Showing 87001 words to 89323 words out of 89323 words

Chapter 30 - MACIJINE SHI COMPLETE

Start ads

10 Aug 2025

499

Middle Ads

slow agurin,suna tsaye cikin mota,masu bara sai zuwa suke suna Bara.
Wani dattijone cikin shiga ta almajirai,kallo ɗaya zakayi masa kasan yana shan wahala yazo jikin motar su fattu yana Bara,kasancewar gilas din motar irin mai duhun nan ne,yasa na waje baya ganin na ciki.

Fattu ce tayi firgigit tatashi daga jikin Adeeb tana kallon tsohon dake barar.
Wani dan ihu ta sanya tana mai ƙoƙarin buɗe kofar motar.kira take
"Hamma baffana,baffana"tana faɗa cikin rawar jiki tana kokarin buɗe motar.
Da sauri shima Adeeb ya kai kallonsa inda fattun ke nuna masa.
Tabbas baffa ne kuwa.gana ɗaya fattu ta rikice tana kici kici buɗe kofar Amma tsabar farin ciki tama kasa,budewar sai kira take"baffana,baffana"
Hannunta Adeeb ya riko yace "ki nutsu hulwa,karkije kiki ciwo kinji bari muje gurin baffan"ya faɗa yana bude kofar motar.
Da sauri fattu ta fito daga cikin motar ta nufi gurin mutumin da yayi dan gaba dan zuwa wajen wata motar ya sami sadaka.
Da sauri ta kamo hannunsa tana faɗin "baffana kaine,haka ?"cikin azama baffa ya juyo sakamakon jin Muryar da akullum saiyayi kukan rashin ta,kuma duk kuɗin da yake samu na bara tarawa yake,dan yayi ta zaga garuruwa yana neman fattu,yasan watarana zasu hadu.
Jifa yayi da dan buhun dake hannunsa,wanda yake tara kudin barartasa ciki.
"Fattu,kece"baffa ya faɗa cike da shauki.
Kuka fattu keyi tana kallon baffa,kafin ta rungumeshi ajikinta tana kuka.shima baffa kuka yake cike da godewa Allah,yau gashi ga fattunsa,shikenan burinsa ya cika.
Sultan habib,da innar fatyu ma,fitowa sukayi,dan kobasu tambaya ba,sunsan wanna shine baffan fattunsu.
Adeeb kansa saida yaji kwalla ta cika masa ido,dan tausayin tsohon da yadda ya koma.

Horn din da motoci ke musu ne ya dawo dasu cikin hayyacinsu,dan tuni an janye motar data haddasa go slow ɗin,dan haka cikin hanzari suka shige mota dan ba mutane hanya.
Motar su fattu baffa ya shiga,su Sultan ma suka koma cikin tasu ,sannan suka bar gurin.

Kai tsaye gidan da suka sauka suka koma,dan yau suke don komawa Ghana,
Fattu sai murna take daga ga baffanta.
Wanka kawai suka bari baffa yayi,aka bashi wasu kayan ya sanya,kafin suka daga sai Ghana....

Masu karatu bari muyi musu rakiya zuwa ghanar muma.



Ina kuke
Masoya anty mammy?

Albishirinku,ina mai farin cikin sanar daku,sabon littafina mai suna RAINON DAWA,yana nan akan hanya,da zarar mun kammala MACIJINE,hmmmm
Daga jin sunan kinsan ba magana.

Karku bari abaku labari.
Ga mai bukata ,zai iya biyan kudinsa tun yanzu,domin nan da kwana uku zaku fara samun wannan kayataccen labarin na RAINON DAWA.

akan fashi mai sauki,

Normal group 300

Special group 500

Sannan akwai manyan mata dake son atura musu private to kuma ga naku farashi,1000
Dan haka saina jiku,

Acc. No.
Saratu kabir
A.u.b
2215749011


Saiku nuna shadar biya ta wannan no.
08148360851


Saina jiku,masoya.

