Showing 18001 words to 20356 words out of 20356 words
shi?”
106
jihadi
Koda jin wannan tambaya sai Boka
Aulad ya ja numfashi ya ajiye sannan yace “Ai har
abada jarumai basa qarewa a cikin duniya sai mu
lalubo wata, ina son ku barni mini komai a hannuna
zan san abin da zan yi.
A yau xin nan zan kawar da wannan
amarya ta sarki cire silin gashi daga cikin tandun
mai yafi wannan aikin sauqi a wajena, tunda kun
sani cewa babu wani mahaluki daya fini samun
aminci a wajen sarki”.
Koda jin wannan batun sai farin ciki ya
lulluve dukanin bokayen suka kama yiwa Boka
Aulad jinjina cikin farin ciki gami da samun
nutsuwa.
A can filin gidan sarauta kuwa bayan an
gama xaura aure sarakai da manya baqi suna zuwa
su taya shi murna, kuma suna bashi kyaututtuka a
lokacin da amaryarsa ke tsaye daf da shi, sai ya lura
babu boka Aulad a filin gaba xaya. Hakan nan
‘yarsa Gimbiya Zuhaira ma bata zo ba.
Koda ya sake hangawa ko ina sai yaga
ashe gaba xaya bokayen qasar ma basa nan, nan
take hankalin sarki masrud ya dugunzuma ainun ya
aiyana a cikin ransa cewar lallai Boka Aulad yaci
107
jihadi
amanarsa kuma akwai wata maqarqashiya da yake
shirin tafka masa, shi da sauran bokayen.
Nan take sarki masrud ya kirawo sarkin
yaqinsa yace da shi, maza kasa a rakani izuwa
turakata kuma daga yau kada a sake barin kowa ya
shigo inda nake ko a inda amaryata take koda kuwa
Boka Aulad ne, kai kaxai na yarda da ka shigo
turakar mu yi magana.
Sarkin yaqi ya risina ya ce “An gama ya
shugabana”.
Nan take sarki masrud ya kama hannun
amaryasa Muzainat suka nufi cikin gidan sarauta
dakaru sama da miliyan xaya na mutane da aljanu
na take masa baya.
A daidai wannan lokacin ne Bola Aulad
da sauran bokayen suka dawo filin fadar koda Boka
Aulad ya hango sarki da amaryarsa za su shige cikin
gidan sarautar sai ya rugo da gudu ya nufi inda sarki
ya ke da nufin ya shiga.
Kwatsam sai Boka Aulad yaga sarkin
yaqi ya sha gabansa cikin fushi Boka Aulad ya dube
shi yace “Wane irin shirme ne haka zaka zo kasha
gabana alhalin kasan cewa sarki baya son na gusa
daga kusa da shi daidai da tsawon rabin sa’a”.
108
jihadi
Koda jin haka sai sarkin yaqi ya yi xan
guntun murmushi yace.
“Ai wannan da ne, yanzu nan sarki ya
bani umarnin cewa kada na sake barin kowa ya je
inda yake, koda kuwa kai ne”.
Koda jin haka sai ran Boka Aulad ya
vaci ainun ya dakawa sarkin yaqi tsawa yace “Wai
shin ni kakan ka ne har da zaka zo mini da maganar
wasa”.
Da jin haka sai sarkin yaqi ya turvune
fuskarsa yace “Na tava yi maka wasa ne? ko kuwa
zan yi wa sarki qarya ne saboda kawai biyan wata
buqata tawa? Inda sarki bai sauya ra’ayinsa ba ai
babu yadda za a yi ya tafi ya barka. Ni ina ganin
sarki yana zarginka da wani laifi don haka kasan
hanyar da zaka bi ka gyara tsakaninka da shi”.
Koda sarkin yaqi ya zo nan a zancensa
sai hankali Boka Aulad ya dugunzuma ainun fiye da
koyaushe ya dubi sarkin yaqi cikin alamun matuqar
damuwa yace.
