Showing 6001 words to 9000 words out of 55760 words
lokacinda ta shigo tsakiyar gidan daukeda kayanta kamar sabuwar bokanyar datayo gudun hijira.
##MAMUH#
#LOVE#
#ROMANCE#
##INAYA A MAJEED ABBI#
IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
09134848107
[10/15, 3:51 PM] Mariyamah: *_INAYAH_*
_Mamuhgee_
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
4
Inna ce dake kokarin fitowa bandaki riqeda mama ta amsa sallamar Kai tsaye batareda ta Gama tantance waye me sallamar sbd hankalinta gaba daya dake kan Mama data riqo wadda ko tsayuwa Bata iya yi Dan jikinta matuqar sosai yayi tsanani a kwanakin.
Sai data fito tsakar gidan da kyau ta dago tana sake amsa sallamar da hadizar takuma tana kallon mahaifiyarta data sauya kamanni gabaki daya sbd tsanani da azabar ciwo.
Hawayene suka ciko idanuwanta da sukai zurfin Rama da irin kukan rayuwar datake ciki ta dago qafafuwanta dasukai Mata sanyi da nauyi ta tunkarosu tana Dan kasa kallon cikin idanuwansu da suka zuba Mata dukkaninsu.
Inna da qafafunta suka kusa sakewa sbd tsananin mamaki da faduwar gaba
A 'dan rude muryarta na gwamutsuwa tace"
Hadiza kece Wannan a tsaye???
Jin hakan yasa mama da Bata gane kowa sosai ta Dan sake riqe hannun innar tana bude idanuwanta ko zata sake ganinta da kyau
Sai idanuwanta suka sauka kan tsohon cikin gaban hadizar
Ta Dan motsa kadan tana bude Baki cikin sanyin ciwo tace"
Lami?
Kasa amsawa Inna tayi sbd idanuwanta data kasa daukewa kan tsohon cikin Hadizar.
Lami?
Wace hadizar Kika ambata?
Hadizata ce tadawo?
Itace Wannan a tsaye?
wani busasshen yawu Inna ta hadiye tareda sake riqo mamar da kyau sbd hannuwanta dataji suna sanyi da daukar rawar tashin hankali mugun ganin datai safiyar fari.
Dakyar ta qarasa da maman kofar dakinta tana kokarin kwantarwa kan shimfidar datai Mata a wajen
Maman ta Dan janye tana waiwayowa ta kalli hadiza da har lokacin take tsaye a inda take cikin mutuwar jiki da qamewar zuciya.
Hadiza?
Hadiza kece agurin tsaye?
Sai alokacin ta daqo qafafunta ta janyo jiki ta qaraso gaban mamar ta zube tareda fashewa da wani irin kuka dukkanin zuciyarta na Mata wani irin radadin qunci da damuwa da baqin ciki.
Kukanta ya tabbatarwa da maman tabbas hadiza ce kuma cikine ajikinta ta samo ta dawo dashi.
Cikin rawar murya ta firgici Inna tace"
Hadiza cikine ajikinki?
Ba musu ba Jan dogon yanayi ta dago jajayen idanuwanta ta kasa kallon innar ta bude Baki murya a shaqe tace"
Eh.
Hadiza Ina nufin ciki fa na haihuwa?
Kuma amsawa tayi da "eh..
Hadiza daga Lagos fa kikaxo da Wannan cikin.,
Aure kikai acan bamu saniba?
Girgiza kai tayi ahankali tareda cewa"
Aa inna,Amma wallahi tallahi......
Zubewar innace da sautin salatin Yaya Umar Mai qarfine yasa maganarta yankewa hankali tashe ta dago tana kallonsa idanuwanta jajir.
Inna gurin mama ta nufa tana Kiran sunanta,
Aishatu?
Aishatu? Aishatu Dan Allah karki kashe kanki sbd wannan mugun abun kunyar da hadiza tadauko,
Innalillahi Aishatu Dan Allah karki tafi ki barni banida kowa,
Malam ya tafi ya barmu ke kadai Kika rage karki tafi ki barni.
Kuka Inna ta fashe dashi tana Kiran sunan inna data jima da somewa.
Sabon tashin hankali hadiza tasamu kanta aciki
Da sauri tayi kan maman itama tana kiran sunanta cikin mummunan mawuyacin hali sbd ita kanta tanaji batada lafiya.
