Showing 30001 words to 33000 words out of 39731 words
dake zaune ta saki tagumi jin motsin da tayi daga Hurriya ya sanya ta kalleta cikin mamaki taga idon Hurriya bude suna kallonta da wani irin jin dadi da murna Bintu ta nufota girgiza mata kai Hurriya tayi tana mata kallon kada ki sake ki tabani
Daga mata kai Bintu tayi tana ta hamdala Hurriya kuma kallonta kawai take yadda take murna
Shiru Hurriya tayi tana tunanin wadanda suka sanyata jinya inda ace a masarautar Heral ne to babu abinda zai hana su bakunci lahira don abinda suka aikata hukuncinshi kisa ne how dare they messed with Princess wani evil smirk tayi don ita she’s someone that doesn’t take nonsense from anybody whether she’s princess or slave tasan sai tayi maganinsu ita batajira wani ya kwatar mata yanci da kanta da hannunta zata kwatar ma kanta yanci
Hurriya bata da dadi ko kadan idan ka tabata zatayi masu salon azabar da ko a masarautar Qamar ba’a tabayi ma waninsu irinta ba because they almost killed her lamoniyar dake gareta is not an ordinary lamoniya ciwo ne mai hade da poison wanda yake babbar barazana ga rayuwarta all this while tasan Allah ke tsareta and nobody knows about her health condition don ko a masarautar Heral ciwonta is a secret duk wanda yasan da ciwonta sai yabar masarautar tare dayin nesa sosai da masarautar zatayi masu abinda idan akace gobe su kara bazasu kara ba tayi alkawarin sai sun biyata with bigger price Dukansu sai sunyi jinyar da tafi tata tayi wani evil smirk tare da rufe idonta masu kyau tana taune lebanta.
[12/02, 4:53 PM] Khadyn Sp: 🌚Masarautar Qamar
A story about a mysterious palace
By Khadija (KMU)
25&26
Bintu kallom Hurriya kawai take with pure love Hurriya lumshe ido tayi tana yamutsa fuska alamar jikinta na damunta Bintu tace bari in kira maki baba hanne ta kara dubaki
Bintu aguje taje kitchen ta kira Baba hanne wadda take tuka tuwo ai tanajin ance Hurriya ta farfado ta saki muciyar ta rugo aguje sai dakinsu Bintu murmushi tayi tana biyota a baya
A kwance suka iske Hurriya tadan tada kanta da bango ta lumshe idanunta dogayen lashes dinta kwance sai kyalli suke sai pink lips dinta da take dan cijewa Inna hanne kara kallon Hurriya tayi don ba karya tanada kyau kallonta ta karayi ganin irin kwarjini da kuma tsantsar mulki da yake bayyane ajikinta dama saidai idan baka gani Amman kallo daya zakayi ma Hurriya kasan jini sarauta ce bude idonta Hurriya tayi aiko da sauri inna Hanne ta sadda kanta kasa duk tasha jinin jikinta ta kasa motsi Hurriya kallo daya tayi mata ta kauda kanta
Hurriya Bintu ta kalla tace Bintu ki samo man ruwan zafi inyi wanka da sauri Bintu tace to inna hanne ce tace kije kitchen kice nice na aiko ki a zuba maki ruwan zafi Bintu juyawa tayi ta fita domin amso ma Hurriya ruwan wanka
Inna Hanne kam kanta duke a kasa Hurriya batasan ma Allah yayi wata hallita a wurin ba har Bintu ta kawo mata ruwan a hankali ta sauko kafarta wadda tayi mata nauyi da sanyi
Bintu har tazo zata taimaka mata girgiza mata kai Hurriya tayi alamar bataso da kyar ta iya tashi ta fara tafiya a hankali Bintu ta shiga ta ajiye mata ruwan sannan ta bata brush da macline sai sabulun wanka
Saida tayi brush sannan ta mika ma Bintu brush din ita kuma ta shiga toilet domin yin wanka
Ta dade cikin toilette tana wanke jikinta saboda kyankyamin da takeji saida tayi kamar zataji ma kanta ciwo saboda yadda take dirzar jikin sannan ta dauraye jikinta ta fito tana mai jin matukar kyankyamin kayan da ta maida
Hurriya dakinsu ta shigo inda tayi sa’a Bintu da inna hanne basu nan don inna hanne ce tacema Bintu suje kitchen tare domin dafa ma Hurriya abinci dajin haka Bintu taita murna sannan tabi inna hanne kitchen din kallon Bintu tayi sannan tace mi Hurriya tafiso acikin abinci shiru Bintu tayi sannan ta girgiza ma inna hanne kai alamar batasani ba don bata taba ganin Hurriya na cin abi da farin ciki ba don kullum cikin dacin rai take cin abinci kamar dole
Inna hanne murmushi tayi ta debo dankali wanda bai kai goma ba sannan ta fere.
