Showing 72001 words to 75000 words out of 100927 words

Chapter 25 - MAKAUNIYAR KADDARA complete

Start ads

24 Aug 2025

402

Middle Ads

ce tai musu bayani. Amsar wayar suma sukai duk suka gani. Duk wanda ya kalli hoton sai ga mamaki ya bayyana a fuskarsa da ruɗani.
        Duk wannan al'amari dake faruwa Zinneerah nacan ɗaki tana shirya kayanta data kwaso a ɗakin Yah Adnan cikin wadrobe ɗin Hajiya iya. Hakan yasa batasan hidimar da akeyiba. Dan so take ta gama shiryasu a daren yau tunda gobe idan ALLAH ya kaimu monday akwai makaranta.
        Kasancewar dama bata fara aikin da wuriba sai gashi har Hajiya iya ta shigo domin sallar magrib bata kammalaba. Sai kusan sha ɗaya ta gama lokacin hajiya iya ta jima dayin barci mai cike da mafarkin yaron da Safiyya ta kawo musu a hoto, takan dai tashi tai salla idan lokaci yayi. Su meenal kuma sunɗan lekota, sanin hajiya iya idan ta kwanta batason surutu yasa suka fice suka barta ita kaɗai ta cigaba da aikinta.
          A falo kuwa hirarsu suka cigaba dayi bayan tasowar hajiya iya. Dan duk sun barma kansu cewar kamannine kawai da akan samu a rayuwa tsakanin wani da wani koda babu alaƙar jini saboda hikimar UBANGIJI. Basu wani jimaba suka fice duk da Moos'ab yaso ganin Zinneerah kafin ya wuce ɗin. Rashin samuwar hakan ya sakashi haƙura kawai.

        Tun daga wannan ranar babu wanda ya sake tada zance akan hoton yaro, sai dai abin na nan maƙale a zuciyar Hajiya Iya ta kasa mantawa. Tanason yin maganar kuma wata zuciya na kwaɓarta akan kamannine kawai. Idan kuma tace zata kawoma zuciyarta wani tunani daban ya zata alaƙanta al'amarin ma to. Hakan yasata tsuke bakinta ta barma ranta komai kawai.

     kwanaki sun cigaba da shurawa a hankali sai ga Khalipha da Adnan na cika kwanaki goma da zuwa. Ko kaɗan Zinneerah ta kasa sabawa da kasancewar sa a gidan duk da a kwanakin nan bai cika zamaba kullum suna hanyar Jigawa gonar da zaiyi noman shinkafa. Sukan fitama kafin su su fito, wani lokacin kuma sai sunyi barci suke dawowa. Wannan dalilin yasa takanyi kwanaki uku biyu ma bata sakashi a idontaba har Khalipha ɗin da take marmarin gani a ko yaushe.
      A kwanakin nan daya ɗauka gaba ɗaya hidimar gyaran ɗakinsa ta dawo kan Zinneerah. Kullum ita yake cewa taje ta gyara masa ɗaki. Bata damuba dan dama ta rigada ta saba.
Idan ta ganshi tsoro na matuƙar kamata, dan kullum abubuwan daya dangancesa suna sake danganta kansu da abinda sam ta kasa gaskatawa. 
       A randa suka cika kwanaki goma sha uku a gidan basuje gona ba, amma duk da haka babu wanda ya sakashi a ido sai yamma. Yana ɗakinsa yana harkokinsa na business a lap-top.

        Zinneerah, Meenal, Bahijja sai Jamal na zaune a falon hajiya iya Yah Khalipha ya shigo. duk sannu sukai masa ya amsa yana zama kujerar dake facing ɗin Zinneerah da Bahijja. Cikin kafe Zinneerah ɗin da idanu ya miƙa mata ledar hannunsa yana murmushi.
        “Ƙanwata yau dai ga wayarki na cika alƙawari”. Kafinma ta kai ga yunƙurawa amsar wayar Jamal yay azamar zuwa ya amsa yana washe baki. A take suka rufi akan wayar suna tayata murna duk da ba irin tasu Meenal ɗin bace ba, amma itama ta haɗu. Tasowa Zinneerah tai tsam inda yake takai tsigunne kanta a ƙasa tana faɗin, “Nagode sosai Yah Khalipha, ALLAH ya ƙara buɗi mai albarka”.
      Kansa ya jinjina mata yana sake faɗaɗa murmushinsa. Sai kuma ya miƙe ya fice zuciyarsa na bashi ƙwarin gwiwa akan yau ya tunkareta da zancen nan. Dan yauɗin kawai ke garesa Yah Adnan yace nanda kwanaki huɗu idan ALLAH ya kaimu maybe zasu wuce Abuja. Daga can kuma bazasu dawo Kano ba London zasu koma zaiyi wasu uzirinsa kafin ya dawo akan zancen auren su Ni'ima da ayanzu haka an tsaida rana da kuma maganar Company da yake tunanin buɗew na shinkafa.
     Binsa da Kallo Zinneerah tayi ƙwalla na cika mata idanu, sai kuma ta miƙe tsaye tana murmushi saboda wani abu data tuna. Idanuntane suka sauka akan Yah Adnan dake tsaye bakin ƙofarsa da waya a kunne yayi wani kicin-kicin da fuska............✍


