Showing 3001 words to 6000 words out of 39731 words
cigaba da bata labari shine yau larai da lalu suka hau ni da duka wai sai sun kasheni suna ta dukana shine na rugo na taho wurin ki
Hurriya bazaka iya gane miye a fuskar ta ba fuskar nan blank koda yake ita duk bala’e baka iya reading emotions dinta don fuskar nan kullum a hade take
Muryar ta mai dadi don ba fluent hausa take ba saboda mixed din yaren Ethiopia da English da take dashi ta kalli Bintu tace kinajin yunwa Bintu ta daga mata kai taliyar da ta rage saura ta bata Bintu ta amsa da godiya Hurriya tana kallon yadda take cin taliyar tamkar wadda bata tabacin abinci ba.
Bintu bayan tagama cin abincin ta kalli Hurriya da kitson kanta ya Dan fara tsufa tace In kwance maki kitson nan girgiza mata kai tayi alamar Aa Bintu turo baki tayi tace kai Hurriya shiru tayi ba tare da ta tanka ta sannan ta dauki tsinke ta fara kwance kalabar
Murmushi Bintu tayi don tasan halin Hurriya na rashin son wani ya taba mata ko yatsa
Fira suka fara har ta gama kwancewa ta sharce kan Bintu tace Hurriya kinada gashi damani Hurriya ta yamutsa fuska sannan tace inaso in rage gashin yana damuna Bintu tayi dariya tace don’t even start don ba kyau shrugging Hurriya tayi sannan tace I don’t bloody care Bintu da tasan halinta sai tayi shiru tabar maganar.
Tare sukaje kasuwa inda ta saba siyen waken Awara da murmushi mutumin ya tarbesu Bintu itama maida mashi murmushin tayi Hurriya kam ba wani murmushi bare gaisuwa don Bintu sai washe baki take suna gaisawa dagan gan yace kinga murmushi ma sunnah ne a musulunci dariya tayi Mahnoor da tariga tasan da ita yake kwata kwata bata damu ba.
Hurriya jam da tagaji da surutunshi cikin zakin muryarta da accent dinta mai dadi tace mashi ya sanya mata waken idan kuma ya cigaba da surutu zata canja wurin siye saboda ita ba magana ya kawota ba she’s here for a business tana kallon tsakiyar idonshi tayi maganar murmushi yayi sannan ya zuba mata waken ta amsa ta kama gabanta.
Ashiru kam tunda yazo yake kallonta yana zaginta a ranshi yayi alkawarin bazai taba yafe mataba don lokaci kawai yake jira ya dauki fansar shi
Hurriya yau tare suka soya awara itada Bintu banda murmushi ba abinda Bintu takeyi don duk wanda yace abashi awara sai tayi mashi murmushi Hurriya kam ita take soyawa suna gama soyawa suka tattara komai suka tafi gida.
