sai dai Dr Mahmud da Khalipha sun canja masa tunani da shawarar mizai hana ya buɗe company kawai tunda dai yanzu Alhmdllh noma ya fara farfaɗowa a arewan. Ya yarda da Dr Mahmud sosai, dan ya jima yana bashi shawara tai masa amfani kuma, Shiyyasa ya amince babu wani ja'inja ya fara shirye-shiye. hakama Khalipha na hannun damarsane, akwai shaƙuwa mai ƙarfi a tsakaninsu kasancewarsa mutum maison ƴan uwansa. Kosu sauran yaran gidan gama fahimtarsane kawai basu yiba, shiyyasa suke nuna tsoronsa da ganin tsaurinsa a garesu, dan da shima Khalipha hakanne a tsakaninsu, sai a ɗan zaman da yake tare da shi yanzu London ya fahimci yayansu mutumne mai sauƙin kai da haƙuri, sakewace dai kawai baida ita ga mutane sai wanda yaso. A yanzu haka suna kan yin cinikin wani fili ne da za'a fara ginin company ɗin.        A fusace Hajiya Iya tace, “Anƙi ai shirun dan ubanku”.      Bakuna suka shiga turawa gaba, dan duk ɗinsu sukanji haushi idan ta zagar musu iyaye. Yanda sukayinne ya sata hararsu ta koma kitchen.       Baki Ni'ima ta buɗe baki zatai magana ƙarar takun takalma masu azabar tsini suka katseta. Su dukansu ƙofar suka zubama idanu banda shi da yayma wajen kallo guda ya maida kansa ga aikinsa duk da baisan wanene ba.        “Hii Guys!!”. Ta faɗa dai-dai tana shigowa cikin falon.       Duk idanu suka waro waje na mamakin ganinta matuƙa, dan badan ma akwai hotunan bikinta da Yayansu a gidanba, babu yanda za'ai su iya ganeta. Cikin ƙarfin hali Khalipha ya miƙe yana murmushi da faɗin, “Woow Aunty Farah Surprise Kece tafe haka?”.          Ɗan yatsine fuska tai tana wani yarfar da hannu gefe da juya idanunta manya masha ALLAH, “Oh ko bakuyi murnar ganinaba na koma?”. Tai maganar tana kafe Khalipha daya nufeta da ido. Amsar handbag ɗinta yayi da cewa, “No. no auntynmu, taya zamu ƙiyin murnar ganinki bayan duk gidanan ƙishirwar ganinki sukeyi daman”.       “Oh nice”.   Ta faɗa cike da yanga tana sauke idanunta kan mai gayya mai aiki da yay mata kallo guda tun shigowarta ya maida kansa. Inda yake ta nufa cikin takunta na izza da tsantsar gayu da yanga mai gauraye da wayewa. “I miss you my hero”. Ta faɗa tana kaiwa duƙe ta sumbaci gefen fuskarsa na dama. Tare da nufar bakinsa da ware duka hannayenta zata rungumesa............✍ *_Wa yaga ƙawar su aunty Shahudah ƴar turawa😜😂😂_* *_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 *_★ MADUBIN ZUCIYA_*💖 *_★ DALAAL_*💝 *_★ UBAYD MALEEK_*💓 *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 *_08085405215_* IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   0903 234 5899 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 *_ALLAH ka gafarma iyayenmu🙏🏻😭_*        *_TYPING📲_* *_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_* *Page 23* ______________________ _*YERWA INCENSE & MORE**_ _(The scents with diff essence for YOU& your HOME)_ _(MASARAUTAR KAMSHI)_ _Ina masu neman kayayyakin kamshi yan nahiyar ketaran chadi da Senegal? Kai harma da ingataccen had’i yan bornu? To ku matso domin nesa tazo kusa..._ _YERWA INCENSE & MORE: Sun zo muku da kayayyakin turaruka kamar haka:_ _Khumra kowacce Iri._ _Turarukan Wuta_ _Mopping khumrah_ _Washing khumrah_ _Bathing khumrah_ _body mist_ _kullaccam_ _scented hair cream/spray_ _wardrobe balls_ _carpet spray_ _air-fresheners_ _scented pebbles_ _body sprays_ _oil perfumes_ _Perfumes_ _kabbasa_ _burners_ _coal igniter_ _tong_ _kasko_ _kujerar tsugunno_ _english coal_ _dilke&halwa set_ _scented body mist_ _kai dama sauran kayayyakin da bamu ambata ba, YERWA INCENSE AND MORE, Na tura kayayyakin su ko’ina a fadin Nigeria da ketare. Domin tuntubar su. Suna instagram: _@yerwaincense_and_more. Ko _Facebook site:YERWA _COLLECTIONs. Ko a duba su ta number su: ___08095215215/09044191709! _ _suna bada kayan su kan sari ko sayi dai-‘dai_ _______________________ *Page 23* ...........Mamakinta ya sakashi ɗago manyan idanunsa ya zubasu cikin nata. Ɗunbin al'ajabin sabon salon nata na bayyaya ƙuru-ƙuru a cikinsu. Dan wannan salon iskancin tabbas ba nata bane aroshi tayi saboda wani dalilinta.          Itama ganin yanda ya zuba mata idanunne yasa gwuyawunta yin sanyi, ta sakar masa Murmushin ƙarfin hali da cije leɓenta na ƙasa tana janye jikinta baya.           Duk da yaji ɓacin ran ganin nata bayan ya gargaɗeta jiya da daddare akan kar tazo amma tay watsi da maganar tasa tazo, ga kuma salon isanci data shigo dashi gidan alhalin hakan ba ɗabi'arta baceba sai ya basar ya sakar mata wani lallausan murmushi daya sata sauke ajiyar zuciya babu shiri.      Su Saifudden kam dake dining jin shiru ya sakasu ɗagowa daga duƙar da kawunansu da sukayi, ganin  abinda sukai tunanin zatayi bashi ya faruba duk sai suka saki numfashi. Musamman da suka hangota zaune a gefensa suna kallon juna da murmushi kamar ba yayansu ba. Itama kuma kamar ba itace ta shigo da salon rawar kai ba yanzun. Ta koma Farah ɗinta da suka sani mai tsanin miskilanci a garesu da jan aji.        Cikin magana ƙasa-ƙasa da babu wanda yake iya jiyosa. Dan saima ka ɗauka wani magana mai daɗin gaske yake faɗa mata, yace, “Wannan salon bai dace da ke ba, kowaye ya baki shawarar shigowa cikin shirawa dashi ya ɗoraki a kan keken ɓera da ta zubewar mutuncikine, da sakaki a layin masu ƙarancin tarbiyya”.            Shiru kawai tai tana kallosa cikin ido, tabbas gaskiya ya faɗa mata, dan ita kanta yanda ƙannensa duk suka zubo mata ido sanda ta shigo sai taji kamar ta muzanta a cikin idanunsu.. Dama da ƙyar ta iya dauriyar hawa kan shawarar auntynta da tace ta shigo musu gidan a salon gatse-gatse zasuji shakkarta fiye da da da take musu isa da shariya kawai. Kamar zatai magana sai kuma ta fasa ta ɗago tana kallon sashen dining ɗin.        Ganin duk yanda sukai ƙasa da kawunansu yasa ta wani yatsine fuska tana taɓe baki, dubanta ta maida ga Yah Adnan daya sake maida hankalinsa ga aikinsa. “Baby ku baku iya tarbar baƙo bane da masauki a gidan naku?”. Tai maganar a Farah ɗinta daya sani mai tsananin son nuna isa da miskilanci.       Cak ya tsaya daga danna keyboard ɗin da yakeyi. Sai dai bai ɗago ya kalletaba. Kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa yay wani guntun murmushi na takaici ya cigaba da abinda yakeyi batare daya tanka mataba.        Ganin zata ƙara magana Khalipha yay saurin tareta da faɗin, “Sorry Aunty. muko muka iya tarar baƙi. Amma muje ki gaisa da Granny first”.       “Oh no Khalipha, zan fara wanka kafin na iya gaisuwa-gaisuwa ɗin nan naku da baya ƙarewa”.            Saurin girgiza mata kai Khalipha yay yana nuna mata Yayansu da ido, dan yasan hakan da zatai ba ƙaramin kuskure bane duk da yasan itama ta sani, tunda tafi kowa sanin halin Yayan nasu ai.......        “Kai lafiya na ganku cirko-cirko?”. Hajiya iya dake fitowa daga ɗakinta ta faɗa batare da hankalinta yakai ga Farah ba. Kafin wani ya samu damar bata amsa Farah ta miƙe tsam cikin komawa ainahin takunta ta nufi hajiya iyan. Idanu Hajiya iya ta zuba mata harta ƙaraso gareta dan ta ganeta sarai duk da zuwanta gidan uku ne kacal, kuma duk kwananta bibbiyu ta koma         “Granny barka da safiya” ta faɗa tana ɗan kai jikinta ga hajiya iyan ta rungumota kamar yanda larabawa keyi. Duk da abun yazo banbarakwai Hajiya Iya bata damuba. Dan tasan akwai banbancin al'adu da yanki a tsakaninsu, kuma ko wancan zuwan da tayiyyi haka ta dinga mata gaisuwa, shiyyasa takemata uziri idan tayi wani abun. Hannu biyu ta karɓeta tana sake faɗaɗa murmushinta. Kafin ta ɗagota tana faɗin, “Uhm lallai yau munada manyan baƙi ashe”.        Murmushi Farah tayi cikin  basarwa, dan tanajin hausa ras yine saita gadama take, tafi yin larabcin ƴan Morocco da turanci.            Sai a yanzu suma yaran gidan suka fara gaidata, duk da mamakin a yanda ta shigo gidan ɗazun ya kasa barinsu. Binsu kawai take da kallo tana amsa musu a yatsine. Kowa ta gane a cikinsu tunda tanada hotunansu na biki, duk da sanda akai auren nasu su Meenal basu da wayo sosai, amma tana jin hirarsu bakin Khalipha koshi uban gayyar idan yaso, musamman idan ƙanwarsa tana tare dashi.        Kafe Zinneerah dake can ƙarshe tai da idanu, kamar zatai magana sai kuma ta basar abinta ta maida kallonta ga Khalipha da Hajiya Iya ke masa magana ya rakata ɗakin Moddibo ta huta.         Da to ya amsama hajiya iyan. Shi dai oga na zaune har yanzu yana aikinsa kamarma ya manta dasu a falon, sai da Hajiya iya ta zauna a kusa dashi sannan ya ɗago ya kalleta. Ganin yanda launin idonsa ya canjane ya sata sakin murmushi ta shafa fuskarsa.        “Babba da haƙuri aka sanshi, tunda ta kawo kanta karka wani saka damuwar hakan a ranka. Mu dama ai burinmu ta dinga shiga cikinmu a koda yaushe. Ba daɗin nisantarmu da kuke mukejiba”.         “Amma Granny sau nawa nake cemata tazo domin gaisheku tace batason zuwa. Sai yanzu dan son fitina. Wai kinmaga a yanda ta shigo gidannan da farko ma kuwa?.......”         “Shiii! ya isa, koma dai a wane dalili tazo ko ta shigo kai ka ɗaukesa ƙyaƙyƙyawa a ranka, ka kuma ɗauki ɗamarar canjata yanda kakeso duk da kayi sakaci tun farko, amma lokaci bai ƙure makaba”.      Huci ya ɗan furzar kawai yana jingina da kujera da lumshe idanunsa.          Sudai su Zinneerah da bajin mi su Hajiya iyan ke faɗaba sauri-sauri duk suka kammala cin abincinsu suka miƙe dan suna neman makara. Ɗakin hajiya iya ta nufa ɗakko school bag ɗinta, lokacin data fito su Yah Moos'ab duk sun fice, harsu Jamal ma. Da alama ita kaɗaice ta rage. Sau ɗaya ta kalli sashen da yake zaune har yanzu yanata faman aiki a lap-top, shi kaɗai ne a falon yanzun. Hajiya iya ta tashi zuwa kitchen saka su Baba Rahi haɗama Farah breakfast tare da Khalipha dake nuna musu yanda zasuyi.     Sum-sum ta wucesa a tunaninta baya ganinta saboda aikin da yake kamar ya kwashe dukan hankalinsa.       “Zonan”. Ta tsinkayi muryarsa cikin kunnenta a bazata. A lokaci guda ƴan cikinta da jinin jikinta suka yamutsa na tsoro, tuna maganar su Jamal da sukace baya maimaita magana idan yay maka yasata nufosa. Zinneerah yarinyace mai tarin nutsuwa, sam bata da garaje akan komai, hakan yasa ko tafiya takeyi saika ɗauka yangace. sai dai sam ba haka bane, halittartace hakan. Komai nata cikin sanyi da nutsuwa bana sakarciba ko rawar kai.        Gabansa takai tsugunne kanta a ƙasa tana faɗin, “Yayanmu gani”.        Batare daya ɗago daga abinda yakeba, a daƙile yace, “Ɗiba tissue ki kwashe wannan jambakin”.         Ɗagowa tai babu shiri ta kallesa tare da waro manyan idanunta masu tsananin haske, cikin suɓucewar baki tace, “Iyeee Yayanmu miye laifinsa? Malaman basa faɗa f.....”        Sai kuma tai saurin ɗora hannunta a baki saboda tuna a ida take.       A karan farko yaɗan ɗago ya dubeta, hararar data saka kayan cikinta sake hautsunawa ya wulla mata tare da maida kansa ga aikinsa. Da sauri takai hannu ta cira tissue ɗin dake a centre table ta kaisa kan bakinta ta kwashe pink lipstick ɗin da yay mata ƙyau sosai tana ƙoƙarin haɗiye ƙwallarta. Cikin ɗan rawar murya tace, “Na kwashe”. Yanzun ma batare daya ɗagoba yay mata nuni da hannu alamar taje.      Tana miƙewa Hajiya iya na fitowa da ga kitchen, tabi Zinneerah ɗin da kallo. “Inno lafiya baku tafi bane?”.       Ɗan juyowa Zinneerah tayi kanta a ƙasa tace, “Eh Granny yanzu zamu tafi”. Daga haka ta fice da sauri kafin hajiya iya ta sake cewa wani abu. Duban inda yake zaune Hajiya iya da zuciyarta ke ayyana mata ba lafiyaba tayi, “Moddibo mike faruwane da Inno, ko wani abu akai mata?”.         “Waye haka?”. Ya faɗa yana ɗan ɗagowa ya dubeta. Harara ta zabga masa tana kaiwa zaune. “Kaifa wulaƙancinka yawane dashi Moddibo, ita Zinneerah ɗince baka saniba ko yau na fara kiranta Inno a gabanka?”.       Ɗan murmushi yayi hankalinsa a aikinsa, a taƙaice yace, “ALLAH ya baki haƙuri”. Daga haka yaja bakinsa ya tsuke batare daya amsa mata maganar farko ba.        Ƙwafa tayi ta miƙe da sauri ta nufito ƙofar fita danta leƙa. tana fitowa maigadi na rufe gate alamar su Zinneerah sun wuce. Dawowa tai ranta daɗan damuwar ALLAH yasa ba wanine yayma Zinneerah ɗin wani abuba mara daɗi. Koda ta dawo falon bata kulashi ba saima harar inda yake da tayi ta shige ɗakinta abinta.        Murmushi yayi a karo na biyu yana girgiza kansa. dan yaga hararar da Hajiya iyan tai masa. Ajiye lap-top ɗin yayi zai miƙe Khalipha ya fito ɗauke da tire. Yaɗan bisa da kallo harya ƙaraso inda yake. “Yayanmu ga abincin Aunty”.      Kauda kansa yayi yana ƙarasa miƙewa. Sai da ya raɓa Khaliphan zai wuce sannan ya bashi amsa da, “Ka ajiye mata anan mana ta fito taci inma zatacin”.        Sanin abinda Yayan nasu ke nufi ya sakashi yin ƙaramar dariya, ganin zai shige yace, “To kaima ai baka karya ba”.        “Karka damu Besty yau ina azumine”. Ya bama Khalipha amsa yana shigewa corridor ɗin ɗakin nasa.          Zaune a bakin gado ya iske Farah ɗaure da towel nashi ajiki alamar wanka tayo. Sallamarsa ta sakata saurin zare wayar dake a kunnenta ta ajiye alamar magana takeyi da wani, kuma bataso yaji. Wayar yaɗan kalla tamkar zaiyi magana sai kuma ya fasa.         Cike da basarwa itama ta miƙe duk da tasan ya fahimci waya take ya basar dan shi mutum ne mai lura. Sai dai bai zama lallai ya nuna makan ya fahimtaba sai yaso.            Ganin yanda ta ciskule fuska cike da isar tata shima sai ya basar da ita ya nufi wadrobe zai dauka abu. Bayansa ta harara da miƙewa sanin idan miskilancine ya fita iyawa. Rungumesa tai ta baya tana jero masa kalaman kewarsa da tayi a kwanakin nan da basa tare. Komai bai ceba sai janyeta a jikinsa da yayi. Tabbas yana son Farah fiye da hasashen mai tunani. Dan duk inda mace takai ƙyaƙyƙyawar Farah takai, a zaman takewarsu tana ƙoƙarin ganin ta ƙyautata masa da faranta masa. matsala ɗaya ce ke cimasa tuwo a ƙwarya game da ita zuwa uku. Na farko shine ƙin danginsa. Sai dai yasan wannan training ɗin su Mammah ne, dan mafi yawan rayuwarta a hannunta tayi. Shiyyasa yakan mata uziri da hakan da ƙoƙarin ganin ya canjata. Sai kuma shegen kishinta da sam ta tsani taga wata mace ta raɓesa koda a wayane, ga ɗan banzan zargi daya tabbatar duk kishinne yake kawo matashi. Na uku son isa da nuna gadara a dole ita isashshiyace ƴar masu mulki.       Zaune yakai saman sofa yana lumshe idanu. Da wannan damar tazo ta zauna a cinyarsa tana ɓata fuska da faɗin, “Wai kana nufin fushi kake dani? Bayan nice ya kamata nai fushi da kai Yah Mutallab”.       Banza yay mata kamar bazai tankaba, sai da yaji ta fara masa murje-murje a jiki cike da salo ya buɗe idanunsa da sauri. “Kinga tasarmin a jiki azumi nakeyi”.       “Azumi kuma? Nami to?”. “Ina ruwanki da ko namiye?”. Ya faɗa yana tureta.        Kallonsa tayi da ƙyau idanunta na kawo ruwan hawaye dan tanada saurin kuka dama. Muryarta na rawa tace, “Dan nazo gidanku zakaimin wulaƙanci?”.          “Anmiki wulaƙancin, ni bance karkiyi abuba amma kikayi saboda kin rainani yanzu kina ganina dai-dai dake ko? Sannan tsabar iskanci wai gidanmu zaki shigo da wani salon sakarci, yanzu da Hajiya iya ko Baffah wani na falon kika shigo ɗin nan mi zasuyi tunanin kin koma kuma?”.        A take jikinta yayi sanyi, hawaye na rige-rige sake zubowa. Kamar baza tayi maganaba sai kuma mita tuna oho mata ta kallesa da sakin ƙaramin murmushi tana share hawayenta. “Kayi haƙuri nayi kuskure, kuma daka tabbatar min hakan sai naji ban ƙyautaba, nima kuma salon bai dace dani ba sam. Amma maganar tahowa ba laifina bane har da su Mammah”.        “Tunda su Mammah ɗin ke aurenki saiki kirasu ki sanar musu kin iso su nema miki wajen zama. dan ba zaki zauna a gidan nan ba. Lokacin da nake lallaɓaki kizo domin gaishesu matsayinsu na iyayena kai tsaye kike cemin bakison zuwa inda suke. To suma yanzu basa buƙatarki”.         Ya ƙare maganar da miƙewa ya fice a ɗakin batare da ko waiwayenta ya sakeyiba.        Bayansa ta raka da kallo idanunta na wani ƙankancewar bacin rai, ta cije baki zuciyarta na mata zugi da sakejin zargin jiya na dawo mata a rai sabo. Tabbas huɗubar aunty data hauce taso jamata wannan wulaƙancin nasa. Duk da dama bata isa tanƙwarashi ko juyasa yanda takeso ba tunda shima bauɗaɗɗen ne, dan ya fita zafin kai da shegen taurin kai tamkar shine jinin mulkin ma ba itamba.         Tayi alƙawarin bazata ƙara kamanta irin kuskuren dataso tafkawa a yau ba nason kwatanta zubar da kimarta. Dan wani raɗaɗi takeji a zuciyarta idan ta tuna a yanda ta shogo gidan a dole ita wayayya. Bandama shirmen aunty data bata shawarar ba ita kuma ta hau ai ko ba'a faɗaba duk wanda ya ganta yasan wayayyace ita, bawai saita nunama duniyaba kodan jinin mulki dake yawo cikin jikinta da tarihinta.            Taja ƙaramin tsaki da ɗauka waya ta kira Mammah, labarta mata duk yanda sukai yanzun tayi. Faɗa sosai Mammah keyi kafin ta yanke wayar domin nemansa.        Itakuma sai ta juya akalar kiran ga auntynta. dan dama da ita suke waya ɗazun daya shigo, itama ta labarta mata komai daya faru da nuna mata gaskiya shawaran data bata na shigowa gidan a yanayin gatse-gatse baiyiba. Dan gashi hakan da tayi yaso taɓa mata kima har a idanunsa, balle ƙannensa da tasan suma kowa ya gumtsi gulma ne dan babu damar yi a gabanta ne ko shi Abdul-Mutallab ɗin dan tasan yanda suke shakkarsa a gidan.        