Showing 18001 words to 21000 words out of 95534 words

Chapter 7 - GURBIN IDO COMPLT

Start ads

11 Aug 2025

605

Middle Ads

fada tana hade rai tare da miqawa anni wayar

"Kin fada dai dai ai,sunan ubanki kenan" ta amsata tana warce wayar daketa harbawa da sunan super dad,ta shafa ta kara a kunnenta.

"Sai da salma ta gargadeni kan tafiyar nan,ashe ni zan karba gashin" bata daddara ba dai ta sake yin qorafin murya can cikin maqoshi,saidai babu yadda za'ayi anni taji,saboda tayi nisa a waya da shalelen dan nata.

Sai da tayi duk wani abu daya zame mata al'ada idan ta dawo da dabbobin daga kiwo sannan ta kira sunan innar,saidai babu ita ba motsinta,dole ta fara takawa zuwa cikin gidan,qirjinta yanata dukan uku uku,don batasan me zai biyo baya game da takalmin qafarta ba.

Daga qofar dakin innar ta tsaya

"Miwarti ɗilaulake inna(na dawo daga kiwo inna)" shuru taji,hakan yasa ta sake maimaitawa

"Dalla malama matsa ki bamu waje,kinxo kinata yiwa mutane hayaniya aka" muryar gaje ta fito daga cikin dakin,da alama itace kwance a dakin,wanda dama kusan aikinta kenan ko da yaushe,taci ta sha ta kwanta.

A sanyaye ta juya don barin wajen,dai dai sanda innar ta fito daga makewaye dauke da buta,sam bata lura da yanayin da fuskarta ke ciki ba

"Miwar......." Ragowar kalmar ta tsaya mata a maqoshi,sakamakon wani zazzafan mari daya sauka a kuncinta hagu da dama,a take ta gigice,ta dafe dukka kuncin nata da tafukan hannayenta tana kallon inna,wadda ta taka gefan wani qaramin rumbu dake daura da ita,take tashin hankali ya bayyana muraran saman fuskar maimunatu,tunda taga ta doshi wajen tasan me zata dauko.

Tsumammiyar bulala ce,wadda ta debi shekaru ana azabtar da ita da bulalar,yadda ta tsani mutuwar ta haka tabtsani bulala,wannan ne dalilin da yasanya take dukka iya bakin qoqarinta taga bata aikata wani laifi da bulalar zata taba lafiyarta ba,zata iya cewa tabon da bulalar ta bar mata a gadon bayanta ba zaya lissafu ba.

Kusan daukewa numfashinta yayi sanda innar ta ware dukka qarfinta ta zuba mata ita,kafin daga bisani qarfin dukan ya sanyata ta sulale ta duqe a wajen,tun tana iya roqarta tare da bata haquri har bakinta ya mutu,duk da batasan me ta aikatawa innar ba,sai data gamsu don kanta da yawan dukan data yi mata sannan ta tsaya tana maida numfashi

"Gaje....gaje zo nan" ta qwalawa gaje dake daki abinta kira,gajen da duk yawan dukan da akewa maimunatun,duk magiyar da takewa innar bai sanyata ta koda leqo ba,hatta da sassan dake maqotaka dasu dukka kowacce ta leqo tana tsaye tana kallo,wasunsu suna qus qus a junansu tare da tir da dabi'a da halayen inna,wasu kuma suna fadin

"Allah ne kadai yasan me tayi mata,kila ko yau ta dana halin uwarta ne" saidai babu ko mutum daya a cikinsu da ya isa ya tukari innar da sunan ceton maimunatu,kowanne irin hukunci ko horo kuwa zatayi mata.

A gadarance gajen ta fito daga dakin,tsaf da ita cikin kwalliyar kayan saqi,wanda kusan ko da yaushe cikin canza mata su innar take,idanun gajen sun kumbura sunyi jazur,abinda.ya bayyana har saman fuskarta,da alama kuka tasha ta qoshi.

