Showing 6001 words to 9000 words out of 26903 words

Chapter 3 - AUREN KATIN KASA

Start ads

02 Sep 2025

90

Middle Ads

wanda sai bayan mutuwar malam ya baiyyana, binta tayi rainon cikinta har wata tara sannan ta haife danta inda yaci sunan sa Aliyu haidar koda sammani yaso yasama yaron suna sai binta ta nuna tanason ta sawa danta suna da kanta aikuwa ya barta da abinta.

Badaru ya taso cikin koshin lapiya da son dan uwanshi Mustapha wanda shima haka Mustapha ya nuna mashi qauna sosai sun taso tare inda badaru keda shekara goma shi kuma Mustapha yanada shekara ashirin dama shekaru goma ne tsakanin su in badan an fada maka ba bazaka taba sani cewa ba uwa daya ce ta haifesu ba, suna kaunar junan su sosai inda aliyu haidar kuwa yakeda shekaru tara aduniya don kuwa badaru ya girmeshi da shekara daya, yanda Mustapha keson badaru kwata kwata baya yima aliyu wannan soyayar, dama gashi shi aliyu bashida hayaniya kuma bai damu da sha’aninsu ba, lokacin da badaru ya kammala secondary school dinshi alokacin shikuma Mustapha ya aje bokon ya shiga kasuwanci inda allah ya buda mashi lokaci guda ya zama tambatsentsen dan kasuwa mai shegen kudi ganin haka yasa badaru ya bishi zuwa kano anan ne ya samu admission ah BUK inda ya fara karanta architecture,Mustapha kuwa anan kano ya hadu da kareema awajen wani taron yan kasuwa tazo tare da baban ta nan kuwa taji itama Mustapha ya zauna mata bayan yan watanni akayi aurensu. badaru yaro ne mai basira da son mutane cikin kankanin lokaci BUK tasan da zaman badaru inda yana kammala karatunshi yayi bautar kasa anan ne wani company suka daukeshi aiki ya zama babban mutun sbd irin kwazon da yake dashi wajen iya zane, har competition akayi na architects cikin ikon Allah shine ya zama gwarzo afadin Nigeria anan ne duniya tasan da badaru daukaka tazo mashi har Allah ya daga shi ya fara tafiye tafiye,alokaci yana da shekaru ashirin da biyar aduniya anan ne yayi tafiya izuwa morocco domin yin wani project anan ne allah ya hadashi da shuwaira, shuwaira marainiyace batada iyaye sun rasu amma tana tare da kanin mahaifinta da matarshi waenda Allah bai taba basu haihuwa ba, shuwaira haifaffiyar yar morocco ce irin black beauties din morocco’s tana aiki ah wani private hospital, amatsayi nurse, ranar da suka fara haduwa da badaru kuwa ranar yaje overall body check up domin office din da zaiyi aiki dasu ah morocco ba a fara aiki dasu saika kawo health history dinka, aranar kuwa ta kasance duty din shuwaira, bayan ta shigo patient scanning room kanta akasa tana karanta information dinshi, muryarta ce ta dawo dashi daga danne dannen wayan da yake yi, wani irin melodious voice yaji akunnan shi ‘’ hey mr badaru how are you today? I will be the nurse to check you up today’’, da sauri ya dago kanshi domin jin me daddaden muryar nan, ya shagala da kallonta saidatayi gyaran murya bayan itama ta gama kallonshi sannan tace ‘’sorry i’m i in a wrong room?’’ cikin inda inda da kuma shauqin ganinta yasa badaru cewa ‘’no noo you’re in the right room, right close to my heart, ganin yanda badaru ya lalace da kallonta yasa tayi dariya tace ‘’kallon ya isa haka karkasa na kasa aikina mana’’ aikuwa kunya ta lullube badaru baisan lokacin dayace mata ‘’mss na kasa daina kallon ki don allah ki bani magani ko zan iya cire idanuna akanki, ganin badaru na neman zaucewa yasata cewa “lallai kana da enough time yau dinnan don inaga kwana zamuyi ahaka you’re not ready for the full body scanning, ganin zata fice yasashi rike hannunta,