Itama dai auntyn tata kamar Mammah faɗan ta kamayi kamar Adnan ɗin ne a gabanta. Ta kumace ita ai batace tayi gatse-gatse a gabansu kamar wata sashasha ba ko mara tarbiyya, tadaice ta nuna musu banbancin da da yanzun kawai, daga haka ta yanke wayar itama ta koma neman Yah Adnan ɗin.       Su dukansu daga can nemansa a waya suka shigayi, sai dai babu wanda ya iya samunsa dan cama ake musu switch off. Mammah tai ƙwafa dan tasan kashe wayar yayi tunda yasan tsiyar daya shuka.          A falo kam a yanda ya fito ɗakin a fusace ya fice abinsa yasa Khalipha dake zaune yana karyawa fahimtar babu lafiya. Duk da dama dai ba wannan ne karon farkon daya fara ganin rikicin yayan nasu da matarsa ba. Duk da shi yayan nasu kan kauce faruwar hakan a gaban idonsa, amma da yake Farah mace ce mai nacin masifa da mita saita kaisa ƙarshe ya yaɓa mata maganar da zata koma rusar kuka. Dama kuma da yawan faɗan nasu ana yinsane akan zamansa gidansu nacan london ɗin, dan kullum zancenta baya wuce sai ya barmata gidanta ya koma hostel da zama.       Hajiya iya na ɗaki tana gabatar da walha dan haka batasan wainar da ake toyawaba. Sai da ta idar ta fito ne ta iske shi da Khalipha ɗin duk basu a falon. Baba Rahi ma ta sake gyara falon tsaf sai tashin ƙamshi yake. A tunaninta yana ɗaki tare da matarsa yasa bata damuba ta koma ɗakin danta ɗan kwanta itama ta huta.    ________________________ *_DANYA_*             Yau a lissafi kwanaki bakwai kenan da bizne aikin Malam da Inna tayi, hakan yasa tun a daren jiya take zuba ido akan dawowar baba. Sai dai har garin ALLAH ya waye babu shi babu labarinsa. Bata damuba dan tasan akwai yau.     Aiko yau ɗinma dai tunda gari ya waye idanunta basu huta da kallon ƙofa ba. Da taji an motsa ƙyauren gidan sai ta hau washe baki, sai kuma taga bashi ya shigoba saita haɗe fuska dajan tsaki. Kamar wasa tana zaune a bishiyar tsakar gidan har aka kira azhar. Maimakon ta tashi tai sallar sai ta cigaba da zama wai idan ya shigo ta haɗa duka tayo ai.      Duk wannan zaman zuba ido da Inna keyi na dawowar Baba Tinene na a gidan tana wanki, ta ƙure waƙa a wayarta da inna bata taɓa tambayarta daga ina ta samotaba. Koda ta tambayi Innar zaman mi take ta sanar mata sai kawai ta hau dariyar shaƙiyanci tana faɗin, “Oh kice tsohon tsimin soyayya ne ya motsa Innarmu”.      Banza Inna tai mata tunda tasan ba kunyace da Tinenen ba, yanzu saita yaɓa mata wata maganar. Haka ta cigaba da zama a wajen har akai sallar la'asar. Tinene data gama wankinta har tayi wanka tana kwashe kayan da alama fita zatayi a gidan. Buga ƙyauren gidan da akai da masifar ƙarfi ya sakasu dubar hanyar zauren a firgice su duka.        A bazata Karima ta shigo gidan jaye da akwati buju-buju da ita tamkar wadda aka ƙwato daga bakin kura. Babu shiri Tinene ta watsar da kayan hannunta ƙasa. Innama ta zabura kan Karimar dake tafiya kamar ma da tangaɗi.       “Mi nake gani haka ni Asabe. Karima daga ina kike tahe da maraicen nan?”.      Ina babu bakin amsawa daga Karima, sai ma zubewa datai a ƙasa cikin hakki tace, “Innarmu ku bani abinci yunwa nakeji”.        Tinene dake tsaye tana kallonsu har yanzun tace, “Tab abu mai wahala anan gidan yanzu Yaya Karima, amma bara naga inada wazobia ko awarar gidan Rashida a samo miki idan bata ƙareba dan maraice yayi”.      “Nagode auta. Inna bani ruwa”. Ta sake faɗa tana kaiwa kwance da zare hijjabin jikinta gaba ɗaya ta jefar. Ruwan Inna ta ɗebo mata da sauri ta kawo mata, ta ɗagota daga kwancen da take danta bata sai a lokacin idanunta suka sauka akan sayin duka dake a wuyan Karima da damtsen hannunta ruɗu-ruɗu ga tsohon ciki. Duk da kasancewarta baƙa hakan bai hana fitar sayinba da ƙyau.       “Na shiga uku ni Asabe waya maki wanga bugun haka ga ciki Karima? Badai sheɗanin yaron nanbane Babawo?”.       Karima ta sake zamewa ta kwanta cikin tirɓayar jar ƙasar batare data bama Inna amsaba. Ganin Innar zata takura mata tace, “Inna ki barni dan ALLAH, ku bani abinci nide karna matu”.       Kafin Inna ta samu bakin sake cewa wani abu Tinene ta shigo gidan ɗauke da farar leda da awara a ciki. Kwano ta dauka a wanke-wanke ta juye mata takai gabanta. Cikin rawar jiki Karima ta tashi zaune taja kwanon. Bibbiyu ta dinga haɗa awaran tana turawa a baki. Ganin tana neman shaƙewa Inna tai azamar bata ruwa ta sha. Koda ta cinye saita kuma zubewa tana sauke numfashi wani irin zufa na karyo mata ta ko ina duk da kuwa awaran bamai zafi baceba.      Sudai suna tsaye shiru cirko-cirko kowanne da kalar tunaninsa akan wannan al'amari..........✍                      *_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 _Na Safiyya Huguma_ *_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖 _Hafsat Rano_ *_★ DALAAL_*💝 _Na Miss xoxo_ *_★ UBAYD MALEEK_*💓 _Na Mamu gee_ *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 _Na Bilyn Abdull_ Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 *_08085405215_* IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   0903 234 5899 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 *_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_* *_TYPING📲_* *_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_* *Page 24* _________________________ _RANO NET! RANO NET! RANO NET!_ _WHO NO LIKE BETA AWUUF THINGS?_ _IDAN KAJI GANGAMI DA LABARI....! INA MASU ZUBIN ADASHEN DA BA RANAR DAUKA NA DATA?_ _TO KU MARMATSO KUJI, KU KUMA SHARE HAWAYEN KU, MUNZO MUKU DA SABBIN TSARE TSARE NA DATA, WADDA KOWA ZAI IYA SAYA DAI DAI KARFIN SA. A FARASHI MAI RAHUSA_ _RANO NET! RANO NET! RANO NET!__ _(Afford data at chikini price)_ _MALLAKI DATA A KUDI KALILAN DA RANO NET_ _TSAYA KUJI, A RANO NET ZAKA IYA ZAMA RESELLER KO WHOLESALER KAI MA, EH ZAKA/KI IYA ZAMA MA SAYAR DA DATA A FARASHIN SARI MUKE BAYARWA, KAI/KI KAFA KASUWANCIN KU KUMA. DA KUDI KALILAN._ _MUNA KUMA SAYARWA AKAN ‘DAI DAYA, KOWANE NETWORK MUNA SAYARDA DATA PLAN DINSA AKAN KUDI KALILAN, MASU FARASHIN SARA KUWA MA KU KUDIN BAI KAI HAKA BAMA_ _AIRTEL_ _9MOBILE/ETISALAT_ _MTN_ _GLO_ _DUK MUNA SAYARDA TSARIN DATA DINSU. KAMAR MISALI MTN MUNA SAYARDA 1GB.24MB AKAN FARASHIN NERA 300 KUMA YANA KAIWA WATA DAYA, GWARGWADON YADDA KAKE AMFANI DA DATA, 2GB 600, 3GB 900!!_ _DUKA WADANNAN TSARIN DATA DAMA NA SAURAN LAYIKA MUNA SAYRWA AKAN FARASHI MAI RAHUSA, WANDA KOWA ZAI IYA YIN TSARIN DAI DAI ALJIHUN SA_ _Ranonet.com.ng_ _GA SITE DINMU NAN DAKE YANAR GIZO, KAI TSAYE ZAKI/KA IYA SIYAN NAKA TA NAN. _ _KO A TUNTUBE MU TA NAMBAR TARHON MU: +234 803 081 1300/+234 808 540 5215_ _KYAU, INGANCI, RAHUSA, ADADE ANA YAWO A YANAR GIZO SAI RANO NET._ _RANO NET..!!!!_ ________________________ *Page 24* ...........Koda Farah ta gama surutan haushinta gado ta faɗa daga ita sai towel ɗin da tai wanka tai kwanciyarta batare data tuna ya kamata taje ta gaida matan gidanba. Barcinta tasha sosai kafin ta miƙe saboda shigar kiran salla a kunnenta dan bata da sakaci da ibada. Ruwa ta ƙara watsowa tayo alwalar salla.       Koda ta fito ta gabatar da sallar kwalliya tayi dai-dai misali ta shirya cikin baƙar doguwar rigar jallabiya mai ƙyau, ɗan kwalin rigar ta naɗa a kanta yanda larabawa keyi dai.        Farah ƙyaƙyƙyawa ce kamar yanda mijinta ya faɗa. Tanada jiki mai ƙyau ga kuma ilimi, matsalarta kawai itaɗin ƴar gatace ta gani kasheni, ƴar shagwaɓace bugun farko kuma jinin mulki. Dan itace auta a gidansu shiyyasa kowa sonta yake. Sannan ta girmane a Morocco hanun kakarsu dan a wajen haihuwarta mahaifiyarta ta rasu, daga bayane bayan rasuwar kakar tasu itama riƙonta ya dawo hannun Mammah duk da babbar yayarsu taso ita ta zauna a hannunta. Tana da son girman tsiya da miskilanci, dan koshi kansa oga kwata-kwatan yimasa isarta da taƙama takeyi. Sai dai shima da yake gwanine wajen iyawa duk da baɗan masu mulkin bane sai sukeyin dai-dai da juna harma ya kaita ƙasa ta risina tana mitar ya cika baƙin hali.         Tana son Yah Abdull-Mutallab kamar yanda kowama yasan shima yana sonta. Sai dai tanada matsalar tsananin kishi, wanda da alama ta gadane wajen su Mammah. Dan ita kanta Mammah ɗin ta rabu da Baffah ne saboda kalmar ƙara auren nan daya furta gareta duk da ɗunbin son da take masa har yanzu. Dan ko aure taƙi sakeyi.       Bayan ta shirya ta feshe jikinta da turarenta masu shegen ƙamshi da ɗaukar hankalin mai shaƙa ta fito. A falo ta sami Khalipha daya shigo zaune yana lunch. Ta ƙarasa inda yake taja kujerar dining ɗin ta zauna itama. Duk da ya girmeta shine ya fara gaidata dan yasanta da son girman tsiya. Babuko kunya ta amsa masa kuwa tana buɗe kulolin dake dining ɗin.        Yanda take yatsina fuskarta ne ya tabbatarma Khalipha komai bai mataba a wajen. Dan haka yay ɗan murmushi da fadin, “Ki faɗa abinda kike son ci sai a sayo miki idan duk nanan basu mikiba”.      Kanta tsaye kuwa ta shiga zayyano masa duk abinda takeson ci ɗin. Batare da damuwar komaiba kuwa ya miƙe ya fita dan dama ya kammala nasa cin abincin.      Khalipha na fita babu jimawa su Zinneerah suka shigo gidan. Ita kaɗai ta shigo sashen na Granny cike da ƙarfin hali dan mararta ciwo take mata. Batare data lura da Farah dake zaune a dining tana latsa wayaba ta nufi ɗakin Hajiya iya.     Farah da tun shigowar Zinneerah ita idanunta suka sauka gareta ta wani bita da kallo a yatsine tanajin rashin son yarinyar a ranta haka kawai. Sai dai kuma mamaki take ita wacece a gidan ma? Dan bata santaba a tarihi da labari. (To anya kuwa ƴar gidan nan ce?) ta ayyana a ranta gabanta na faɗuwa. Yunƙurawa tai ta miƙe zata bita ɗakin Hajiya iyan dan yanda Zinneerah ta wuce bata gaidataba sai abin yay mata zafi taga kamar rainine dan ta lura da yarinyar itama akwaita da nuna isa tun kallon datai mata ɗazun, sai kuma mita tuna oho mata ta koma ta zauna tana yin ƙwafa.        Zinneerah kam da batasan tanayiba tana shiga suka gaisa da Hajiya Iya wanka ta shiga. Bayan fitowarta ta shirya cikin doguwar rigar boyal less da yay mata ƙyau ɗas a jiki, dan ɗinkin ya zauna da ƙyau masha ALLAH. Tayin abinci hajiya iya tai mata. Amma sai tace ta ƙoshi sai anjima. Basu jima da cin abinciba a makaranta. Daga haka ta kwanta a sofa sai barci.        Barci tayi sosai, dan bata farkaba sai bayan sallar la'asar da Hajiya Iya ta tadata. Toilet ta shiga ta ɗan gyara jikinta ta fita zuwa falo cin abinci. Yanzu kam mafi yawan yaran gidan sun dawo. duk suna ma a falo zaune suna hira har Granny. Sai matar yayansu baƙuwar ɗazun dake zaune gefe ta haɗe fuska tamau kamar tanajin warinsu.     Cikin ƙarfin hali tai mata barka da yamma. Batare da sauraren amsartaba ta gitta zata wuce saita dakatar da ita. Juyowa Zinneerah tai gareta fuskarta ɗauke daɗan murmushi. A ɗage sosai Farah dake ƙarema Zinneerah kallon sama da ƙasa tace, “Kema anan gidan kike?”.       Kai Zinneerah ta ɗan jinjina mata kawai batare datace kimaiba.     “Uhyim! Amma ban sankiba ni”. Kallonta Zinneerah tai cikin ido kamar zatai magana sai kuma tai shiru fara'ar fuskarta na raguwa. Dan tsaf ta fahimci dizgata matar Yayan nasu da taji suna kira da Aunty Farah ke neman yi. Itama Farah ɗin da har yanzu ke mata kallon wulaƙanci da isa duk da kuwa babu wani abin kushewa tattare da Zinneerah ɗin, dan duk da take ƙyaƙyƙyawa babbar yarinya babu abinda zata nunama Zinneerah, itama idan dirin jikinne ALLAH ya bata, musamman ma yanzu da take a kan ganiyarta na kammaluwar sirrikan budurci, sannan jikinta a mulmule yake dan ba siririya bace bakamar Farah ɗin. Ga fatarta kalar ɗaukar hankali gamai kallo. ta buɗe baki zatai magana Hajiya iya ta katseta dan dama ta saka musu idone taga mi Farah ɗin zatayi.        “Tunda ba zuwa cikinmu kikeba ta yaya zakisan kowa. Ke Zinneerah wuce kici abinci”.      Sum-sum Zinneerah ta wuce dining tana ƙoƙarin maida duk wani ɓacin ran Aunty Farah ɗin daya fara yunƙuro mata. Dan a rayuwa ta tsani wulaƙanci da raini da disgi a rayuwarta. Zata iya jure komai banda waɗannan abubuwan.      Sosai su Jamal sukaji daɗin abinda Hajiya tayi, itako Farah a fusace ta miƙe tabar falon zuwa ɗakin mijinta. Yi hajiya iya tai kamarma bata ganiba. Ta kuma haɗe fuska dan karma wani a cikin yaran yace wani abu. Daga hakama hirar ta watse. Dan barin falon itama Hajiya iya tayi.          Kusan 6 Zinneerah da tuni suka fice suna can harabar gidan anata hira ta shigo sashen hajiya iya saboda matsa mata da mararta tayi. Bedroom ta nufa inda ta iske hajiya iya na waya. Sai da ta kammala ta dubeta tana ajiye wayar data gama ɗin.  “Fitinar Moddibo dabance wlhy. Inno dubamin ko su Rahi sun wuce?”.        “Lah Granny ai sun tafi, bakuyi sallama bane?”.      “Munyi sallama. Na zata basukai ga tafiyar banebam wannan fitinatunne yay kirana yanzu, wai ashe azumi yakeyi amma bai faɗaba tun ɗazu ba sai yanzu. Kuma wai abinci yakeson a haɗa masa. Gashi su Rahi ba tuwo sukaiba yau”.       Cikin ƙarfin hali Zinneerah tace, “Granny yaya za'ai yanzu to?”.          “Nima ban saniba to Zinneerah, sai dai ko ke zaki shiga kitchen ɗin ki haɗa masa tunda waccan malalaciyar matar tasa na tabbata ƙila ko shayi bata iya dafawaba balle wani tuwo”.      Idanu Zinneerah taɗan waro waje da faɗin, “Kai Granny nikuma? Ta ina zai iya cin jagwalgwalona”.       “Ci kuwa zaiyi harda santi Inno na. Kinga tashima kije kar ya dawo ya samu ba'ayiba ya fara baƙar zuciya danshi baya wasa da cikinsa. Tuwon zaki masa da ɗan wani abun mai sauƙi tunda azumi yakeyi”.        Zata ƙara magana Hajiya Iya ta girgiza mata kanta. “Kinga babu abinda zai faru, lafiya lau zakiyi insha ALLAH kinji ƴar albarka. nina ai dana idar da sallar magrib zanzo nama tayaki muyi tare”.     Jin abinda Hajiya Iyan ta faɗa ya sata miƙewa tana fadin to ta fice zuwa kitchen da kwarin gwiwarta. Sai da ta fara karanto addu'ar nasara kafin ta ɗauraye tukunya tasa ruwan tuwo dai-dai misali, dan itama dai tana ganin tuwon zataɗanci ko zataji sassaucin ciwon marar nan da taketa dannewa dan karta tadama hajiya Iya hankali.       Cikin ƙanƙanin lokaci ta kammala tuwon semo.. data bama nutsuwa sosai gudun yimasa kuskure, sai da ta kammala kwashewa zuciyarta keta ƙara ƙarfafata akan miyar da taketa tunanin masa tunda ta fara tuwon. Ɗanyen kifi ta cira ta gyara tasashi a wuta da kayan ƙamshi da albasa dan rage masa ƙarni. Kafin ta koma ta ɗiba kayan miya zallar attarigu da tattasai sai albasa da tumatur guda biyu kacal ta wankesu suma tasa a blender da ɗan ruwa bamai yawaba can tai musu markaɗe ɗaya da yay kamar jajjage amma yaɗara jajjagen laushi kaɗan. Kifin ta sauke ta tsamesa a ruwan ta buɗesa ta cire ƙayarsa duka ta farfasashi, ta ƙara ɗora tukunya tasa manja a wuta ta zuba wannan fasashshen kifin da albasa da magi ƙwara ɗaya ta rage wutar can ƙasa. Sallamar hajiya iyace ta sakata juyawa tana kallonta. Ta ƙaraso cikin kitchen ɗin tana magana cike da tsokana. “Wai wai, anya kuwa yau kunnen moddibo bazai kai ƙasaba Inno. Irin wannan ƙamshi haka da aka cika mana gida”.      Dariya Zinneerah tai tana faɗin. “Kai Granny bammafa fara miyanba”.        “Amma kuma ga ƙamshi ya cika ko ina”  Hajiya iya ta faɗa tana buɗe tukunyar data saka kifin nan dake fidda ƙamshi mai daɗi a cikin manja. “Masha ALLAH miyar mi zakiyi?”.        “Granny ɗanyen kalkashin nan dana gani da zanyi”.        “Eh lallai kinyi tunani mai ƙyau, dama ɗazun Rahi tazo dashi wai ko zamuyi amfani dashi a gidanta suke ɗan shukashi”.      “Aiko gashi yayi ƙyan fita Granny. shiyyasama ya birgeni. Kuma ta taimaka ta tsinkesa tun daga can yankawa kawai zanyi yanzu nasa a wuta”.       “To bara na tayaki yankawa saiki haɗa miyar”.     Babu musu ta bama Hajiya iyan, tunda dama tanason ɗan haɗa masa ko fruit salad ne haka da ɗan coconut juice idan zata iya. Ganin kifin ya mata yanda takeso ta zuba kayan miyarta a ciki da daddawa ta ƙara rufewa. Inda suke ajiye kayan fruit taje ta ɗauka komai dai-dai misali ta ajiye gefe, ta ɗauka kwakwa ta fasata itama ta ajiye gefe. Komawa tai ga miyarta taga kayan miyan yaɗan soyu, saita zuba ruwa ɗan kaɗan da kayan ƙamshi da magi amma ba star ba dan yana hana miya yauƙi. Da duk abinda take buƙata na saka miya ƙamshi ta saka ta maida ta rufe a binta da sake maida wutar can ƙasa. Dai-dai Granny ta gama yanka mata ɗanyen kalkashin. Amsa tai tana mata sannu da godiya. Granny ta bita da kallo tana murmushi. Madaidaiciyar tukunya ta samu ta saka kalkashin nan dan babu zancen wankesa shi. Tasa ruwa kaɗan da kanwa ta barsa a buɗe wutar naci daidai misali.     Fita Granny tai dan an kira sallar isha'i, ita kuma tahau gyaran fruit salad ɗinta dan ɗan kaɗan zatayi ba yanda aikin zai mata yawaba. Saiko gashi ta gama a ƙanƙanin lokaci, tasa flavor na gwaba dana strawberry ta motsa. Kaɗan ta ɗan-ɗana, jin zaƙin ya mata dai-dai ta ɗaukesa tasa a fridge ta dawo wajen miyarta da dudduba. Komai yayi, kalkashinma ya dahu, kashe gas ɗin tayi ta koma wajen gyara kwakwar da zatayi juice itama, tabar kalkashinta dayay kauri sosai yana hucewa. Hakama miyar kayan miyanta tayi kauri yanda ko an haɗata da kalkashin bazata tsinkashiba. Sai da ta kammala haɗa coconut juice ɗinta ta saka a fridge shima sannan ta tattara kayan data ɓata ta wanke tsaf sannan tazo ta juye kalkashin cikin soyayyun kayan miyarnan ta motsa da kyau suka haɗe. Ɗanɗanawa tai taji komai dai-dai yanda take fata duk da dai akwai fargaba tare da ita har yanzun.       “Inno an gama ko?”. Hajiya iya data sake dawowa ta faɗa tana shigiwa. “Eh Granny duk an kammala, amma dan ALLAH ki ɗanɗana wlhy inajin tsoro”.       “Haba ɗiyar albarka nasanma komai yayi daɗi. ALLAH ya saka miki da kairan ya baki miji nagari dazai riƙemin ke gam, bar wani jin tsoro”. Kanta kawai ta duƙar tana ɗan murmushi. Sai dai a ƙasan ranta tana tunanin ita data haihu a waje ina ita ina yin aure. tafi ganema ta dage taita karatunta har itama ALLAH ya kaita lokacin da zata taimaki kanta da iyayenta......        “Inno kinga ga naman kai nan da Rahi tai farfesu kafin ta tafi a haɗa masa dashi, sai akai masa gashi can ya dawo har yay wanka yana jira”. Hajiya iya ta katse mata tunaninta. Amsa mata tai da to tana haɗiye ƙwallar dake neman ciko mata idanu.       Kular tuwon ta ɗauka tasa kan tire, ta zuba miyar a wani bowl mai murfi na tangaran mai haske, hakama farfesun tasa a ƙaraminsa duk ta ɗora a tiren. Fruit salad ɗin da lemon kwakwar ta fiddo a fridge duk da basuyi sanyi mai tsananiba sunyi dai-dai gamai sha. Fruit ɗin ta saka a bowl fruit salad, juice ɗin kuma tasa a jug da ruwa a wani tiren. Ta kuma gyara ɗan kwalinta cike da ƙarfin halin danne ciwon dake cinta ta ɗauka ta fito ranta fal fargaba.      Zaune ta samesu shi da matarsa a dining ɗin. Tai sallama ya amsa batare daya ɗago daga latsa tab da yakeba. Farah kuwa bata amsaba saima harara data galla mata na tsananin kishin babu gaira babu dalili da haushin abinda hajiya iya tai mata akanta ɗazun. Ita dai Zinneerah gaishesu tai da masa barka da shan ruwa ta ajiye tiren ta koma ɗakko sauran kayan ba tare data damu da ƙin amsawar tataba.       Harta gama shirya komai a dining ɗin bai ɗago ya kalletaba. Ta juya zata bar wajen ganin ta gama aikinta taji yace, “Zoki zuba”.         Dawowa tai da baya cike da ƙarfin hali dan mararta ƙullewa takeyi. Sama-sama take jin tsawar Farah na faɗin, “Kinga dalla kama gabanki zan zuba masa ni tunda inada hannu”. Juyawa Zinneerah tai zata wuce dan taimakontama ita Farah ɗin tayi, amma saita tsinkayi muryarsa a karo na biyu. “Malama ki zubamin abinci nace ko”.      Jitai kamar ta fasa ihu dan takaicinsu, ta kalli yanda Farah ɗin ke watsa mata harara kamar idanunta zasu faɗo. Shima ta dubesa har yanzu kansa a ƙasa yanata danna tab. Dawowa tayi da baya tunda tasan dai itama matar tasa ai ƙarkashinsa take duk da wannan isar tata da rainin wayo. Batare data sake kallon sashen Farah ɗinba ta fara zuba masa komai tana ajewa gabansa.        Tana cikin zuba masa lemon kwakwar mararta tai matuƙar ƙullewa. Dole ta ajiye jug ɗin tai saurin zama a kujera tana kifa kanta a teble ɗin dan azaba.        Karan farko ya ɗago kai ya dubeta. Farah kuma da kishi keci ta daka mata tsawa, “Kujimin ƴar barikin yarinya. bakin gama aikin da aka sakiba miye kuma na zama?”.      Bata samu amsa daga Zinneerah ba dan bama jinta da ƙyau takeyiba. Shiko tab ɗin ya ajiye da maida hankalinsa gareta cike da nazari, ganin kusan sakan talatin bata ɗagoba yaɗan lumshe idanu ya buɗe akanta. A karon farko na rayuwarsa ya ambaci sunanta cikin muryarsa mai taushi da tarin nutsuwa da rashin sakewa. “Zinneerah are you ok?”.        Har cikin rai da jini sai da Zinneerah taji fitar sautin sunanta akan harshensa. Ta ɗan ɗago hawaye shaɓe-shaɓe a fuskarsa ta. “Ba komai Yayanmu kaina ke ciwo”. Ta faɗa tana miƙewa tabar wajen.      Da kallo ya bita kawai, Farah kuma ta rakata da harara tanajan tsaki da faɗin, “Lallai yarinyarnan idan kikace zakishiga gonata zanko juya fuskarki daga gaba ta koma baya a gidan nan wlhy”.          Goshinsa ya murza kaɗan, dai-dai yana maida kansa ga abincin. Ya ɗan furzar da huci yana ɗaukar juice ɗin data zuba masa kaɗan a ƙaramin kofi ya kai baki. Duk jarabar da Farah keyi akan Zinneerah ɗin bai ma nuna yasan tanayiba balle ya tanka mata. Sai dai a ransa haka kawai yakejin dariya nazo masa.           Zinneerah kam tunda takai ɗaki kwanciya tai a sofa tana riƙe mara dan Hajiya iya na bayi tana wanka. Taja kusan mintuna goma a wajen tana murƙususu harta faɗo a kujerar dan azaba kafin Hajiya iya ta fito.       “Subahanallahi, Inno lafiya kuwa?”.       Cikin kuka ta nunama hajiya iya saitin mararta. “Ikon ALLAH, nikam dai wannan ciwon mara daga ina? Keda baƙya ciwon mara mai ƙarfi irin haka amma wannan karon da alama ta canja miki sallo. Kinga tashi kije kiyi wanka da ruwan zafi sosai bara na leƙa su Haneef ko sun dawo, bansan ina Khalipha ya kwashesu suka tafiba tun ɗazun.        Da ƙyar ta amsama hajiya iyan. Sai dama ta taimaka mata zuwa bayin, ta kuma haɗa mata ruwa mai zafi tace tai wankan tana zuwa.       Ganin yanda Hajiya iyan ta fito da hanzari daga ɗaki Yah Adnan dake cin abinsa hankali kwance matarsa na gefe tana masa hira bayan ta gama bala'in Zinneerah ya ɗago ya dubeta. Tana gab da fita yace, “Granny lafiya kuwa?”.       Juyowa tai ta dubesu dan ita hankalinta baima kai garesuba. Cike da damuwa tace, “Moddibo Zinneerah ce bata da lafiya. Inason na duba cikin su Moos'ab ne wani yazo ya kaita asibiti kar abin ya ƙara mata tsanani”.        Shiru yay yana kallonta kamar bazaice komaiba. Ganin Hajiya Iya ta juya zata fita yace, “Granny su da basa nan ki jira na kammala dan zanje wajen Mahmud dama”.       Dawowa Hajiya iya ta sakeyi tana faɗin, “To Alhmdllh shikenan ma, bara naje ta shirya kafin ka kammala”. Kansa kawai ya jinjina mata yana lumshe idanu da buɗewa alamar amsawar kenan.          Wani irin kallo Farah ta zuba masa na tsananin takaici da kishi. Muryarta har rawa yake wajen faɗin, “Wai ban ganeba. kaine zaka kaita asibitin kuma?”.        Idanunsa ya ɗago ya dubeta ya maida ga abincinsa batare daya bata amsaba. A ƙufule ta miƙe tana cewa, “Wlhy to sai dai mutafi tare. Dan bazan yarda ka tafi da wannan shegiyar yarinyar mai kama da aljanu kai kaɗaiba. Ni wlhy bazan iyaba ka shirya mukoma gaskiya”.      Da kallo ya bita harta shige lungun da ɗakinsa yake. A bazata murmushi ya suɓuce masa ya girgiza kansa da ɗan taɓe baki ya ɗauke kai.         Harya kammala abinda yake ya miƙe zuwa ɗakin bata fitoba, koda ya shigo isketa yay tana waya. Yasan dai bazai wuce Mammah ko cikin yayuntaba. Dan haka bai tsaya sanin dawa takeyiɗin ba ya shiga toilet. Cikin abinda baifi mintuna uku ba ya fito. Key ɗin mota da ke a bed side drawer ya ɗauka ya nufi hanyar fita ya barta tana wayar har yanzun.        Yana fita itama ta miƙe ta ɗauka ɗan kwalin abayarta ta bisa tanayin sallama da yayanta da shigowarta ɗakin kiransa ya shigo mata a waya. Shine ta zauna amsawa. Sai da yay sallama a ƙofar ɗakin Hajiya iya ta amsa masa da bashi izinin shigowa sannan ya shiga. Zinneerah data fito wanka ta gama shiryawa cikin baƙar doguwar riga tana kwance a bakin gadon idanunta a lumshe hawaye na zirara. Kallo guda yay mata ya ɗauke kai ya maida ga hajiya iya data ɗakko mata hula da ɗan kwalin rigar.           “Haka take ciwon kai?”.   Ya tambaya kansa tsaye kamar yanda ta sanar musu ɗazun. Kallonsa hajiya iya tayi, “Ciwon kai kuma Moddibo? Zinneerah ce zata zauna yima ciwon kai raki kamar haka?. Ita jarumace ai da kake ganinta, tunda ka ganta haka ai abinda yafi ƙarfin ciwon kanne mararta ke ciwo, kuma da ba haka take mataba”.        Jin abinda Hajiya iya tace ya sashi janye idanunsa daga kallonta ya maida kan Zinneerah data zumɓuro baki alamar bataso Granny ta faɗa abinda ke damun nataba. Baki yaɗan taɓe da nufar hanyar fita yana faɗin, “ta sameni waje”. Daga haka ya fice abinsa ya barsu da ƙamshinsa........✍ *_Sauran inji wani yace kaɗanne gobe na rage mudu😂🤒🤒._* *_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 _Na Safiyya Huguma_ *_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖 _Hafsat Rano_ *_★ DALAAL_*💝 _Na Miss xoxo_ *_★ UBAYD MALEEK_*💓 _Na Mamu gee_ *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 _Na Bilyn Abdull_ Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 *_08085405215_* IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   0903 234 5899 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 *_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_* *_TYPING📲_* *_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_* *Page 25* ________________________ *ZAUREN GIRKI* Abinci na *gargajiya* ...Kuka,Taushe,Danbu, Sinasir,Waina Abinci na *zamani* ...Afang,Edikaikong, Coconut Rice, Ofada Rice *Garabasa* ...Salads,Pancakes, Plantain mosa, Gyaran nama/kifi kafin girki,Shirin/shinfida abinci kan table. • A kowane sati,in shaa ALLAAH, za a koyi miya/abinci daya da kuma wani abu ta karkashin *Garabasa* . • Duk ranar *Lahadi* za fito da sabobin *videos* guda biyu na miya/abinci da na wani abu daga karkashin *Garabasa* . • Kowacce daga cikin masu koya zasu bibiya video su kwaykwaya su gwada yin abincin bisa ga umurnin *video* • Kowane ranar *Asabar* za a yi *Q&A* a inda kowa zai samu yin tambayoyi akan *videos* din satin daya gabata, da inda suke neman karin bayani/gyara akan kokarinsu na gwada abincin *video* da kawunansu • Ga wace taga dama,daga ranar *Talata* za a iya fara turowan *video* ta kokarin da aka yi na kwoyon abincin da aka kwoyar ta *video* na ranar *Lahadi* . • Inda akwai me bukatan wani fanni na abinci,ana iya hada *aji(Special Personal Video Classes)* musamman domin wannan bukatan.Anan za a shirya live *video* sessions domin cimma wannan burin • Za a biya dubu biyu *(#2,000)* na watan farko,sannan za dinga biyan dari biyar *(#500)* ta kowane sati ga masu bukatan shiga group dinnan namu mai albarka • *Zen Commute,account number 0119343451 Union Bank* ,asusunmu • Duka lokacin da aka biya sai a turomana da hoton teller ko bank confirmation akan wannan number ta *WhatsApp 0817-541-7533* • Ana iya tuntubammu akan wannan number domin karin bayani; **0817-541-7533(WhatsApp kawai)*                                   ZA MU FARA ZAUREN GIRKI LAHADIN SATIN FARKO TA WATAR SEPTEMBER,IN SHAA ALLAAH! *MU TSARE MUTUNCINMU,MU KARE MAZAJENMU...MU KOYI GIRKI!!!* _________________________ *Page 25* ............“Kajimin ja'iri, basai ka tsaya ka kamata ba kuma? Kinga Inno na tashi muje ni na rakaki”.         Zinneerah da tonon sililin Granny yasata fahimtar shine zai kaita asibitin tace, “Granny dan ALLAH muje da wani cikinsu aunty Abidah ko su Meenal basai shiba”.        “Keda kike a wannan halin sai kin zaɓi mai tafiya. Kinga maza miƙe karma ya tafi dan shi ba saiti ne da shi ba wani lokacin”.       Dole ta miƙe Granny ta kamata badan taso ba. Tsaye suka samesu su duka a jikin mota, shi yana waya Farah na tsaye jingine tana danna tata wayar. Batare da hajiya iya ta damu da ganinsu su biyunba ta buɗe gaban motar ta saka Zinneerah shiga. Sai lokacin suka lura da zuwanta. Farah tabi Hajiya iya dake duban inda Yah Adnan ɗin yake da kallo. “Moddibo kuje dan ALLAH, kasan shi mai ciwo ƙosawa ne da shi”.        Kansa ya jinjina mata kawai batare daya bar wayarba ya buɗe murfin zai shiga Farah da haushi ya kume tace, “Granny ai sai dai ta dawo baya dan tare zamuje”.       “Asibitin? A'a idan kin bisu ni motsinwa zanji kuma tunda su Jamal basa nan. Kinga muje ciki muyi hira mai sunan ƴan gayu”. Ta ƙare naganar dajan hannun Farah batare data jira abinda tai niyyar faɗaba.       Ta cikin mirror Yah Adnan ke kallonsu. Ya danne murmushin dake neman suɓuce masa a fuska saboda rigimar Granny. Daga haka yay horn yana harba motar zuwa gate.          Tunda suka hau hanya baiyi ko tari ba duk da yana jin shashshekar kukan Zinneerah daka ƙudundune kanta cikin ƙafafunta data naɗe sama gaba ɗayanta ta dunƙule a kujera. Sai dai duk kiran wayarsa da akeyi tunda ya gama ta farko bai sake ɗagawaba har suka iso Shira hospital.      Duk da darene ko ina cikin haske yake kamar ka yarda allura kaga abunka. Sai da ya gama dai-daita fakin yaɗan dubeta ya ɗauke kansa. Wayoyinsa biyu ya ɗauka batare daya mata magana ba ya buɗe ɓangarensa ya fito. Sai da ya rufo murfin ta fahimci ya fita dan haka ta ɗago cike da ƙarfin hali fuska shaɓe-shaɓe da hawaye.     Tana ɗaura hannunta akan handle ɗin ƙofar da niyyar buɗewa ta fita tunda tasan bacewa zai ta fito ɗinba sai taji ƙofar ta buɗe. Akansa idanunta suka sauka da mamaki, sai dai ganin yanda yaci toka yasata saurin maidawa ƙasa. Gudun kartai laifi ya sata ziro ƙafa ɗaya zata fito ɗayar kuma ta riƙe. Tsareta da ido da yayi ga kuma azabar da takeci yasata sakar masa kuka.         A ransa yace (sai shagwaɓan tsiya). a fili kam sai ya girgiza kai kawai ya ɗauke kai yana miƙa mata handkerchief. “Malama goge waɗanan hawayen tunda ba satoki naiba”.          Duk da halin da take a ciki saida tace (bama gara wanda ya satoni da kai ba) amma a zuciya😂. A zahiri kuwa baki ta tura gaba da amsar handky ɗin nasa da keta uban ƙamshin turarensa tahau share hawayen. Shi kuma yay gaba abinsa cikin asibitin batare daya jirataba duk da ya fahimci bazata iya taka ƙafarba dan tun'a gida ya lura dama da ɗingishi ta fito sanda Granny ta kamota.           Kanta ta ƙara maidawa cikin ƙafafu ta dasa sabon kukan takaicinsa dana ciwo. A haka Nurse ɗin daya turo tazo ta sameta. Itace ta taimaka mata ta fiddota a motar suka fito. Da ƙyar ta taka ƙafar data ƙara riƙewa zuwa cikin asibitin. Suna shigowa a bazata sukaci karo da Khalipha.        “Kai! Beauty lafiya kuwa? Ke da wa haka?”.         Bata iya bashi amsaba sai dai ganinsa yasata jin sanyi har cikin rai. Shima bai damu da rashin amsawar tataba ya maida dubansa ga Nurse ɗin. “Sister Sadiya ita da waye sukazo?”.       Cike da girmamawa tace, “Ogane nidai yace naje na shigo da ita sir”.     Yasan Yayansu suke cema oga a asibitin. Dan haka cike da mamaki yace, “Yana ina shi ɗin?”.      “Dr Mahmud office sir”. “Okay kuje ina zuwa nima”. Ya faɗa yana nufar wani hanya alamar akwai abinda zaiyi.         Sai da Nurse Sadiya tai sallama aka basu izinin shiga sannan ta shigo riƙe da Zinneerah da ganin Khalipha yasaka kukan nata tsagaitawa. Miƙewa Dr Mahmud yayi yana mata sannu, shiko kansa yana duba wani file bai ɗagoba balle ya nuna yasan sun shigo office ɗin. A kujerar dake kallon wadda yake zaune Dr Mahmud yasa Nurse ɗin ta zaunar da ita.          “Sorry ƙanwarmu kukan ya isa ko?”. Dr Mahmud ya faɗa yana murmushi da kallon Zinneerah ɗin a zuciyarsa yanaji kamar yasan fuskarnan.        Kanta taɗan jinjina masa tana ƙara takure kanta waje ɗaya a cikin kujerar dan kusancinsu ya sakata jin ta takura, duk ya cika wajen da kwarjininsa. Kallonsa taɗan sata taga har yanzu yana a yanda suka samesa. ta janye tana maidawa ga Dr Mahmud daya jeho mata tambaya.        “Ƙanwarmu mike damunki ne?”. Ɗan jimm tai kamar bazatace komaiba dan har sai d Yah Adnan dake saurarensu ya ɗan ɗago ya dubeta ya maida kansa. Fahimtar da Dr Mahmud yay kamar tanajin nauyin maganar saboda AK ya sashi faɗin “To ko dai zamu tada boss a wajen nan ne? Ranka ya daɗe kamarfa........”      Saurin katsesa tai da cewa, “Cikina ke ciwo”.      AK daya ɗan ɗago ya dubeta a karo na biyu saiya girgiza kansa kwai kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa ya sake maida kansa ga takardun hannunsa. Takarda da pen Dr Mahmud ya tura mata, “Idan babu damuwa rubuta anan kawai”.         Har cikin ranta taji daɗin hakan, babu musu taja takardar ta fara rubutawa tana cije baki. Koda ya amshi takardar ya duba yaga mita rubuta sai baice komaiba ya jin jina kansa yana nuna mata ɗan gadon duba marasa lafiya dake can gefe. “jeki kwanta acan ina zuwa”.          Miƙewa tai cike da ƙarfin hali ta nufi gadon ta kwanta. Shima sai ya miƙe ya bita da wani ɗan dogon roba a hannu da syringe. Tambayoyi ya ɗan ƙara mata tana bashi amsa cike da jin nauyinsa. Daga haka ya ɗiba jininta.      A dai-dai nan Khalipha yay sallama ya shigo office ɗin. Ɗagowa Yah Adnan yay ya dubesa da ɗan mamaki. Amma baice komaiba. Khalipha da hankalinsa duk yana ga yanda yaga Zinneerah ɗin ya ƙaraso yana faɗin, “Yayanmu barka da dare”.         “Dama kana nan?”.   “Eh wlhy ban jima da zuwaba. Dr Muneer ne ya kirani mukai wani aiki. Miya samu Beauty ɗin ne?”.        Wani ɗan luu da idanu yayi da tsatstsare Khaliphan da idanu tamkar baiji miya faɗa ba. Shima Khaliphan sai yanzu ya fahimci katoɓarar da yay na cema Zinneerah beauty ɗin. Ya ɗan sosa gefen wuyansa yana murmushi. “I'm sorry yayanmu”.         “For what?”. Ya faɗa cike da salon basarwar tasa yana maida kansa ga file ɗin hannunsa.       Dariya Khalipha ya ƙyalƙyale dashi yana barin wajen ya nufi can inda Zinneerah da Dr Mahmud suke. “Oh oh sweet sister sorry, dama haka kike ragguwa ashe?”.         Dr Mahmud ne ya bashi amsa cikin dariya. “A'a Khalipha karfa ka cika baki, dan sai na bata labarin naka rakin kaima”.        “Lalala Yah Mahmud yi haƙuri kar kaja ta rainani, mike damunta ne? Naga kamar sun shigo tana ɗingishi”.      Kai tsaye Dr Mahmud yace, “Tana complain ne na mara, inaga zamuyi mata text mugani, duk da ina zargin dai bazai wuce....” Sai kuma yay shiru yana ɗan duban sashen da AK yake zaune. Addu'ar samun lafiya Khalipha yay mata yana ɗan murmushi da kauda zancen ta hanyar cewa, “Bara naje da jinin lab to”. Daga haka ya fita. Duk abinda suke tattaunawa Yah Adnan na jinsu. Amma saika rantse ma baya office ɗin, daga ƙarshema waya ya kira har Khalipha ya dawo bai gamaba.        