Hurriya kallon ko ina tayi da yayi datti cikin yanayin natsuwarta ta amso tsintsiya wurin uwale da murna uwale ta farayi mata ya jiki daga mata kai Hurriya kawai tayi tazo ta gyara dan wurin ta share wurin tass
Sannan ta cire kayan jikinta vaseline ta shafa ta bude ledar kayanta ta zaro jeans dark blue sai farar top mai shara shara saida ta sanya inner wears hade da vest sannan ta sanya rigar
Kwanciya tayi ta mike kafafunta ta lumshe idonta tunani take neman ta farayi wanda sam babu lisaafin tunani a rayuwarta bude idonta tayi sai kam ga giftawar su barira kallonsu tayi Dukansu tana karantar su
Inna hanne ce ta shigo itada Bintu inna hanne rike da yar karamar kula mai kyau Bintu kuma hannunta rike da ruwa da plate
Da sallama suka shigo kallo daya Hurriya tayi mata tagane ta don itace matar da ta fara bata ruwan zafi. acikin zuciyar ta take tambayar kanta mi takeyi anan Shiru tayi tana kallon matar sai sadda kai take kamar munafuka tana durkusa mata alhalin ranar farko ba haka tayi mata ba
Inna hanne ta zuba mata faten dankalin da tayi mata wanda yaji kayan miya ta mika mata Hurriya kallonta tayi ba tare da ta amsa ba don haka Bintu da sauri ta amsa tazo ta mika mata amsa Hurriya tayi sannan tace Bintu ta miko mata ledar kayanta ba musu Bintu ta miko mata ledar kayanta spoon ta dauka cikin kayanta saida ta daurayeshi sannan ta faraci lumshe ido tayi ta cigaba daci wanda alama ke nuni da tana enjoying abinci
Dukansu kallonta suke inna hanne kanta a kasa saida taci Sosai sannan ta ture plate din Bintu ta kalleta sannan tace kin koshi daga ma Bintu kai Alamar Eh ta koshi
Pure water inna hanne ta miko mata alamar ta ajiye tayi mata inna hanne ta ajiye mata dauka tayi ta fasa ta shanye
Inna hanne ta miko ma Hurriya magani ba tare da tayi musu ba ta amsa tayi chokali uku ta mika mata murmushi inna hanne tayi tana mai jin dadi ganin Hurriya har tayi acknowledging dinta
Kwanciya Hurriya tayi tareda lumshe idonta tana mai neman fadawa duniyar tunani tana tuna lokacin da idan ciwon ta ya tashi yadda iyayenta ke shiga tashin hankali sosai ganin tana Neman ta fada duniyar tunanin wanda bata cika son haka ba don haka ta tashi wayarta ta dauko wadda ta dade batayi amfani da ita ba ta kunna waka sannan lumshe ido tana bin wakar fire on fire by sam smith a haka har bacci ya dauketa
Inna hanne bayan tagama aikinta ta shigo ta iske Hurriya kwance tana Bacci kamar karamar yarinya duk da bacci take amman zaka iya gane yadda ta hade fuska murmushi tayi sannan tace rigimar Duniya
Hurriya bayan ta warke saida tayi kusan sati biyu bata fara zuwa aiki ba don so take sai sanyi ya gama fita daga jikinta tasss don a lamarinta batasan weakness ko kuma ace wani ya gane weak point dinta shiyasa saida ta tabattar da ta warke tasss sannan zata koma aiki
Bangaren kam inna hanne kam hidima takeyi mata babu kakautawa don abinci masu dadi kala kala takeyi ma Hurriya Ruwan wanka kam kullum ita take tafasa mata ta kai mata toilet hatta kayan Hurriya kwana uku sukeyi sai ta daukesu ta wanke mata
Duk hidimar da take ma Hurriya bata taba ce mata ta gode ba don kamar daman dolen ta ne ita kuma Inna hanne bata taba kallon Rashin kulawar da Hurriyyar take mata ba as wani abu ba