Show ne your love akan novel ɗi Nan,
😍😍😍🥰🥰🥰🥰

Mrs babi ce💘💘
[8/29, 10:26 AM] Aishat Anty: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄



MACIJI NE🪱🪱🪱


Na mammy kabeer
(Anty mammy)



Elegant online writers📚📚


Free book

Page 93/94





_______________Ko a cikin jirgi fattu na kusa da baffanta,wanda yayi tsuru cike da tsoron jirgin,dan kuwa wannan shine karon farko daya hau jirgi.amma haka fattu ke kwantar masa da hankali har suka ƙarasa Ghana.
Part guda aka warewa baffa wanda ke dauke da duk wani kayan more rayuwa.baffa ya cika da farin cikin ganin irin rayuwar jin dadin da fattunsa keyi.abinci kala kala aka ajiye masa,har yama rasa wanda zaici.haka fattu keta zuba masa abincin tana tura masa.

Saida ya huta sosai nutsuwarta ta dawo jikinsa, sannan aka taru apart din da aka saukeshi, har Sultan Habib.godiya suka farayiwa baffa,bisa irin taimakon da yayiwa rayuwar yarsu,sannan suka ce suna bukatar yayi zamansa anan gurinsu,tunda bashi da kowa acan Nigeria.
Kuka kawai baffa keyi na gani yadda bayin Allah nan ke karramashi, suna son ya kasance tare dasu,amma wadanda ya taso cikinsu,haka suka koreshi korar kare bayan sun karbe masa dukiya.
Fattu ce ta dan turo baki tana kallon innarta da mahaifinta,kafin tace "Ni gaskiya ban yarda baffana ya zauna anan ba,tare zamu tafi dashi can gida,bana son yayi nesa dani,kuma shima yafi son zama kusa da fattunsa ko baffa"fattu ta faɗa cikin salon shagwabarta.

Murmushi baffa yayi,yace kwarai kuwa fattun baffa,duk inda kike to Nima Ina can koda kuwa cikin dokar dajine"baffa ya faɗa cikin murmushi.
Dariya sukayi suma,kafin mahaifin fattu yace "wato dai zara kin kwace mana baffanki ko?"ya faɗa da murmushi akan fuskarsa.
Dariya fattu tayi kafin tace "Allah ba haka bane daddy nayi kewar baffana,kuma nima inason in kula dashi,kamar yadda ya kula da rayuwata abaya"
Jinjina kai sukayi gaba ɗaya,suna ayyana irin kaunar dake tsakanin fattu da baffanta.

Kafin su bar kasar Ghana saida mahaifin fattu ya mallaka wa baffa kanfaninsa na ƙera takalma da jakunkuna,ya maida sunan sa akan takardun kamfanin,sannan ya bashi gida,wanda idan yazo zai rinka sauka aciki sannan ya damkawa fattu takardun gida dana kamfanin,harda mukullin sabuwar mota yar yayi.
Kuka sosai baffa yayi yana godiya,fattu ma tayi matukar murna sosai.adeeb kam godiya yayiwa Sultan habeeb,haka innar fattuma ba'a barta abaya ba,dinkuna ta sanya aka yiwa baffa,na gani na faɗa, masu kyau da tsada.sosai baffa ke yaba karamcin iyayen fattu,ba abinda zaice saidai Allah ya saka musu da aljanna.

Washe gari kuwa jirginsu ya daga zuwa Misra,fattu harda kukan rabuwa da yan uwanta,haka innarta ta cika ta da kayan gyara kala kala.
Wani ƙayataccen bangare su fattu suka sauka,wanda bayan tafiyarta Ghana ,Adeeb sanya aka kera musu.tsyawa fadar irin tsaruwar da bangaren yayi abune mai matukar wahala.kallo daya zakayiwa gurin kasan an kashe kudade makudai.