*_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*

Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.

*_★ AL-ƘIBLA_*💘

*_★ MADUBIN ZUCIYA_*💖

*_★ DALAAL_*💝

*_★ UBAYD MALEEK_*💓

*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔

Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.

Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.

Kamar haka👇🏻💃🏻

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

*_08085405215_*

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

  0903 234 5899

💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍

*_ALLAH ka gafarma iyayenmu🙏🏻😭_*


*_TYPING📲_*


*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*


__________________________


*_ina 'yan uwa musulmai masu kishin addinin islama???_*

*_maza ku matso ga wani aikin lada ya samu_*

*_Ɗanku kuma dan uwanku kuma qaninku wato ABDURRAHMAN, yaro mai hazaqa, ƙwazo da tarin baiwa, gami da kwadayin haddace littafin Allah mai tsarki, ya bude YOUTUBE CHANNEL nashi na qashin kansa, ku tallafa masa ta hanyar shiga wannan shudin rubutun ku danna masa subscribe, ba abunda xai rageku dashi saima samun dimbin lada dalilin KARFAFA MASA GWIWA, MUN GODE 🙏🏽🙏🏽🙏🏽_*
👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽

https://youtu.be/WWIGq5Jbtb0


_______________________


*Page 22*

.........Cikin sauri ta haɗe murmushinta dayin diri-diri na alamar rikicewa. Dan wani irin kallo da take kasa fassarawa a duk sanda yay matashi ya watso mata yanzuma ya ɗauke kansa fuskarsa na ƙara tsukewa fiye da yanda ya fito. Sum-sum ta juya gasu Bahijja da suma sukai tsitt daga ihun da sukeyi na murnar wayarta zata zauna yace, “Haɗomin black tea yanzun nan”. Daga haka ya juya ya koma ɗakinsa.
       Da sauri duk suka kalli Zinneerah da itama kallonsu take. Meenal tace, “Wlhy ki tashi kafin yace kin ɓata masa lokaci”. A take idon Zinneerah ya fara tara ƙwalla. Dan wannan shine karo na farko da ya sakata irin wannan aikin bayan gyaran ɗakinsa.
     Bahijja tace, “Kinsan mi zakiyi?”
Zinneerah ta girgiza mata kai da sauri. “Kije kima Baba Rahi magana ta haɗa miki, dan tafi kowa sanin abinda yakeso a nan gidan bayan Granny. ALLAH yasa basu tafi ba, tunda ba gani yayba ki fiske abinki ki kai masa kawai a rabu lafiya. Dan shi inhar ya sakaka abu bakayi dai-dai yanda ya buƙataba ka shiga uku”.
       Jin abinda Bahijjan ta faɗa ɗinne ya sake tsurar mata da ciki, amma shawarar saka Baba Rahi ta haɗa matan ya sata jin sassauci. Da sauri ta miƙe zuwa kitchen, sai dai wayam babu baba Rahi a ciki. Tai saurin kallon agogon dake a kitchen ɗin wanda ya bata tabbacin Baba Rahi ta wuce gida dan ba'a nan take kwanaba daman.
     A take ƙwallan da take maƙalewa suka silalo mata. Jiki a sanyaye ta ɗiba kayan ƙamshi tasa a turmin ƙarfensu ɗan ƙarami ta hau dakawa. Cikin ƙanƙanin lokaci ta gama dafa shayin daketa uban ƙamshi a kicin ɗin, sai dai duk wannan ƙamshin nasa dazai iya saka mai kallo buƙatar sha ita a tsorace take. Ƙaramin flask ta samu ta juye tare da ɗorawa a tire ta saka kofuna biyu da mitsilin bowl data zuba suga a ciki ta ɗakko ta fito tana karanto addu'ar nasara a cikin ranta.
       Bata iske kowa a falonba su Jamal sun gudu, hakanne ya sake ɗarsa mata tsoro a cikin rai ta nufi ɗakin tamkar an daddoke mata gwiyawu. Sai da tai sallama kusan sau huɗu sannan ya amsa mata da bata izinin shiga. Ta tura ƙofar ta shigo ƙamshinsa na rige-rigen shiga mata hanci. Tsaye yake a gaban mirror sanye cikin farar jallabiya ruwan madara yana ƙoƙarin ɗaukar wayarsa dake vibration.
     Tai saurin kauda kanta ƙasa murya na ɗan rawa tace, “Yayanmu ga tea ɗin”.
        Juyowa yay dai-dai yana ɗora wayar tasa a kunne ya kalleta da fararen idanunsa da suka nema ruɗata. Dan itama yayi dai-dai da ɗago nata zata saci kallonsa. Ƙasa tai da kanta shima ya janye nasa yana zama kan sofa. Ƙafa ɗaya ya ɗora kan ɗaya yana kai bayansa ya jingina da kujerar ya sake dubanta ya ɗauke kai. “Zaki cigaba da tsayamin a kaine?”.