Tana addu’a kullum Allah ya bama Hurriya ikon yadda da ita duk da ta fahimci Hurriyar kamar bata yadda da kowa ba
A bangaren su Imad sun baza ido suna taso suga ko ta ina zata bullo don Liya ta bincika masu ance ta warke don Hamdan da Amrah kullum sai sunce zasu je Amman yan’uwan sunki barinsu saboda zai zama abun fadi a masarautar duk dasu ba ruwansu
Fitowar ta daga wanka kenan daga ita sai zani sai kuma doguwar hijab dai dai zata shiga ciki su kuma suna fitowa Dukansu kallonta sukeyi tundaga dogayen kafafunta har zuwa kyakyawar fuskarta wadda babu fara’a saidai zallah kyau da annurin dake fita kafe su tayi da idanunta masu masifar kyau saidai baka iya jure kallonsu saboda yadda suke imnating danger flames ne kawai ke fita daga idanun acikinsu ba wacce bataji shakkarta ba saboda wani kwarjini da ta karayi masu
Saida ta kare masu kallo tass sannan ta shiga daga ciki inna hanne da Bintu na ganin dawowarta suka tashi inna hanne ta kalli Hurriya sannan tace mi zakiyi yanzu cewa tayi sallah shimfida mata dadduma tayi sannan suka fita domin bata wurin saboda shiryawa don sun san bata sanya kaya wani na kallonta
Wata doguwar riga ta sanya mai kyau saidai tana kama da abaya yau kawai taji tanason dan decent dressing dankwali ta daura ma gashinta wanda yake ta kamshin mai na soulmate don Hurriya na yawan wanke gashinta sai ta jirashi ya bushe ya gama shan iska tukuna ta shafa mai ta sharce shi.
Hijab ta sanya tayi sallah hade da rama sallahr da ake binta don daman yaune karshe idan ta rama la’asar tohm sauran magriba da isha’i
Tana gama sallahr inna hanne ta shigo wadda dama dama yanzu Hurriya na kula ta saboda tana kula da ita duk wani motives nata tana kallo duk da tana nuna halin rashin damuwa gareta ganin batada wani motives shiyasa ta kyaleta ta shigo rayuwarta kuma she knew she’s too smart itadin fa sunanta Hurriya Faisait Hamood she’s her fathers daughter wanda zai iya cutar da ita yanzu ai sai yayi babban shiri beside ba wanda yasan kowacece ita saidai she have to be very cautious duk dama ita din she’s always cautious
Turarenta ta fesa mai saukin kudi sannan ta fito domin samun iska wayarta kirar burin yar garuwa sai a hannunta sai earpieces dake makale a kunnenta wakarta takeji wasba ce tazo inda take tana kuka tana sharbar majina kallo daya Hurriya tayi mata taganeta
wasba yar karamar yarinyar ta dukar da kanta tanata sharbar kuka Hurriya batace mata komai ba har ta gama kukanta
Saida tagama kukan sannan ta kalli Hurriya ta washe mata baki tace kinyi kyau kinfi kyau a haka Hurriya batace mata kala ba Amman tana kallon yarinyar surutai wasba ta farayi mata tace ina kikaje ne kullum sai nazo na jira inga ko zaki zo Amman baki taba zuwa ba sai yau yar dariya wasba tayi tace bari muga kwana nawa nayi banganki ba hannunta ta fara kirgawa kamar wata yar baby har saida ta kirga kwanakin da tayi bataga Hurriya ba tashi tsaye wasba tayi idonta na cika da kwalla sannan tace ki yawaita yin addu’oi Saboda banason na rasaki irin fareedaa you’re beautiful ta sakar mata murmushi sannan ta ruga ta tafi