[12/02, 4:53 PM] Khadyn Sp: 🌚Masarautar Qamar
By Khadija (KMU )
Page 5&6
lokacin da suka dawo anata kiraye kirayen sallah magriba Don Hurriya zaiyi wuya takai bayan magrib a wurin suyar Awara Bintu tayi alwala sannan ta shigo dakin kallon Hurriya dake kwance saman katifar tana jin waka tayi idonta a lumshe suke Bintu ta kalleta tana admiring irin kyaun da Allah yayi mata long lashes dinta da suke kwance kamar tayi fixing dinsu dogon hancin ta sai kuma cynical mouth dinta banda glowing ba abinda fuskar ta take because of her smooth and flawless skin a hankali ta kalli shafefen cikinta wanda kamar bata sanya mashi komai Hurriya is extraordinary beauty duk wanda ya kalleta yasan tana da kyau kuma har ka gama rayuwarka da ita baza ka lura da wani muni nata ba saboda kana kallonta a kullum tana kara maka kyau irinsu ne wanda ake gasar kyau dasu kuma tayi imani da cewar idan daHurriya zata fito gasar kyau ba abinda zai hanata cin wannan gasar irinsu ne za’a iya biyansu ko nawane don su kasance manya manya models irin nasu france da america Everything about her is screaming perfection with nothing left to criticize
Sallah Bintu ta kabbara har tagama sallah Hurriya bata matsa konan da can ba Bayan Bintu ta gama addu’a ta kalli Hurriya tace Hurriya ki tashi kiyi sallah lokaci na tafiya Hurriya kam da batajin Mai take cewa don ta kure volume a burin yar garuwarta Bintu kara mata magana tayi shiru tayi Bintu da taga kamar batajin mi take cewa sai ta sanya hannu ta taba ta Aiko kamar an tsunkuli Hurriya din da a firgice ta tashi tana Bintu wani irin mugun kallo ta Hurriya kallon take sosai Bintu kam da tasan yadda Hurriya ta tsani wani ya tabata don tanada tabbacin idan wani ne ya tabata ba ita ba to saukar mari ne kawai zaiji Hurriya tace Bintu don’t ever repeat this mistake again Bintu tace ki tashi kiyi sallah lokaci na wucewa Hurriya ta daga mata kai sannan taje tayi alwala da sauri tayi sallah don Bintu kallon yadda take sallah kawai sannan girgiza ta kai kawai
Hurriya ta kalli Bintu sannan tace kina jin yunwa Bintu tace inajin yunwa Hurriya
Hurriya daure gashinta tayi saboda wanda tayi taji yana damunta so take tasamu lokaci ta rage gashin don ya kara taruwa da yawa gashi bata san takura tana gama gyaran gashin ta kalli Bintu tace bari na samo manah gari can shagon Bintu tace zan rakaki
Tare suka jero suna tafiya su biyu duk inda ta gifta kallonsu ake ba Kamar Hurriya don crop top ce jikinta pink sai wani bakin wando gashin kanta ta da yake a bude sai sheki yake har suka zo shagon da ake saide saide
Da murmushi a fuskar shi yace Hurriya mi za’a baku gari tace ya sanya masu na dari sai sugar na hamsin gyadar hamsin Hamza da murmushi yace su Hurriya gari za’a sha wani kallo Hurriya tayi mashi ai sai ya fara to to sannan ya miko garin da suga da gyada Bintu ta amsa sannan tace mun gode Hurriya dai banza tayi dasu dukan su.
Suna shigowa suka ga talatu a zaure itada tasi’u hannunshi sanye cikin rigarta tana ta dariya kasa kasa kwata kwata basu lura dasu Hurriya ba da suka shigo don Bintu ba karamin tsorota tayi ba don sauran kadan ta fadi Hurriya kallo daya tayi masu ta dauke kanta tayi gaba har ta sanya kanta taji maganar su kasa kasa tasi’u yace ya za’ayi da yarinyar can ne ni wallahi duk unguwar nan ba wanda yake burgeni Kamar ta yarinya shigar banza kuma Kamar tsohuwar baturiya Amman ace duk unguwar nan gani nan bari ina da burin in lasa wannan yarinya nima tasi’u yace ma talatu dariya tayi sannan tace Hurriya ai karuwa ce ta karshe kawai dai ta iya allonta
Ganin Hurriya da tayi a tsaye saida gabanta ya fadi wani irin mugun kallo take mata fuskar nan kwata kwata babu emotion tana a yadda take kamar kullum tasi’u ta kalla cikin ido hannun tasi’u dake cikin rigar talatu ta kalla sannan cikin muryarta mai dadi ta kalleshi sannan tace nima ka sanya hannunka cikin rigata tana kallon tsakiyar idanunshi tsotsar bakinta tayi kadan tace ka sanya hannuka cikin rigata mana
Shiru tasi’u yayi yama kasa kallonta duk ya daburce don wani irin kwarjini da tayi mashi kilan saboda kyaunta take da irin wannan kwarjini frowning face dinta tayi in a mocking way tace kai dan akuya ne? Are you mad kallon shi tayi sannan tace kaje ka kalli kanka a madubi sannan tazo saitin talatu kallon cikin idanunta tayi sannan tace miye ma’anar karuwanci shiru tayi talatu tace ina tambayar ki shiru tayi
Hurriya tace sana’ar kice keda tabawa and please stop sleeping with young boys masu empty pockets idan zaki kwanta da namiji gwara ki nemi baban tasi’u yadda idan yagama zai baki koda dari biyu ce wadda zaki iya cin tsire wawaye makwadaita.
