Showing 51001 words to 54000 words out of 55760 words

Chapter 18 - INAYAH

Start ads

20 Aug 2025

430

Middle Ads

tabbatarda hakan sbd akaro na biyu takuma sakasa masifar da kusan tafi ta baya yaqare da rataya igiyoyinsa na aure a wuyan 'yarsa baisan wane mummunan Al'amarin Zata Kuma kawo masaba a gaba Dan yasa zaifi wainnan zauta Kai da qwaqwalwa.

CM ne yayi saurin kallonsu Alhaji buhari ganin ransu yafara baci sosai sunason Jin bayanin abinda yake faruwa Dan haryanzu sunkasa yarda da auren matar 'dansu aka daura da wani sbd har lokacin Babu Wanda yakawo da AA MAJEED aka daura auren tunda ba abune Mai yiyuwaba uba ya aura 'yarsa Dan hakan kaf gurin Babu Wanda yakawo ABDULMAJEED mahaifinta ake nufi suma su CM da Alhaji babbah sunqi barinma agane wane ABDULMAJEED Dadi da qari kusan duniya da AA MAJEED tasansa bada cikakken sunansaba ABDULMAJEED ABDALLAH.

Cikin qarfin hali Abbin yataso Yana sallama da mutanensa dake wucewa suna Masa Allah ya sanyawa auren 'yarsa albarka Yana amsawa da amin.

Kaurewa da gurin yayi da jiniyar motocin 'yan sanda da civil defense ga yawan jama'a kowa nata kokarin miqa barkarsa ya wuce shiya taimakawa su CM gurin Jan su Alhaji buhari zuwa cikin gida palon Alhaji babbah Wanda shine da kansa ya iya fara tankwafarsu sbd fadan tozarci dasukagani qarara dasuka fara yi.

Alhaji buhari ne mai iya dan danne tsananin bacin ran dasuke ciki su Alhaji kabiru 'yan Nan Hadiza kuwa kasa dannewa sukai suka fara zuba masifar tashin hankali Dan duk Inda ake wulaqantawa an wulaqantasu ankuma tozartasu sun debo jiki tun daga adamawa sunzo Lagos daurin aure ace suna zaune suna kallo kaman wasu gumaka andaurawa amaryar aure da wani koma Dan uban waye ai Basu cancanta wannan tozarcinba.

Abdulsamad a rikice cikin tashin hankalin daya zaburo Masa tako Ina ya ringa kutsa jama'a Yana neman iyayensa maza dasune wakilan Amma Bai gansuba Dan haka ba Shiri ya zare hular kansa Yana Jin akwai gagarumar matsala Mai tsananin girman gaske kuwa.

Saida mutane suka rake sosai aka fara Ankara da abinda yafaru ganin rudewa da tashin hankali da Abdulsamad yake ciki da yawa wainda suka dauka sune basuji sunan daidaiba suka fahimci cewan daidai sukaji Ashe auren ne dai bada Dr Abdulsamad aka dauraba.

Take kurar hayaniya tafara kaurewa daga gurin
Ganin Abdulsamad na Neman zarewa yasa Abbi daya Gama sallamar baqinsa ya Kama hannunsa sukai cikin babban gidan na Alhaji babbah.

Qanin CM Professor Ibrahim shine ya tsaya yaqarasa sallamar sauran jama'ar aka watse wasu nata sake sawa auren albarka wasu Kuma na shiga mamaki da son Jin yanda wannan mugun Al'amarin yafaru hakama wasu take suka ringa maimaitawa wainda basujiba cewan sunan fa AA MAJEED ne aka daura dashi.
Mamaki da firgici wasu suka Kuma shiga Jin sunan Wanda aka daura dashi din aikuwa take tun anan suka fara shigar da gulmar Internet.

An watse tsaf ba kowa Dan hakan Alhaji babbah ya kalli su Alhaji buhari dake cikin mummunan yanayi na bacin Rai da fushi.

Cikin sanyi da taushin murya ga Wanda baa kyautawaba yace"

Alhaji buhari kuyi hakuri nasan baa kyauta mukuba tako Ina Musamman da baa sanar daku komaiba ko fahimtar daku komaiba Saida kukazo cikin baynar jama'a hakan tafaru.