Drip Dr Mahmud ya sakama Zinneerah ya dawo inda AK yake ya zauna suka cigaba da tattauna abinda ya shafesu har Khalipha ya dawo da result ɗin da magunguna daya sayo. Bayan Dr Mahmud ya amsa ya duba yace, “Dama abinda nai zargi kenan, bazai wuce harda Imfection ɗin ba, zamuyi treating ɗinsa insha ALLAH zai barta tunda baiyi ƙarfi ba. Tunda ma ka haɗo maganin inaga kai mata allurar nan kawai”. Miƙewa Khalipha yay yana faɗin, “Okay ALLAH yasa dai bata tsoron allura to”. Dariya kawai Dr Mahmud yayi, shima bayan ya mata allurar duk da barci naɗan figarta sai ya fita ƙarasa uzirinsa. Yabar Dr Mahmud suna cigaba da tattaunawa da Yayan nasu da ya koma kamar baya office ɗin. ★★★         A gida kuwa Farah tamkar zatai ƙaramin hauka a cikin ranta. Tanada kishi sosai wanda ita kanta wani lokacin abun har tsoro yake bata, dan Adnan dai ba taɓa mata alƙawarin bazai ƙara aure yayi ba. Ko lokacin da su Hajiya Iya suka takura masa saiya ƙara aure badan tsayawar Mammah a kansa ba da babu abinda zai hanashi ƙarawar duk da ba nuna mata yanada buƙatar hakan yayiba.        Tsaf hajiya iya tana lure da ita. Kuma dama da biyu ta hanata bin nasu. Dan haka ta shige ɗaki abunta tai shirin barci ta kwanta tunda tasan dai ba binsu Farah ɗin zataiba a yanzu.                Kamar yanda ta ƙware akai ƙara wajen Mammah yanzu ɗinma sai da ta faɗa mata tana kuka. Ran Mammah ya ɓaci sosai jin yarinyarma ba'a cikin ƙannensa takeba kamar yanda ita Farah ɗin tace tana tunani. Koda Mammah ta kirasa ashe wayar a nan gida ya barta, bai fita da ita ba, na hannunsa na alaƙar business ɗinsa ne kawai.      Wannan abinne ya ƙara ƙular da Farah ta dinga kai kawo tsakanin ɗakinsa da falo ita kaɗai dan hajiya iya dai ta shige. yaran kuma da suka dawo basu shigo nanba dan a gajiye suke.          ★★ Sai kusan sha ɗaya ruwan da aka sakama Zinneerah ya ƙare suka nufo gida. Tana a baya ita kaɗai, Khalipha ne yanzu ya amshi driving ɗin, shi kuma yana a gefensa zaune. Babu mai magana a motar dan duk sun gaji kwanciya duk suke buƙata, sai sanyin ac daya takurama Zinneerah, hakan ya sata dunƙulewa waje guda barci sama-sama nason figarta.          Koda suka iso gidan Khalipha ne ya buɗe mata ta fito, ganin yanda take ɗan tangaɗin barci dana rashin ƙwarin jiki yace, “Ƙanwata kodai na kamaki ne?”.     Kanta ta girgiza masa a hankali cikin yanayin kasala tana dafe jikin motar dan ji take tamkar zata faɗi. Ɗan matsawa Khalipha yay da ita gab yana ƙoƙarin kai hannunsa zai kamo nata. Yah Adnan dake kallonsu ta gefen ido, amma saika ɗauka gaba ɗaya hankalinsa baya tare da su ya katse hanzarin Khalipha ɗin dake neman kamo hanun Zinnerah, “Besty kaje da takardun nan ɗakinga zuwa safiya idan ALLAH ya kaimu saika dubasu zamuyi magana daga baya”.      Dole Khalipha ya haƙura daga son taimakon Zinneerah ya juya garesa ya amshi takardun.      “Kaje kawai sai da safe muma bara mu shige dare yayi. Ke kuma muje”. Ya sake faɗa ciki-ciki yana duban Zinneerah da duk tana saurarensu.         Dole Khalipha yay musu sai da safe yana nufar sashen samarin gidan. Shikuma ya tasa Zinneerah dake tafiya da ɗan layi na barci suka nufi sashen hajiya Iya. Abin tsautsayi tana tura ƙofar falon da niyyar shiga hannunta ya gota akan handle ɗin saboda tuntuɓe da takalmi da tai.      Saurin tarota yay ganin zata faɗi, saboda ya rigada ya kawo jiki ita kuma tayo baya. Sai kuma ya ɗagata da hanzari yana miƙar da ita tsaye sosai akan ƙafafunta. Ɓoyayyen numfashi ta sauke da saurin yin gaba har ƙafafunta na neman harɗewa. Ya ɗan bita da kallo ƙasa-ƙasa harta shige bedroom ɗin hajiya iya. Janye idanunsa yay da zummar nufar nasa ɗakin shima yaci karo da gimbiya Farah mai zamani hakimce cikin kujera tacika tayi fam. yanda tai mugun tsatstsaresa da idanu ya bashi tabbacin tunda suka shigo tana a falon kenan.. Sanin halinta yasa bai tanka mataba ya ɗauke kansa yay gaba.         Sai da yay kusan mintuna biyar da shigowa sannan ta biyosa. Tana shigowa yana shiga bayi. Duk da tsahon lokacin daya ɗauka bai fitoba a tsaye ya sake isketa ta kuma cika fam fiye da farko.         Hidimar shiryawarsa ya shigayi yanzunma bai kulataba. Sai da ya gama tsaf cikin kayan barci ruwan sararin samaniya sannan. Kamar zai shareta dan takaici sai kuma ya ɗan dubeta ya ɗauke idanunsa. Inda take ya matsa sosai tare da dafe bangon da hannayensa biyu ya sakata a tsakkiya yana zuba mata fararen idanunsa da alamun barci ya bayyana a cikinsu.        A take dukkan fushinta ya fara rauni dan waɗanan idanun nasa suna ladabtar da ita idan tai laifi. Suna kuma tabbatar mata da ɗunbin soyayyarta a cikinsu idan yaso lallashi. Suna kuma mata kwarjini da girmama kimarsa a gareta a duk sanda shi ɗin yazam mai laifi a gareta.        A karan farko ya saki murmushi ganin yanda ta lumshe nata hawaye na silalowa. Fuskarsa yakai gab da tata suna musayar shaƙa da zuƙar ƙamshin juna. Kafin ya cire hannunsa guda dake dafe da bango ya saƙalo ƙugunta ya sake mannata da jikinsa sosai yana wani sakar mata numfashinsa da ƙarfi akan fuskarta. A take ta saki nannauyar ajiyar zuya da saka duka hannayenta ta zagayoshi ta ƙanƙame itama.       Murmushin ya sake saki, batare daya ce komaiba ya ɗauketa cak ya nufi gadon da ita. Yana sauketa bargo yaja ya lulluɓa musu, zatai magana ya rufe mata bakin da nashi. Daga haka ɗakin yay tsit kamar ba ita ta gama cin alwashin karta masa shika shikan rashin mutunci cassa'in da tara ba. ______________________________★        *_DANYA_* Duk yanda Inna tasoji daga Karima hakan ya gagara. Dan ciwo ta kwanta kashirɓan tun randa ta dawo. Abin kamar wasa sai ga ƙaramar magana na neman zama babba. Tuni Inna ta manta da wani zancen kiranyen dataima Baba saboda ruɗanin halin da Karima ke ciki.       A rana ta uku duk yanda taso ɓoyewa hakan ya gagara. Dan dole ta nufi gidansu Babawo ta sanarma innarsa. Sunyi mamaki matuƙa. Dan shi dai baice dasu Karima tana Danya ba, kuma koda safe sai da sukai waya da shi. Dole Innar Babawo ta ɗakko gyale ta biyo Inna gidanta. Itama hankalinta ya tashi ganin yanda jikin Karimar yay kaca-kaca da sayin duka ga ciki tsoho haihuwa ko yau ko gobe.        A ruɗe tace ma Inna ta shirya karimar suje asibitin kusada. Bara taje ta nemo ƙanin Babawo ɗin tunda yanada mashin. Daga haka ta fice ita kuma Inna daketa tsinar Babawo ɗin ta shiga kimtsa Karima......... _____________________★               Hajiya iya batasan su Zinneerah sun dawo gidanba sai da asuba ta ganta kwance a bayanta. Hannu tasa ta shafa mata fuska tare da gyara mata bargo. Itama cike da ƙarfin hali ta nufi bayi yin alwala dan ƙafarta ciwo take mata tun da daddare dama. Da ƙyarma ta iya kai kanta bayin. hakama da tayo alwalar da gyar ta fito. Duk yanda taso gabatar da salla a tsaye hakan ya gagara sai a zaune tayita. Bayan ta idar kuwa ko azkar yau batayiba ta zame ta kwanta a wajan.        Itama Zinneerah farkawa tai, sai dai koda taga Hajiya Iya kwance a ƙasa bata kawo komai a rantaba ta shige bayi kimtsa jikinta. Ganin harta fito Hajiya Iya na kwance a wajen sai abin ya ɗan bata mamaki amma batai magana ba ta hau shiryawa dan wanka tayo. Batajin ciwon komai yau sai rashin ƙwarin jiki. Ta shirya cikin siket da riga na baƙin Material mai adon firanni golden. Ganin Hajiya Iya taɗan motsa ya sata zuwa gabanta ta tsugunna tana gaisheta.      Hajiya Iya ta buɗe idanu da ƙyar tana duban Zinneerah ɗin. Murmushin ƙarfin hali tayi da miƙa mata hannu ta kamo nata. “Inno na yaya jikin?”.      Kasa amsawa Zinneerah tayi saboda jin zafi jikin na Hajiya Iya. aɗan rikice ta sake damƙe hannun cikin nata tana faɗin, “Granny baki da lafiya ne?”.         Kamshinsa ne ya katse Hajiya iya dake ƙoƙarin bama Zinneerah amsa. Zinneerah ma sai ta ɗan dubi ƙofar dai-dai ya shigo idanunsa suka shige cikin nata. Saurin janye natan tayi tana maida kai ƙasa dan wani irin matsananciyar kunyarsa taji saboda tunowa da faɗa masa a jiki datai jiya da dare. Ga sirrinta daya gamaji a bakin hajiya iya kafin su wuce da kuma tabbacin ya sakejin wani wajen Dr Mahmud.       Shima nasa idanun ya janye yana duban Hajiya iya dake kallonsa a kwance. A take ya gano babu lafiya dan yasan hajiya iya sosai a rayuwarsa. Duk da kuwa zaman da yay a wajenta na shekaru tara ne kacal, sai hutun da yake zuwa mata kuma bayan ya koma London karatunsa.        Ta inda Zinneerah ke tsugunne ya ƙaraso ya ɗan ranƙwafo kansu yana kai hannu goshin Hajiya Iyan. “Granny lafiya kuwa?”.         “Wlhy ƙafafun nan ne ke neman takuramin kwana biyun nan Moddibo ”.       Idon Zinneerah na cikowa da ƙwalla tace, “Amma Granny shine baki faɗaba? Wlhy jikinki zafi dan ALLAH ki tashi muje asibiti”.      Yanda ta ƙare maganar hawaye na silalowa ga rawar murya ya sakashi ɗan dubanta, kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa. Ɗayan hannun Hajiya iya ya kama shima ya tadata zaune sosai dan tanada jiki itama masha ALLAH.         Gaban Hajiya Iyan yay wani ɗan tsuggunne idanunsa na sauya launi zuwa damuwa. Dole Zinneerah ta miƙe saboda kusancin da suka samu yayi yawa. Cikin wayancewa tace, “Bara na haɗo miki kunu kiɗansha sai kisha maganinki”.      Murmushi Hajiya Iya tai tana binta da kallo harta fice, kafin kuma ta sake maido idonta kan Yah Adnan dake mata tambaya muryarsa a ƙasa.       Al'amarin kamar almara sai ga jikin hajiya iya na neman rikicewa a wannan yini, dole Dr Mahmud da Khalipha suka rufu a kanta duk da shi bai kammala nasa karatunba ma. Amma kwazon da yake nunawa yasa ko ƙasar yazo yakanje Shira hospital yay wasu ƴan ayyuka dai-dai saninsa.         Tashin hankalin ruɗewar jikin ya saka Yah Adnan cewa zai wuce da Hajiya Iyan london a yau. Amma sai Baffah da ake saran zai dawo ƙasar yau ya taushesa akan yay haƙuri yana zuwa shima.     Badan yasoba dole yabi umarnin mahaifinsa da yake zuwa yamma jikin Alhmdllh ya ɗan ɗaga mata. Duk wanda ya kalli Zinneerah yau yasan tasha kuka. tayi wuni firgai-firgai da ita na damuwa. tabi ta nane a ɗakin wajen Hajiya iya ita dasu Jamal. Ko yayansu ya shigo su su Jamal tsoro na sakasu fita da shakkarsa. Itako duk da tanajin shakkar tasa da kwarjin da yake mata saita fiske abinta taƙi fita.          Dama tun lokacin da jikin ya rikice tai kiran Maman Sadiq ta sanar mata. Itama hankalinta ya tashi matuƙa dan haka tace zuwa yamma zata shigo tare da yara su dubata dan yanzu duk sun wuce makaranta Little ne kawai a gidan.     Aiko kamar yanda Mman Sadiq tai alƙawari bayan sallar la'asar sai gata tare da Sadiq, Abdull, Aliyu sai Little. A napep sukazo kasancewar Abba baya nan yaje ɗanmusa duba yayansa da baida lafiya shima.         A gate ya saukesu mmn sadiq tai kiran Zinneerah a waya dan tazo ta shiga dasu. Duk da tana tare da damuwar ciwon hajiya iya cike da ɗokin ganin ƙannen nata da gudan jininta ta fito zuwa hanyar gate. Sai da suka gaisa da maigadi ta sanar masa baƙine zasu shigo.       “To Hajiya bara a buɗe musu”. Ya faɗa yana ajiye butar hannunsa daya ɗauka alamar zaiyi wani abu. Da gudu su Abdull sukayo kanta lokacin da suka shigo. ganin yanda Little ya biyo rububi a guje shima ya bata dariya. Tsugunne yakai da buɗe musu hannayenta duk suka shige su huɗun. Mmn Sadiq dake binsu da kallon sha'awa taɗan murmusa tana ɗauke kanta. Da ƙyar Zinneerah ta samu ta miƙe tsaye hannunta riƙe dana Aliyu tana ɗauke da Little a ɗayan ta dubi mmn sadiq da faɗin, “Mama sannunku da zuwa kumuje ciki”.        Kai kawai Mmn sadiq ɗin ta jinjina mata tana mamakin yanda ɗiyar tata ta ƙara canjawa a ƴan kwanakin data dawo gidan. Zuwansu tsakkiyar harabar gidan yay dai-dai da fitowar AK daga sashen Hajiya iya kunen sa manne da waya alamar magana yakeyi, sanye yake cikin ƙananun kaya da suka sakko fiddo zallar ƙuruciyarsa da hutu dajin daɗi, ya cigaba da takowa a hankali garesu suma suna nufarsa duk da Zinneerah jitake tamkar zata faɗi dan har haɗewa ƙafafunta keɗanyi..........✍            *_Harda na gobe😫😫🤧_*        *_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 _Na Safiyya Huguma_ *_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖 _Hafsat Rano_ *_★ DALAAL_*💝 _Na Miss xoxo_ *_★ UBAYD MALEEK_*💓 _Na Mamu gee_ *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 _Na Bilyn Abdull_ Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 *_08085405215_* IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   0903 234 5899 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 *_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_* *_TYPING📲_* *_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_* *Page 26* ___________________________ 💫💥💫💥💫💥💫💥💫💥💫 *_ALBISHIRINKU MATAN AFRICA DA KEWAYE , SHAHARARRAR KUMA KASAITACCIYAR MAI SAIDA KAYAN MATAN NAN WADDA KUKAFI SANI MAMAN YUSUF YAR SOKOTO TANA YI MAKU ALBISHIR DA CEWA ZAKU IYA SAMUN KAYANTA ADUK INDA KUKE CIKIN FADIN NIGERIA DA NIGER KARKU MANTA MACE MAI GYARA KANTA BATA BORANCI_* 💃💃💃💃💃💃💃 07069711327 _Akwai zafafan kayan Mata masu kyau da arha cikin sauki da rahusa Kuma duk inda kike zamu aika maki kayanki cikin aminci da yardar Allah ba cuta ba cutarwa don a Dade anayi sai gaskiya uwargida da amarya ku garzayo Kar abaku labari_ Munada kalolin Kaya kamar haka💥💫💥💫💥💫👇🏻👇🏻 Maganin sanyi sahihi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata Maganin gyaran nono domin dawo da martaban nononki hadin gargajiya da bashida illah ajiki Maganin hips Mai tado da hips cikin kankanin lokaci Maganin kiba Wanda zaisa ki ciko dai dai misali kiyi kyau kema ki shigo cikin jerin Mata masu aji Maganin rage kiba da tumbi Wanda zaisa ki sace ki koma Yar dai dai abin alfaharin kowane namiji, Akwai kalolin gumbuna masu kyau da saukar da ni'ima Maganin matsi masu ciko da gaba da matseki Kamar Yar budurwa uwa uba zasu Baki dandano Mai gamasar da maigida Kalolin garrika masu bawa mace niima da jimawa ajiki Kalolin tsumi Sha yanzu magani yanzu dasa Mai gida ihun Dadi Zumar mallaka Zumar goron Tula Zumar ridi Zumar Mai rubutu Hadin mallaka Turaren mallaka Shu'umar humra Turaren AL'AJABI Matan gaske Ak 49 Sirrin tafin k'afa Turaren fuska Hatsabibin turare Kwallin mallaka Zoben mallaka Jigidar maida tsohuwa yarinya Maltinar Mata Karya gado Yajin Mata (yajin Mai ciko da mace) Yajin maza (domin Karin k'arfi) Muna dahuwar Kaya kamar haka💫💥💫💥👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Dahuwar zabo (mallaka) Kazar Yar gata Yan shila Ciccibi Dambu Zuciya Yan ciki Kwai ukku Tsoka Tara Kifi Da sauransu Akwai sirrika sosai da muke hadawa ga wacce kishiya ta addabeta ko wadda take fama da butsarin namiji ko mafadacin namiji ko namiji Mai yawon dare ko Wanda yake bin Mata insha Allah duk zaku samesu Kuma da yardar Allah za'asamu biyan bukata Muna bada magani ga yarinyar da tsautsayi ya fad'a Mata ta rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar da namiji Kuma insha Allah zaadace da yardar Allah Abubuwan da yawa gsky Wanda in nace Zan lissafasu sai nakwashi tsawon lokaci maiso tabini PC don ganin kalolin kayan da muke dasu , Karku manta mace Mai gyara kanta Bata boranci taku ce maman yusuf Yar mutan sokoto 07069711327 . Don Allah wadda Bata shirya ba tabari sai ta shirya sannan tayimun magana🙌🏼🙌🏼🙌🏼🙌🏼🙌🏼ngd 07069711327 __________________________ *page 26* ...........Baki ya buɗe zai bama wanda suke maganar amsa dai-dai da isowarsa gab dasu hakan ya gagara. Dan a take harshensa ya sarƙe saboda sauka da idanunsa sukai akan fuskar Little dake ɗauke a kafaɗar Zinneerah ya wani lafe jikinta hannunsa na wasa da jelar kitsonta ta bayanta. Ita kanta sake shiga ruɗani zuciyarta tayi kasancewar kusancinsu sosai yau da little ɗin ya ƙara fiddo mata da kamanninsu ainun.        Sannan ganin yanda yake kallon little ɗin shima sai da hanjin cikinta suka motsa. Ba ita da shi bane kawai a ruɗanin hatta da mmn sadiq sai da tayi kamar zata kifa daga bayansu. Ƙirjinta kuwa yay wani mummunar bugawa tanabin AK ɗin da kallo. Duk da ƙarancin shekarun Sadiq da Abdull suma dai su kalli little su kalli AK ɗin da ayanzu yay ƙarfin halin ɗauke idanunsa yana maida hankalinsa ga wanda suke wayar duk da a baɗini sam hankalin nasa baya tare da shi.       A haka suka wuce juna su Sadiq na waiwayensa, hakama mmn sadiq sau kusan uku tana waiwayowa ta kallesa, kamar yanda shima ɗin ya kasa daina binsu da kallo. Zinneerah kam da ƙar ta cigaba dajan ƙafafunta ta ƙarasa dasu sashen hajiya iya. Inda acanma kallo ya koma sama. Dan tun sallamar da sukayi kowa ya amsa su Meenal suka taso da gudu suka rungume Mmn sadiq suna mata sannu. Sun juyo da nufin ma su Sadiq sannu da zuwa idanunsu ya sauka akan little.       “What!”. Jamal ya faɗa a hankali yana tsare little ɗin dake lafe a kafaɗar Zinneerah har yanzu da ido. Sam hankalin Zinneerah baya tare dasu a yanzu, dan yau tafi kowacce irin rana shiga ruɗani akan kamannin little da Yah Adnan. Shiyyasa harta sauke little ɗin ƙasa bama tasan tayi ba. Hakan kuma dataine ya bama duk sauran yaran gidan ganinsa sosai. A take sannu da zuwan da suke Mmn sadiq ya shiga maƙalewa a maƙosansu. Dan yau harsu Momie suna a sashen suma.          Cikin ƙarfin hali Khalipha da yay mutuwar tsaye shima ya nuna musu hanyar ɗakin hajiya iya yana faɗin, “Mama ku shiga tana ciki”.      Kai Mmn sadiq ta ɗaga masa tana murmushin yaƙe dabin Khalipha ɗin da idanu itama dan ta ganesa duk da ya ƙara buɗewa fiye da wancan sanin datai masa.     