Earpiece dinta ta maida tayi cikin gida abinta kamar batayi komai ba she hate nonsense mutanen yanzu you’v to stand and for yourself ita batama ga dalilin da zaisa mutum ya zageta tayi shiru ba she doesn’t care ko waye kai zata kalli tsabar idonka tayi maka daidai abinda kayi mata Amman dai ba ruwan ta da kowa kawai miskila ce ta karshe and don’t talk behind her back saboda Allah ya bata wani irin ji sosai kilan shine baiwarta Don tana iyajin magana daga nesa Sosai wadda nisanta ya wuce tunani Amman cikin ikon Allah zataji lokacin da bata ma iya hausar ba Sosai don ko magana taso ta fada ma mutum marar dadi to ba lallai yaji mi take cewa ba saboda she’s using British and Amacharic Amman yanzu idan ta yanko maka magana kamar daman asalin yaren hausan takeji don duk kalmomi mararsa dadi ta iya amfani dasu.
Bintu kam har ta jika masu garin tanata jiran Hurriya din tazo domin susha suyi sallah su kwanta Bintu ta kalli Hurriya tace ina kika tsaya ahankali tace waje tasan bata cika san magana ba don ta tsani unnecessary zance don haka Bintu taja Bakinta tayi shiru
Tare suka sha garin don ita Hurriya a hankali take sha don har tagama shanye nata Hurriya bata shanye ba tanajin waka tana kada kanta Bintu murmushi tayi sannan ta fita ta wanke kofin tayo alwala sannan ta kabbara isha’i tana gama sallah tana lazimi saiga sallama
Hurriya idonta lumshe Amman duk abinda Bintu suke cewa tanajin su Bintu ta kalli Hurriya tace Hurriya na tafi baba ya dawo yace a kirani tana goge dan hawayen da ya zubo mata Hurriya tayi shiru kamar bataji mai Bintu take cewa ba sannan Bintu ta fita tana dan gyara ma Hurriya labule.
Bintu na isowa kofar gida gabanta ya fadi don batasan mi zata tarar ba a gidan a hankali tasa kanta a soron Gidan tana tafiya kamar munafuka lalu da suka shirya abunsu da larai daman yasan dole zata dawo gida shiyasa ya tsaya zaure ya tarbeta saboda ya lalubi rabonshi
Daidai inda take yazo yana wani munafukin dariya yace wa naka ma matsowa ya farayi tana matsawa baya yana Dariyar har saida ya kawota karshen bango riketa yayi gam yana dariya yellowing hakoranshi suna bayyana kugunta yarike yana kokarin sanya mata hannu cikin riga tureshi tayi yayi baya ya kalleta sannan yace ni zaki ture to yau Mai rabani dake sai Allah kugunta ya rike aiko suka fara kokowa karfinta ne ya fara karewa sosai
Hurriya da take kallon ikon Allah zuwa tayi daidai inda yake ta dauke lalu da mari a harzuqe ya dago da niyyar sauke ma kowaye ya mareshi ruwan tijara saidai da kyar ya iya hadiya maganar shi da kuma yawun dake bakinshi kallonta yakeyi da yar crop top din da ko cibi bata rufe mata ba sai bakin wandon dake jikinta gashin kanta kam ba’a daure ba tunda lalu yake bai taba ganin halitta mai kyan mahnoor ba saidai kyawawan idanunta da Allah ya basu matukar kwarjini Hurriya ta janye bintu daga wurin lalu tana mashi wani irin banza kallo da kyawawan idanunta cikin muryarta mai dadi da tace duk randa na karajin wani Abu makamancin haka ya faru sai kaji a jikin ka sakarai mai karamar kwakwalwa
Bintu kallon Hurriya tayi sannan tace nagode Hurriya kam baka iya karantar yanayinta don ta kwarai wurin shutting emotions dinta
Tare suka shiga inda suka tarar abbanta na kwasar tuwo larai na kusa dashi Larai na lura da shigowar su ta saki wani munafukin murmushi Abbanta da ya kula dasu aiko zumbur ya taso da hannunshi duk miya zai mari Hurriya cikin sauri ta rike hannunshi tana rikewa ta saki don kamar ta rike kashi tana kallonshi Abba da ya harzuka yace daman kina wurin wannan shedaniyar marar tarbiya marar addini.
Hurriya a kalleshi sannan tace babban shedani ya wuce bayanka wanda har zai tsallake kafa ya tafi gantali ba tare da tunanin halin da diyarshi zata fada ba a hannun kishiyar uwa bakasan mi taci ba bakasan mi tasha ba baka san wazai lalat maka diya ba kallon Larai da tabata fuska tana kallonta tayi sannan tace koda yake ba abin mamaki bane tunda duka jikin ka daure yake da asiri.
Rashin addinina da Rashin tarbiyata duka dauka nayi a wurin wanda baisan hakkin diyarshi ba ido cikin ido tace sakarai wawa mijin tace Bintu da take kallon komai tasan a haka Hurriya na ganin mutuncinta tasan idan tayi wani abun ba zataji dadi ba.
Hurriya ta kalli Bintu sannan tace ai baki jin yunwa ko Bintu ta daga mata kai tace muje dakinki Hurriya na gaba Bintu na baya har suka zo dakin kallonta tayi mata da ido ta shiga kuka take shirin yi Hurriya ta nuna mata alama da tai shiru.
Abba da Larai kam sunsan halin shegiyar Hurriya ldinan da ta zame masu karfen kafa a cikin garin nan don bata da mutunci
Hurriya tazo ta kallesu sannan tace idan har naji ko harar Bintu kunyi to zan kira maku hukuma ta kada kai ta bar gidan lalu da yake boye yana kallon su duka ya fito yana kallon Larai yace wacece wannan Larai ta kalleshi tace fitacciyar marar kunya kenan don haka duk abinda tace to ba mamaki zata iya aikata shi.
[12/02, 4:53 PM] Khadyn Sp: 🌚Masarautar Qamar
By Khadija (KMU)
Page 7&8
Gida Hurriya ta koma tana shiga ta kwanta a katifar tana tunani bata gama tunanin ba bacci ya dauketa sai karfe bakwai ta tashi ruwa ta dan kashe sannan ta juyeshi cikin bucket tayi wanka kanta ta fara wankewa sannan wanka tayi alwala saida ta sanya gashin kanta saitin fan ya bushe tukunna scissors ta duba inda take ajewa bata gani ba dubawa tayi sosai bata gani ba tsoki tayi ta gyara gashinta ta daureshi kawai don taso ta yankeshi saboda gashin ya fara yi mata yawa wani dan karamin box ta fiddo can cikin kayanta ahankali ta bude tana kallon sarkoki guda biyu masu masifar kyau Rufe box din tayi ta maida sannan ta fiddo wani jeans blue ne sosai Amman yanada dan fadi kasan shi sai tsagar dake a cinyoyin wandon da gwiwar wandon shiryawa tayi cikin wando ta sanya bakar riga yau kawai taji tanason ta sanya dan kwali don haka ta zaro wani blue and black vintage scarf ta daura ma kanta saida tagama shiryawa tsaff sannan ta dan murza dan oil turaren ta mai saukin kudi
Saida tagama komai sannan ta kabbara sallahr asuba don har takwas da mintuna tayi da sauri tagama komai ta nufi gidan mai anguwa .
Tadan makara yau wurin aiki tana shiga laminde tace kina raina Hurriya yanzu nike da niyyar daman In sanya a Duba ki ko lafiya Hurriya ta share tambayar da tayi mata tace ina kayan murmushi laminde tayi ta fiddo mata kayan yau cikin sauri take komai saboda yau zata kwashi adashenta kuma tanaso ta siye kaya saida ta tabbatar tagama komai don ko laminde ko Bankwana batayi ma laminde ba ta fito
Hurriya kam saida taje gida ta fiddo asusunta har ta maida wurin maida asusun ne wani dan box 📦 ya fado a hankali ta bude tana kallon sarkoki guda biyu da banda kyalkyali ba abinda sukeyi maidawa take kokarinyi kawai sai a ranta tace bari ta sanya it’s been a long time a hankali ta warware sarka guda daya wadda plain ce kawai Amman gold ne a sarkar ta sanya Kallon dayar sarkar take wadda kamar diamond ce Amman stone din anyi mashi carve da H Maidawa tayi a box din sannan ta sanya shi a aljihun wandonta Emotions din da taji ya fara taso mata ne ya sanya kawai ta cire kudin asusun wanda suka kama dubu takwas ta tafi gidan Asabe wadda ta kasance uwar zubin adashen Hurriya ba sallama ta shiga gidan a tsakar gida ta iske asabe tana shan rake
Asabe saidai ganin mutum tayi a kanta don ta tsoro ta matuka Hurriya ta kalla daga sama har kasa tace Nagode ma Allah kece cikin gidanan namu da ace bake bace da sai anjimu dake yau Hurriya kallon Asabe tayi fuskar ta babu alamun murmushi ko daya tace nazo kwashe kudina
Dariya Asabe tayi sannan tace oh kece fa kwasar karshe kusan kowa yasan halinki shiyasa duk angama maki zubin adashen ki tun kafin ma kizo ta ida maganar da dariya hurriya batace mata kala ba saidai ta jawo kujerar dake kusa da Asabe ta zauna
Asabe tace kinga bari na dauko maki kudin ki labule asabe ta daga ta shiga daki sai gata tafito da yar lalitar tsaff ta kirga ma Hurriya dubu sha biyar da dari takwas tace ga kudin ki kece daman zaki ida zubin yau shine zai kama dubu sha shida kenan Hurriya amsar kudinta tayi daman hannu biyu tayi zubin na wata biyu kenan kuma itace kwasar karshe ta hada da dubu takwas din da ta fiddo daga asusun ta wanda suka kama dubu ashirin da uku
Amsar abunta tayi ba tare da tace ta gode ba asabe har zata wuce asabe tace yawwa Hurriya ga fa irin kayan da kike sawa gwanjo ki duba Hurriya alama tayi mata da ta miko cike da murna asabe ta shiga daki don tasan indai Hurriya ce sai ta siye kayan kusan dubu biyar indai tanason Abu zata siya gashi ita bata taya kaya duk yanda aka batasu saye takeyi
Kulli guda asabe ta fitoda kayan tana nuna ma Hurriya murmushi tayi tare da bude kayan tace kalla Hurriya kallon da Hurriya take ma kayan kawai zai tabbatar maka da cewar sun burgeta a hankali ta fara zabar kayan masu kyau har kusan kala goma sai hula kala uku Asabe ce ta kalleta sannan tace Hurriya gafa wata jalabiya zatayi maki kyau ki hada da ita Hurriya kallon jalabiyar tayi sannan tace ta sanya mata da murmushi asabe ta sanya hada wani dan kwali Mai silbi sai hijab Mahnoor kallonta tayi sannan tace nawa ne duka kudin kayan Asabe ta gyara tsayuwa sannan tace dubu shida Hurriya ba tare da bata lokaci ba ta kirgo dubu shida ta bama asabe
Asabe kam dadi kamar ya kasheta daman tasan Hurriya bata da bakin ciki indai tanason Abu zata siya à yadda ka batashi leda ta dauko ta kwashe ma Hurriya kayan sai zuba kam godiya take da addu’a Hurriya bata bi takanta ba ta fito daga gidan ta nufi gidan mai unguwa cikin aljihun