         A sanyaye Zinneerah ta ƙaraso ta ajiye tiren saman table ɗin gabansa, dai-dai yana faɗin, “Ina ruwanki da ko wacece. Ki cigaba da maganarki kona kashe wayata”. Ya ƙare maganar dajan guntun tsaki.
        Zinneerah dai dake saurarensa haka kawai ranta ya bata matarsace. maganar su Meenal data tuna yasata kaiwa tsuggunne ta fara ƙoƙarin zuba masa a kofin. Sai dai jin kamar ana kallonta ya sata ɗan daburcewa, kamar zata ɗago sai kuma ta fasa.
     Kamar ya fahimci ta gane kallonta yake sai ya miƙe gaba ɗaya yana bama matarsa dake tambayar ya bata hajiya iya amsar da cewar “Bama tare”.
           Tabbas Zinneerah taji kalmar “Bama tare” daya faɗa, sai dai batajin mi matar tasa ke faɗa dagacan, a bazata taji saukar wata gigitacciyar tsawarsa cikin kunnuwanta. Ai batama san sanda ta zube ƙasa daɓar ba tana cusa kanta a ƙafafunta jikinta na rawa. Shiko da baisan tanayiba ya cigaba dayin magana a hasale matuƙa.
        “Farah! Ki shiga hankalinki, ke miyasa a kullum tunaninki baya a layin na masu hankali? To kije hakaɗinne ma, ai dai nima namijine ko? Wawuya kawai mtsoww”. Ya ƙare maganar dajan wawan tsaki yana yanke wayar ya jefa saman gado. Wadrobe ya nufa ya finciki murfin da ƙarfi ransa na nasa suya, ya rasa wane irin hukunci zai fara yima Farah akan yawan furta kalmar zargi gareshi a duk lokacin da yay nesa da ita zuwa wani waje. Inhar zaiyi tafiya ta dinga bin ƙwaƙwƙwafinsa kenan tamkar wani ɗanta saboda shegen kishinta na tsiya.
          “Zan koya miki hankali”
Ya fada zuciyarsa na sake kumbura. Ɓacin ran da yake a ciki ya sakashi mantawa da Zinneerah a ɗakin ya fara ƙoƙarin fara shiryawa.
        Shirun da tajine ya sakata ɗago kanta a tunaninta fita yayi. Babu shiri ta miƙe ta fita da gudu ganin ya fiddo kaya alamar sanyawa zaiyi.
       Shikam baimasan tanayiba, Sai da ya gama saka kayan ya nufo mirror dan saka turare idonsa ya sauka a kan kayan data ajiye, sai dai babu ita a wajen. Wani sabon takaicine ya sake lulluɓesa tuna abinda Farah ta faɗa akanta. Ya cije baki da rumtse idanunsa da ƙarfi yana raya wannan karon sai tasan shi take dangantawa da Zina wlhy.....
       Yana ƙoƙarin zaman shan shayin da Zinneerah ta zuba kira ya shigo masa. Sanin mai wannan ringtone ɗin yasashi miƙewa ya ɗauka wayar yana ƙoƙarin sassauta fushinsa.
       “Barka Mammah”. Ya faɗa cikin nuna girmamawa a gareta. A take zuciyarsa ta kara rinewa da ɓacin rai dan dama yasan bai wuce Farah takai ƙararsa wajentaba kamar yanda ta saba. Uffan baiceba har Mammah dake zuba faɗa daga can tayi ta gama. Sai daga ƙarshe da tace Farah ɗin zata biyowa Nigeria itama sannan yay magana.
       “Mammah abinda nazoyi nanfa important ne, karki biyema shirmen.......”
    “Saurara min Abdul-Mutallab!!” Ta katsesa a tsawace. “Kana nufin bansan abinda ubanka da kakarka suke shiryawa a kanka bane?, to wlhy su sani ƙwatarka a hannuna wannan karon sunyi kaɗan. Idan har bakaso Farah ta biyoka ka dawo London yau yau ɗin nan tunda kasan tanada lalura a jikinta. Inba hakaba bayan itama tazo nima zanzo dan ina dai-dai da kowa cikinku”.
       “No, Mammah Please, nafa faɗa miki abinda zanzoyi tukan na taho”.
      “Amma baka sanarmin zaka daɗe haka a nanba, dama an manna maka harkar noman ne saboda munafunci ai. Sannan wannan munafikin yaron dake nane da kai ko yaushe idan kun dawo ya wuce hostel da zama, inba hakaba Abdul-Mutallab sainayi bala'i bala'in ɓata ranka, wlhy ubanka ma sai yayi dan.........”
       “Mammah Pleaseeee!”.
Ya faɗa cikin zafin rai, dan ya mugun tsanar yaji tana zagar masa mahaifinsa da ƴan uwansa.
         Ƙitt ta yanke wayar batare data sauraresa ba.