“Dole ne naga sarki yanzu domin na
hana shi Tarawa da wannan amaryar tasa domin
kuwa akwai babbar matsala, abin da nake so da kai
shi ne ka yi min jagora izuwa ga sarki yanzu nan
kafin lokaci ya qure”.
109
jihadi
Sarkin yaqi ya girgiza kai yace.
“Ba zan iya ba, domin ni ma idan na
kaika gare shi zan iya rasa matsayina gaba xaya”.
Koda jin haka sai Boka Aulad ya dakawa
sarkin yaqi tsawa, a karo na biyu yace.
‘Shin ka manta ne cewa ni da kai duk
munyi rantsuwa da girman abin bautarmu cewa
zamu sallama rayuwarmu da komai na mu domin
mu kare wannan gidan sarauta na mu da qasar gaba
xaya.
Na rantse da girman iyayena idan ban
hana sarki taraiya da wannan amarya tasa ba sai
mulkin ya suvuce masa gaba xaya domin ita
amaryarce zata haye karagarsa kuma ajalinsa a
hannunta yake, ta yaya muna ji muna gani za mu bar
‘yar almajiri mara cikakken asali zata zo ta karvi
mulkin qasar nan dare xaya?
Sa’adda Boka Aulad ya zo nan a
zancensa sai hankalin sarkin yaqi ya dugunzuma
ainun ya yi shiru yana tunani da nazari har izuwa
tsawon yan daqiqu ya rasa abin da zai ce daga can
sai ya xago kai ya dubi Boka Aulad yace.
“Tabbas dole ne na baka haxin kai xari
bisa xari domin ganin mun ceci rayuwar sarki da
kuma darajar qasar nan ta kowane hali, amma ka
110
jihadi
sani cewa tsalle xaya shi ke jefa mutum a cikin
rijiya, gaggawa a cikin wannan al’amari a gare ni
yana da matuqar haxari, ka tuna cewa kai fa boka ne
wanda babu kamarsa a qasar nan don haka ka yi
amfani da qarfin sihirinka wajen magance wannan
matsala”.
Boka Aulad ya yi ajiyar zuciya cikin
alamun takaici yace “Ai in da zan iya yin hakan da
tuni na yi ba sai na tuntuve ka ba, ai idan ka ji Sarki
Yaki yace a yi wasan jifa to lallai ya taka hoge, ka
tuna cewa duk faxin qasar nan ba a sami budurwa
da ta amince za ta auri sarki ba a cikin wannan
larura tasa face Muzainat kasan kuma lallai akwai
abinda ta taka.
Bisa wannan binciken da na yi a kanta na
gano cewa akwai wani babban sihirin tsafi a jikinta
wanda duk wanda ya tunkareta da nufin ya hallakata
mutuwa zai yi, maganinta kawai shi ne sarki ya fasa
aurenta kuma ya nisanta da ita.
Tun da ba zamu iya tava Muzainat ba ai
za mu iya raba sarki da ita, ni yanzu ba ni da sauran
aminci sarki kai kuwa kana da shi, ka yi amfani da
wannan dama a yau xin nan kafin sarki ya shiga
xakin amaryarsa kasa a sace shi a sirrance mu fitar
111
jihadi
da daga cikin gidan sarautar gaba xaya, mu kaishi
can gidana na bayan gari mu voye shi.
A sannan ne zamu yi tunanin hanyar da
zamu bi mu fitar da Muzainat daga cikin gidan
sarautar gaba xaya a cikin ruwan sanyi”.
Lokacin da Boka Aulad ya zo nan a
zancensa sai hankalin sarkin yaqi ya qara
dugunzuma ya shiga cikin halin wasi-wasi,zullumi,
fargaba da zargi kawai sai ya xago kai ya dubi Boka
Aulad cikin alamun rashin yadda yace.