Kallon bayan yarinyar da take gudu tayi wadda damuwa ta bayyana a duka fuskar yarinyar Hurriya can kasan makoshinta tace what is wrong with the girl aranta tace ina ruwanki
Kallon mutanen da suke wucewa suna kallonta tayi itadai tanajin wakarta tana kallon kowa da kowa
Hurriya ta dade zaune a wurin don har saida taga magrib ta tafi zuwa dakinsu
Sallahr magrib tayi bayan tagama ta nufi part din Imad ganin taji sauki don haka bari yau ta koma bakin aikinta
Kitchen ta shiga ba sallama ba komai zubaida datake bakin kofa sakalau tayi da baki tana kallon Hurriya wadda bazaka ce mata yar aiki bace yadda tayi wani irin kyau kuma sai kamshi takeyi zubaida bakin ciki ne ya turniketa don bata manta yadda uban gidanta da Hamdan suka shiga damuwar rashinta ba
Ta tsani Hurriyar nan don batada mutunci ko kadan gashi duk inda taje ita ake kallo duk sauran mutanen dake zaune sun zama banzaye indai tana wuri haka ko su Hamdan basu tabayi mata magana ba karewa ko maganar Imad bata tabaji ba Amman ga yarinya da tazo jiya jiya tafi ta matsayi abun gaskiya yana matukar bata mata rai Amman zatayi maganinta very soon don ba zata zuba mata ido ba
Duk aranta take wannan sake saken
Baba RaBI ce ta kalli Hurriya tace ya jiki kinsha ciwo ko daga yanayin maganar ta zakasan ba har cikin ranta tayi maganar ba jiran amsar Hurriya take saida tana juyowa taga batanan Dariya suka saki Dukansu yan kitchen din shiru baba rabi tayi sannan ta daure fuska
Store ta shiga ta debo basmati tayi continental rice sai vegetables spaghetti wadda taji namomi sai kamshi take kowa kallonta yake amman ita kamar batasan anayi ba saboda earpiece ne ma makale a kunnenta
Saida ta gama suka jera trays din akace su shiga sukai masu ba musu Hurriya tabi bayansu da nata tray din
Basu tarar dasu a falo na farko ko a parlour na biyu basu nan sai a parlon na uku inda suka shiga kansu duk a kasa
Hurriya kallo daya tayi masu ta dauke kanta suka shiga jera abincin
Saidai tanajin idanun dake binta
Ludo sukeyi Dukansu su shiddan kallo daya zakayi masu kasan suna cikin farin ciki kuma suna enjoying game din Hamdan ne yake kokarin cinye game din Neela kuma kiri kiri taki bashi dama
Tunda Hurriya ta shigo Imad yasan ta shigo don lokacin data juyo ta kallesu with distaste yana kallonta saidai bata lura dashi ba shidai yana mamakin halinta na iko da raini wayau Because he never came across someone like her ba all his entire life komai nata ya bambamta bata tsoron kowa acikinsu abinda takeso shi takeyi yasan tana aiki yanda ya kamata indai ta fannin aiki ne baza a kamata da laifi ko ha’inci ba
Bata gaishe da kowa sannan bata kula kowa he can’t read her duk yanda yaso ya dan fahimce ta ya kasa saboda ta rufe kowace kofa da dan mutum zai iya karantar ta
Saidai akwai abinda har yanzu yake bude wanda ta kasa rufe shi duka she’s lonely saidai kallo daya idan kayi mata baza ka gane kadaicin dake tattare da ita ba saboda yadda ta rufeshi ta ko ina
Liya ce ta kallesu tace please Quit the game for now your food is ready Ammar ne yayi saurin tashi yace daman yunwa nikeji ya nufo din dining su Hamdan da amrah suka biyo baya kowa yaja kujerar shi ya zauna