       Kansa ya dafe saboda wani jiri-jiri dake neman kwasarsa. Shin wai wace irin rayuwace wannan mahaifiyarsu kesan taga sunyi? Gaba ɗaya ta tsani taga sun raɓi mahaifinsu da ƴan uwansu. Ta yaya kuwa hakan zata kasance bayan hausawa sunce da uba ake ado. Duk ƙoƙarin da yake wajen fuskantar da ita muhimmancin family ɗinsa bata fahimta. nata ƴan uwan kawai takeso su girmama su raɓa. Anya kuwa idan ya cigaba da biye mata bazai halaka ba. Tunda suke da Baffah bai taɓa nuna masa matsanancin ɓacin ransa akan abinda Mammah takeyi na katangesu daga garesaba irin wannan karon. Har a yanzu haka ya kasa tarosa gaba ɗaya. A da kam idan yayi masa faɗan yakan sakko ya koma nasiha. Amma wannan karon yaƙi sakkowa. Ya dage akan sai yabi umarnin hajiya iya ya ƙara aure yabar matar anan Nigeria idan ita waccan tafi ƙarfin dawowa cikin family ɗinsa ta zauna.
     Zazzafan huci ya furzar yana zamewa ya kwanta a sofar da dafe kansa kawai ya lumshe idanunsa.
       Lokaci mai tsaho ya ɗauka a haka batare da ya saniba. Dan har saida Hajiya Iya ta shigo ɗakin dubashi dan taga har anyi magrib bai gitoba.
       “Moddibo kana lafiya kuwa?”.
Ta faɗa tana kai hannu ta cire nasa daya dafe kansa. Idanunsa ya buɗe a hankali yana kallonta, ta sake maimaita tambayar tana taɓa goshinsa.
     “Lafiya kuwa kake yau har anyi salla baka fito kaje massallaci ba Moddibo?”.
       Zaune ya tashi sosai, Sai kuma ya girgiza mata kansa, “Kaina ke ciwo kawai Granny, bamma san anyi sallanba ai”.
     Tsura masa idanunta tai cike da nazarinsa. Dan ta riga ta gama karance halayyarsa tun ƙuruciya. Duk da ta hango damuwa tattare da shi sai batace komai a kai ba. ta nufi hanyar fita kawai tana cemasa ya tashi to yay sallar”.
      Goshinsa ya murza yana cige laɓensa na ƙasa, har yanzu yana takaicin da mamakin yanda Mammah ke biyema Farah a kowanne lokaci. Duk da yasan akwai nata halin itama ya fahimci akwai zuga mai ƙarfi da akai mata a yau ɗin, a bazata wani guntun murmushi ya suɓuce masa, ya miƙe yana abinsa harya shiga toilet dan shi kaɗan yasan muguntar daya shiryama Farah da mai zuga Mammah ɗin dan ya tabbatar itace taje London ɗin kokuma sunyi waya akan tahowar tata.
     Alwala yayo yazo ya gabatar da sallar magrib data wucesa. Daga haka ya fito zuwa massallaci samun jam'in isha'i. Koda aka idar tare da samarin ƙannensa suka shigo gidan abin sha'awa, su sukai sashensu shi kuma yanufo sashen Hajiya iya. Kamar yanda ya fita bai samu kowa a falonba yanzuma haka ya dawo bai samu kowaba.
     Ɗakin Hajiya iya ya shiga da sallama. Tana zaune a inda tai salla Zinneerah dake fashin salla na kan kujera kwance tana latsa waya, lokaci-lokaci takan matse idanu da baki saboda mararta dake ɗan mata ciwo can ƙasa. Saurin miƙewa tai zaune saboda jin sallamarsa. Sai dai kafin tace zata tashi harya rigada ya shigo. Akanta ya fara sauke idanunsa ya janye. Batare da damuwar ganinta zaune a Sofa ɗinba yakai zaune yana cema hajiya iya “Barka da dare”.
      Zaram Zinneerah ta miƙe a sofar har tana neman faɗuwa. “A hankali mana Zinneerah. Koma saman gado ki kwanta, jira nake wani ya shigo cikin su Mas'ood su nema miki magani”.
     Da sauri Zinneerah tace, “Granny yama daina ai, bara naje wajensu Bahijja”
    Kafin Hajiya Iya tace wani abu harta nufi hanya da sauri. Tana gab da fita yace, “Zonan”.
        Tamkar ta fasa ihu taji. babu yanda ta iya dole ta dawo kanta a ƙasa. Batare da shima ya ɗago daga latsa wayar da yakeba yace, “Ki ɗauka min lap-top a ɗaki da abinda kika kai ɗazun”.
         Amsa masa tai da to tana fita cika umarninsa. Harga ALLAH yana burgeta saboda baida hargowa. Banda ɗazun bata taɓa ganin yayi faɗaba ko tsawa ma wani a gidan. Shi dai kawai baida sakewane, idan kaga fuskarsa a sake yana tare da Yah Khalipha ne ko Hajiya Iya. A zatonta yanda yasan ita ba komai bace a gidan face mai cin arziƙinsu zaita karta mata wulaƙancine. Amma sai taga saɓanin hakan.
     Da wannan tunanin ta ɗakko duk abinda ya sakata ta dawo ɗakin. Magana ta samu yanayi da Hajiya iya. Amma ko a cikin ɗakin kake da wahala ka jisa. 
      Wani shayin ta sake zuba masa zata saka suga uku yace, “two is ok”.
    Maida ɗaya tay ta saka masa biyun, daga haka ta ɗauki ƙaramin hijjab ɗinta da waya ta fice ta barsu