Baffama bangare guda aka ware masa inda zai zauna.haka yasha kyaututtukan gurin iyalan Adeeb,sannan shima Adeeb ya ba baffa kanfaninsa na motoci,baffa neman zaucewa yayi da irin wannan kyautukan da ake ta bashi.
Sosai ake girmama baffa cikin fadar,dan kowa yasan shidin waye.
Cikin lokaci kalilan baffa ya wanke yayi fes dashi,masha Allah kyakykyawan bafillatani,yayi kiba ya koma Alhaji sosai.ba jimawa suka shirya shida Adeeb da fattu dasu nanny sukaje suka sauke farali.
Sun dawo da kwana uku aka shirya gagarumin taron nadin Adeeb matsayin sarki.sannan ranar za'a gudanar da bikinsu shida fattu.
Anyi taro na ban mamaki wanda saida ya girgiza duniya,taron daya hada sarakunan hasashe daban daban,daga turawa,larabawa zuwa hausawa,ba kalar mutanen da babu agurin.
Taro yayi taro,an nada Adeeb matsayin sarkin misra,SULTAN ADEEB MUHAMMAD ASHRAF.
haka aka kammala taro ya tashi lafiya,kuma ranar Adeeb ya mallaka fattu dankareriyar mota mai shegen tsada da kyau,sannan ya mallaka mata kamfaninsa wanda ake hada mayukan shafawa na mata da kayan kwalliya.
Murna dai agurin fattu ba'a cewa komai.

Sati biyu da nada Adeeb matsayin Sarki,fattu ta kama laulayi, wayyo kuzo kuga murna gurin bayin Allah nan,haka nanny ta zage tana kula da fattu,ita da amma,suna bata gata da kulawa sosai,haka uban gayya,dan har kuka yayi lokacin da labarin cikin fattu ya sameshi.kuma yayi mata alƙawarin idan ta haihu ta zabi inda take son zuwa yin karatu.

Cikin fattu nada wata biyar aka yi auren tareeƙ da wata yar uwarsa,rana daya aka daura auren dana Rashad,anyi biki na kece raini,su fattu sune akan komai na biki, zakuyi mamaki yadda fattu ta zama babbar mace,tayi mugun kyau har ta gaji,suna nunawa juna soyayya mai tsafta ita da Adeeb,yayin da suke rainon cikinsu cike da so da kauna.saidai fattu tana da girman ciki,dan yanzu haka inka ganta zaki tunanin cikin yakai wajen watanni bakwai, dan girmansa.

Komai yana tafiya daidai arayuwarsu fattu,basu da wata matsala yanzu,domin suna cikin aminci da kulawar yan uwa,sarauniya suhaimat da Sultan habeeb,sunyi matukar murna da samun cikin fattu,addu'oi kuwa,ba irin wanda fattu bata samu,domin takanas ake biyawamutane makka,dan suke suyi mata addu'a.

Lokacin da cikin fattu ya cika wata tara,ko tashi bata iyayi da kanta,saidai idan Adeeb ya tasheta idan tana zaune ko kwance,amma kasancewarta mai hakuri da kawaici,haka take daurewa tana nuna bata jin wahalar ciki,shikuwa Adeeb tausaya mata yake sosai.
Wata rana da safe suna barci nakuda ta kama fattu,aikuwa,nan da nan likitoci kwarraru,wadanda ke mata awo suka rufu akanta,cikin hikimar ubangiji,fattu ta haifi yaranta takwaye, mace dana miji masu matuƙar kama da Adeeb, kyakykyawa na ban mamaki.

Irin murnar da ahalin nan suka nuna abin ba'a cewa komai,ta ko ina zuwa ake ganin jarirai,ranar suna aka sanya musu sunan baffa dana Nazli,Abubakar,amma ana kiransu da Ameer da ameera.
Fattu ta sami alkairi sosai haihuwar yaran nan.dan motoci ma sun sami sama da guda sha biyar,banda gidaje da tsabar kudi.sai muce Allah ya raya twince.
Bayan suna da sati biyu aka daura auren baffa da nanny,bisa ga amincewarsu,bayan fattu tayi shawara dasu,ba nuna ja suka amince,dan dama sun kamu da son juna.

Ammi kullum abu sai kara lalacewa yake,hauka take tun ƙarfi,gaba ɗaya ta gama kwarzane jikinta,tananan kamar wata horuwa, tayi ta ihu tana yakushun jikinta.(ai dama ammi hausawa sunce idan zaka gina ramin mugunta ka gina daidai da kai,hakkin rayukan da kika kashema kadai sun isheki)
Waziri ma yana gidan yari,saidai shikam yayi ladama,ya koma ga Allah,kullum yana istugfari.
Yaran fattu sun taso cikin kulawa da soyayya,idan kun gansu gurin fattu,to nono kawai zata basu,dan tuni ta fara karatunta ,tace anan gida zatayi karatu,bazata je ko ina ta bar mijinta ba.