Duk wannan al'amari dake faruwa Farah na ɗaki kwance dan taƙi sakewa a cikinsu kamar yanda takeyi dama idan tazo gidan. Saboda karma Adnan ɗin ya zargeta catai masa bata da lafiya. Yarda yay tunda yasan tana laulayin ƙaramin ciki kamar yanda Mammah ta sanar masa.         Hajiya iya na kwance suka shigo. amma tunda idonta ya sauka akan little itama babu shiri sai gata zaune. Ta haɗiye yawu da ƙyar tana miƙa masa hannu shi dasu Aliyun. Babu musu duk suka nufeta. Sai da suka gaisheta da jiki sannan suka zazzauna inda ta nuna musu a kusa da ita kan gadon. Little kuwa matsawa yay jikinta ya kwanta dan shi dama akwai son jiki. Su Sadiq sun shagwaɓa shi, harma dasu Mmn Sadiq ɗin.          Hajiya iya takai hannu kan little ta shafa zuciyarta na wani irin harbawa. A ranta ko rayawa take tamkar Moddibo na ƙarami. A fili kuma saita maida hankalinta ga Mmn sadiq dake gaisheta cike da kulawa.         Tunda suka shige aka shiga ƴar kallon kallo a falon, dan bakin kowa ya kasa furta komai. Sai can kamar a fisge Saffiya tace, “Wannan ai yaron dana ɗakko muku hotonsa ne. Amma kuma ba maman bace wannan”.       Shigowar Baffah da AK ne ya hana kowa amsa zancen Safiyya ɗin. Sai ma zubama Yayan nasu ido sukai zukatansu fal ruɗani. Shima kansa a ruɗanin yake. Amma kasancewarsa gwanin kamewa yasa babu mai iya fahimtar halin da yake a ciki akan fuskarsa. Sannu da zuwa duk suka shiga yima Baffah. Ya amsa musu sama-sama yana nufar ɗakin mahaifiyarsa dan ba'a cikin hayyacinsa ya dawo ba.      Da sallama ya shigo, AK biye dashi a baya. Ganin Mmn sadiq ya saka Baffah nuna jin daɗinsa. Suka gaisa cikkn girmama juna. Suma su Sadiq suka gaishesu ya amsa musu da kulawa. Sai da ya maida hankalinsa ga Hajiya Iya data kafe AK da kallo sannan shima idanunsa suka sauka akan little da barci ya fara ɗauka a jikin hajiya iya.      Wani irin muƙut, Baffah ya haɗiye yawu da ƙyar yana kallon little da ƙyau. Kasa jurewa yay sai da ya juyo ya kalli AK da gaba ɗaya hankalinsa ke akan little shima. Ya sake maidawa ya kalli little again zuciyarsa na wani irin rawa. Dan ƙarara zakaga shi ruɗaninsama akan fuska. Kasa jurewa yay sai da yace, “Ikon ALLAH innata kunga wani kamanni yau dake neman hargitsa tunanina anan, ɗan wanene wannan?”.         “Bakai kaɗaiba Babangida. Ni kaina bakaga na kasa daina kallon yaron da Moddibo ba. Ai wani hikima sai UBANGIJI. Wlhy sai kace Moddibo na ƙarami. Hauwa'u wannan yaro nikam idan a wani guri na gansa ai sai nace namune ma. Ina kika samosa?”.      Duk da faɗuwa da gaban mmn Sadiq yayi cikin juriya tai murmushi zata bata amsa Aliyu yay saurin faɗin, “Mama ƙaninmu ne”.         Shiru ɗakin yayi, Mmn Sadiq ta sauke wani ɓoyayyar ajiyar zuciya. Dan a ganinta ba'a wannan halin da hajiya iya ke a ciki yakamata tasan matsayin little ba. Amma insha ALLAHU tayi alƙawarin tana samun lafiya zasuzo ita da Abba sumasu bayanin komai. Shiyyasa taso tunma kan Zinneerah ta taho su faɗa musu. Amma batasan dalilin Abban na hanawaba.        Baffah ne ya katse tunanin na maman sadiq da faɗin, “Kai masha ALLAH, ALLAH ya albarkaceku, hikimar UBANGIJI ai tafi ƙarfin mamaki. Hakan na ƙara nuna mana muhimmancin zuminci da ƙarfin jini dake tsakaninmu Hauwa'u. ALLAH ya sake ƙara mana ƙarfi da kusanci, ya kuma sa muci amfanin hakan duniya da lahira”.      Da amin duk suka amsa. Baffa ya shafa kan yaran duka har little daya ɗan buɗe ido ya dubesa na kusan sakan goma sannan ya maida ya rufe. Daga haka aka koma gaishe-gaishe duk da zuciyar kowa dai ba adaidai takeba.                    Bayan Baffah ya fita aka kawoma su mmn sadiq abinci da ruwa. Ruwanma kawai suka sha dan a ƙoshe duk suke dama. Suna nan zaune tare da hajiya iya har akai kiran sallar magriba Khalipha yaja su Sadiq suka tafi massallaci. Bayan an idar ne sun dawo suka iske Little ya tashi. Sai dai suna toilet Zinneerah ta kaisa zaiyi fitsari. Sannu suka sakema Hajiya iya dake zaune ta idar da salla duk suka fita.          Zinneerah ta fito riƙe da little dake mata maganar da ba wani fahimta takeba sosai saboda bawani ya iya bane da ƙyau. Murmushin ƙarfin hali take masa itama tana magana ƙasa-ƙasa. Hakan yayi dai-dai da shigowar AK ɗakin da sallama. Amsa masa duk sukayi idanunsa na sauka akan Zinneerah da little ɗin. Ita dai bata yarda ta kalli sashen da yakeba, sai da a bazata suka ji little yace, “Abbah ruwa zan ca”.          Gaba ɗaya suka kalli yaron da mamaki dan AK yake kallo, kuma shine ya shigo hannunsa riƙe da goran ruwa.        Murmushi AK ɗin ya saki wanda ya sake fidda kamanninsa da little ɗin ainun yana nufosu. Ƙirjin Zinneerah ya harba da ƙarfi lokacin da yazo gab da su ya miƙama little ɗin hannu alamun yazo gareshi yana faɗin, “Oh my Sweetheart zo, zo”.       Saurin sakar masa shi tayi tana ja baya, shiko little cike da farin cikin daya bawa kowa mamaki musamman ma su su Zinneerah da suka san miskilancin yaron ya wani maƙalƙale Yah AK ɗin yana sauke ajiyar zuciya. Shi kansa AK ajiyar zuciyar ya sauke a ɓoye da sake manne yaron a jikinsa jininsa na tsinkewa. A hankali ya sumbaci goshin yaron sannan ya zauna a bakin gado ya saka masa ruwan a baki yana shafa kansa.        Baki little ya janye yana faɗin, “Ƙoshi Abbah”.       A bazata sukaga AK ɗin yayi dariya da jan hancin yaron yana faɗin, “Wannan hausan naka bai cikaba little Handsome”.       Ƙaramar dariya hajiya iya da zuciyarta ke ƙara raunana da shiga ruɗanin wannan al'amari tayi. hakama Mmn sadiq tai murmushin yaƙe kawai. Kallon Zinneerah hajiya iya tayi. “Inno na a bashi abinci ko”.        Kai ta kaɗama Hajiya iyan da nufar kulolin da aka kawoma su mmn sadiq ɗin basu ciba. Ta buɗe ta zubo abincin kaɗan a filet. Kallo ɗaya tayima little ɗin dake jikin Yah AK yana masa firar da baya fahimta dan maganar tasa ba nuna taiba ta ɗauke kai. “Malami sakko ga abincin”. Tai magana tana dubansu.      Kafaɗa ya noƙe alamar bai zuwa. Hakan yasa Zinneerah hararsa ta ɗauke kanta ta maida gasu Aliyu. “Kuma zakucine Abdull na saka muku?”.        Kai suka girgiza mata alamar a'a. Dan haka ta sake duban inda little yake ganin ko motsi baiyiba har yanzun. Zata sake magana AK ya harareta kaɗan da miƙa mata hannu alamar ta bashi abincin. Baki ta ɗan tura gaba da miƙewa takai masa. Harta juya little yace, “Aunty!”.    Juyowa tai ta kallesa, ganin ya maida kansa kamar bashi ya kiraba yasata hararsa, sai ko a cikin idon AK daya ɗago. Da sauri ta ɗauke kanta ta nufi hanyar ƙofa tana ƙunƙuni a cikin ranta.            Baya taɗan ja saboda Khalipha da zai shigo. Ya dubeta da murmushi dan zuwa yanzu kam ya yarda wannan Zinneerah ce daya sani a Shira hospital. Sai dai little ya saka zuciyarsa a tsananin ruɗani da firgici, dan inhar zai auna da ma'aunin hankali shekarun little zasu iya kaiwa dai-dai da hasashen haihuwar Zinneerah. Amma yaƙi ya yarda da cewar shine ɗan data haifa ɗin.          “Kanwata sai ina kuma?”. Murmushi tai masa daɗan shafar wuya. “Yah Khalipha zan fitane kawai”. Murmushin ya sake sakar mata shima, da matsawa ya bata hanya ta fice shikuma ya ƙarasa shigowa idanunsa na sauka akan Yayansu dake bama Little abinci a baki. Ji yay sun wani bala'in birgesa. Har yana ayyanawa a ransa inama ace yaron nan jinin yayan nasune da gaske.        Takawa Khalipha yay ya zauna kusa da yayan nasu yana mai shafa kan little ɗin. Juyowa little yay ya kallesa sai kuma ya juya ya cigaba da karɓar abincin. Kaɗan yaci abincin yace ya ƙoshi, badan AK ya gaji da bashiba ya haƙura ya barsa. Haka ya cigaba da zama a jikinsa har ya sake komawa barci.       Su Mmn Sadiq basubar gidanba sai wajen tara saura na dare. Da ƙyar aka raba little da jikin Yayah Adnan, dan lokacin da Khalipha dazai kaisu yazo amsarsa sai gashi ya farka a bazata. ya ƙanƙame AK ɗin yaƙi zuwa wajen Khalipha. Murmushi AK yay da lumshe idanun yana sunbatar little ɗin a goshi da shafar bayansa. Shi kansa ƙarfin hali kawai yakeyi, amma ji yake kamar karya rabu da yaron dan yayi bala'in shiga ransa.       Daga ƙarshe dai da ƙyar ya yarda Khalipha ya ɗaukesa dan sai da aka haɗa da masa wayo. Motar na ficewa ya sauke wata nannauyar ajiyar zuciya hawayen da baisan kona minene ba suna ciko masa idanu. Ƙoƙarin maidasu yay yana furzar da huci mai zafi da nufa garden ya zauna dan babu abinda yafi buƙata a yanzu kamar kaɗaici.               Yanda AK ya kaɗaice kansa Zinneerah ma harabar gidan ta fito can wajen motoci ta hau bayan ɗaya daga ciki ta zauna tare da faɗawa duniyar tunani. Gaba ɗaya zuciyarta a ruɗani da ɗimuwar kiɗima take. Shin a ina aka faɗi a ragaya ne? Wane darasi rayuwa keson karantar da ita a wannan gaɓarne bayan darasissikan data baro a shekarun baya?. Ko mahaukaci ya kalli little ya kalli Yah AK dolene ya danganta alaƙar jini a tsakaninsu. Dan abinda zai matuƙar baka mamaki ba kammaninne kawaiba. Hatta da wasu a cikin halayen Yah Adnan akwai alamunsu ga little. Kenan to.......      “Kai ina”. Ta faɗa a fili tana girgiza kanta dake matuƙar sara mata. Kamar ance ta ɗaga kai can ta hango Baffah a barandar sama yana kaikawo alamar shima akwai abinda ke damunsa, wanda bata raba ɗayan biyu zancen kamanin little ne da Yayan nasu.        “Ya ALLAH kai ne gagara misali, ka buɗemin tunani, ka yalwatamin fahimtata. Ka gafarta mini zunubaina”. Ta faɗa hawaye na silalo mata akan kumatunta masu zafi. Zurfi sosai ta ƙarayi a tunani har motar Khalipha daya kaisu mmn sadiq ta shigo gidan bata saniba. haskatan da yayne shima ya sakashi ganinta. yana gama fakin ya nufo inda take. Sau biyu yanayin sallama babu amsa, har dai ta kaisa ga ɗan bugar motar ta gefen kunnenta sannan ta kawo nannauyan numfashi tana dubansa.        “Wane irin tafiya tunanine haka da zurfi ƙanwata?”.       Murmushin yaƙe tai masa tana duƙar da kanta ƙasa. Hakan datai sai ya ƙara fiddo masa da kamanninta na baya sosai. Yay murmushi yana gyara tsaiwarsa da faɗin, “Zinneerah na tambayeki mana?.”          Gabantane ya faɗi, amma sai cikin dauriya tace, “Ina jinka Yah Khalipha”.       Kansa ya kaɗa mata yana ajiye keys ɗin hannunsa da wayarsa alamar maganar mai muhimmanci ce. “Dan ALLAH ki faɗamin gaskiya kin manta dani ko?”.        Duk da tambayar tasa tazo mata a bazata dan ba ita tai zaton jiba sai da taji dumm. Ganin ya kafeta da idanu ya sata yin murmushin yaƙe tace, “Ban gane mi kake nufi ba Yah Khalipha”.          “Nasan kin gane Zinneerah, amma tunda hakane bara na miki dallah-dallah”.          “Tun randa na ganki a gidan nan nasan nasan fuskarki, amma na rasa ina na sanki dan kin banbanta da waccan ɗin dana sani a yanzu. Nasha gwadaki naga ko zaki nuna ke kin sani amma baki nunaba, sai yau da naga mama na tabbatar da cewa kece. Shiyyasa mamaki ya kamani na rashin nuna kin sanni da kikai kafin yau”.         Tabbas taji kunya. amma sai ta dake, ta buɗe baki da zummar bashi amsa sukaji ƙamshin turarensa da takun tahowarsa. Duk kallon waje. sukai Zinneerah na haɗiye maganar da tai niyyar yi. Ganin yanda yake kallonsu ya sata jin wani iri, babu shiri ta diro akan motar tai cikin gida sum-sum duk da alamar ta zauna da Khalipha ke mata da hannunsa.             Khalipha da shi kansa kallon da Yayan nasu ke musu ya bashi mamaki, cikin dauriya yace, “Yayanmu na zata ka kwanta ma ai”.         “Shiyyasa kazo nan kake taɗi?”. Ya faɗa yana wucesa. Saurin waro idanu Khalipha yay waje da biyo bayansa. “Ni Abdul-Mutallab, jikan Abdul-Mutallab, ƙanin Abdul-Mutallab wane ni Yayanmu”.     Ɗan juyowa yay ya dubesa. Hakan yasa kunya kama Khalipha yakai hannu yana shafa wuya da risinar da nasa idanunsa ƙasa.          Wani irin juya idanunsa da suka ɗan fara sauya kala yayi yay gaba batare da ya sake cema Khalipha ɗin komaiba, dan harga ALLAH baya cikin hankalinshi da nutsuwar. Binsa da kallo Khalipha yay harya shige sashen Hajiya Iya. Kasa binsa yayi, sai kawai shima ya nufi sashensu zuciyarsa na ƙoƙarin karkato masa wani abu daban.         ★★★★     Washe gari da safe suka tashi da tashin hankalin ruɗewar jikin Hajiya Iya. Dan tunanin data kwana yi jiya game da kamanin little da AK ya ja jininta sake hawa sama matuƙa. Ita Zinneerah bata fahimtaba dan duk zatonta Hajiya Iya barci takeyi, dan itama kanta barcin nata rabi da rabi ya kasance. Sai da ta farka da asuba taji hajiya iya na wani irin wahallen nishine hankalinta ya tashi. Ruɗani ya sata fita da gudu zuwa ɗakin AK ta hau bugawa tana kiran sunansa.      Zaune yake saman sallaya yana karatun Al-Qur'ani dan shi ko sau ɗayama bai rintsa ɗinba. Yanda yaga rana haka yaga dare, a daren na jiya. Tunda yaji bugun ƙofar yasan ba lafiyaba. Ya ajiye Qur'anin tare da miƙewa a nutse ya nufi ƙofar ya buɗe ko sauraren Farah data farka da jan tsaki baiyiba.      A rikice Zinneerah ta damƙo hannunsa jikinta na rawa ga hawaye na kwarara. “Yayanmu Granny, Granny Yayanmu, dan ALLAH kazo Granny karta mutu”.       A take shima ya rikice. Ya shiga binta a baya tana riƙe da hannunsa har sannan tana jansa. Tunda suka shigo yaga halin da Hajiya Iyan ke a ciki sai hankalinsa yafi nata tashi, a take yay kanta yana kiran sunanta da ƙarfi.       Zinneerah daketa yarfe hannu kukanta na ƙara tsananta ya duba cikin sarƙewar harshe yace, “Ɗakkomin waya a ɗakina, m....”     Batama bari yakai ƙarsheba ta kwasa da gudu ta fice. A guje ta shigo ɗakin har tana bangaje Farah data sakko daga gadon tana mitar an tasheta tana barcinta. Wanwar Farah ta zube a ƙasan tiles ɗin amma ko kallonta Zinneerah bataiba ta nufi wayar data hango a drawer gefen gado duk da bata da tabbacin nasane. Sai dai tana kaiwa garesu ƙamshinsa dake manne dasu suma ya tabbatar mata nasanne. Duka ukun ta kwasa ta sake tsallake Farah dake nishi a ƙasa ta fito.          Da ƙyar ya iya saita kansa ya lalubo Number Baffah, shima Baffah da yake ba wani barcin kirki yayiba akan idanunsa kiran ya shigo. Mamaki da tsoro ya sakashi ɗagawa ganin sunan Adnan.      Cikin ƙanƙanin lokaci dukkan ƴan gidan suka gama taruwa sashen hajiya Iya dake cikin mawuyacin hali. Khalipha ne keta ƙoƙarin bata taimakon gaggawa kasancewar ɗalibin likitanci dake gab da kammalawa insha ALLAH. Da ƙyar ya samu yaɗan saita wasu abubuwa. sai dai ya basu tabbacin dolene a wuce asibiti da ita tunda nan gida ba kayan aikine da shi ba.      Suna idar da sallar asubahi ko Shira Hospital suka wuce. A canne likitocin da sukai duty ɗin dare suka rufu kanta. Yayinda AK kuma ya shiga bige-bigen waya na shirin wucewa da Hajiya Iya London kamar yanda dama yaci buri tun da, sai dai tace bata zuwa Nigeria ma akwai likitoci ƙwararru. A yanzun kam tunda bata a hayyacinta yaci alwashin sai ya kaita insha ALLAH an duba wannan ciwon ƙafartata mai kama dana gado. Dan mafi yawan ƴan family ɗinsu na ɓangaren mahaifiyarta duk sanadin ciwon ƙafa suke barin duniya kamar dai Inno. Ga su duk ALLAH ya basu jikin ƙiba dama masha ALLAH............✍         *_Kuyi haƙuri naji kunata cewa bana bana yayinku naƙi muku surprise. Wannan karon abin ya haɗa da wasu uzurorine wlhy. Amma insha ALLAH zan baku mamaki indai pages ne, ina kuma sake baku haƙuri wannan karon akan tafiyar hawainiyarmu ta Typing gaba ɗaya. Ku ɗauki hakan matsayin yau da gobe sai ALLAH. Sannan wasunmu sunada lalurorin yau da kullum tattare da su, da kuma uzirorin rayuwa da duk sukazo mana tamkar an saita. Mukammu bama jin daɗin hakan, dan babban burinmu shine muga mun taru gaba ɗayanmu mun faranta muku tamkar yanda kuka faranta mana kuma kuke zuwa kuna sayen buks ɗinmu a koda yaushe. ZAFAFA TEAM na godiya gaba ɗayansu tare da fatan alkairi a gareku da ban haƙuri. da babban albishirɗin ganin gyara daga garemu baki ɗaya insha ALLAH_* *_Masu karantawa a waje kuma dan ALLAH ku daure kuzo ku saya naku copy ɗin da halalinku kuma ALLAH zai sakama kasuwancinku albarka ta inda bakuyi zato ko tsammaniba insha ALLAHU. Dan duk wanda ya kare mutuncin wani da fita haƙƙinsa kaima ALLAH zai fita naka ya kuma kare mutuncinka da izininsa._* *Muna godiya da zaɓin zafafa a koda yaushe😍😍😘😍😋🤗🙏🏻*. *_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 _Na Safiyya Huguma_ *_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖 _Hafsat Rano_ *_★ DALAAL_*💝 _Na Miss xoxo_ *_★ UBAYD MALEEK_*💓 _Na Mamu gee_ *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 _Na Bilyn Abdull_ Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 *_08085405215_* IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   0903 234 5899 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 *_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_* *_TYPING📲_* *_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_* *Page 27* _______________________ *_WANI KAYA SAI AMALE💃🏻💃🏻💃🏻._* *_INA MATA ƳAN ƘWALISA MA'ABOTA SON KALOLIN GIRKE-GIRKEN ZAMANI. KU GARZAYO GA DAMA TA SAMU A TAFIN HANNUNKU CIKIN SAUƘI💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻😋😋😋😋_* Nigeria @ 61 COOKING COMPETITION!!! from lavender Catering ina masu son koyon girki ga dama zaku shiga gasarmu ta girki bayan kunyi register damu akan 10k,wanda yazo na 1zai shiga ajin mu free hade da wasu prize din na 2 da na 3 kuma zasu bayar da rabin kudine da wasu prize suma saura kuwa zasu ayi musu ragin 5% da wasu prize wannan gasa zamu yita ranar lahadi ne 3/10/21 zamu rufe registration na gasar ranar asabar. Lavender catering school zamuyi practical class. zamuyi 30 dishes continental, snack & desserts, traditional dishes, drink. Fee din 40k phone number WhatsApp and call 09080299283 akwai discount na 5% ga mutum uku farko wadanda sukai register aranakun independence 1/10/2021 to 3/10/2021 Nigeria @ 61 Shi class zamu fara on 14/10/21. *_KU GARZAYO KAR ACI KASUWAR SAMA BABUKU, DAN NAMU BA IRIN NASU BANE💃🏻💃🏻💃🏻😋😋_* ________________________ *Page 27* ...........Alhmdllh an samu daidaituwar jikin hajiya iya, amma bawai tana a cikin hayyacinta yanda ya kamata baneba. Shiyyasa shima AK ya kammala dukan shirinsa akan tafiyar da ita. A wannan karon Baffah baiyi yunƙurin hanashiba. Sai ma taimaka masa da yay da wasu abubuwan kasancewar tafiyar ta zama ta gaggawa.         