Neela ce tazo ta zauna sannan Imad ne karshe Ammar ne ya dago zaiyi magana aiko cikin sa’a idonshi akan na Hurriya wadda itama shi take kallo tana karantar shi saidai he looks very familiar to her kamar tasanshi kallon imad tayi wanda ya zauna a wani miskilance ya lumshe ido yanajin saukar idonta masu kaifi shima kallonshi tayi Dukansu tasansu amman A ina?Ganin idan fa tanason tagano inda tasansu sai ta koma duniyar tunani wadda batasan hakan kwata kwata
Ammar dariya yayi yace Hurry ya jiki please come and join us
Hamdan yanajin ance hurry yayi saurin dagowa kamar hadin baki Dukansu suka rinka kallonta Amrah ce ta taso tazo wurin Hurriya wanda ta kasa boye murnarta alamun zata rungume Hurriya tayi saurin ja baya sannan tace kada ki tabani idan ba haka ba marinki zanyi daga mata kai amrah tayi stiill tana farin cikin ganinta
Bude baki kowa yayi don jin furucin Hurriya na zata mari amrah saidai ba wanda yace kala saboda sunsan halin amrah indai akan abun da takeso ne yanzu ko maganar banza idan sukayi ma Hurriya to ba wanda zai kwana lafiya don idan ta farayi masu rigima da kuka to sai Allah
Bude bakinta amrah tayi sannan tace Hurry please grant me a wish tana daga mata hannu alamar don Allah ta taimaka mata shiru Hurriya tayi ganin tayi shiru amrah sai tayi tunanin kilan Hurriya batajin turanci sai tace don Allah kiyiman abu daya
Hurriya frowning brows dinta tayi ta kalleta mockingly tace mi kikeso dariya Amrah tayi tace don Allah muci abinci tare shiru wurin yayi kowa na jiran amsarta Ammar ne yayi breaking silent din ta hanyar cewa haba yar mai kyau please join us yana karya murya hade da kanne mata ido kamar mace trying to look funny Hurriya gyara tsayuwarta tayi sannan tace you Better stop acting that way if not I promise you’ll be a transgender by tomorrow morning saboda ka koma kamar wata amarachi Dariya kowa ya dauka shikanshi Imad duk yanda yaso kada yayi dariya saida ya dara
Neela a ranta take maganar muryar Hurriya ta hadu ba karya don wani accent mai matukar dadi take amfani dashi wurin magana Ammar ba karamin dadi yaji ba yadda tayi mashi magana don bai tsammaci hakan ba don yarinya ya lura bata magana kwata kwata don idan bakayi dagaske ba zakayi tunanin bebiya ce .
Hurriya zagayowa tayi taja kujera ta zauna kowa serving abincin shi yayi
Serving ta farayi ahankali don komai ahankali ta zuba tundaga kan appetize komai nata accordling takeyinshi cikin tsari ba wanda bai kalli yadda ta fara cin abincinta ba don da appetizer ta fara sannan taci kadan shima main dish kadan taci yadda zata ida cin komai don a doka tun suna kanana ake koya masu table manners don shine yake determining they are from royalties kuma not an ordinary royal family
Don haka they’ve to be always mindful of their table manners duk wanda yaga yadda take cin abinci yasan she’s from an elegant family because he the way she held her spoon ba kowa ya iya irinshi ba
Ganin almost all of them are staring at her plate ya sanya a hankali tace bloody hell what am I doing cikin wayau da dabara ta lalata plate din ta canza salon cin Abincin.
They ate in silence tana gamawa tasha ruwa sannan ta tashi kallonta Dukansu sukayi