“Duk waxannan abubuwan da ka shirya
mini yanzu sunyi kama da hanyoyin da ake bi a
shirya juyin mulki, da wace hujja zan yi amfani na
gamsu cewa ba juyin mulki kake shirin yiwa sarki
ba?”
Boka Aulad ya dakawa sarkin yaqi tsawa
a karo na uku yace “Yau shekara ta arba’in ina bauta
a wannan gidan na sarauta na yi bauta ga mahaifin
sarki masrud da kakansa duk tsawon waxannan
shekarun ba a tava kamani da laifin cin amanarsu ba,
duk abinda nake nema na jin daxi duniya ina da shi
a can fada ta ina da dukiya mai tsananin yawan da
ban san iyakar adadin yawanta ba, ina da matan aure
guda tamanin da xaya, ina da ‘ya ‘ya arba’in da biyu
fadata ta ginu kuma ta qawatu fiye da wannan
112
jihadi
wacce muke ciki ina da fadawa kuyangi,barori da
dakarun tsaro waxanda suka ninka na wannan fadar
sau uku, a kan wane dalili zan yi sha’awar wannan
fada ko karagar cikinta?”.
Koda sarkin yaqi ya ji waxannan
tambayoyi da Boka Aulad ya yi masa sai jikinsa ya
yi sanyi matuqa ya rasa abin da zai ce daga can sai
ya xaga kai ya dubi Boka Aulad yace.
“Kafin dare yayi akai amarya xakin
angonta zan san abin da zan yi akai kuma zan
nemeka na sanar da kai komai”.
Koda jin haka sai Boka Aulad yayi
doguwar ajiyar zuciya, sannan yace “Lallai ka
tabbatar da cewa ka yi duk motsinka kafin a kai
amarya xakin sarki”.
Koda gama faxin haka sai Boka Aulad
ya juya ya yafito wani hadiminsa da hannu take
hadimin ya janyo dokin Boka Aulad da sauri ya
kawo masa.Cikin alamun fushi Boka Aulad ya kama
dokin nasa yah aye ya zabureshi da gudu ya nufi
hanyar fita daga cikin gidan sarautar gaba xaya,
aikuwa sai wasu dakarun Boka Aulad kimanin su
arba’in bisa dawakai suka rufa masa baya.
Koda jama’ar gari suka ga Boka Aulad
ya fice daga ciki gidan sarautar gaba xaya sai suka
113
jihadi
cika da tsananin mamaki saboda an san cewa dare
da rana yana tare da sarki baya yarda ya yi nisanta
da shi,shi ma sarkin haka fa aka fara tsegumi, kowa
ya riqa faxin albarkacin bakinsa.
Tun lokacin da Gimbiya Zuhairat ta
samu labarin mahaifinta da Muzainat hankalinta ya
gama dugunzuma. Tasan dai tunda mahaifinta ya
shiga cikin wannan mayuwanciyar cutar data
kamasa dare xaya. Kuma gashi bokaye sun kasa
warka da shi.
Don haka tabbas akwai wani abu a qasa
amma kuma abu xaya yasata farin ciki da auren ya
kuma saka duka baqin cikinta gushewa shi ne. A
yanzu tasan tabbas wannan ciwon na mahaifinta duk
lokacin daya ta shi to zai iya shaqe muzainat har sai
ya kasheta. Amman duk da haka sai ta kirawo wani
amintaccen bawanta tace ya je ya saka mata ido
akan duk abinda yake gudana.
**
Al’amarin sarki masrud kuwa lokacin
daya kama hannun amaryarsa Muzainat ya yaja ta
izuwa cikin gidan sarauta bai zame ko ina ba sai
cikin wani babban falo wanda girmansa ya kai na
fadar gidan sarautar. Babu komai a cikin wannan
114
jihadi
falo face kujeru da tebura na cin abinci birjik da
yawa iya ganin mutum.