Duk wanda ya kalla shirawa a yinin yau yasan lallai an taɓa musu wani babban jigonsu, dan kowa idanu jajur. Daga masu kukan zuci har masuyin na zahiri irinsu Zinneerah. Dan ita dasu Bahijja haɗe kawuna sukai sukaita rusar uban kuka sai da Yah Haneef yayta lallashinsu da ƙyar da nuna musu sumata addu'a sannan suka ɗan nutsu.         Haka suka kasance yau yini guda a asibiti likitoci nata ƙoƙarin su, yayinda AK keta shigi da fici na ganin sunbar Nigeria a yau insha ALLAH. Yau ko ƙwaƙwaran abinci babu wanda ya samu yaci a cikinsu, sai ruwa da ƴan kame-kame. Salla kawai ke tashinsu.      Yah Adnan bai farga da babu matarsa a asibitinba sai da zasu koma gida domin shiryawa. Ransa ya ɓaci matuƙa amma ya daure ya shanye har suka isa gidan. Kamar yanda yay hasashe kuwa a gidan ya isketa wai taji ciwo a ƙafa saboda turewar da Zinneerah tai mata da asuba, ga kuma zazzaɓi tanaji. Duk da ya lura da yanda take alamar kuka ta zauna tasha baibi takantaba ya hau shirya musu kaya da kansa batare daya mata bayaniba. Yana gamawa kuma fiwowa yay zuwa ɗakin hajiya iya. Inda ya iske Zinneerah zaune tanashan sabon kuka.      Tsaye yay kawai shiru yana kallonta batare dayayi maganaba tsahon lokaci. ita kuma batasan da shigowar tasaba kanta na a cikin ƙafafunta ne. Yaɗan furzar da huci da cije lip ɗinsa yana ƙarasa takawa cikin ɗakin da ƙyau. Gyaran muryar daya saka Zinneerah ɗagowa yayi. Kallon cikin ido sukaima juna sai kawai ta fashe masa da kuka. Idanunsa ya lumshe yana ɗan kauda kansa gefe.          “Dan ALLAH Yayanmu kaje dani duk inda zaku kaita”. Ta faɗa kukanta na kuma tsananta. Baice mata komaiba ya nufi bathroom ɗin ɗakin dake gyare tsaf duk da yau babu wanda yabi takansa. Ruwa mai ɗumi ya tara a botiki ya fito, inda ya barta anan ya isketa tana cigaba da kukan nata. “Tashi kije kiyi wanka”. Ya faɗa yana nufar inda littatafan hajiya iya suke na addini batare daya sake kallontaba.      Jin abinda yacene ya saka Zinneerah miƙewa da saurinta duk zatonta ƙorafinta ya karɓune. Littatafan ya gama ɗauka da wasu ƴan abubuwa na Hajiya Iyan yasa a ƙaramar jikka. a saman gado ya barta ya fice domin zuwa shima yayi wankan.      Sauri-sauri Zinneerah tahau shiri bayan fitowarta wanka kasancewar ba salla takeba. Tana gamawa ganin jikkar daya ajiye akan gado itama ta jawo akwati tahau haɗa nata kayan. Tana tsaka da neman wayarta da tun jiya bayan ta kira mmn sadiq bata sake ganin wayarba, har so tai ta kirata yau ma ta sanar mata halin da ake ciki amma sai bataga wayarba.        Shigowar AK ɗakin da sallama ciki-ciki, Baba Rahi biye da bayansa ɗauke da tire ya sata dakatawa da leƙe-leƙen neman wayar da takeyi.  Juyowa tai tana kallonsu, yanzu kam shima yayi wankan dan yana sanyane cikin ƙananun kaya sai uban ƙamshinsa ke tashi dan yama danne nata turaren data saka. Shiko kallo ɗaya yay mata ya ɗauke yana maidawa kan akwatin data haɗa kaya. Baiyi maganaba sai zama da yay  cikin sofa ya ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya yana sauraren Baba Rahi dake lallaɓata ta zauna taci abinci.       “Baba Rahi na ƙoshi, ALLAH bana jin yunwa”.        Manyan idanunsa da launinsu ya canja gaba ɗaya a yunin yau ya ɗago ya zuba mata cike da gargaɗi, babu shiri ta amshi kofin shayin da Baba Rahi ke miƙo mata tai ƙasa da kanta tana kaiwa baki badan yana mata daɗi ba, dan bakintama ji take yana wani ɗaci-ɗaci. Ɗauke idanun nasa yay ya jingina da kujerar yana mai lumshe su. Sai dai kuma yana kallonta ta ƙasan idon.        Baba Rahi ce ta cigaba da lallashinta har taɗanci abincin shima kaɗan ta ture idanunta cike da kwalla tace ta ƙoshi, Batare da Baba Rahi tace komaiba tahau tattare kwanikan zata fita da su ya dakatar da ita. “Baba barsu anan jeki abinki”.        Amsa masa Baba Rahi tai tana maido tiren ta ajiye, Zinneerah kuwa kallon inda yake ta ɗanyi kamar zatai magana sai kuma ta maida kanta ta duƙar. Shi kuma batare daya tashi koya buɗe idanunba yace, “Tashi ki ɗauka maganinki da abincin kizo nan”.        Ita tama manta wai bata da lafiyane. Shakkarsa yasata miƙewa ta ɗakko din tayi yanda yace batare data musa bin umarninsa ba. Ɗagowa yay daga yanda yake a zaune ya buɗe abincin da kansa ya sake tura mata gabanta. “Na baki 10minutes kawai ki cinyesa”. Daga haka ya koma a yanda yake kamar ɗazun. Cika idanun Zinneerah sukai da ƙwalla. Taja abincin gabanta tana ƙoƙarin haɗiye ƙwallar tata dan bataga wajen yin wargi ba. ALLAH ma ya sota abincin ba wani mai yawan tsiya bane dan baba Rahi dama ta santa bawani cin abincin take sosai ba. Sai da ta gama tasha maganin sannan ya sauke ƙafarsa da gyara zamansa yana faɗin, “Zonan”.      Babu musu ta miƙe zuwa garesa. Sai dai inda ya nuna matan ta zauna ne yasata jin shakku tatsaya tana duban gefen nasa. Harar daya balla mata ce ta sata zaman babu shiri daga can ƙarshen kujerar duk da tazarar ba wata mai tsaho bace a tsakaninsu.         Ƙasa tai da kanta tana wasa da yatsun hannunta, ji take ba'a taɓa saka rayuwarta a takuraba irin ta yau ba, dan kwarjininsa da ƙamshinsa gaba ɗaya sun sakata jin ɗakin ya musu kaɗan. Shiko ko a jikainsa kallon hanunta da taketa faman cuɗawa a juna kawai yakeyi cike da nazari. Mikuma ya tuna oho masa sai yay saurin kauda kansa. Kusan mintuna uku suna a haka shiru kafin ya sake dubanta.         “Kikace zaki bimu?”. Ya faɗa ciki-ciki idanunsa ƙyam akan fuskarta.      “Eh Yayanmu dan ALLAH”.   Ta bashi amsa itama murya na rawa. Kwarjininsa na sake tsumata dan ta kasa ɗagowa ta dubesa. Tamkar bazai sake cewa komaiba sai kuma yaɗan girgiza kansa. “Idan kin bimu karatunki fa? Ko kin jinginesa kenan?”.      Idanunta da suka ciko da ruwan hawaye ta ɗago a karo na farko ta kallesa, sai gasu a cikin nasa dan shima ita ɗin yake kallo. Yanda ya tsatstsareta dasu ne ya tilastata maida nata ƙasa hawayen cikinsu da batasan na miyeba na gangarowa. Sai dai tana danganta zubar tasu da takurar da tayi na kasancewar su zaune a waje ɗaya yanda mafalkinta bai taɓa kaiwaba.     Ya sake maimaita mata cewar, “Nace karatunki fa idan kin bimu?”.       Muryarta na rawar kuka tace, “Yayanmu nidai kaje dani dan ALLAH, idan na dawo naje makarantar, inason na kasance da Granny kawai”.         “Saboda karatun baida muhimmanci a wajenki ko?”.      Kasa cewa komai tayi a wannan gaɓar, hakan ne ya sakashi sauke murya ƙasa da alamun lallashi a ciki yace, “Bazaki bimu yanzuba, dan shi ilimi abune mai muhimmanci ga mai nemansa, adalci ɗaya zan miki shine idan kunyi hutu zakizo ki ganta ok”.       Sharrr hawaye suka sake ɓalle mata. Ta ɗago zatai magana ya miƙe abinsa yana faɗin, “Na gama magana ki tashi ki saka mata kaya kala biyu a wancan jikkan dana ajiye, sai abubuwan da kika sani masu muhimmanci da take amfani dasu yau da kullum. Wannan kayan naki da kika haɗa kuma ki kaisu sashen Momie dan zaki koma da zama can wajenta”.        Daga haka ya fice abinsa ko waiwayenta baiyiba duk da yaji kukan data fashe dashi. Kansa kawai ya girgiza yana ƙara jinjina ƙuruciyarta da shagwaɓa a ransa.        Karo ya kusanci da Farah wadda ke ƙoƙarin shigowa ɗakin alamar biyosa tayi, ya ɗan bita da kallon mamaki kamar zaiyi magana sai kuma ya ɗauke kansa da raɓata ya wuce abinsa. Har tayi kamar ta shiga ɗakin Hajiya iyar taga mi yayo a ciki tun ɗazun sai kuma ta fasa tabi bayansa da sauri. Yana shiga ɗakin itama tana shigowa. Zama yay cikin kujera ya hau haɗa shayin daya saka Baba Rahi dafa masa shima. Sai da ya kammala zai fara sha sannan ya kalli Farah data zauna kusa da shi ta wani tsatstsaresa da idanunta manya.       “K kina ganin abinda kikayi yau shine dai-dai? Kowa yana asibiti ke kina gida kwance?”.        Cike da isarta tace, “Amma dai kasan nima banda lafiya ne ai. Sannan wannan shegiyar yarinyar sanda ta shigo ɗakinan ta ɗauka wayoyinka turenifa tayi a ƙasa amma ko waiwayena batayiba. Jiba kaga yanda ƙafata ta kumbura”. Tai maganar tana nuna masa ƙafar da cigaba da faɗin, “Wlhy yanda ta sani jin azabarnan itama sai na sakata taji wadda ta fita dan saina karyata kafin nabar gidan nan”.        Ɗauke idanunsa yayi daga kan ƙafar kamar baiji mita faɗaba. Duk da masifar data cigaba dayi akan Zinneerah ɗin bai tanka mataba harya gama shan tea ɗinsa sannan ya miƙe. Hakan da yay ya ƙona ran Farah, sai dai ganin ya ɗakko man zafi ya dawo ya zauna da kama ƙafar tata ya ɗora a jikinsa ya sakata sauke ajiyar zuciya.      Duk da ya jita baice uffanba ya hau shafa mata maganin a wajen yana ɗan dannawa kaɗan-kaɗan itako tana zuba shagwaɓa. Sai da ya tabbatar maganin ya shigeta sannan ya ajiye ƙafar yana dubanta cikin ido. “Yau zamu wuce”.      Mamaki ƙarara a fuskarta tace, “Ina?”.        Kansa tsaye yace, “London, Granny zataga Doctor acan”.      Jitai kamar an daɓa mata mashi a ƙirji. ta tattaro yawun takaici ta haɗiye muƙut tana dubansa, “Amma my Hero duk likitocin ƙasarnan har sai an kwashi kamar Granny dake fama da jikin tsufa an wahal da ita zuwa wani waje”.        “Ke kika kallesa a fuskar wahala. mu neman sauƙi zamu insha ALLAH ”.        Harara ta zuba masa a kaikaice zuciyarta nayi mata zafi, cikin ɗan rawan murya tace, “To sai dai kuje ni kasan dai babu inda naje. Bazai yuwu na shigo ƙasarnan ba kuma ban ziyarci kowaba”.         Juyiwa yay ya kalleta cikin ido fuska a tsuke ainun, cike da gargaɗi da barazanarsa yace, “Da zaki taho ai nan aka turoki, dan haka iya nan ɗin zaki tsaya. Nan da awanni shida jirginmu zai tashi”.        Yanda ya tsareta da idanun ya hanata iya cewa ƙala, dan tasan mi wannan kallon nasa ke nufi a gareta. Dole ta tsuke bakinta hawaye na rige-rigen sakko mata. Batare dayabi takantaba ya miƙe ya fice dan yanason yin magana da Baffah.      Miƙewa tai a harmutse itama ganin ya fice tana masifar bazata yarda hajiya iya ta bisuba. Dan babu yanda za'ai a jajubar musu gayya a takurawa rayuwarsu. Khalipha ɗinma ta ɗauki alwashin wannan karon bazai koma mata da zama a gidaba. Sai dai ya koma hostel kamar yanda Mammah ta faɗa. Haka taita masifa tana kuka da neman wayar Mammah amma taƙi shiga. daga ƙarshe sai auntynta ta samu ta kira sukaita masifar tare, Auntyn ta ta katse wayar ta kirashi. Yana ganin kiran sanda yake tare da Baffah yaƙi ya ɗaga dan yasan zancen dai bai wuce mai hali tayi halin nataba...........✍ ★★★          *_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 _Na Safiyya Huguma_ *_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖 _Hafsat Rano_ *_★ DALAAL_*💝 _Na Miss xoxo_ *_★ UBAYD MALEEK_*💓 _Na Mamu gee_ *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 _Na Bilyn Abdull_ Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 *_08085405215_* IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   0903 234 5899 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 *_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_* *_TYPING📲_* *_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_* *Page 28* ___________________________ *MG’s SKIN CARE* (With us, your skin is elegant..) Are you guys  looking for where to buy ur skincare product @ mg's skincare is the best plug for you🤗 Do you wish to have that flawless skin that's free of all skin prblm Do you wnt to achieve that milky skin that turn heads wherever you go😉 Try mg's product nd I assure you you'll never use any other product except mg's product✅ Mg's will gv you the best out of all With mg's product ur skin is 💯 clear,fresh,smooth nd ur skin will absolutely glow all day💃 We have herbal whitening black soap now nd beauty set available Nd both the soap nd the beauty set is for all skin type everyone can use it🤗 Just gv it a try now nd see wonders✅ Chat:08062991549 Call:08064532391 Soap price:3k set:11k Follow us on Instagram@glow_with_mgs Facebook:mg's skincare Nd guess wht🦻 Duk Wanda zesiya Kaya daga yau Alhamis  30-9-21 zuwa Nanda 5days that is ranar talata there will be 20% off discount a soap nd the set😍so what are you guys waiting for hurry nd grab urs💃 now is  the time to glow🧖‍♀️ Pamper ur skin🦵 Shine like a bride 👰 be part of the glow team karkubari abaku lbr Just chat 08062991549 to plc ur orders😘 Do not forget to follow us👆 Like nd comment pls dearies😘 Patronize us🙏 mg's always serve you the best✅❤️ KAYAN MG’s SKIN CARE, GANGARIYA NE, SAI AN GWADA AKAN SAN NA KWARAI, KU GARZAYA KU SAYI NAKU KAYAN A KULI KALILAN DOMIN DAGA YAU TAFARA BONANZA. IDAN ANJE ACE DAGA ZAFAFA NE, AKWAI RANGWAMEN KUDI SOSAI, KYAU, INGANCI, RAHUSA.. SAI KAYAN MG’s SKIN CARE. ___________________________ *Page 28* ............Ƙarfe takwas da kwata dai-dai jirginsu ya tashi zuwa ƙasar London. Farah nata ƙunci akan ita batai shirin komawaba yau. Sai dai shi uban gayyar yasan haushinta bai wuce na tafiya da Hajiya iya ban. Har cikin ransa mamakinta ke ƙara faɗaɗa a ransa. Yanaji kuma lokaci yayi dazai maidota cikin hayyacinta akan danginsa.      Ita kanta Mammah wannan karon ya shirya mata tsaf, dan yasan ba ƙaramin rikici zadu kwasaba akan wannan tahowa da Hajiya iyan da yay, shiyyasama ko faɗa matai biyiba sai sun isa ta gansu. Ita kanta Farah sai da suka isa airport hankalinta ya ƙara tashi.           Tun bayar wucewarsu zazzaɓi mai zafi ya rufe Zinneerah. Ta kuma maƙale a sashen hajiya iya taƙi tafiya wajen Momie da yace mata. Sai da su Meenal da suma suka gama shan nasu kukan suka biyota sannan. Ganin halin da take ciki suka koma suka sanarma Momie. Da kanta tazo har sashen hajiya iya ta lallaɓata da lallashinta sannan suka kashe komai na sashen ta ɗauki duk abinda take buƙata na amfaninta da kuɗin da Yah Adnan ya bata, dana Khalipha suka wuce. Sai dai fa wayarta ce sunsha nema yanzun ma amma basu ganiba. Ta rasa inda ta jefata tun jiya da rana bayan tayi waya da Mmn sadiq. Momie ce tace subar wayar da safe azo a sake dubawa tunda an kira ma a kashe take. Haka ta haƙura suka tafi can sashen duk da dama ta saba kwana wani lokacin.    Tun daga wannan ranar rayuwar Zinneerah ta koma sashensu Jamal, tanajin daɗin zama da kowa dan babu mai tsangwamarta ko nuna mata banbanci, sai ma wani al'amari mai ƙarfi dake neman saƙuwa tsakaninta da Yah Moos'ab duk da har yanzu bai firta mata cewar yana sonta ba. Yabarma ransa har sai ta kammala secondary kamar yanda yaci buri.          Amma sai kaf-kaf yake da ita musamman da yaga tafiyar Granny ta sakata shiga wani hali. Itako tsaf ta fahimci inda ya dosa amma take nuna masa bata gane komai, ɗaukarsa take kamar sauran samarin gidan kawai, dan ita bata saka soyayya a lissafin rayuwarta duk da tanajin Yah Khalipha a ranta shikam. Amma sai take ɗaukar hakan matsayin ganin girmansa akan taimakon da yay mata wancan karon da bata da gata.        Kullum takanyi waya da Khaliphan a wayar su Jamal, anan ne takejin cigaban da ake samu game da jikin hajiya iya da Yayansu keta kashe kuɗi akan ganin ta samu lafiya. Bata taɓa waya da shi ba. Sai dai duk santa ta buɗe akwati zata ɗauka abu takanci karo da kuɗin da ya bata bandir guda na ɗari biyar, sai turarensa shima daya bata tare duk a ranar da zasu tafin, duk da ko sau ɗaya bata taɓa shafashiba ya gauraye mata kayan cikin akwatin da ƙamshinsa.            Sai da suka cika sati uku cif da tafiya Zinneerah taji muryar Hajiya iya. ALLAH sarki zokaga murna da farin ciki ita dasu Bahijja. Bama suba duk wanda yake a gidan ranar saika fahimci yana a cikin farin ciki, dan duk sai da ta gaisa dasu. Kwana biyu dayin haka kuma Baffah ya dawo daga can ya ƙara sanar musu da cigaban da aka samu.         Hajiya iya na cikin sati na bakwai a london su Zinneerah suka sami hutun makaranta. Kai tsaye ta sanarma Momie tanason taje gida hutu, duk da tana waya dasu kullum ta wayar su Bahijja dan ita dai tata wayar an rasa inda ta faɗa har yanzun, harma ta haƙura dan tasu Meenal ma ta wadatar da ita tunda dama daga amsa waya da kiran su mama sai games suke da wayoyin, sauko abinda ya shafi karatu idan ta kama. Yah Khalipha kuma ya mata alƙawarin zuwa mata da wata idan zaizo.        Shiri Momie tai mata na zuwa gida ita da Baffah duk da kuwa anan cikin garine. Ranar da suka cika kwana biyu da samun hutu Moos'ab da kansa ya kaita gida tare dasu Jamal. Ganin little ɗinta daya ƙara girma da ƙannenta da mama ya mantar da ita kewar su Bahijja da suka wuce. Tuni suka shiga hira tana ƙara bama mama labarin yanda jikin hajiya iya keta ƙara ƙyau. Amma Yayansu yace bazata dawoba sai bikin su Aunty Safiyya.      