Tsaye tayi saman kan maimunatu tana hura hanci tare da harare harare

"Daga kanki ki kalleta.....tayi kama da sa'arki?" Inna ta fada cikin hargagi,koda ciwon mutuwa maimunatun takeji a jikinta ya zame mata dole ta kalli gaje kamar yadda inna ta buqata,idan kuwa ta saba hakan wani sabon tashin hankalin ne,da qyar ta daga kanta ta dubi gaje,suna hada idanu gajen ta sanya qafa ta haureta cike da baqinciki da kuma jin haushin maimunatun,tasa hannu ta dafe wajen saboda radadi da zafin da ya ziyarceta

"Shegiya munafuka,ni zaki ha'inta,ashe yaron dana ganki dashi rannan ibrahimu ne?,to idan bakisan waye ibrahimu ba bari na gaya miki,shi din alqawarin gaje ne,bashi da matar aure sai gaje kiji na gaya miki,kusantar inda yake kuma shine babban kuskure da zaki aikatawa rayuwarki,wallahi wallahi kinjin na rantse miki,kome kike taqama dashi baki isa ki shiga tsakanin tsohon alqawari ba.....kukan da kika saka gaje yau sai kinyi mafiyinsa,ki bata haquri!" Inna ta fada tana kai mata harbi da qafa,ta sameta kuwa a gwiwarta wadda ta bugu sosai,tana dafe da wajen,cikin tsananin azaba tana dafe da gwiwarta ta fara baiwa gaje haquri,wadda keta qunci,tana jin babu abinda maimunatu zatayi mata ta huce haushin kula mata Ibrahim da tayi,tsahon wanne lokaci sukayi suna tare da ibrahim din?,tunda hatta da mutanen gari sun san da haka,baya ga haka kuma ace har sai da daadarsa tazo da kanta don yiwa tufkar hanci sannan sukasan da batun,lallai maimunatun ta cika cikakkiyar makira kuma macijin sari ka noqe kamar yadda innarta tasha fada mata.

"A'ah,lafiya?,me yake faruwa?" Muryar jauro ta ratsa kunnensu,abinda ya sanyasu waiwayowa gaba dayansu,duk da cewa innar bata so dawowarsa yanzu ba amma sai ta dake

"Meye hakane?,me ya faru?" Ya sake tambaya yana kallon gaje kafin ya maida dubansa ga maimunatu dake zube a qasa,hakan ya baiwa gaje damar sulalewa zuwa dakonsu,tasan halin jauro tabbas yau cikin gidan ba za'a qarke lafiya ba

"Gata nan ka tambayeta maciyar amana" inna ta fada tana huci.

Gabanta ya duqa yana kiran sunanta,ta daga kanta wande ta sokeshi tsakanin qafafuwanta tana duban ardo din,yanayin yadda yaga maimunatun ya tabbatar masa lallai ta daku,hatta da bakinta a kumbure yake,gefan fuskarta yayi kwanciyar jini da shacin bulala

"Wanne irin rashin imani ne wannan furera?" Jauro ya fada a mugun fusace yana miqewa tsaye

"Ita ya kamata ka yiwa wannan fadan bani ba,qanwar bayan gaje har ta iya hilatar maza tana binsu?,saboda rashin kintsi ta rasa wa zata bi sai ibrahimu?"

"Shine kikayi mata irin wannan dukan?,inda kuma kin nakastata fa?"

"Shikenan da kowa ya huta da ganin shegiyar fuskar dake daukan hankalin maza" cacar baki ce taso barkewa a tsakaninsu,ran jauro yayi mutuqar baci

"Waike wacce iriyar macace furera?,maimunatun zaki yiwa irin wannan dukan?,kowanne irin laifi ma tayi miki?,don kinga ina dauke kai ina barinki saboda kina nuna min kunfi kusa ko?"

"To dama meye naka a ciki?" Kai ya gyada cikin bacin rai,iskar data fara kadawa wadda ke tafe da dan yayyafi yasa jauro ya maida hankalinsa ga maimunatu

"Tashi ki shiga dakinku,Allah zai saka miki,a kusa ko a nesa,baya yafe zalunci" kasa miqewa tayi,ya tabbatar ba zata iya tashi ba,cikin muryar fushi ya qwalawa gaje kira.

A tsorace ta qaraso tana raba ido hadi da matse hawaye,tsawa ya daka mata

"A'ah ya haka?,ka bita a sannu,rai aka bata mata fisabilillahi sannan ka bita da irin wanna tsawar?" Kallon banza ya watsa mata,yana ganin zallar son rai da son kai irin na innar

"Munafuka,kamata ki kaita daki" ya fadi yana zabga mata harara,da sauri ta zabura ta matso ta kama maimunatun,irin riqon tsaurin da tayi mata na mugunta yasa maimunatun cewa

"Wash hannuna"

"Sassauta mata riqon kafin nayo kanki na maimaita miki irin dukan da uwarki tayi mata"

"Dalili dame?,ke bi masharranciya a sannu ku rabu lafiya kada ta shafa miki jarfa ba gaira ba dalili" inna ta fada saboda tasan tsaf jauro zai aikata daga yadda ranshi yayi mummunan baci.