Dr Abdulsamad dake tsiyayar wasu ruwan zufan tashin hankali da fita hayyaci ya kalla duk saiyaji jikinsa yayi sanyi da tausayin Abdulsamad din sbd duk Wanda ya kallesa yasan yana tsananin son Inayah so Mai tsanani,

Tayaya Za'a kallesa ace Masa uwarsu daya,
Uban ne kawai Basu saniba ko dayane tunda A MAJEED cewa yayi uwar kawai yasani itama a bisaga qaddara.

Shi kansa Dr Abdul idanuwansa duka da hankalinsa suna kan Alhaji babbah sbd ya fahimci agurinsa zasuji abinda suke buqatan ji Wanda zuciyarsa ayau harbawar datake yasan ta wuce kowane irin tsari da akeson zuciyar Dan Adam ta buga.

Babu wani yaren dazai gane ayanzu idanba na maganar aurensa da Inayah bane.

Dan jinjina maganar dake bakinsa Alhaji babbah yiyi tareda dauke idanuwansa daga Abdul ya maida kan su Alhaji buhari dasuke manya zasu fahimtarsa a natse yace"

Ita wannan yarinya Inayah wadda mahaifiyar Abdulsamad ke Kira da Ayshatouh 'yar mahaifiyar Abdulsamad ce wadda ta jima da Bata tun jarinta Wanda A jiyan bayan haduwar mahaifin Inayah Wanda yanzu zance mijinta da ita mahaifiyar tasa suka tabbatarda Dr Abdulsamad da Inayah uwa dayace ta haifesu,

Dr Abdulsamad da Inayah uwarsu daya Kuma kaman yanda duk muka sani Babu aure tsakaninsu,

Sauyin Wanda aka daura dashi Kuma wannan nine Nan na tayasa yanke wannan hukuncin sbd kaman barazana da ita mahaifiyar yarinyar takeson tayiwa MAJEED Dan hakan muka yanke hukuncin ya aureta.

Dan haka a taqaice ABDULMAJEED shine ya aura AYSHATOUH INAYAH,
Shine mijinta ayanzu,
Sauran bayanin Inda ita mahaifiyar Dr ta samo yarinyar har suka Zama uwa daya da Dr wannan saidai aji daga gareta.

Wani mummunan shock da matsiyacin zufane ya fesowa Alhaji kabiru zuciyarsa na harbawa da mamaki ya juya ya kalli malam Umar Dan uwansa Wanda harya fisa jiqewa jagab da zufa.

Alhaji buhari daya Gama samun qullewar Kai da mamaki da Yar rudewa yace'

Inayah kuma Yar Hadiza?
Tayaya?
Garin Yaya?
Yaushe?

Shaqewa muryar Alhaji kabiru tayi a Rikice murya na yankewa yace"

Inayah itace AYSHATOUH????
'yar da Hadiza ta Haifa ranarda mahaifiyarmu ta rasu??

Da tashin hankali malam Umar ya karba da cewa"

Innalillahi wainnan ilaihrrjiun
Tabbas Hadiza ta haifi 'ya takuma saka Mata Ayshatouh.,
Idan har ya tabbatarda Hadiza ce dimun wadda tabar Masa 'ya to tabbas kuwa wannan 'yar ta Hadiza ce halak malak sbd ranarda ta haifeta ranar tabar gida.

Sai alokacin zufa ta karyowa Alhaji buhari Jin dai ta tabbata Hadiza haihuwa tayi ba aure bayan rasuwar salisu.

Da sauri malam Umar daya fahimci tunanin dake zuciyar Alhaji buharin yace"

'yar Hadiza 'yar halak ce
'yar sunna Dan kuwa cikinda salisu yabarta dashine muma sai daga baya muka Ankara da hakan Dan haka 'ya 'yar halak ce
Uwarsu daya ubansu daya da Abdulsamad gashinan zaun....." Ya qarasa fada Yana waiwayawa Inda Abdulsamad ke zaune sai kawai sukagansa zube baya numfashi da alama ya jima da sumewa Basu saniba sbd tashin hankalin da kowa yake ciki.

Arikice Alhaji buhari yayi kansa shida malam Umar suna Kiran sunansa Amma da alama ba sumar kadai yayiba kaman harda attack yasamu.

Innalillahi wainnan ilaihrrjiun""Alhaji buhari yake fada Yana kamo Abdulsamad din da qarfinsa
Ba arziki Dole zaman bayanin yaqare sukai asibiti dashi hankali tashe.

Bayan fitarsu kallon Abbi Alhaji babbah yayi yana nazarin halin tsananin damuwar dayake ciki da rashin ta Ina zai Kama wannan rakitaccen Al'amarin.

Tausayinsa ne Dana Abdulsamad ma dayafi kowa tausayi yanzu Dan yasan Al'amarin zai daki yaron sosai sudai dama saukinsu da hamdalar dasuke shine da baa daura aurenba da komai yafi lalacewa uwa daya uba daya.

Bayason qarawa MAJEED damuwa da wasu zantukan Dan haka ya taqaita da cemasa,

"MAJEED kaje gida kasamu ka nutsa kanka ya sake kafin shima Abdulsamad asamu lafiyarsa saiku zauna duka kuyi taron fahimtar juna,

Itama yarinyar kada kace zaka kasa karban wannan qaddarar sbd ko ahakan Allah ikonsa ne ya nuna,
Haisawa sukace matar mutum kabarinsa
Allah yayi itace matarka shiyasa Bai baka ikon aureba tun kuruciya har gashi manyanci nason zuwa hakama rabon zamtowarta matarka ya hadaka da mahaifiyarta harta dawo hannunka dan ka tarbiyantar da matarka da kanka Dan haka shi Allah Babu ruwansa idan ya jarabta mutum to akwai tanadin dayayiwa wannan bawan idan har yayi tawakkali yacinye wannan jarabawar.

Allah yasa mudace,
Allah Kuma yabaku zaman lafiya yasawa wannan auren albarka.

"Amin" CM ya amsa adduar ta Alhaji babbah Yana cewa"

Allah yaqara girma.

A natse MAJEED shima yayiwa Alhaji babban godia kafin suka fito.

Dayake da lafiyayyar Lexus din CM sukazo Dole shine ya maidasa gida.

Suna Isa gidan Yana ajiyesa harabar gidan yakira matansa yace kowaccensu ta fito su koma gida sbd yasan ba qaramar rigima zaayiba idan zancen auren ya Isa cikin gidan tunda duk matane bare ita kanta Inayah din
Gwara idan zatai Rigimar ya Zama ba kowa a gidan.
##MAMUH#
#LOVE/MARRIAGE/ROMANCE#




_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

Shedar biya👇
07040727902

MTN card👇
09134848107
[10/31, 10:10 AM] +234 803 697 6096: *_32_*
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
Private hospital din dake anguwarsu Alhaji babbah aka kaita sbd kafin suce sunje AA specialist wato private hospital dinsu akwai nisa daganan da hakan suka tsaya tanan kusa.

Cikin gagawa suka karba Inayah din
Neesah ma bata barmusu aikinba su kadai da ita sukayi Dan sunada fahimta tana sanar dasu itama likitace suka barta ta taimaka musu tunda dama itace kusan tasaba taimakawa Inayah idan irin hakan ta taso.

Umma yaganah gabaki daya kanta neman sake cakewa yakeyi da wannan Al'amuran daketa faruwa daga wannan sai wannan,

Har cikin ranta takejin kauna Mai tsafta da tsanani akan MAJEED da Inayah sbd sune danginta itace danginsu Dan lokuta da dama sukan mantama basuda alaqar jini da juna.

Badan a yanda yanayin komai ya fallasa kansa ba lokaci daya ba zato ba tsammani da Babu Wanda zai kaita murnar Auren MAJEED datake addua da fatar gani tsawon shekaru.

Hakama auren Inayah wani babban burinta ne shima datake fatan Allah ya nuna Mata ya cika a yau din
sai gashi Allah yacika Mata burin Auren dukansu a yanayinda Babu wanda yataba tsammata,

Ku kansu basuma San farin ciki zasuyiba ko damuwar sanin ba Abbi ne ya haifi Inayah ba.

Anty Hafsat ma zuciyarta kusan Kashi Kashi take kasuwa tana rarraba Mata tunani sbd ayanzu Bayan Jin bayanin yanda Al'amarin yake daga bakin Alhaji babbah taji zuciyarta na farin ciki da auren Dan kuwa Inayah Allah yayimata kyakkyawan sauyin dayafi duka tarin mazan data rasa abaya sbd Abbinta yakai kowanne level da ake kwadayin namiji yakai badan tashin hankalin halinda Inayah tashigaba da a fili Zata fara bayyanarda farin cikinta akan wannan tsintar damu akala da Inayarsu tayi Dan kuwa Abbi kam Masha Allah.

Sbd wadda tasaba ji da matsalarta na kusa yasa ma'aikatan asibitin Basu Sha wuyar taro yanayinta ba tadawo hayyacinta saidai take bacci ya dauketa sbd kusan wannan attack din yafi wainda tasaba samu abaya.

Kwantawa hankalinsu yayi ganin tadawo daidai tasamu bacci Amma kallo daya zakawa fuskarta ka gano baccin na tattareda yanayin firgici data shiga.

Suna zaune a dakin datake anty Hafsat na kokarin daidaita ACn dakin da yayi yawa umma yaganah Kuma na zaune tana kokarin amsa wayarta da Mimi ke Kira saigashi ya iso yashiga dakin cikin nutsuwa sanyeda Lululemon wears har lokacin da alama Bai tsaya sauyawaba zuwa wasu manyan kayan.

Fresh skin dinsa daya bayyana sosai cikin kayan anty Hafsat da Neesah suka kalla suna sake tabbatarda kyau da tsarin da Allah yayiwa Abbin
Take suka sake Jin tabbas ta wannan fannin Inayah Dinsu tagama dacen miji illa kawai baqin cikin dazata Shiga sanin Abbinta datafi so fiyeda komai baida alaqan Jini da ita
Tsintar yayi,kyautarta akai Masa kokuma tayaya ya sameta Allah ne kawai yasani saishi da umman Abdul din.

Cikin girmamawa anty Hafsat da Neesah sukai Masa sannu da isowa

Da qaramin sauti ya amsa Yana dan kallon Inayar kafin ya kalli anty Hafsat sbd umma yaganah na waya yace"

Doctors din sungama dubata ne?

Neesah ya nisan yanayin nata?

Firgici ne kawai data shiga ya daketa sosai Amma Inshallah lafiyanta kalau yanzu anmata allura ne sbd tayi baccinda kanta zai Dan warware ya rage Mata tashin hankalin.

Gyada Kai yayi ahankali tareda sake kallon Inayah datai wani iri cikin lokaci qanqani.

Dan gajeran numfashi ya sauke tareda juyawa yafita zuwa ganin likita Dan bayason ta kwana a asibitin gida zasu koma tunda suna tareda qwararrun likitoci a gidan.

Fitarsa da mintuna biyar sai gasu Mimi sun iso asibitin a gigice sbd tashin hankali biyu,
Na farko Jin auren MAJEED da Inayah dakuma Jin uwarsu daya ubansu daya itada Dr Abdul ga qarin halinda Inayar tashiga.

Jigum jigum sukai a dakin wasunsu na sake Dan jajanta wannan alamari da masu godewa Allah da baa Riga an daura aurenta da Dr Abdul dinba dan da abin yafi lalacewa.

Umma dai bayan taga Inayah ta tashi babu abinda take fata Dan ita kanta yanzu tanajin dacin da Inayah Zata Shiga,.

A sanin dataiwa Inayah kuka da baqin cikin dazata Shiga na zaman Abbi ba mahaifintaba zaifi Mata ciwo da radadi fiyeda auren Dan kuwa tafi buqatan ace alaqar jini suka hada Bata auratayyaba.

Har yamma lis suna asibitin Inayah Bata farkaba sai magriba.

Tana farkawa takasa kallon kowa a dakin sbd yanda duk sukai jigum jigum yabata tabbacin abinda yafaru kafin zuwanta asibitin Gaskia ne haqiqanin Gaskia Kuma Dan haka Batasan ta Ina Zata fara bayyanarda babban abinda takeji tokare da zuciyarta da maqoshinta.

Cikin kulawa da sanyin jikin yanayin da Inayah din ta nuna umma yaganah da Anty Hafsat suka fara kokarin magana saiga shigowar Abbi Wanda Yana shigowa qamshinsa ya gauraya dakin suka tsit suna jiran abinda zai faru Kuma ga Inayah din ga Abbi a amatsayin ma'aurata.

Yanayinsu yasashi basarwa tareda Dan kamewa ya kalli Inayah data dago ta zuba Masa Ido tana Neman fashewa da kuka yace"

Kina farkawa Kuma Zaki fara wani kuka agurin.

Neesah dake gefenta ya Dan kalla yace"

Ku shirya gida zaa koma da ita yanzu.

To" Neesah tace tana kallon Inayah din dake kokarin fashewa da kuka Amma takasa sbd abun datakeji ya girma qwaqwalwarta.

Juyawa yayi ya fice suka biyo bayansa.

Anty Hafsat motar CM zatabi itada Mimi da Safnah
Su Kuma su Inayah din motar Abbi zasubi Dan haka suka nufa motar Kai tsaye umma yaganah na riqe da hannun Inayah dake kokarin zubewa sbd tangadin datake na Bata cikin cikakkiyar nutsuwarta.

Kaman yanda suka Saba fitarsu da Abbin idan takama Inayah ce a gaba Dan haka yau dinma itace agaba sai umma da Neesah a baya.

Bayan sanyin Ac na motar da qamshinsa daya cika motar Yana zagayawa Babu Mai ko motsi acikinsu kaman ba kowa a motar kowa da tunanin daya shiga Banda Inayah da har lokacin qwaqwalwarta Bata fara aiki daidai ba dif take Bata ji Bata gane komai yanzu.

Suna Isa gida Dole Neesah ce ta kamota suka nufi ciki tana kokarin kaita bedroom dinta ta qwace Takoma Palo tana kokarin bin bayan Abbi cikin dimauta tana cewa"

Abbi ne kawai zaifadamun Gaskia na yarda da abinda duk ake fada,
Abbina ne kawai zan yarda da maganarsa.

Da sauri umma yaganah ta riqota tana cewa"

Ki nutsu Mana Inayah,
Me zakije kice Masa yanzu?
Bakiji anfada Miki yanzu mijinki bane,
Qarya zamu taru mu Miki ne?
Alhaji babbah zai Miki qaryane?
MAJEED din dakikeson saiya fada Miki komai Yana cikin damuwa sosai bakya gani?
Zaki sake daga Masa hankali da kukan Nan nakine idan kikace rikicewa zakiyi.

Rikitaccen Kuka ta fashe dashi Mai tsananin qunci tana cewa"

Ni bazan yardaba wlh abbin ne mahaifina,
Banason kowa a mahaifi sai Abbi,
Har umman Abdul din banaso amatsayin uwa Ni Abbi ne kawai uwa Kuma ubana...

Da sauri umma ta rufe Mata Baki jikinta na rawa sbd jikinta daya fara sanyi itama da irin kukan da Inayah din fasawa Wanda tunda take Bata taba yin irinsaba sai yau.

Rirriqeta sukai ta zube qasa tana sake tsananta kukanta zuciyarta na Mata wani irin zafi da radadi...

Idan ba abbine mahaifinta ba ai ita asaran duniya da baqin cikin duniya tana cikin cikinsa da wannan mummunan labarin da gwara ayita fasa aurenta har abada akan wannan labari...

Bazata taba yarda da maganar kowaba sai taji daga Abbinta cewa gaske bashine ya haifetaba.


Dukkanin sautin kukan datake yanajinsu Amma Bai iya zuwa Inda suke dinba Dan kusan yafita baqin ciki da wannan bankadar,
Dan yaso ya tsaya a ubanta na har abada saidai qaddara Bata bar hakan ba Dan kuwa Koda warware auren Nan akayi har abada ita zaa Kira da matarsa ta farko wadda tafara daukan igiyoyin aurensa haka itama har abada shi zaa Kira da mijinta na farko daya fara riqe martabar aurenta.

Kuka Inayah da tashin hankali sosai tashiga lokaci daya Wanda ya gigita umma yaganah da Neesah harma dasu zubbi da Salimat sun Shiga tashin hankali da damuwa sosai ganin halinda Inayah din ke ciki

Ta bangare daya shi kansa Mai gidan babu Wanda yakuma ganinsa har washe gari,

Abincin gidan ranar haka aka daukesa aka fitarwa Bosco ya rarrabawa securities din anguwar abokanansa sbd Babu Mai nutsuwar cin wani abinci.

Da zazzabi Mai zafi Inayah ta kwana Dan kaman yarinya qarama Takoma musu daqyar baccin wahala ya daukeda jikinta da mugun zazzabi.
MAMUH#
#LOVE/ROMANCE


_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

Shedar biya👇
07040727902

MTN card👇
09134848107
[10/31, 10:10 AM] +234 803 697 6096: *_31_*
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
Sake Shan jinin jikinsu dukkaninsu sukayi Jin cm yace sufito atafi gida Nan suka sake tabbatarda ba lafiyaba
Amma Kuma bilyamin qanin Anty Hafsat ya tabbatar musu da an daura aure,
To Kuma menene matsalar?
Sudai koma menene suna ganin da sauki idan har andaura auren Inayah da Dr Abdul dinta.

Ita kanta Inayah data dawo hayyacinta tuntuni zaune take tana jiran ta Inda labarin halinda aurenta yake ciki zai bullo.

Lokacinda bilyamin ya sanar dasu cewa andaura auren wani irin Al'amari taji atattare da ita shi ba farin cikiba hakama ba baqin cikiba
Tadaisan jikinta ya mutune kawai Dan haka daqyar ta iya sauya Kaya kaman yanda su Anty Hafsat suka takura Mata sbd Ango na tafe da jama'arsa suyi hotuna takuma gaisa da abokansa da zasu bi jirgi a ranar su koma.

Tafiyar su Anty Hafsat shine ya fara daga hankalin umma yaganah harma da Inayah Dan haka da kanta ta Kira cm din a waya tace Inayah tace Dan Allah abar Mata Hafsat da Safnah har zuwa anjima.

Bai Musa ba yabar Anty Hafsat da Safnah Dan haka gidan yayi tsit daga umma yaganah sai Anty Hafsat da Safnah da Neesah
Dr farhat ma ta tafi gida sai zaa wuce da Inayah din tace akirata.

Babu Mai wata doguwar walwala acikinsu sbd sudai anbarsu a duhu basusan meyake faruwaba sai jiran tsammanin zuwan Ango da jama'arsa suke Amma basuga alamar hakan Zata faruba ga wayarsa da Inayah ke Kira kaman zata zare Amma batama shiga kwata kwata.

Sanin Abbi yadawo yasa ta miqe jiki mace ta nufa gefensa tana sake trying din Abdul.

Kodata Isa knocking daya tayi tabude kofar tashiga daukeda sallama Mara sauti sosai.

Baya Palo da alama Yana bedroom dinsa Dan haka ta zauna kan kujera tana sake trying din Abdul.

Tunanin Kiran ummansane ya shigota ta nema numbern umman aikuwa tafara ringing.

Harta katse baa dagaba Dan haka ta fara rubutawa Abdul text.

Kofar bedroom dinsace ta bude Dan haka ta dakata rubutun tareda dagowa tana kallon kofar.

Sanye yake da ash Lululemon wears navy blue dasuka fidda hasken fatarsa sosai da alama wanka yayi ya shiryo cikin kayan Dan samun nutsuwa,
Qamshinsane ya gauraye palon take ya qaraso da yimata kallo daya yanajin wata qululuwar damuwar auren da aka daura Yana dawo Masa.

Cikin

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login