Suna shigowa cikin wannan babban falon
sai suka yi arba da gaba xayan sarakunan nahiyar
waxanda suka zo taya sarki masrud murna wannan
aure nas kowane sarki yana tare da matarsa a zaune
ga kayan ciye-ciye dana shaye-shaye, iri-iri babu
adadi akan teburin amma a saboda girmama sarki
masrud ko ruwansha babu wanda ya xauka ya kai
bakinsa sai ya iso tukuna.
Koda sarakuna da matayensu suka ga
sarki masrud tare da amaryarsa sun shigo cikin falon
sai gaba xayansu suka miqe tsaye suna kama yi
masa tafi ya yin da waxannan sarakunan suka yi
arba da amaryar Muzainat a cikin gagarumin ado da
aka cava mata sai dukkaninsu suka ximauce bisa
ganin irin tsananin kyawun da Allah ya bata.
Nan fa wasun su suka fara munafunci da
tsegumi ga ‘yan uwansu sarakuna.
Sarkin birnin kirishna ne ya dubi sarkin
birnin lamras ya yi masa raxa a kunne yace “Tabbas
banga laifin sarki masrud ba da ya auri wannan
yarinyar ‘yar almajiri saboda ko ni ne ba zan bari ta
wuce ni ba”.
115
jihadi
Koda jin haka sai sarki lamras ya yi
murmushi yace “Amma ba don kyaunta ya aure ta
ba an ce saboda kawai zata iya bashi labaru ne masu
daxi waxanda za su sa hankalinsa ya kwanta ya
daina hauka da shirme, abin tambaya a nan shi ne a
ina wannan yarinya zata iya samo labarai masu daxi,
kuma masu ban al’ajabin da za su iya saita wannan
mahaukacin sarki?”
Koda gama faxin hakan sai ga sarki
masrud tare da amaryarsa sun iso daf da sarki
lamras,kawai sai sarki masrud ya dubi sarki Lamras
yace.
“Na yi murna da ganinka a wannan biki a
zatona ba zaka zo ba saboda laifin da na yi maka
sa’adda muka haxu a bikin naxin sarautar birnin
sin”.
Koda jin haka sai sarki lamras ya kama
yaqe gami da murmushin dole muryarsa na rawa
yace.
“Haba ya kai sarkin sarakuna ai ban isa
na qi amsa gayyatar bikinka ba”.
Ita kuwa Muzainat sai ta dube shi tace
“Zaka sha mamaki idan ka ji irin labarum da zan
baiwa sarki daga daren yau, zaka ji daga bakinsa”.
116
jihadi
Koda jin wannan batu sai jikin sarki
lamras ya kama tsuma saboda tsananin mamaki
gami da razana.
Daga nan suka yi gaba abinsu haka dai
aka ci gaba da gudanar liyafar bikin na su.
Har tsawon wani lokaci kafin aka
kammala sarki masrud da amaryasa suka wuce cikin.
Da shigarsu sai ta fahimci kan sarki ya
fara ciwo nan da nan idanunsa suka juye ya fara
tangaxi.
Koda ganin haka sai ta fahimci cewa
lallai ciwon sarki ne zai tashi a daidai wannan
lokacin maimakon ta ji tsoro ta nisanta da shi sai ta
janyo shi jikinta ta shiga yi masa raxa a kunne tana
mai cewa.
“Ya kai wannan sarki mai daraja ka yi
sani cewa an tava yin wani gagarumin sarki a birnin
kisra wanda ya shekara xari da ashirin akan karagar
mulki batare da ya tava fuskantar wata matsala ba a
rayuwarsa amma a karon banza aka rabashi da mulki
yana ji yana gani da qarfinsa da lafiyarsa ya dawo
bawan sarkin da ya hau karagar alhalin da shi sabon
sarkin ya kasance bawansa kuma ko kaxan ba shi da
wata alaqa da gidan sarautar”.
117
jihadi
Koda jin wannan batu sai sarki masrud
ya ji kansa ya wattsake take kuma ya ji kansa ya
daina ciwo don haka sai ya dubi Muzainat cikin
tsananin zaquwa yace, ta yaya wannan al’amari ya
faru, maza ki bani wannan labari yake tauraruwar
taurari.
Sa’adda Muzainat taga sarki masrud ya
zaqu da son jin wannan labarin sai ta qyalqyale da
dariya tace.
“Ai kuwa akwai xinbin darasi a cikin
wannan labarin kuma gashi yanzu dare ya soma yi,
ina ganin har gari ya waye ba zan iya gama baka shi
ba”.
Da jin haka sai jikin sarki masrud ya
kama tsuma zuciyarsa ta kama tafarfasa kamar zata
qone, kawai sai ya zare takobinsa ya dakawa
Muzainat tsawa yace.
“Maza ki ci gaba da ba ni labarin da kika
soma ko kuma yanzun na sare miki kai”.
Koda jin haka sai Muzainat ta dubi sarki
masrud cikin alamun tsoro tace.“Kwantar da
hankalinka ya kai mijina ai yanzu nan zan ci gaba da
baka wannan labarin” Muzainat ta yi doguwar ajiyar
numfashi sannan tace.
118
jihadi
“Wannnan abinda na karanta maka shi ba
komai bane facce hanyar tsira, wanda addinin
gaskiya ya zo da shi, ta hannun manzo mu Annabi
Muhammad (s.a.w) shi ne alqur’ani littafin daya fi
komai daraja da qima da xaukaka. Qissar dana baka
ta Anabi Musa ce da fir’auna. Ka kuma ji yadda
qarshen sa ya kasance. Don haka kaima matuqar
kana son warkewa duka daga cutarka, haka nan ka
zamo gagabadau na a cikin sarakuna to ka zamo
ma’abocin addinin”.
Koda sarki masrud ya ji haka sai ya yi
murmushi, bai ce mata komai ba ya nemi gefe guda
ya kwanta. Bai jima da kwanciya ba bacci ya xauke
shi. Washe gari da safe sarki ya tashi cikin qoshin
lafiya. Amma duk da haka sai yace Muzainat ta qara
karanta masa wani vari na littafin nan ta sake
karanta masa. Bayan ta gama yace mata zai fita fada
don haka ta shirya tare za su fita.
Nan ya shirya ya fita cikin taqama ta izza
da isa, jama’a suka cika da mamakin ganin sarki ya
fito cikin qoshin lafiya, nan aka shiga murna. Daga
nan ya saka aka tara masa mutane haka yasa aka
kirawo masa ‘Yarsa Gimbiya Zuhairat ya kwashe
labarin duk abinda ya faru ya sanar musu. Ya kuma
119
jihadi
tabbatar musu cewar shi ya aminta kuma daga yau
ya zamo ma’abocin musulunci.
Gimbiya Zuhairat ta dubi Muzainat cike
da mamaki “Wanne sihiri ki ka yiwa mahaifina?” Ta
yi murmushi kafin tace mata.
“Nima kakana ne ya bar mun littafin
hikayoyi, a bayan na gama karance shi sai a qarshe
yace mun duk wannan labarin, su zame mun tsani na
shiga addini tsira shi ne addinin musulunci. Don
haka sai na saka aka riqa mun bincike akansa har
Allah ya haxani da mujaddadi Salhif shi ya ganar
dani abinda ban sani ba” Koda jin haka sai Gimbiya
Zuhairat ta yi murmushi tace mata.
“Nima na jima da amsar addinin
musulunci, tun ranar da mahaifina ya bani labarin
Barde Barhuzu da Jarumi Nusurul Ashman da
Gimbiya Ramlatul Auliya. Daga lokacin kuma na ke
roqon Allah ya ganar da mahaifina gaskiya, na
godewa Allah daya bayyana mana gaskiya”.
Nan jama’a suma suka amsa da cewar
sun ji sun aminta sun amshi addinin gaskiya.
Masha Allahu
QARSHE
120
jihadi
121