Mmn sadiq taji daɗi sosai, dan tana ƙaunar hajiya iya da zuri'arta kodan karamcinta garesu. Sai dai kuma a wannan karon ta shirya binciken Zinneerah akan samuwar little. Dan tun ganin AK datai hankalinta bai sake kwanciya ba. Ita harma zargi take itama Hajiya Iya dalilin little ɗinne ciwonta ya motsa.       Ba ƙaramin girgiza zukatansu Sakina wannan zuwan ma Zinneerah tayiba. Dan su kansu sunsan ta wuce da ajinsu yanzun, samarin anguwar kuwa da suka nuna suna sonta a baya suka dingi ɓata Zinneerah a wajensu ganinta ya sake dawo dasu gareta. Sai dai taƙi bama kowa fiska dan burinta bana aure bane yanzu karatu ne.       Tana kwana huɗu da zuwa sai ga Yah Haneef da Yah Mas'ood sunzo wai zasu kaita ai mata passport inji yayansu. Bata fahimci inda zancen ya dosaba amma saita shirya suka tafi harda Little da tun zuwansu gidan suka janyesa. Shiko duk da rashin son mutanensa sai gashi ya saki jiki dasu kamar yanda yayi randa su Jamal sukazo.         Wajaje sukaje kusan uku kuma duk sun jima. basu dawoba sai yamma lis tare da siyayyar kayan ciye-ciye fal leda da suka yima little. Bayan wucewarsu ne Mmn Sadiq dakema little shirin barci ta duba Zinneerah ɗin.        “Niko nace dama tunkan kizo nan kinsan wannan Yayan naku ne Zinneerah?”.      Zinneerah dake cin gyaɗa ta ɗago tana kallon mama. “Mama wane Yayan a ciki?”.        Kai tsaye Mama tace “Adnan”. Shiru Zinneerah tai tana kallon Mama na wani ƴan sakkani, a ranta tambayar na bata mamaki. “Wai badake nake maganaba ne kika tsaya kallona?”.        Numfashi Zinneerah ta sauke dan itama ta tafi wani tunani ne kuma daban. “Yi haƙuri Mama, tambayarce wlhy ban ganeba”.       “Basai kin fahimceniba dama ai. Amsa zaki bani”.       Da ƴar dariyarta tace, “A'a wlhy mama ban sanshiba sai a wannan karon da yazo gidan, bamma taɓa ganinsa ba nikam. To shi dama akace baya zuwa ma ƙasar a ina zan sanshi Mama?”.       Idanu Mmn sadiq ta zuba mata cike da nazari, kamar zatayi magana sai kuma tai shiru ta barta kawai. “Tashi ki kai Wannan ɗaki tunda barcin nasa yayi nisa”. Miƙewa tai ta ɗauka little da yay barci tunkan su dawo, sai da maman zatai masa wanka ya farka. Ana gamawa kuma ya sake komawa dan ya gaji matuƙa sunsha yawo.     Da kallo kawai mmn sadiq ta bita harta shige ɗauke da little ɗin. Harga ALLAH ranta cike yake fal da fargabar abinda zuciyarta ke ayyana mata a koda yaushe tun ganinta da Adnan ɗin. Shi kansa Abba data bashi labari zancen ya girgizashi, har yau kuma sun kasa daina tattauna maganar a duk sanda take tare da shi. Sai dai sun kasa fahimtar komai akan al'amarin sam. To gashi wadda ma suke da hope ɗin samun wani bakin zare a gareta tace bama tasanshiba itama. Duk da ta fahimci Zinneerah bata iya ƙarya ba wannan karon ta gagara gaskatata akan batun rashin sanin Adnan.     Washe gari da taci burin sake zaunar da ita akan batun sai ga Moos'ab wai yazo ɗaukarta dan zasu wuce da sassafe gobe idan ALLAH ya kaimu wajen hajiya iya. A take farin ciki ya bayyana ga Zinneerah tahau shiri, mmn sadiq kuma suka hau gaisuwa da Hajiya iya ta wayar Moos'ab ɗin itama. Sai da suka gama wayarne ta miƙe ta shiga haɗama hajiya iya ƴar tsarabar data san zataji daɗinta idan an kai mata. Cikin ƙan ƙanin lokaci Zinneerah ta gama shirinta tsaf suka wuce bayan sunyi sallama da Abba ta waya duk da dama jiya mama ta sanar masa fitar su Zinneerah ɗin, shine ya ɗanyi zargin ko wajen hajiya iya zasuje dama. To amma baiyi tunanin tafiyar haka gab ba.          Tunda suka iso gidan suka haɗu dasu Jamal suketa murnar tafiyar musamman ma ita da ko jirgin ƙasa bata taɓa ganiba😹, dan su huɗu kawai zasuje ashe. Ita, Jamal, Meenal, Bahijja. Anan ma koda ta dawo ba zaman sukaiba, fita suka sakeyi ita da Moos'ab ta ƙarasa abinda ya rage mata tunda wannan ne karon farko da zata ƙetare 9ja. Abinka da maganar kuɗi kuwa sai gashi a tsakanin fitarsu ta jiya data yau ɗin komai ya kammala, tunda dama ƙasar tamu waka sani ya sanka akeyi.     Suna dawowa sashen hajiya iya taje ta ɗakko abinda zata buƙata suka shirya kayansu tsaf duk da bawasu uban kaya suka ɗauka ba. Gara itama ta haɗama Hajiya iya da saƙonta na wajen mama da kuma abinda tace ta ɗakko mata. ________________★★         Abin mamaki yau sai ga Zinne ta danya mai tallar riɗi da gyaɗa a airport za'a ƙasar burtaniya. Babu wani ɓoye-ɓoye murnarta take nunawa a fili musamman da suka iso airport ɗin. Aiko su Jamal suka tasata gaba da tsokana suna dariya. Ko'a jikinta dan iya gaskiyarta ta faɗa. Bayan kammala tsarabe-tsaraben airport jirginsu ya ɗaga zuwa ƙasar burtaniya zuciyar Zinneerah cike taf da tsoro lokacin da jirgi zai tashi. Dan sai da ta ƙanƙame hannun Bahijja dake kusa da ita hanjin cikinta na wulƙitawa tamkar zata amayosa ta baki. Sai da jirgin ya gama dai-daita a gajimare ta buɗe idanunta tana sauke tagwayen ajiyar zuciya.        Tun Zinneerah na marmarin tafiyar da ɗoki harta fara ƙosawa, dan bata da jimirin dogon zama dama ita. Lokacin da jirgin ya samu kaiwa ga ƙasa jitai kamar tamafi kowa farin ciki tsabar gajiyar datai da ƙaguwar son ganin Hajiya Iya. A wannan gaɓar ba itace kaɗai baƙauya ba hatta dasu Jamal ɗin ƙauyawa suka koma. Dan shine karonsu na farko zuwa ƙasar london.        A yayin sakkowar tasu Jamal ne gaba. Ita a bayansa sai Bahijja da Meenal biye dasu. Kowanne yana jaye da trolly ɗinsa ƙarami a hannu. A kallo guda dolene su birge ka musamman da suka kasance a ganiyar shekarunsu na ƙuruciya..............✍ *_Masha ALLAH. Guys asha hutun weekend lfy ko😋😉😘😍😘😍🤗._* *_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 _Na Safiyya Huguma_ *_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖 _Hafsat Rano_ *_★ DALAAL_*💝 _Na Miss xoxo_ *_★ UBAYD MALEEK_*💓 _Na Mamu gee_ *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 _Na Bilyn Abdull_ Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 *_08085405215_* IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   0903 234 5899 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 *_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_* *_TYPING📲_* *_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_* *Page 29* _________________________ *MG’s SKIN CARE* (With us, your skin is elegant..) Are you guys  looking for where to buy ur skincare product @ mg's skincare is the best plug for you🤗 Do you wish to have that flawless skin that's free of all skin prblm Do you wnt to achieve that milky skin that turn heads wherever you go😉 Try mg's product nd I assure you you'll never use any other product except mg's product✅ Mg's will gv you the best out of all With mg's product ur skin is 💯 clear,fresh,smooth nd ur skin will absolutely glow all day💃 We have herbal whitening black soap now nd beauty set available Nd both the soap nd the beauty set is for all skin type everyone can use it🤗 Just gv it a try now nd see wonders✅ Chat:08062991549 Call:08064532391 Soap price:3k set:11k Follow us on Instagram@glow_with_mgs Facebook:mg's skincare Nd guess wht🦻 Duk Wanda zesiya Kaya daga yau Alhamis  30-9-21 zuwa Nanda 5days that is ranar talata there will be 20% off discount a soap nd the set😍so what are you guys waiting for hurry nd grab urs💃 now is  the time to glow🧖‍♀️ Pamper ur skin🦵 Shine like a bride 👰 be part of the glow team karkubari abaku lbr Just chat 08062991549 to plc ur orders😘 Do not forget to follow us👆 Like nd comment pls dearies😘 Patronize us🙏 mg's always serve you the best✅❤️ KAYAN MG’s SKIN CARE, GANGARIYA NE, SAI AN GWADA AKAN SAN NA KWARAI, KU GARZAYA KU SAYI NAKU KAYAN A KULI KALILAN DOMIN DAGA YAU TAFARA BONANZA. IDAN ANJE ACE DAGA ZAFAFA NE, AKWAI RANGWAMEN KUDI SOSAI, KYAU, INGANCI, RAHUSA.. SAI KAYAN MG’s SKIN CARE. _________________________ *Page 29* .............Meenal da ke ƙarshensu ce ALLAH ya bata ikon hango Yah Khalipha. Cike da jin daɗi da zumuɗi tace, “Guys ga Yah Khalipha can”.      Kusan duk a tare suka kalli inda ta nuna ɗin, hakan yayi dai-dai da ɗagowar Khalipha ɗin kuwa shima idanunsa suka hango masa su. A tare suka nufi juna cike da zumuɗi da farin ciki. Jamal ya shige jikinsa suma su Bahijja haka. Hannu ya miƙama Zinneerah alamar tazo itama sai ta noƙe kafaɗa tana murmushi. Sosai hakan da tai yay bala'in birgesa. Ya saki ƙannensa yana nufowa inda take fuska ɗauke da murmushi.       “Uhm Gimbiyar mata ke ta dabance fa”.      A bazata kalmar tazoma Zinneerah daga bakin nasa. Kamar yanda shima tazo masa a suɓutar baki. Ta ɗago manyan idanunta cikin nasa tana wani warosu irin alamar dai mamaki. Kansa ya girgiza mata shima yana waro nasa idanun dariyarsa na ƙara faɗaɗa. Babu shiri Zinneerah tai dariya da saka tafin hannunta ta rufe fuskarta dan taji kunya kuma.         Su Jamal dake musu dariya suma suka shiga gaishesa. Da kulawa ya amsa musu har ita Zinneerah data samu ta gaishesa a ƙarshe. Daga haka suka nufi taxi suka shiga yana faɗin, “Kuyi haƙuri fa nan kunsan ajiye mota ga talaka sai yayi nishi, motar gidan Yayanmu ya fita wajen aiki da ita”.           Cikin rashin damuwa da wannan suka shiga dariyar maganarsa. Sai ma suka koma tambayarsa Hajiya iya. A take ya fara basu labarin tana nan suna zuba tsiya da Aunty Farah. Yana basu labarin rikicin da akeyi a gidan suna kwasar dariya. Sai dai ko sau ɗaya Zinneerah bata saka baki a hirar tasuba. Murmushi kawai takeyi tana dai saurarensu da kallon hanya, zuciyarta na yaba ƙyawun ƙasar burtaniya da tsarinta. Tare da godiya ga UBANGIJI da ya bata damar ƙetare ƙasarta zuwa wata ƙasa batare da ko a mafarkinta hakan ya taɓa zuwa mata a cikin ranta ba.         Sai da suka iso inda ya dace ta kawo numfashi, waje ne daya samu tsararrun gine-gine da burgewa ga mai kallo. Babu wani hayaniya a wajen dan saima ka ɗauka ba gidaje baneba wata ma'aikatace. Su kansu sai bayan shigarsu ainahin cikin estate ɗin suka fahimci nannefa inda gidan Yayan nasu yake kenan. Sun haɗu da mutane ɗai-ɗai dake kai kawo, kamar masu fita da masu shigowa. Duk da kasancewar ginin estate ɗin a dunƙule yake waje ɗaya idan ka shiga baka da alaƙa dana kowanne, abinda kawai zakai nufar hanyar da zata kaika ainahin number naka building ɗin. Abinda kuma zai birgeka a rayuwar wajen babu ruwan wani da wani. Iyakarka da kowa hello hii idan an gamu.         Zinneerah daketa tunani a ranta taketa ayyana dolene turawannan su dinga ganinmu a banza. Dan duk wani jin daɗin duniya tamkar an tattarashine garesu. Basusan wani tashin hankalin rayuwaba sukam sam. A African kashe-kashen nan kawai ya ishi bawa da yunwa. Mu baga neman lahirarba duniyar da mukeso kuma kullum cikin wahal damu take. Gamu nan dai babu fasali ko wasu abubuwan birgewa duk mun fita a hayyacinmu.....     Nannauyan numfashi ta sauke saboda taɓatan da Bahijja tayi, “Haba Baby ina kika tafi haka ne?”.      Ɗan murmushi Zinneerah tayi da duƙar da kanta saboda kallon da Khalipha ya kafeta da shi. A hankali tajawo trolly ɗinta ta fito a cikin taxi ɗin tana gyara bag ɗinta. Jamal sarkin tsokana yace, “Ashe ni ƙauyancina ma kaɗanne ga wadda ta fini”.      Harara ta zuba masa da kai masa duka ya goce yana dariya. Khalipha ya girgiza kansa yana nufar ƙofar da zata sadasu da gidan na yayansu yana faɗin, “Uhm kudai tuna a ina kuke yanzun, kokuma ku koma Nigeria ba'a yanda kuka zo Burtaniya ba”.         Dukansu sun fahimci inda zancen nasa ya dosa. Dan haka duk sukai ƙaramar dariya kowa na faɗin albarkacin bakinsa.          Tunda suka shigo man kan kowa ya tsiyaye tas suka koma santin zuciya, sunaji a ransu dolene Aunty Farah da take hura musu hanci ashe tasan abinda ta taka. A ɗan corridor ɗin kafin ka shiga ainahin falon duk suka cire takalmansu suka saka cikin drawer dake a wajen alamar ba'a buƙatar ganinsu a waje. Sabbin Slippers na zaman gida Khalipha ya ciro daga cikin drawer ɗin ya miƙa musu. Kowa cira yay ya saka sannan suka shigo ainahin falon daya tsaru harya gaji. Sai ka rantse ma ba'a amfani dashi tsabar yanda yake fes. Tozali da Hajiya iya dake hakimce zaune ta ƙara ƙyau ya mantar dasu a ina suke da kuma santin. Tuni suka yadda bags suka nufeda da gudu cike da ihun farin ciki duk suka ɗaneta.     Itama dai cike da farin cikin ta tarbesu tana dariya dajin ƙaunar ƴan jikokin nata da kewarsu.         Cikin ɓacin rai Farah ta fito daga wani lungu danjin hayaniya na neman halaka mata kunnuwa, sanye take cikin wando dogo da riga da sukai mata ƙyau ainun, taku take cike da isa da ƙasaita fuska a yatsine. Taja ta tsaya turus tana dubansu alamar batama san da zuwansuba, dan sosai mamakin ganin nasu ke bayyana mata kan fuska ƙuru-ƙuru. Gashi kuma babu damar magana saboda hajiya iya. Sai dai wani kallon tsantsar takaici takema Khalipha da shima kai tsaye ita ɗin yake duba.      Kamar zatayi magana sai kuma ta fasa ta janye idanunta daga kansa ta maida kansu Meenal da sai a yanzu nasu idanun suka ganta. Duk da sunsan halinta na wulaƙanci sai sukai ƙoƙarin nuna murnar ganinta suna gaisheta cike da girmamawa kodan darajar wanda ya ajiyeta a gidan. A yatsine ta amsa musu ɓacin ranta na kasa ɓoyuwa, ta kafe Zinneerah da ko kallon inda take bataiba balle gaisheta da ido. Zinneerah da batasan tanaiba gaba ɗayama hankalinta nakan Hajiya iya batasan da zuwanta wajenba. Lura da kallon da Farah kema Zinneerah ɗinne yasa Khalipha kiran sunanta.     Ta juyo fuskarta ɗauke da murmushin da takema Hajiya iya ta dubesa. batare da yayi maganaba ya nuna mata Farah.      Da iya gaskiyarta tace, “Ayyah Aunty kiyi haƙuri bansan kin fito bane. Mun sameku lafiya? Yaya jikin Granny”.       (Buhun bura uban nan kayyasa) Farah ta ambata a zuciyarta tana kafe Zinneerah da wani shegen kallo, dan babu abinda ta hango a zancenta sai tsantsar rainin wayo a gareta. Batare data amsama Zinneerah ɗimba tabar wajen cike da takunta na ƙasaita da izza kai kace wata sarauniya ce.      Gaba ɗayansu da kallo suka bita. Hajiya iya ta girgiza kanta kawai tana mai nema mata shiriyar UBANGIJI a ranta. Yayinda su Jamal duk jikinsu yayi sanyi. Zinneerah kam ko'a jikinta, dan itako a masu mugun hali taga waɗanda suka taka Farah suka shanye mizaisa na Farah ya dameta. A bazata dariya ta siɓicema Khalipha ya kauda kansa gefe yanayi. Dan haka kawai ta bashi dariyar. Ita dake takaicin zamansa shi kaɗai ga wasu huɗun nan an kuma kwaso mata bayan Hajiya Iya. Sai dai kuma shi duk zatonsa tasan da zuwan nasune tun farko, amma a yanda tayi yanzu kam ya tabbatar Yayansu ya ɓallo ruwa yau.        Hajiya iya ce tai masa daƙƙuwa, ya ɗauke kansa yana haɗiye dariyar badan yaso ba. Itama maida hankalinta ta sakeyi gasu Bahijja dake gaisheta da tambayar lafiyarta, itama tana tambayarsu mutanen gida da hanya.         Sai da Khalipha yace, “Ashe ƙaryar gajiya kukeyi daman”.         “Yah Khalipha ganin Granny yasa gajiyarma ta gudu ALLAH”. Bahijja ta faɗa tana dariya. Murmushi yayi da kallon Granny dake magana da Zinneerah fuskarta a washe itama alamar tana cikin farin ciki yau fiye da kullum, sai yaji daɗi a ransa. Koba komai sa huta da mitarta na a maidata gida ita ta gaji da zaman kurkuku.       “Assalamu alaikum”.    Suka tsinkayi muryar Yayansu dake ƙoƙarin shigowa a bazata. A take duk sukai tsit da maida dubansu ga ƙofar. Khalipha ya miƙe ya nufesa ganinsa ɗauke da ledoji a hannu. Suma ɗin duk tsaye suka miƙe domin bashi girmamawa. Ledojin ya miƙama Khaliphan yana faɗin, “Thanks besty” ba tare dasu sunji miya faɗa ɗinba. Sai motsawar laɓɓansa kawai suka hanga.       Cikin haɗa baki sukace “Barka da dawowa yayanmu;       Sai yanzune ya kallesu fuskarsa da ɗan sakewa amma ba murmushi yakeba. Ya zame rigar sanyin saman suit ɗinsa yana hanging ɗinta a hanger ɗin dake gefensa, sannan ya ƙaraso cikin falon. Gaba ɗayansu gani sukai ya ƙara musu ƙyau da cikar haiba a idanu, kamar yanda Hajiya Iya da Yah Khalipha suka ƙara musu. Sai da yakai zaune ya harɗe ƙafa ɗaya kan ɗaya sannan yay magana. “Kun iso kenan?”.      Nanma a tare sukace, “Eh Yayanmu”. Batare daya kalli kowansuba ya jinjina kansa yana musu nuni dasu zauna. Babu musu suka zauna suna gaisheshi da tambayar jikin Granny.        “Ta warke ai, tunda gashi tana mana boren sai kunzo”.       Duk da ba cikin raha yay maganarba sai da sukai ƴan ƙananun dariya suna gumtse bakuna. banda Zinneerah da tun shigowarsa kanta ke a ƙasa murmushi yanzunma kawai tayi.     Granny dake hararsa tace, “Ai ni ba irin wasu bane da basa son mutane. Na saba jina cikin hayaniya da karaɗin ƴan jikokina ina jin daɗi”.      Karan farko ya saki lallausan murmushi yana miƙewa da ɗan taɓe baki, duban Khalipha daya kai ledojin abincin kitchen ya dawo yayi. “Besty ina zuwa”. Ya faɗa yana nufar hanyar da Farah ta fito ɗazun.        “A fito lafiya Yayanmu” Khalipha ya faɗa yana wata shaƙiyyar dariyar tsokana ƙasa-ƙasa da kaiwa zaune. Hajiya Iya data fahimci mi yakema dariyar tace, “Halan zargina ya zama gaskiya akan ƴar tutsun tasa? Tunda yanzu dai ba lokacin dawowarsa gida bane ba”.         “Ai da alama itace tai kiransa a waya ko kuma ta kira Mammah ita kuma ta kirashi, dan a yanda ta nuna mamakin ganin su Jamal na tabbata bai sanar mata zuwan nasuba. Kinsan wannan jikan naki shine dai-dai dasu ai, ya manna musu rashin m ya noƙe da barinsu suyita masifa”. Khalipha ya bata amsa magana ƙasa-ƙasa kamar wani munafiki yana ɗan dariyar ƙeta.        