      koda taje sashensu Bahijja da suka tambayeta labarin yanda ta ƙare da kai shayi catai musu ai babu abinda ya faru, dama takai masa shayin yana wanka ajiyewa kawai tayi ta fito abinta. Mararta ke mata ciwo kaɗan-kaɗan shiyyasa taje ɗaki ta kwanta ganin sun fito.
       Meenal tace, “Yo tsoro mukaji kar wani abu ya faru yazo ya haɗa damu. dan laifinmu sai yafi naki. cazaiyi mune bamu nuna mikiba yasin”.
     Ƙaramar dariya kawai Zinneerah tai ta zame ta kwanta. Daga haka suka cigaba da hirarsu. Daga ƙarshe ranar anan ta kwana abinta.

_____________________★

    *DANYA*

     Ta daɗe kwance tana maida numfashin gajiya dana yunwa daya jigatata. Kafin ta miƙe dan ɗan kunun da tasha ya taimaketa. Ledar data shigo da ita ta jawo, ta buɗe tana fiddo kayan da malam ya haɗa mata da ƙara bitarsu yanda bazata mantaba. Baki ta washe na farin ciki tunawa da baba ya kusa dawowa gareta. Ta ɗaga wata ƴar kwalbar turare tana jujjuyawa.
        “Yanda ka bani wahala akan ƴarka Sule, sai na sakaka mantawa da ita na

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login