Sakin maimunatu tayi sanda suka isa dakin,abinda ya sanyata ta buge gefan kanta,qauuuuu taji wani abu na yawo cikin kwanyarta,ya dafe wajen tana kiran sunan Allah,gaje na tsaye a kanta tana zuba mata harara

"Shegiya mayya,wallahi kikayi gangancin sake rabar ibrahim sai mun kasheki a gidan nan nida inna mun binneki,kuma mun kashe banza,tunda babu wanda zai tuhumemu" daga haka ga tsallaketa kamar zata takata,ta haure kan katifarta.

Ta jima tana jinta a wata duniya ta daban,kowacce gaba ta jikinta ta zame mata kamar wani gyambo,da qyar take iya motsawa.

Kiran sunanta da jauro yayi ya sanyata bude idanunta da qyar

"Tashi zan shigo" ya fada yana tsaye daga bakin qofar dakin,duk da yayyafin dake sauka har yanzu,jikinta taja ta miqe ta zauna sosai tana jingina da bango,ya dage labulen bayan ya shigo ya maqale shi sannan ya tsugunna daga gefe yana turo mata kwanon abincinsa

"Dauki kici maza diyam" sunan da ya kirata dashi yayi matuqar karya mata zuciya,ya tuna mata da tata daadarta,itace wadda ke kiranta da sunan,suna mafi soyuwa a gareta,fararen manyan idanunta suka cika da qwalla,tasa hannu a kasalance ta jawo kwanon gabanta ta fara ci.

Wasa wasa sai gashi ta kusa tashi da abincin duk yawansa,ta riga ta saba ba kullum take samun abinci ba,idan ma ta samun to sau daya ne a rana,tana ci yana mata nasiha tare da kwantar mata da hankali,gaje na kwance tamkar mai barci,ranta ya baci sosai,shi babanta wai baya kishinta?,me yasa yafi nuna kulawarsa ga maimunatu fiye da ita diyar cikinsa?.

"Miyatti bappa" maimunatun ta fada a tausashe kanta a qasa cikin nuna jin dadin kulawar da ya bata

"Ba komai,kema diyata ce kamar yadda gaje take" kai ta jinjina,tana kin sauqi cikin ranta,ko babu komai yau din ba zata kwana da yunwar dake da take matuqar wahal da ita ba a duk dare.

Har jauro ya juya ya fita maimunatu tana binsa da kallo,sai daya sauke labulen ya qarasa ficewa sannan ta sauke nannauyar aiiyar zuciya tana janye idanunta daga wajen,dai dai lokacin da gajee tayi caraf ta miqe zaune

"Munafuka algunguma,kamar a idanun inna akayi wallahi,Allah ya kaimu safiya" tsoro ne ya cika zuciyar maimunatu,saboda tasan tunda gajen ta fada sai ta aiwatar,idanunta fal da qwalla ta shiga roqon gajeen tayi haquri,maimakon ta amsa mata sai ta lullube kanta da mayafi tayi kwanciyarta gami da juyawa maimunatun baya.

Sai da dukka yawun bakinta ya dauke kan roqon gajee tayi haquri,daga qarshe dole ta haqura da roqon,ta rufe idanunta,hawayen da suka taru suka gangaro mata.

Wani wahalallen barci tayi mara dadi,saboda ko ina na jikinta ciwo yake mata,ko da tayi sallar asuba ma zaune tayi a wajen,saboda ciwon da jikin yake mata,inda ace shimfida ce mai laushi irin ta gaje wala'alla ta iya rabawa takwanta,amma shinfida irin tata da bata da maraba da tattauran dutse babu ta inda zata iya kwanciya taji dadi.

"Maimunatu!!!,ke maimunatu!!"kiran mafarautan da ya ratsa tsakiyar baccinta ya sanyata farkawa firgigit,inna ce tsaye a kanta,hannunta riqe da robar da yawancin lokuta suke tatsar nono a cikinta,duban maimunatun take kamar zata afka mata

"Yahudillo dirgul.....(zoki tafi kiwo)......"
"A ina?" Maganar jauro ta katse hargagin da inna ta fara yi mata,ratsowa yayi sanye da riga 'yar shara da malfare a kansa,hannunsa riqe da baqar leda,bisa dukkan alamu fita zaiyi

"Daga yau.....har zuwa ranar da maimunatu zata warke babu ita babu zuwa kiwo,wallahi wallahi wallahi sau nawa kenan?"

"Tati(uku)" innar ta amsa masa tana riqe da qugunta tana kallonsa

"Idan naga akasin hakan zakisan waye ainihin jauro wanda ada can baki sanshi ba,wannan shine hukuncinki na irin dukan da kikayi mata"

"Wai dakata,wai me kake nufi ne?,ko kana yimin baqinciki ne da dukiyar dabbobin da Allah ya bani ne?,wanda dama an jima ana fada,ganin muna zaune shekara da shekaru tare yasa ban gasgata ba,amma ayanzu na fara ganin alamu ganin idona kuwa" dubanta yayi

"Ki bari sai zuwa sanda kika tara taki dukiyar ta halastacciyar hanya saiki gayamin haka" sosai maganar daya fada tayi mata ciwo,tana ganin jauro shi daya ne mutumin da yasan sirrinta yake kuma shirin xamar mata tarnaqi a rayuwa,wannan amsar da ya bata ta hautsinata,ta dinga jifansa da kalamai,wanda kalmarta ta qarshe ita ta sanya ya tsaya cak yana dubanta

"Ban sani ba ko son maimunatu ma dai kake yi a taqaice,idan sonta kake ai gwara ka fito ka gayamin,saika hadamu mu duka ka aure"

"Idan ke mahaukaciya ce ni da hankalina" sai ya qara gaba kawai ya fice yabar mata gidan,ya tabbata idan ya tsaya yaci gaba da biye mata zasu raba abun fada ne gaban 'ya'yansu,wannan ba komai bane a wajen furera.


08

Fitar jauro daga gidan sai dukkan bala'i da masifar suka dawo kan maimunatun,inna nayi gajee nayi

"Tunda ya daure miki gindi ko?,to wallahi baki isa ki kwanta kiyimin saqe saqe kamar gawar sababi ba,bayan jiya ya shirga miki abinci kin cinye,to kin ciyoma kanki,kinci abincinki na jiya dana yau,waryo wan en jungul!,(zoki dora mana abinci)" ta fada a tsawace,har maimunatun tana jin kanta kamar zai cire.

Tuwo ne na masara miyar danyar kubewa,gaba daya kayan aikin innar ta tura mata,ta baza tabarma tayi zamanta qasan bishiyar dake basu iska.

Zata iya cewa batasan ta yadda akayi take aikin ba,don komai tana yinsa ne a wahalce,cikinsu kuma babu wanda ya taimaka mata koda da firfita wuta ne,yadda bata da lafiya haka aikin yaja lokaci yaqiyin sauri,saboda rashin kazar kazar da kuma qwarin jiki,abinda ya qara iza wutar masifa da bala'in inna,ya kuma sanya maimunatun taji inama ace kiwon ta tafi a haka,tabbas ya fiye mata wannan wahalar girkin.

Tana zaune tana niqan kayan miyan da zata dora miya saman dutsen markade taji sallama,ta daga kanta a wahalce tana amsawa,matashiyar da aqalla zatayi sa'a da ita ce(zubaida),sai kuma yaron dake gefanta(sadam),kasa dauke idonta maimunatu tayi daga kan fuskar yaron,saboda kamarsa muraran da ibrahimunta.

Shima yaron ita yake kalla,kafin daga bisani ya dauke kansa,abinda ya bata mamaki hararan da zubaidan ta wurga mata kafin su miqa zuwa inda inna ke zaune tana kada nono,maimunatun kuma ta maida kanta ga aikin da takeyi cikin mamaki,iyaka saninta da zubaida saidai kallo daga nesa,ba abinda ya taba hadata dasu,koda gaisuwa kuwa,takan jima bata gansu ba,kamar yadda suma suke jimawa basu ganta ba,domin su din zuwansu kiwo na lokaci bayan lokaci ne bawai koda yaushe ba,koda ma koda yaushe ne,tana daukar watanni kafin magana ta hadata da wani a wajen kowo har taje ta dawo,saidai idan baqin makiyaya da ba 'yan asalin rigarsu ba sun ratso ta dajin da suke kiwo.

"Maraba da zubaida da saddam" innar laulo ta fada cikin wani irin kirki da kuma fara'a,wanda ya sanya har sai da maimunatu ta tasa kanta dake mugun sarawa ta saci kallonta.

Daga gefan tabarmar da take kai suka zauna,gaisheta yaron ya farayi sannan zubaidan

"Dama daada ce ta ailo na gaya miki,akwai baqi da sukazo daga gombe,naggen bappa suka saba siya,to wannan karon babu,bappan ya fita dasu gaba daya,shine tace nazo na gaya miki,tasan cikin naki akwai irin wadanda sukeso,gobe zasu zo da safe kafin a fita dasu su gani" madaukakin farinciki ya kama inna furera,cikin ranta ta sake jin duk duniya bata da masoyi sama da daada din,dama ta jima tana shawarin saida wasu daga ciki,ko don ta saku ta sake badda dukka wata alama da zata iya zama shaidar rashin zamowarta mallakin dabbobin,to amma kuma batason saidawa anan kusa,tafison waje me nisa inda zasu siya da daraja

"Miyatti Allah,miyatti daada,amma naji dadi wallahi,Allah ya kawosu"

"Ameen,sannan tace na gaya miki,anjima yaaya himu zaizo wajen gaaje,su sake ganin juna" kamar inna furera zafa taka rawa haka tayi,takai ta kawo ta rasa wanne tukuci zata bawa zubaida,qarshe dai har suka bae gidan bakinta yaqi rufawa.

Saukar zancan a kunnuwan maimunatu sai ta kasa tantance cikin wanne yanayi take ciki

"Ibrahimu zaizo yaga gaaje" wannan shine dalilin da yasa ta daina ganinsa kenan?,me hakan yake nufi?. Tunanin ya sanya aikin nata ya sake yin slow fiye da dazu,tun inna na mita da baki har sai data fara kai mata duka da hannu

"Me shegen baqin halin tsiya,bakyason aikinne,a haka kuma zakiyi shi".

Takanas innar ta taso gaje,ta hada mata madarar shanu da lalle ta murje mata jikinta,zaka tsammaci kamu za'ayi mata irin na amare,duka a wannan lokacin ta sanyata ta tsefe kanta mai yalwar gashi,wanda datti ya dakushe tsahonsa ta wanke mata shi fes,ta raba mata gida biyu ta zubo mata da jelarsa hagu da dama.

Tun yammaci aketa shiri gamida da gwada yadda zata tarbi ibrahim din,duk don saboda ta burgeshi,mudukaje(kayan saqin fulani) na can qasan kayanta ta ciro ta ajjiye,dukka abin nan da ake na maimunatu idanu ne,saidai gefe daya zuciyarta ta gaza hutawa da tunanin abinda zaije yazo.

Dai dai sanda maimunatun ke saman dan mayafin da take shimfidawa tayi sallah....dai dai sannan gaje keta faman fecewa fuskarta kwalliya,ta kalli madubi yafi sau shurin masaki,ta juya ta sake juyawa har sau babu adadi,burinta shine taga komai yayi,sannan ta burge ibarahim matuqa,maimunatu tana zaune a wajen,bata motsa ba bare ta waiwaya taga abinda gajen keyi,saidai kuma kunnuwanta na samun aiken saqonnin waqe waqen da gajen keyi cikin harshen fullanci,tana yi tana juyi,abinda zai nuna maka cikin zallar farinciki take a yau din.

Laulo ne ya shigo dakin,yaron da za'a iya cewa yafi gaje hankali,don wasu abubuwan da shi din yakeyi yana yinsu ne da yarinyata,da kuma rashin samun isashshiyar tarbiyya da kyau

"Himu yazo,inna tace akai masa taburma" sai yaron ya juya ya fita yana tsalle tsalle abinsa.

Juya idanunta gajee tayi cikin farinciki,ta jima tana qaunar himu tun ba yanzu ba,tun daga sanda inna ta gaya mata cewa shine mijin da suka zaba mata ta riqe hakan a ranta,bata taba mancewa ba,hakanan bata yarda ta kula kowa ba saboda ibrahim,duk da tarin masoyan da take dasu a rugar,don dai dai gwargwado tana da irin nata kyan.

"Ki dauko tabarma ki kawomin zagaye"

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login