Dariya Hajiya iya tayi itama, “Kaɗanma ta gani indai nice Amina, ita Hindatun idan ta isa tazo gidan mana ta sameni ja'ira kawai. Nima nan saina saitasu a layi da ƙyau ai kafin nabar wannan garin da ba daɗin zamane da shiba”.       Sudai su Zinneerah da ba sanin ina zancen ya dosaba saurarensu kawai sukeyi, ita babban burintama azo a basu masauki ta kwanta dan kanta ciwo yake mata.        Shiko Khalipha dariyarsa ya cigaba da sha dan show ɗin na Granny na birgesa. Sosai a zaman nan nata take ƙara cusama Yayansu son ƴan uwansa a ransa da sanin muhimmancin su da girman zuminci. Shiko da alama yana haddace karatunta tsaf kuma yana aiki dashi. Dan rana ɗaya babu zato ya sanar masa ya kira cikinsu Haneef akan tahowarsu Meenal nan ɗin. Bashi ba hatta Granny tayi mamaki dan duk tsogumin da take masa nason zuwan su Zinneerah ɗin batai zaton zai saka suzo ɗinba. Aiko ranar yasha addu'a a wajenta da albarka.     To yanzu dai gasu sunzo, shi dai yasan akwai ƙura akan wannan zuwa nasu gidan, musamman daya kasance uwargida gimbiya Farah batasan da maganar zuwan ba, amma bara su zuba ido suga yanda wasan zai kasance dai, tunda shima yayan nasu ba kanwar lasa baneba.............✍        *_Masha ALLAH Guys, ina fatan asha hutun weekend lfy ko😋😉😘😍😘😍🤗._* *_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 _Na Safiyya Huguma_ *_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖 _Hafsat Rano_ *_★ DALAAL_*💝 _Na Miss xoxo_ *_★ UBAYD MALEEK_*💓 _Na Mamu gee_ *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 _Na Bilyn Abdull_ Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 *_08085405215_* IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   0903 234 5899 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 *_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_* *_TYPING📲_* *_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_* *Page 30* ________________________ *MG’s SKIN CARE* (With us, your skin is elegant..) Are you guys  looking for where to buy ur skincare product @ mg's skincare is the best plug for you🤗 Do you wish to have that flawless skin that's free of all skin prblm Do you wnt to achieve that milky skin that turn heads wherever you go😉 Try mg's product nd I assure you you'll never use any other product except mg's product✅ Mg's will gv you the best out of all With mg's product ur skin is 💯 clear,fresh,smooth nd ur skin will absolutely glow all day💃 We have herbal whitening black soap now nd beauty set available Nd both the soap nd the beauty set is for all skin type everyone can use it🤗 Just gv it a try now nd see wonders✅ Chat:08062991549 Call:08064532391 Soap price:3k set:11k Follow us on Instagram@glow_with_mgs Facebook:mg's skincare Nd guess wht🦻 Duk Wanda zesiya Kaya daga yau Alhamis  30-9-21 zuwa Nanda 5days that is ranar talata there will be 20% off discount a soap nd the set😍so what are you guys waiting for hurry nd grab urs💃 now is  the time to glow🧖‍♀️ Pamper ur skin🦵 Shine like a bride 👰 be part of the glow team karkubari abaku lbr Just chat 08062991549 to plc ur orders😘 Do not forget to follow us👆 Like nd comment pls dearies😘 Patronize us🙏 mg's always serve you the best✅❤️ KAYAN MG’s SKIN CARE, GANGARIYA NE, SAI AN GWADA AKAN SAN NA KWARAI, KU GARZAYA KU SAYI NAKU KAYAN A KULI KALILAN DOMIN DAGA YAU TAFARA BONANZA. IDAN ANJE ACE DAGA ZAFAFA NE, AKWAI RANGWAMEN KUDI SOSAI, KYAU, INGANCI, RAHUSA.. SAI KAYAN MG’s SKIN CARE. __________________________ *Page 30* ............Tunda ya turo ƙofar tsararren bedroom ɗin ya shigo da shashshekar kukanta ya faracin karo cikin kunnuwansa. Batare da damuwa da rashin amsa sallamarsa ba ya ƙaraso cikin ɗakin yana kallonta.       Zama yay a kujerar dake ɗakin tamkar bai damu da kukan nataba, a dakile yace, “Kinsa an tasoni daga office, gani to, mike faruwa?”.      A fusace Farah da ke a kwance tana kukan ta tashi duk da tun farko tasan da shigowar tasa dama. Hawayenta ta share tana kallonsa, sai dai yanda ya tsatstsare ta da idanunsa dake rikitata yasa ta janye nata danta samu damar faɗar abinda ke a bakinta.      “Babu abindama bai faruba. Ni wlhy bazan iyaba, tayaya wannan gidan zai ɗauki wannan gayyar dan ALLAH? Hidimar nawa zasuci ta kuɗaɗe tun daga kan abinci, ruwa da wasu wahalhalunsu?. Kawai sai dai muga yara batare da an sanar mana ba daga ni har kai. Ita bata tunani zamanta ma a takure muke bare tasa an ƙaro mana wannan yaran harda mara kunyar yarinyarnan data kusa min sanadin karayar ƙugu. Ko an faɗa musu rayuwar Nigeria da babu tsari da tanan iri ɗaya ce? Nasan duk Khalipha ne munafukin nan dan dashi zata haɗa bak......”         “K ya isa haka malama!!”. Ya faɗa a kausashe cike da nutsuwarsa. Dan inma baka saniba sai kace ba shine yay maganarba. Babu shiri Farah tai baya dan firgita tana kallonsa dan ya fito mata a zakinsa. Ya tsatstsare ta da birkitattun idanunsa yana nunata da ɗan yatsa. “Farah! Farah! Wlhy daga yau, daga yanzu, bakinki ya ƙara kuskure akan Granny saina zubar miki da haƙora a wannan gidan. Da kike cewa ta takura miki, mizai hana bazaki tafi inda zaki shaƙata ɗinba ke?. Ki kiyayeni Farah, ina ɗaga miki ƙafane kawai saboda ra'ayina badan kai ƙarata da kikeyi wajen mahaifiyata ba. Yara kuma nine na kawosu, idan kin isa dan ALLAH ki maidasu Nigeria yau ɗin nan stupid kawai”. Ya ƙare maganar yana karkaɗa mata yatsansa alamar gargaɗi na ƙarshe ya mike ya shiga toilet.        Da wani banzan kallo ta bisa, ji take tamkar ƙirjinta zai buɗe dan tsananin zafin da takeji na cika mata gida da akayi. Ta tsani takura a rayuwarta. Dama Mammah ta faɗa, zuwan Khalipha tamkar buɗe hanyar banbarowar danginsa ne garesa, dan sun sami ƙofar da suka kasa samu tuni. To ita kam sai dai ayi duk ma abinda za'ai waɗanan yaran bazasu zauna a gidan nanba, kai itama makirar tsohuwarnan mai ƙulla komai saita tafi.........          Fitowarsa ta katse tunaninta. Tasa hannu ta share hawayenta tana dubansa duk da kallon fuskar tasa kawai tsoro take bata ma. Zatai magana ya katseta dan yasanta da shegen naci da mita akan abu,  “Ki kwaso duk kayanki na ɗakincan tunda ba amfani kike da shi ba su zauna. Jamal ya zauna wajen Khalipha”.       A zabure ta miƙe tsaye tana dubansa hawaye na rige-rigen sakko mata. “Haba Yah Abdul-Mutallab, ɗakin nawa zan basu?”.       “Zama ɗakin kikeyi ne?”. “To amma dan ALLAH kodai bana zama a ciki ai dai sunansa ɗakina.  Suje ɗakin Granny su zauna mana”.      Wani banzan kallo ya mata idanunsa na sake canja kala. “Wlhy Farah idan kikace zaki bani ciwon kai akan zuwan yarannan tabbas zan baki ciwon zuciya ni kuma. Garama tun muna mu biyu kije ki kwaso abinda yake naki a can ki basu ɗakin, idan kuma kinƙi zakisha mamakina dan ina nan Abdul-Mutallab ɗin ɗin da kika sani”. Yana gama faɗa ya fice abinsa.          Khalipha kawai ya samu a falon, Granny taja su Zinneerah zuwa ɗakinta. Jamal kuma Khalipha ya kaisa nasa ɗakin. Duk ƙoƙarin ɓoye fushinsa da yake sai da Khalipha ya gane. Har cikin ransa baiji daɗiba. Shiyyasa yaso Yayan nasu ya haƙura da batun zuwan yaran tunda ba dole bane. Dan yasan Farah ba zataso suzo ɗinba. Tunda shima a yaya yake zaune gidan ma. Ita kanta Granny ɗan hali Farah ke nuna mata duk da tsufanta.....        “Ina suke?”. Ya katse Khalipha muryarsa cike da ɗaci. Cike da son kauda masa damuwarsa Khalipha ya miƙe yana dariya. “Ai Yayanmu kasan waɗanan yaran ƴan gatan Granny ne. Ta jasu ɗaki wai suyi wanka da barci. Shima Jamal yana wajena”.      Goshinsa yaɗan murza da furzar da huci yana lumshe ido. Batare da ya samu yanda yake so na daidaiton muryar tasaba ya nufi ɗakin yana cewa, “Taya zasu zauna a wannan ɗakin harsu huɗu zasu takura mata ai”.               Bin bayansa Khalipha yay yana magana cike da lallashi. “Yayanmu daka barsu isarsu zaiyi ALLAH, kaga munma huta da mitar Granny akan kaɗaici ko”.         “Bazai yuwuba Khalipha ɗakin Farah zasu koma”.      Dama abinda Khalipha kema gudun kenan. Ya ƙara buɗe baki zaiyi magana a dai-dai isowarsu ƙofar ɗakin AK ya ɗaga masa hannu alamar ya isa. Kai Khalipha ya dafe dan harga ALLAH baya buƙatar wata fitina akan zuwan yaran nan tsakanin yayan nasu da matarsa. Idan ta gaskiya za'abi sune da laifi, gashi kuma dama ba'a sanar mata ba tun farko. To amma yasan halin Yayan nasu tunda yace haka za'ayi dole a yarda ayi hakan”.            Daga can Granny tace, “Khalipha shigo mana”. Dan batai zaton AK ɗin baneba. Batare daya nuna shi ɗin baneba kuma ya murɗa ƙofar ya shiga da sallama ciki-ciki. Akan Zinneerah data fara wanka harta kwanta ya fara sauke idanunsa. Ya janye yana maidawa ga Granny dake gyarama Meenal kwalar riga. Bahijja kuma na toilet tana wanka.       “A'a wai dama baka komaba?”. Hajiya iya ta faɗa idanunta akan AK. Kansa kawai ya kaɗa mata yana kaiwa zaune. “Yanzu zan koma Granny, akan waɗannan dama na shigo, su koma can ɗakin ba'anan zasu zauna ba”.        Shiru tai tana kallonsa cike da nazari, sai kuma ta saki murmushi tana girgiza kanta. “Moddibo bazai yuwuba. Ka barsu anan muyi zamanmu zai ishemu”.        A karon farko ya kalleta shima. Ta kaɗa masa kanta da iya gaskiyarta tace, “Idan akai hakan ba'a ƙyautaba Moddibo. Inda itace taso su zauna mata a ɗaki dan kanta hakan ba damuwa bane. Amma ko nice miji yayma ƙarfa-ƙarfa akan danginsa su zauna min ɗaki zanga kamar an ƙasƙantar da nine. Ka barsu kawai suyi zamansu nan zai ishemu duka zaman kwana nawane ma”.       Bai iya yace mata komaiba, sai idanunsa dake ƙara canja launi ɓacin ransa na bayyana a fili, miƙewa yay a hankali batare da ya sake kallon kowansuba yace, “Saina dawo”. Daga haka ya fice yabar ɗakin..         Da ga hajiya iya har Khalipha da su Meenal da kallo suka bisa suma damuwa fal ransu. Suna son Yayansu dan shima yana son su. Ko rashin sakewarsa a garesu kowa yasan wannan halinsane da kuma yanayin rayuwar daya tashi a hannun Mahaifiyarsa. Amma sunsan badan ƙuntatawa a garesu yake musu hakaba.         Afusace Meenal tace, “Wlhy na tsani matarnan, danma taga ta samu Yayanmu mai haƙuri dajin maganar iyayensa shiyyasa takema mutane wani iskancin”.       “Barta hankali zamu koyama shegiya ai a wannan karon, tunda ta yarda mukazo gidan nan wlhy tayi gamo da gamonta kuwa”. Cewar Bahijja itama muryarta har zuga take.      Rai ɓace Hajiya iya ta kallesu tana musu daƙƙuwa. “Duk kunci iyayenku, ina ruwanku a cikin wannan zancen? Kunsan ALLAH duk wanda ya aikata wani abu a gidannan saina ɓata masa rai kuma ya koma gida. Ina kuma sake gargaɗinku shiga abinda ba'a sakakuba. Wannan ma ai rainine. Koyaya take ai matar Yayankuce taci albarkacinsa a wajenku marasa kunya”.       Duk ƙasa sukai da kawunansu alamar nadama. Dan dama sunsan wannan ba tarbiyyarsu bace. Hasalima Hajiya iya bata yarda da irin wannan maganar a gabansu, yau ma dai akasi aka samu. Haƙuri suka bata. Shima Khalipha ya ƙara musu faɗa sannan yace suzo suci abinci shima zai wuce school ne.      Duk wannan abin da sukeyi Zinneerah najinsu sarai, amma tai shiru kamar barci takeyi. da Khalipha ma yace a tadata taje cin abincin Hajiya iya hanawa tai. Catai su barta idan ta tashi sai taci nata tunda ta riga tayi barci.       A ɓangaren AK kuwa koda ya fito daga ɗakin hajiya iya ɗakinsa ya sake komawa. Zaune ya tarar da Farah da waya a hannu kamar ba ita ta gama kukaba yanzun. Ko'a jikinsa dan ya shirya mata tsaf, ya kuma san Mammah bazatazo gidanba dan yunda Hajiya Iya ta dawo daga asibiti taƙi zuwa, dama kuma ko asibitin bataje ta dubataba. Yanzu hakama tana China batare da sanin Farah ɗin ba, dan shekaran jiya ta wuce da daddare.         “Ki tashi ki tattara komanki dake a ɗakin nan ki maidashi ɗakinki. Karna dawo na taddaki anan ko wani abu naki”. Daga haka ya juya ya fice abinsa bai jira cewartaba.        Fuskarta bayyane da tsantsar mamakinsa ta bisa da kallo. Yana fita ta miƙe a fusace dayin wurgi da wayar hannunta. ‘Ni zaka wulaƙanta akan waɗanan banzayen ƴan uwan naka Abdul-Mutallab? Saboda nace bazasu zaunamin ɗakiba kaima zakace na bar maka ɗakinka bayan kasan nafi son zama a cikinsa. Na rantse da ALLAH sai yaran nan da tsohuwarnan sunbar gidannan zan baka mamaki kai dasu. Bazan sake zubar da hawayena akansu a banzaba mu zuba mu gani’.      Yanda take surutai ita kaɗai a kuma matuƙar fusace sai ta baka dariya. Ta koma tamkar wata zararriya. Sanin halinsa yasa bata ƙetare maganarsaba ta shiga tattare duk wani abu nata tana saka mai aikinta tana kaiwa ɗakinta. Sai dai kuma alwashin ƙuntata su Hajiya iya a gidan tacisa yafi sau shurin masaƙi.          Bayan ta gama tattare komai nata tsaf ta saka mai aikin nata sake gyara masa sannan ta jawo masa ɗakin ta rufo harda saka key. Su dai duk wannan abu dake faruwa su Hajiya iya basu saniba suna ɗaki abinsu tana hira da jikokinta. Abincin ma anan sukaci kusa da ita har Jamal da yana gama kimtsawa ya tafi can. Shiko Khalipha ya wuce school kamar yanda ya faɗa. ________________★          *_DANYA_*    Su inna sun kai Karima asibitin kusada. Likitocin nata faɗa ganin yanda jikinta ko ina sayin duka ga tsohon ciki da a yau ma yaketa nuna alamun zai fito duniya. Dan tunkan su wuce ashe naƙuda take shiyyasa jikin nata ya nema rikicewa.        Ɗakin haihuwa suka kaita dan shine yafi cancanta da ita a wannan halin. Daga haka suka shiga bata taimakon gaggawa. Suka bar su Inna a waje da zaman jigum-jigum. Tun suna zuba idanun jiran kukan jariri da wuri har al'amarin ya fara fin ƙarfinsu. Dan ihun Karima kawai suke jiyowa babu na jariri. A haka suka cinye wannan yinin suka shiga marece. mahaifiyar Babawo sai kiransa take a waya yaƙi ɗauka. dan tunda ta sanar masa abinda ke faruwa kafin su baro Danya bai sake yarda ya ɗaga mata wayaba. Dole sai ƙaninsa keta kaiwa da kawo akan komai har ALLAH ya sauki Karima wajen ƙarfe goma na dare.      Tsabar wahalar data sha daga ita har jaririyar sun fita hayyacinsu ko kukan kirki batayiba. Koda aka buƙaci kayan haihuwa babu abinda sukazo dashi asibitin. Aiko Nurse ta balbalesu da masifa dan haushi. Inna ta miƙe itama a fusace tana danƙarama Nurse zagi abu ya nema zame musu faɗa sai da aka lallashi Nurse ɗin da ƙyar. Dan sun fahimci Inna ma ba kanwar lasa baceba.       Wannan abin daya faru yasa gari na wayewa aka basu sallama suka dawo gida duk da Karima na buƙatar zama ƙarƙashin kulawar likita. To amma jarabar Inna bazaisa su iya cigaba da kulawa da Karima ɗin cikin kwanciyar hankaliba dan haka suka sallamesu..........✍            *_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_* Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻. *_★ AL-ƘIBLA_*💘 _Na Safiyya Huguma_ *_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖 _Hafsat Rano_ *_★ DALAAL_*💝 _Na Miss xoxo_ *_★ UBAYD MALEEK_*💓 _Na Mamu gee_ *_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔 _Na Bilyn Abdull_ Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻. Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 *_08085405215_* IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   0903 234 5899 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 *_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_* *_TYPING📲_* *_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_* *Page 31* _________________________ _*LAVENDER RESTAURANT..*_ _(Palace of mouthwatering food/delicacies)_ _IDAN KUKAJI GANGAMI DA LABARI, INA MASU SON INDA ZASU SAMU INGATACCEN ABINCI MAI DADI DA LAGWADA? KAI BA ANAN MUKA TSAYA BA, INA SABBIN AMARE? MAMAs, YAYYU? DA KANNEN MU MASU SON KOYAN GIRKUNAN YAN GAYU NA KASAR NIJERIYA DA KETARE?_ _*TO KU MATSO...! AT LAVENDER RESTAURANT GOTS YOU COVERED. ABINCIN KASASHE DA DAMA MUKE KOYARWA,,COME LETS UPGRADE YOUR FOOD TIME TABLE, MATSO KUSA YAR UWA GA DAMA DA ZAKI CANZA YANAYIN ABINCIN GIDAN KI, KOWA YASAN IYA SARRAFA ABINCI NA TAKA RAWAR GANI A GIDAJEN AURE. KAI KO BUDURWA CE INDE KIN IYA GIRKI ZAKIGA KOWA YANA HABA HABE DAKE.._* _*UNCLES, DADDIES, BROTHERS., NEWLYWED HUBBYS..! KU ZO KU YIWA ‘YAYAN KU, MATAN KU DA KANNEN KU RAJISTAR WANNAN HARKA TA KOYAN GIRKI.._* _*Lavender catering school zamuyi practical class. zamuyi 30 dishes continental,snack & desserts, traditional dishes, drink. Fee din 40k NE. phone number WhatsApp and call 09080299283 akwai discount na 5% ga mutum uku farko wadanda sukai register aranakun independence 1/10/2021 to 3/10/2021 Nigeria @ 61_* _*ZA’A FARA CLASSES RANAR 14/10/2021. WATO SHA HUDU GA WATAN OKTOBAR DA MUKA SHIGA YAU._* _*GIRKE GIRKE GUDA 30😫😨AKAN DUBU 40 KAWAI, HARDA BONUS NA SNACKS, DESSERTS, TRADITIONAL AND MODERN DRINK, GARGALIYA DA ZAMANI🥂WATA DAYA CHAS ZA’AYI ANA KOYAN GIRKE GIRKEN. _* _*KU SAKE KARANTA WANNAN BONUS DIN👇🏾RIGIJI GABJI_* _*Nigeria @ 61 _* _*COOKING COMPETITION!!!_* _*from lavender Catering ina masu son koyon girki ga dama zaku shiga gasarmu ta girki bayan kunyi register damu akan 10k,wanda yazo na 1zai shiga ajin mu free hade da wasu prize din na 2 da na 3 kuma zasu bayar da rabin kudine da wasu prize suma saura kuwa zasu ayi musu ragin 5% da wasu prize wannan gasa zamu yita ranar lahadi ne 3/10/21 zamu rufe registration na gasar ranar asabar_* _*LAVENDER RESTAURANT: NA GARIN KANO, CLASSES DIN AKWAI PRACTICAL AND ONLINE CLASS GA WANDA KE NESA_* ____________________ An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels