Showing 30001 words to 33000 words out of 95534 words

Chapter 11 - GURBIN IDO COMPLT

Start ads

11 Aug 2025

612

Middle Ads

fuskarta ta fara da tafin hannunta bayan taji zuciyarta ta fara mata sanyi daga radadi da suyar da take mata.

"Kiyi haqurk,komai mai wucewa ne,watarana sai labari" daga kai tayi ta bi laila da kallo jin abinda ta fada,tasan wace ita ne?,tana tantama,inda tasan wace ita tatabbatar ba zata tsaya tana magana da ita ba,amma duk da haka a sanyaye sai tace

"Miyatti" murmushi laila ta sake

"Me kenan?" Murmushin da bata shirya masa bane ya qwacewa maimunatu,ta manta ba da daya daga cikinsu take magana ba

"Nace na gode" murmushi lailan ta sakeyi

"Babu komai" daga haka maimunatu ta juya tayi gaba,sai kuma a sannan fargabar kada inna taga dadewarta ta qara cikata,don haka saita qara sauri.

Bin maimunatu da kallo laila tayi har sai data bace mata,ta sauke ajiyar zuciya me nauyi,a yanzun tana jin zuciyarta ta gamsu dari bisa dari da daukar maimunatu da anni zatayi,saboda hakan tamkar wani babban jihadi ne a wajensu gaba daya,to amma kuma dai dai da qwayar zarra zuciyarta bata gamsu ko kuma kwanciya da qudurin annin na biyu ba,yaa ja'afar fa?,ya ja'afar take magana,ba khalid ba,ba kamal ba,bare jabir,ja'afar take cewa,saita girgiza kai kawai tana komawa hanyar gida,don dama neman network ta fito yi,cikin gidan gaba daya network ya dauke.

A ranar maimunatu tayi kuka tayi kuka qwarai da gaske,tana jin cewa farin cikin rayuwa yana sake yin nesa da ita,tana jin cewa tana sake rasa komai nata,sai ta samu kanta da addu'a a karon farko

"Ya ubangijina,ka kulaa dani,ka kula da lamarina" saita juya gefe daya tana sake curewa waje guda,hawaye masu zafi na tsiyaya har zuw cikin kunnenta.



**********Da fari sanda inna furera taga yuuma a gidanta tadan hade rai,amma kuma data tuna cewa dukka arziqin da tayi kwanaki biyu da suka wuce ta silar 'yaruwarta ce sai ta sakar mata fuska,harda sanya laulo ya dauko mata tabarma,ta kuma qwalawa maimunatu dake baya tana ta faman wankau na kayansu,wanda har yau ma jauro ya hana zuwanta kiwo

"Wadi diyam(kawo ruwa)" a nutse ta qaraso ta tsugunna gaban yuuma tana ajjiye ruwan sannan ta gaidata,yuuma ta bita da kallo zuciyarta na tsinkewa tana amsa mata,kullum kwanan duniya maimunatun sake fita daga hayyacinta da kuma kamanninta take,amma a yanzun tayi imanin inda maimunatu zata,zaya kasance mata tamkar tana hannu mahaifiyarta,koma sama da haka.

Bayan gaisuwa data biyo baya tsakaninta da inna furaira,wanda ta manta yaushe rabon irin haka ya shiga tsakaninsu,sai yuuman ta gyara zama tana lanqwashe qafafunta

"Wajenki nazo furaira"

"Allah yasa alkhairi?" Ta fada tana tattara hankalinta ga yuuma

"Alkhairin ne,don kullum mu shike tare damu"

"To ina jinki"

"Ina tunanin baki manta dattijuwar da kukayi cinikayyar nagge da ita ba kwana uku da suka wuce ko?" Fadin haka kawai ya yalwata fara'a a fuskar furaira

"Har nabar duniya ai bazan manta da wannan baquwar alkhairin ba"

"Ashe kinsan wataran zaki bar duniya furaira" yuuma ta fada cikin ranta,amma a fili saita gyada kai

"Ita din tamkar mahaifiya take a wajena...."

"Allahu akhbar....." Inna furaira tayi hanzarin fada tana duban yuuma

"Amma kike zaune cikin wannan rugar tare damu?" Murmushin da yafi kama dana yaqe yuuma tayi,saboda ita sam ba qaunar wata doguwar magana take ba tsakaninta da furaira

"Aure ya gaji haka,yakai diya mace duk inda yaso"

"Shakka babu" ta amsa tana qarewa yuuman kallo,ba banza ba ta zama macen da duk fadin rugarsu babu me sutura irin tata,hakanan yanayin hutu da jin dadi daya bayyana qarara tare da ita,hakanan cimar gidan bappa labaran ba inda labarinta bai karade ba,dama daadan ta taba bata labari kan wadda take kawowar

"Itace ta aikoni,wato kinsan jikin girma,tana fama da ciwon qafa lokaci lokaci,kuma tana da buqatar mataimaki dai a kusa wanda zai dinga mata wasu ayyukan,to taga maimunatu ta kuma yaba da amanarta,shine tace nazo na tambayar mata ko zaki bata ita,zata dauketa a matsayin ma'aikaciya da zata dinga biya da albashi me tsoka,hasalima tace ki yanka dukka albashin da kikeso a dinga biyanki duk wata,sannan kuma dabbobinki da take kiwo,ki dauki.masu kiwo suma su fadi abinda za'a dinga biyansu,ita zata dinga biya shima" shuru furera tayi,fuskarta na rage kaifin fara'ar dake kanta a dazu,ga qoshi ga kwanan yunwa,haqiqa ko shakka babu wannan albishir albishir ne me dadi a gareta,arziqi kuma har cikin gidanta,saidai kuma ta yaya za'a zabi maimunatu bayan ga gaje?,saboda.matar kana kallonta kasan tana cikin sukunin rayuwa da jin dadi,ita kuwa duk duniya babu wanda takeso ya rayu cikin walwala irin gajenta,gaskiya bata jin zata iya bada maimunatu,wadda take sanya ran tana aurar da gaje ba jimawa ta aurar da ita,ta kuma dora da kiwon da take mata koda tana gidan buderi,sunyi yarjejeniya ya kuma amince,dalilin da yasa.ma ta alqawarta masa auren maimunatu kenan.

"Me kika ce?" Yuuma ta fadi ganin furera ta shiga zuzzurfan tunani

"nakega me zai hana na baku gaaje?,babu abinda maimunatu zatayi wanda ba zata iya yinshi ba" murmushin takaici ne ga qwacewa yuuma,tana da wannan masaniyar amma ta tattarawa maimunatu dukkan wata wahalar aiki

"To ni kinga 'yar aike ce,kuma taga gaaje ta kuma ga maimunatu amma ta zabi maimunatun,ina ganin idan maimunatun ba zata samu ba,zanje na shaida mata kawai,saimu laluba cikin yaran dake rugar" yuuma ta fada tana miqewa,abinda yadan kadan hankalin furaira

"Aah,ba za'ayi haka ba,amma inason a bani lokaci kadan zanyi shawara,zan gayawa kuma jauro ma" kada kai yuuma tayi,tasan ba wani jauro da zata gayawa,amma sai ta bita a hakan,sukayi sallama ta tafi.

Yuuman na fita ta aiki laulo a sirrance yayi mata kiran daada,bata bata lokaci ba kuwa tazo,ta kuma rattaba mata dukan bayani,kishi ne sosai ya kama daadan,me yasa bata nema safiya ko zubaida ba?,indai ko haka ne bata ga dalilin da zata aika gaje ba su da sukafi kusa da daadan suna zaune,gwara maimunatun taje,ko da zata samu kudi daga gareta ai dai ba zata samu jin dadi da daular dake gidan anni ba

"Ya zakiyi ragon azanci irin haka furera?"

"Kaman yaya innar himu?"

"Ta yaya zaki tura gaaje?,tafiyar maimunatu ai shine dai dai,zata je fa samowa gaje kudin aurenta da wanda zaki mata kayan daki da sauransu,don na tabbatar miki himu gini yake na kere sa'a,kinga kina buqatar kudin da zaki mata duk wata hidima,na tabbar jauro zaiyi iya abinda yaga zai iya ne,abu na biyu idan maimunatu ta tafi dole ne himu ya sake haqura da ita,ya kuma tattara hankalinsa ga gaje,saboda maimunatu tayi masa nisan da yasan bazai ganta ko ya sameta ba,kinga komai zai tafi mana dai dai babu wata matsala,sannan ke kanki yarinyar nan alaqaqai ce a wuyanki,har mamaki nake yadda kika ci gaba da riqon diyar mai miki kiwo,kinga yanzun kuwa salamun salamun" sosai inna furera ta gamsu da shawarar daada,tabbas ita din masoyiya ce,kuma maganganunta na bisa hanya,maimunatu zata zame mata tamkar wani jari,hankalinta kwance zata zama wata me arziqi tana daga kwance,da wannan gamsuwar ta taka da kanta har gidan bappa labaran,ta kuma tabbatarwa da anni cewa ta amince.

"Nawa ne kudin da za'a dinga biyanki na aikinta?" Anni ta tambayi furaira da kanta tana kallonta,tsanarta na shiga ran annin,murmusawa tayi sannan tace

"Ina ganin a duk wata ki bada dubu biyar" inna furera ta fada tana fatan anni ta amince da kudin data yanka din.

"Na ninka miki sau hudu,zan dinga aiko miki da dubu ashirin da kuma ladan kiwo" mamaki ne ya cika furera qwarai,har ma ta rasa abinda zata fada,bata taba tsammatar samun haka daga anni ba,ashe maimunatu alkhairi ce tare da ita,ashe ita shatu ta haifawa.

Cikin tsananin murna da farinciki ta koma gida,ta samu maimunatu ta gama da wanki ta kuma dora sanwar abinci,bayanta kamar zai karye saboda duqen da tasha,sanda fureran ta kirata ta shiga fargaba da tsoro

"Zauna nan,ki kuma saurara da kyau kiji abinda zan gaya miki" qas tayi da kanta,zuciyarta na tsananta bugu,tana ayyano masifu kala kala a ranta,ko waccece ta sameta a yau din?.

"Dattijuwar da tazo gidan nan kwana uku da suka wuce,ta ganki kuma tayi sha'awar tafiya dake domin ki taimaketa da aikace aikace,na kuma amsa mata,don haka ki zama cikin shiri,daga gobe zuwa kowanne lokaci zata daukeki ta tafi dake can garinsu" da fari maganar ta razanata,ta kuma rude sosai,ta lumshe idanunta tana kiran

"Ya Allahu,ya Allahu" a hankali sai taji zuciyarta ta fara dai daita data tuna daga inda matar ta fito,daga bangaren yuuma,yummar da zata iya cewa kaf fadin rugar ita kadai ce masoyiyarta,ta tabbatar yuuma ba zata bari abunda zai cuceta ya rabeta.

Ta sake maida tunaninta ga matar,akwai cikakkiyar suffar kamala dattijantaka tattare da ita,ta tuna yadda take dubanta fuskarta dauke da fara'a da kuma tarin kulawa,tabbas akwai kyakkyawan zato a kanta.

"Bakiji bane!" Kakkausar muryar inna furera ta saukar mata cikin kunnuwa,sai ta bude idanunta tana gyada kanta

"Kina jina ko?,wallahi wallahi kikaje kika aikata wani mugun hali,ko kikaje kika gwada musu halin maitarki kikayi sanadin da kika dawo gidan nan,na rantse da sarkin da raina yake hannunsa saikin gwammace mutuwa da rayuwa,duk da bansan matar ba a zahiri,amma na tabbatar gida ne na wadata,basu damu da abun duniya ba,duk wani abu me amfani da kikaga sunyi wasarere dashi ki dauka ki adana min,ni ina da buqatarsa,kome zakici maimunatu idan zai ajjiyu baki ajjiyemin ba Allah ya isa" maganganun data dinga yi sun yiwa maimunatun nauyi qwarai,sai tayi qas da kanta tana saurarenta har sai data gama ta sallameta.

Yini tayi cikin taraddadi da kuma fargaba,duk da tana samun relief duk sanda zuciyarta ta gaya mata cewa yuuma ce,masoyiya guda daya da take da,ta bangarenta ne wannan lamarin,sai tayi qoqarin saisaita qwaqwalwarta tare da addu'ar kome meye ya zame mata sauqine na rayuwarta.


*13*


Tunda gari ya waye take zaune tangaram tana duban qofa zuwa window,tana lissafa wucewar mintuna da awanni da yatsun hannunta,wucewar kowacce daqiqa bugun zuciyarta ne ke daduwa,ta kalli qullin kayanta da ba komai bane a ciki illa fararen kayan saqinta,wadanda su daya ne abinda ta mallaka take kuma ji dasu,Sallamar da taji da baqin murya ya tabbatar mata ranar barinta rugar yayi,karon farko da zata fita daga rugar tun sanda suka shigo ita da mahaifiyarta.

Laulo ne ya leqo yayi kiranta,sai ta miqe riqe da qullinta tabiyo bayansa,saboda tasan cewa abinne yazo wai inji mai tsoron wanka.

Laila da yuuma ne tsaye a tsakar gidan,lailan cikin ado take dake nuni da zallar ilimi dukiya da kuma wayewa,ta qaraso a hankali ta gaida yuuma dama lailan,dukka suka amsa mata da sakakkiyar murya.

Sosai inna furera ta kama kunnuwanta,har data dafe gefen fuskarta saboda tsananin zafi

"Banda dauke dauke,banda mugun hali,iya abinda aka kaiki shi zakiyi,kada ki yarda a kawomin qararki,idan haka ta kasance kuwa kashinki ya bushe" kai take gyadawa da sauri don ta samu ta saketa,duka yuuma da laila sai da zuciyarsu ta motsu,saidai kowannensu da sauqi,saboda sunsan taqi kadan ya rage ta rabu da wannan rayuwar .

Sanda suka qaraso gaban motar tsaye tayi kawai tana qarewa motar kallo,tana qissima yadda zata tsinci kanta a ciki,wai yau itace zata shiga wannan abar?.

"Ki shiga maimunatu,anni na jiranmu" laila ta daga kai daga danna wayar da take ta yiwa maimunatu magana,ajiyar zuciya ta sauke sanda ta shiga motar,saidai gaba daya a takure take saboda rashin sabo,sai da suka koma ta gidan yuuma suka dauko anni sannan suka juya suka nufi hanyar barin rugar gaba daya.

Duk inda suka gifta sai maimunatu tabi wajen da idanu,tana jin wata kewa tana ratsata tun yanzu,tana jin wani yanayi mara dadi cikin zuciyarta,tana qissima yaushe zata dawo?,yau ko gobe?,ko kuma ta tafi kenan tafiya ta har abada?.

"Ki saki jikinki maimunatu,ki sanya a ranki zaki je kiyi rayuwa ne irin ta kowanne yaro dake gaban mahaifiyarsa" anni ta fada bayan ta karanci damuwa da tunani daya cika kwanya da zuciyar maimunatu,qas tayi da kanta tana jinjinashi,sannan tasa hannu a fakaice ta goge qwallar dake shirin sauko mata,babu abinda yake dawo mata sai wani lokaci can baya da suka baro garinsu na gembu ita da daadarta shatu zuwa wannan rugar,a zahiri rayuwar sam mara dadi ce,to a yanzun gata ra cira daga nan din zuwa wani wajen,an mata bushara da kyautatuwar rayuwarta,to amma kuma sanin haqiqanin yadda zata kaya din sai ubangiji,sanin gaibu sai Allah,ko wacce irin qaddara ce cikin wannan tafiyar kuma?.

_ku biyo alqalamin 'yar mutan huguma_


Sosai maimunatu ta bude idanunta tana kallon hanya,a wancan lokacin da suka shigo garin akwai qarancin shekaru,shekarunta basu kai haka ba,don haka ta dinga kallon hanya abinta,tun daga cikin rugarsu har suka fito suka dauki hanya dodar.

Bayan 'yan hirarraki motar ta dauki shiru,bacci yayi gaba da anni,haka ma yahaya,sai ita sai driver,sai laila data nutsu ta tattara hankalinta kan waya,ta karanci yadda laila ke son waya,daga dan qaramin sanin data yi mata,ta saci kallonta kadan sai kuma ta sake maida hankalinta ga titi,tana kallon yadda ubangiji ya shimfida qasarsa.

Wani sashe na ranta kuma cike yake da mamaki,gashi dai tafiya suke,amma kamar a tsaye suke a waje daya,banda tana ganin yadda suke wuce dazuka da bishiyu tabbas da zata ce ba tafiya suke ba.

Awa biyu cur sukayi suna tafiya kafin anni ta farka,ta sanya drivern ya shiga dasu cikin wani gari,sukayi sallah,kafin su idar kuma saiga yahaya nan ya shigo musu da takeaway,wanda suka wuce dashi mota,suka dora tafiyarsu.

Tunda ta karba ledar abincin take hannunta a riqe ba tare da ta ci ba,abinci ne data jima rabonta da irinsa,tama manta lokacin,tun a zamanin da suke muhallinsu ita da mahaifiyarta,cikin ranta take tantamar anya abincinta ne?,bata sake budawa ba saida laila wadda ta gama cin nata ta kalleta

"Ki buda mana maimunatu kici?,ko bakison irinsa?" Dan qaramin murmushi ta saki ta girgiza kai,sai ta buda ledar a hankali,laila ta bita da kallo,wani irin kyau fuskarta ke fitarwa fiye da wanda take dashi duk sa'ad da tayi murmushi,janye idanunta tayi,tana gyara zamanta yadda zataji dadin ci gaba da danne dannenta,zuwa lokacin maimunatu ta fara kaiwa cikinta abincin.

Yawan wanda yaci sai yasa ta dinga jin kunyar suga ledar,ita kanta tayi mamaki qwarai,amma kuma daga bisani da taga laila sabgarta take a tab dinta,anni kuma ta koma baccinta sai ta sake itama.

Duk yadda taci burin ganin hanya tun daga adamawa zuwa gombe amma sai da bacci yayi mata tsiya,tana gama cin abincin jikinta ya mutu murus,tsohuwar yunwar data jima a jikinta ta kwanta,tsohuwar gajiya kuma ta shekara da shekaru,basussuka baccin da batasan adadin yawansu ba suka taso mata haiqan,bata shirya ba baccin yayi awon gaba da ita.

*GOMBE STATE*

*_G R A GOMBE_*
_DR SULAIMAN KUMO ROAD_


_Dr marwan khalid akko residence_


Katafaren gida ne wanda ya amsa sunansa ta kowacce fuska,irin ginin da aka yishi ba don alfahari fariya ko taqama gami da almubazzaranci ba,gini ne na ma'ana da sanin rayuwa da kuma abinda duniya ke ciki,duba daya zaka yiwa gidan kasan cewa daga zubi da tsarinsa ginin ya zaunu matuqar zaunuwa,hakanan yakan dauki hankalin mafiya yawan jama'a,tun baka ma shiga cikinsa ba.

Gidane dake dauke da sassa guda hudu,biyu na matan gidan,daya kuma mallakin me gidan,yayin da daya bangaren ya zama mallaki ga mahaifiyar me gidan wato haj maryam Farooq kumo.

Gaba daya gidan mallakin dr marwan khalid akko ne,babban limamin gombe gaba daya,shararre kuma sanannen dan kasuwa,wanda Allah ya yiwa baiwar arziqi dama dukiya gaba daya,gami da tarin ilimin addinin islama wanda shi ya kaishi ga zama cikakken dr,hakanan ta fannin boko din ma ba'a barshi a baya ba.

Wani irin mutum ne da Allah ya yiwa baiwar kwarjini da kuma farinjini,mutum ne me amfani da ilimin addininsa ainun,mai yawan taimako sadaka da kuma kyauta ma gaba daya,dukka sirrin nasararsa ya ta'allaqa ne ga mahaifiyarsa,jajirtacciyar uwa da bata daukan raini ko kuma wargi komai qanqani,tsayayya akan 'ya'ya da kuma jikokinta.

Marwan shine babban d'a a wajen haj maryam anni,hakan ya sanya yayi mata matsuguni cikin gidansa tun bayan rasuwar mahaifinsu,kuma dama shi din mutum ne mai matuqar qaunar mahaifiyarsa

da kuma qawa zuci,hakan ya sanya itama haj maryam anni ko cikin yaranta tafi ji dashi,duk da cewa dan fari ne ba auta ba,autansu alhj sagir yaso daukarta ganin kamar shi yafi dacewa,amma gaba daya ya hanasu hakan,yace shi yafi cancanta tunda shine babba.

Matan Dr marwan akko biyu,akwai haj Aishatu,wadda take da yara bakwai dashi,diyarta ta farko macace mai sunan anni wato maryam suna ce mata maama,sai ja'afar d'a na biyu a wajenta,wanda ya zamto halitta mafi soyuwa a wajensu,duka sauran mata ne,salma,hafsa,nadiya,safina,sai autansu namiji khadim,daya dakin kuwa dakin amarya umamatu tana da yara hudu ne,suma din mata ne,fa'iza ce babba,sai khadija,zahra'u,sai mai sunan yuuma rahama suna ce mata baby.

Tsakanin aishatu da suke kira da amma da kuma umamatu da suke kira da ammy zama ne na fahimtar juna da kuma zaman lafiya dai dai gwargwado,yadda Allah ya dorawa kowa son ja'afar haka ammy ke qaunarsa,shi din dan gidanta ne tun farkon zuwanta gidan,amma kuma ta tattara ta miqa mata shi,shima kuma ya dauketa kamar uwa a gareta.

*_Ja'afar marwan khalid akko_*


matashin saurayi kuma matuqin jirgin sama,mai jini a jika,wanda Allah ya yiwa baiwar qira ta jiki,bashi sahun dogaye ko kuma gajerun maza, moderate ne,yana da murjajjen jiki

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login