Abin sai son barka,rayuwa tayi musu daɗi,suna zaune cikin kwanciyar hankali,fattu ta buɗe gidajen marayu ajahohin Nigeria sosai,ta taimakawa yan kauyen su,tayi musu makaranta, ga ruwa ya wadata,ta tallafawa mabukata, gaba ɗaya sunyi nadama abinda suka yiwa fattu da baffanta,dan lokacin da baffa yaje basu ganeshi ba,haka gwogwgo hansai tayi ta kuwa wai ya maidata dakinta,dariya kawai yayi tare da bata makudan kudade kafin ya bar kasar.

Amare da angwanye ma suna zaune cikin aminck da soyayya,yayinda ko waccensu ke dauke da yaron ciki,saidai muce Allah ya raba lafiya.

Fattu ce zaune akan kujera tana bawa ameer nono,yayinda Adeeb ke gefenta riƙe da ameera,kallonta yeke cike da ƙauna da sha'awa,yadda take shayar da yaron cikin nutsuwa.
Ajiyar zuciya yayi tare da faɗin "Alhamdullah ,Allah na gode maka kacikani da ni'imarka ta ko ina ,ka bani mace mai hankali da nutsuwa,sannan ka hadamin kan ahalina,ka bani yara kyakykyawa har biyu a lokaci daya,Allah Nagode maka"Adeeb ya faɗa cike da kushu'i yana mai jin dadi cikin ransa.

Murmushi fattu tayi tare da kamo hannunsa tayi kissing, sannan ta Dora kanta akan kafadunsa, tace "Ina sonka mijina kaine farin cikina,kuma rayuwata,Allah ya raya mana yaranmu bisa hanya madaidaiciya"
"Ameen Hulwa ana ahubbikteeer Hulwa anti sururi"ya faɗa yana mai kara rungumeta ita da yaran ajikinsa.


Tammat bi hamdillah.anan na kawo karshen wanna littafi Mai suna MACIJI NE.


Jinjina gareka mijina,na gode da gudunmawarka gareni,Allah ya bamu zaman lafiya,ya raya mana zuri'a.
Much love.


Godiya ta musamman gareki,maman nafi,na gode sosai da gudun mawarki akan wannan littafi.

Gaisuwa gareku macijine fans inq kaunarku.

Jinjina ga elegant online writers,Allah ya hade kanmu.

Ina godiya gareku yan uwana,da addu'ar ku gareni 🫠🫠🫠

Allah ya sa mu amfana da darasin dake cikinsa,muyi watsi da sharrin dake cikinsa.
Allah ka yafe mana kuraruranmu,kasanya imaninmu ya nunku fiye da nada.

Godiya agareku masoyansa ,da kukayi ta bibiyar wannan littafi,tun daga farko har karshe,Allah ya hadamu gidan aljanna.
Sai mun haɗe daku cikin sabon littafina
RAINON DAWA.
********************** ? **************************
********** Ai Hausa Novels ****************
*************************? **********************

DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog.

Visit > https://www.aihausanovels.com.ng

Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post.

Email > aihausabooks@gmail.com

******* FOLLOW US ******

Facebook: Ai Hausa Novels

Twitter: Ai Hausa Novels

Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels



Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu.

********************** ? **************************
*************** Ai Hausa Novels ****************
********************** ? **************************


Ga mai bukata,zai fita kudinsa kamar haka.

Normal group 300₦

Special group 500₦

Manyan mata masu bukata ta private,kuma ga naku1000₦

Zaku biya ta wannan acc. Din.
Saratu Kabir
U.b.a
2215749011.
Evidence of payment
08148360851

Saina jiku masoya.

Show me You love,
Kuyi payment na wannan littafin.💘💘💘
Kada kusake baku labari.
Saina jikiku.

Takuce har kullum anty mammy.

Mrs babi💘💘
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya

Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,

Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490

A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,

Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu

Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC

Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services

Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us

Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it

Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT

This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login