Chapter 11-12



ganin zata fice yasashi rike hannunta, juyowa tayi zatayi Magana ya katse ta da cewa ‘’I’m sorry my lady let’s begin with the scan,ganin how cool and gentle badaru keyi mata magana sai taji ya burgeta, preparing dinshi tayi bayan ya chanza outfit dinshi zuwa na asibiti anatse ta taimaka mashi ya shiga cikin body scanning machine din, saida ta tabbatar ta duba lafiyarshi tukunna tayi mashi sallama, zata wuce Kenan yace ‘’ right now at this moment I want to be the only man in your life that will love and take care of u’’ ita abima har mamaki yake bata shiko wannan daga haduwa da ita bai santa ba bata sanshi ba kallonshi kawai tayi sai tayi murmushi ta fita. Koda badaru ya koma gida hankalinshi sam baya jikinshi tunanin shuwaira kawai yake yi ta tafi da imanin shi yanda take magana da yanda take al’amuranta gaba daya ya tafi dashi, haka dai ya lallaba kullum saiyaje asibitin nan, da farko shuwaira bata amince mashi ba daga baya kuma ta fara tausaya mashi harta fara sonshi. Ganin irin soyayyar dake girma tsakanin shuwaira da badaru yasa iyayenta wanda suke riketa suka zauna da badaru domin yayi masu bayanin asalinshi,koda yayi masu bayanin asalinsa Sai uncle ya aminta dashi kuma yayi alqawarin aura mashi shuwaira tunda itama ta nuna tanaso, dukda anty dinta matar uncle bata soba,bayan Yan watanni uncle ya aura ma badaru shuwaira amma da sharadin bazai koma gida ba zai zauna da ita ah Morocco, nan take badaru ya amince da sharadin su. antyn ta bataso hakan ba sbd tana tsoron gujewa matsala don lokacin da akayi auren babu wanda yazo daga bangaren badaru. Badaru kuwa babu wanda ya fadamawa cewa yayi aure saida suka shafe shekara kunsan biyar alokacin ko batan wata shuwaira bata samu ba suna zaman lpy sosai da ita da badaru dukda maganar danginsa yana damunta sosai, tunda sukayi aure saidai ya shirya ya je Nigeria yayi yan kwanakinsa ya dawo. Lokacin da badaru ya sanar da Mustapha auren da yayi a morocco ba karamin zafi Mustapha yaji ba ayanda ya dauki dan uwan nasa har yayi aure amma bai fada ma kowa ba aciki kuwa harda mahaifiyarshi larai wadda suke zaune anan katsina da ita da binta sai kaninsu badaru aliyu haidar.

Bayan komawar badaru da wata daya yaji duk zaman morocco ya chanza masa yaji baya qaunar zama ah garin haka yasa ya samu shuwaira da batun komawa Nigeria, duk da shuwaira tana shaáwar ganin dangin badaru amma hakan bai sata jin babu dadi ba zatabar uncle dinta, bayan yan kwanaki badaru ya lallabata suka shirya sukayima su uncle sallama sannan suka taho Nigeria. Dirar su Kenan ah aminu kano international airport kano badaru ya dauki waya don ya kira dan uwansa, nan ya sanar dashi sun iso, minti kadan saiga Mustapha, Mustapha yaji dadi ganin badaru da iyalinshi, direct gidan Mustapha suka wuce inda anan suka huta sannan sukaci abinci aka kaisu dakin da zasu zauna, shuwaira dai taji dadin tarbar da akayi masu amma duk bata cikin natsuwar ta domin tunda suka iso ta fara jin fargaba hankalinta duk ba ajikin ta yake ba amma dai haka ta daure bata nuna ba, bayan yan kwanaki suka shirya harda iyalan Mustapha wato haj kareema da yayanta uku, wahab, Ibrahim da Muhammad.

Koda suka isa katsina ba karamin mamaki Mustapha yayi ba ganin yanda larai batayi ma badaru fadaba akan auren da yayi, abunda baisani ba ashe ya riga da ya fadi ma mahaifiyarshi komai agame da batun aurenshi kuma tasaka mashi albarka sannan ta umarceshi da ya dungo boye duk wani abun alkairinsa da zai faru dashi, bai dauki zancen baba larai da komai ba shiyasa bai nuna damuwa ba kuma shiyasa bai fadama kowa ba ciki kuwa harda dan uwansa Mustapha.

Free page….



Chapter 13-14



Cigaban labari…….

Sallan asuba da aketa kirane ya farkar da amra wadda ke kwance a kasa miqewa tayi sannan ta tattare kayan shimfidar datayi ta ninke komai sannan ta wuce toilet koda ta fito kwance ta tarar da salima sai salim agefenta, ahankali ta tako ta fara tashin salim…,’’salim salim tashi lokacin sallah yayi”.,..tashi yayi ya zauna sannan ya fuskance ta, yace ‘’ adda amra kin tashi ashe good morning bari na tashi salima’’ dakatar dashi amra tayi sannan tace ‘’ kyaleta zan tashe ta, ka wuce toilet kayi alwala saikazo muyi sallah ko”,

mikewa yayi sannan ya bude kofar toilet, saidata jirashi ya fito tukunna ta shimfida masu sallaya sannan suka tada kabbara, koda suka idar addua sosai sukayi dashi da ita, kallon salima yayi wadda ke baje tana barci sannan yace adda maisa salima bazatayi salla bane ita,? Kallonshi amra tayi sannan tace ‘’salim I will explain to you why salima is not praying but please not now saika girma for now idan nayi maka bayani bazaka gane me nake nufi ba but idan har kaga nida salima bamuyi sallah ba we have our own reason kuma addini yasan da haka kaji ko’’ nodding kanshi yayi sannan yace adda let be get back to sleep,’’ tashi yayi ya kwanta gefen salima itakuwa amra tattare kayan sallan tayi sannan ta wuce wardrop din su ta aje, doguwar rigace ta barci har kasa ajikinta sai hula, fitowa tayi direct daga dakinsu fitilun ko’ina a kashe yake ahankali ta karasa wajen switch din wutan ta fara kunnawa saidata tabbatar ta kunna wanda zata buqata domin gyare gyaren da zatayi sannan ta wuce cikin kitchen, kodata shiga kitchen din yana nan yanda ta bari fess fess,karasawa har cikin kichen din tayi sannan ta wuce store ta fara dibo abinda zata buqata wajen yin breakfast, saidata fara fere irish da doya sannan ta dora shi akan gas, fita tayi backyard ganin gari har ya fara haske yasa ta kwaso tsintsiya da mopper, sannan ta wuce cikin parlor, duk girman parlor nan haka ta share shi tsaf duk da babu wani datti saidata tabbatar ta gama sannan ta fara mopping din ko’ina.



Anaste ta kammala aikin ta sannan ta koma kitchen anan ta fara yan soye soye abubuwa data dafa sannan ta hada masu custard saboda tasan kananu yaran zasu buqata, sannan ta dafa ruwan tea. Wajen karfe 9 daidai suka fara sakko daya bayan daya, Khadija ce ta shugo kitchen jikinta sanye da kayan bacci riga da wanda kanta da ribbom kalar kayan jikinta ta daure yar jelar gashin nata, siririya ce batada haske sannan hancin ta yana nan anane kamar gutsirarren dankali😂, kodata shigo ko kallon amra batayi ba ta wuce wajen tabkeken fridge dinsu ganin haka yasa amra cewa good morning khadi, ko kallonta batayi ba ta bude fridge din ganin bataga abinda take nema ba yasata cewa, “ina avocado smoothie din danace ki dunga hada min duk safiya kina ajewa”??, kallonta amra tayi sannan tace, ‘’avocado dinne yakare shiyasa ban hada ba’’ ..tsaki kawai khady tayi sannan ta dauki bottle water ta wuce dining, ita kuwa amra qannenta ta zubama akula sannan ta aje agefe, mugs din shan tea ta kwasa sannan ta wuce dashi dining room, duk kowa ya hallara amma banda iyayensu mata, daga kan khady, Muhammad, amina, ishaq, jabir,jalal sai khamis da Khalil, halim ce kawai babu acikinsu sai kuma manyan yayyi wahab da Ibrahim wanda basa kasar ma kwata kwata.

Ka’idar gidance duk yaran kowa sai ya sauko anyi breakfast dashi gudun samun misunderstanding kuwa iyayensu basa saukowa saidai ko wacce ta dafa a kitchen din part dinta asama.

kowannan su yana zaune haka amra tazo daya bayan daya tayi serving dinsu, ishaq ne kawai ya bude baki yace mata ‘’thank you sis amra,’’ murmushi kawai tayi mashi sannan ta juya zata koma kitchen, tana gab da shiga kuwa tajiyo muryar halma tana sakkowa daga stair tana sanye da pink riga iya gwiwa,kallon amra tayi sannan tace ‘’ zaki tafi baki bani nawa breakfast dinba kosai na kira mummy?“juyowa amra tayi sannan ta fara zuba mata, ishaq kuwa tsaki kawai yayi, amina kam ko kallon inda take batayi ba,dukda itace akusa da halma .



Saidata sallamesu sannan ta wuce kitchen abunta aranta tana mamakin isa da suke nunawa, kamar basune suke wasa tare ba lokacin da iyayen su na raye lallai baka sanin mai sonka saika rasa gatanka aduniya, murmushi kawai amra tayi sannan ta wuce dakinsu,

Tana shiga ta tarar da su salim har sunyi wanka sun chanza kaya ita suke jira, aikuwa tana shugowa salim jikinshi har rawa yake wajen karban kulan data shugo dashi, waje ta samu ta zauna salima nayi mata sannu da aiki. Kallonta amra tayi sannan tace ‘’salima ku fara ci, ni yanxu agajiye nake zanje nayi wanka idan na fito sai inci nawa nima’’…kallonta salima tayi sannan tace adda zamu jira ki kiyi wankan’’, qwalalo ido salim yayi yace adda gaskia nikam bazan maki karya ba yunwa nake ji,’’ dariya suka fara mashi saida suka tsagaita salima tace “kai salim akwai dan banzan ci”, tura mashi kulan salima tayi sannan tace karba ka ci ka rage mana’’ amra kuwa toilet ta wuce ta watso ruwa sannan ta fito ta bude wardrob dinsu, doguwar riga ta dauko baka mai yan duwatsu ajikinta sannanta ta koma toilet anan ta chanza kayan sbd salim yana cikin dakin sannan ta dawo ta wuce wajen dressing mirror dinsu, dan roll on kawai ta goga sannan ta wuce wajen yan uwanta anan sukayi zaman su daga bisani kuma suka fuce gaba dayansu zuwa kitchen din, nan suka taya ta daura lunch harta kammala sannan suka jera a dining, daki suka koma lokacin ana kiran sallar azhar, sallah sukayi koda suka idar anan suka dinga jin fitar motoci da alamu ko wacce cikin matan ta kwashi yayanta sun fice abunsu, sukuwa su amra da kanneneta da basuda gata sai aka barsu da gadin gida, ganin zaman bashida ammfani yasa suka fito suka wuce compound din gidan anan ne amra ta tsunko masu guava suka wanke sukaci sannan su salim suka fara wasansu shida salima yana gudu tana binshi abaya ita kuwa amra kallonsu kawai take tana jin dadi aranta daga bisani kuma ta shiga tunanin rayuwar su, harga allah tana son kannenta sosai har cikin xuciyar ta kuma batajin zata iya nesa dazu, suna nan har aka kira sallar magrib sannan suka koma cikin gida, daki kawai suka wuce sukayi sallah, amra bata mayi tunanin dora girki ba saboda basuci na rana ba sannan kuma daman yau Sunday ayaune kuma baba rabi zata dawo mai’aikin gidan gaba daya, daman tana zuwa gida friday da daddare sannan ta kwana biyu sunday ta dawo da yammata cigaba da aikinta.

Free page….



Chapter15-16



Duk sanda mama rabi ta fi kuwa amra ce ke karbar duk wani aikinta harsai ta dawo sbd haj kareema ce ta shimfida wannan dokar akan cewa Yayan riqo bazasuyi zaman lalaci ba, ita kuwa amra ta gwammace tayi komai kannenta su zauna su huta kamar yanda sauran yaran gidan suma suke rayuwar su babu takura, shiyasa koda haj kareema ta kawo sabon rule dinnan ita kuwa amra dadin haka taji don kuwa ya taimaketa sosai, babu girkin da za ah nuna mata har matan gidan ma kuma bata sangarce ba itakeyin komai nasu a gidan, abu biyu ne kawai batayi musu, na farko bata zuwa part din kowa acikin su sannan kuma bata yi masu wanki kuma bata shiga part din mai gidan wato alhaji Mustapha, yaya awajen ubanta sannan kuma uba awajen su ayanxu ita da kannenta.

Suna nan zaune adaki ita da kanneneta suka fara jin saukan motocin gidan da alamu sun fara dawowa, har akayi sallan ishaï suna zaune ita da kannenta salima tana zanenta while salim kuwa books din shi ya dauko yana assignment,sallamar da akayi ne yasasu dagowa suna kallon kofar don ganin mai yin sallamar, mama rabi ce ta shugo da yar ledar kayanta ahannu fuskarta dauke da murmushi tace “salim na dawo”, da gudu kuwa ya tafi wajenta yana mama rabi allah yasa kin kawo min tsarabar raken danace maki,murmushi tayi mashi sannan suka karasa cikin dakin, kallonta amra tayi tare da salima sannan suka gaisheta, anan ta bawa kowa tsarabar shi ‘’kai salim ga rakenka, ke kuma salima dama goruba kikace min kina so toh ga naki’’ washe baki salima tayi sannan tace kaii mama rabi allah ya bar mana ke’’, …murmushi tayi sannan ta kalli amra

tace mutuniyar arziki matar manya ga farar kasar ki nan ke ko gajiya bakyayi duk sati idan zan tafi sai kin bani dari biyar na sayo maki saikace mai ciki ko gajiya bakyayi dashan wannan abar”…dariya amra tayi ta kalleta tace mama rabi ke bakisan kwanakin da nakeyi Ina tattala kudin break dina na school ba duk don na tara na baki ki sayo min farar kasar nan, aykuwa nagode yau naga har yafi na last week yawa, nagode sosai’’ karbar ledar amra tayi sannan ta bude ta dauka daya ta fara bantara tana wullawa abakinta, salima kuwa baki ya rufu sai faman gurzar goriba takeyi. Sallama mama rabi tayi masu sannan ta fice ta koma nata dakin dake opposite da nasu. Saida suka gama kusur kusur dinsu tukunna amra ta fita domin zubo masu abinci, anan ta tarar da ishaq, yana ganinta kuwa ya taho, kallonshi tayi sannan tace “bro ishaq yau baku wuni agida ba inata so ka koya min wani assignment da aka bamu a school kasan mun kusa gama exam din second term ni harna kosa wallahi na gama school dinnan wallahi wahalar damu suke yi sosai,’’ dariya ishaq yayi sannan yace sis idan kince kin gaji da school to ai kuwa daddy aurar dake zaiyi wallahi karma kiyi fatan ki gama school yanxu’’ turo baki tayi sannan tace ay kuwa babu auren da zanyi yanxu nida nake da burin zama babbar likita ay aure ba nawa bane’’



kallonta yayi sannan yace “nikam dan allah adama min oat mana dama mun dawo da yunwa naje sama don nayi wanka ina dawowa naga yarannan sun cinye abinci da kikayi kinsan kowa baya resisting abincin ki sis” dariya tayi sannan ta shiga dama mashi oat din sannan ta bashi wucewa yayi yanace mata ‘’Thanks sis nagaji yanxu gobe idan za ah sauke mu a school zan koya maki’’ murmushi kawai tayi aranta tana mamakin mutuncin ishaq sam babu ruwanshi bashida halayyar sauran yaran gidan, juyawa tayi sannan ta fara zuba masu abinci ita da kannenta, daki ta koma saida sukaci abinci sukayi nak ita da kannen ta sannan suka kwanta sbd su tashi da wuri.

Free page….



Chapter 17-18



Washe gari kuwa sunso su dan Makara, shaf shaf suka shirya cikin uniform dinsu

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login