Wani Mummanan Marin Rashin Imani da baqin ciki Umar ya sauke Mata lokaci daya Yana kallonta a qazance ransa a matuqar bace yace"
Karki kuskura ki tabata,
Shekara kusan biyu kena bakya gida
Bakizo musu da kudin dakikaje nemaba sai tsohon cikin banza¿
Gashinan Zaki kasheta lokaci daya da baqin ciki,
Tashi na daina ganinki wlh kafin na illataki daga ke har abin banzan da kike dauke dashi.
Yanda yayi maganar a tsananin fushi da bacin Rai har Yana sake yowa Kanta yasata Jan jiki tayi can gefe tana wani irin kukan zuci Mara sauti.
Kwasar mamar sukayi sukai cikin daki da ita sai firfita Inna ke Mata tana kuka Wanda yake na firgici da tsoron halinda Aishatun zata shiga dakuma zallar baqin cikin al'amarin da hadizar take tafe dashi.
Duk dubarunsu da ruwa dasuka ringa shafa Mata Bai saka ta farfafo saima qarasa rikicewa sosai da jikin yayi gabaki daya.
Hankalinsu duka yatashi Dan haka dole Yaya Umar din ya fidda waya yakira Yaya kabiru,
Shima rabon zaai gabansa ne yasashi zuwa gidan tunda asuba sbd ruwan da aka kwana ana zubawa yasashi tunanin gininsa da akeyi acikin gidan da baa kammalaba Wanda yasa ai masa daki daya da bandaki
amarya yakeson yi to anan zai kawota ya gwamutsa cikinsu innar.
Koda Yaya kabirun ya iso tuni innar tayi nisa Amma basuyi yunqurin kaita asibiti ba saima wani sabon tashin hankalin daya barke tsakaninsu sbd ganin hadiza ce silar koma meya samu mamar.
Kabiru buga rantsuwa yayi akan wallahi saita bar gidan da cikin,
Bazasu taba barinta ta zaunaba a gidan baqin cikin rainon ciki da goyon shege ya kashesu mama
hakama bazasu yarda ta Bata musu sunan dasukai gwagwarmayar samarwa kansuba lokacinda take Lagos tana zubarda mutuncinta da qimartaba.
Yaya Umar dinma bayan kabirun yabi akan Takoma inda tafito da cikin.
Rokonsu takeyi tana wani irin kukan tausayi da tsananin quncin datake ciki akan su yarda da ita Bata taba aikata Zina ba Amma Sam babu Wanda ya saurareta saima qara harzuqa dasukeyi da tsananin fushi da bacin rai,Yaya Umar Dukan mutuwa yakeson yi Mata Amma Inna dake kuka sosai ta Hana ta riqesa tana bayyanarda nata fishin itama.
Riqonsu tadawo yi akan su fito da mama akaita asibiti
Nan ne Umar yabi takan qafafuwanta ynaa neman tattakawa a fusace yace"
Uban waye Zaki fadawa akai mama asibiti? Lokacinda kike zubarda mutuncinki kinyi tunanin halinda zata shiga Idan taganki da wanna abun.
Kukanta qafewa yayi alokacin sbd a yanzu mahaifiyarta kawai takeson yiwa bayanin gaskiyarta,
Mahaifiyarta dake cikin mawuyacin hali takeson tabbatarwa Bata lalaceba Kaman ynada suke tunani.
Gurin Inna ta rarrafa tana roqonta akan subarta taga mama Dan Allah.,
Wallahi tallahi Inna ban taba aikata abinda kuke tunaniba,
Inna ku yarda Dani Dan Allah,
Wlh Inna cikina kwanci yayi sai yanzu yatashi,
Inna wlh cikin Salisu ne,Dan Allah inna ke ki yarda Dani.......kuka ta fashe dashi Mai tsananin ciwo tana sauke kanta sbd babu sassauci ko alamar yarda da ita atareda kowa.
Tashin hankalin data samu kanta dawowarta bata dauka zata tadda hakanba.
Duk wani sauki da rahama Bata samu daga yayyunta har innar ba qarshema haka ciwo ya tasar Mata Wanda tabbatar naqudace Amma tashin hankali yakasa barinta tanema guri ta nutsu ko haihuwarce zatazo.
Irin wulaqanci da tozarcin da yayunta sukai Mata bazai taba barin tasamu sassaucin nauyin zuciyarta ba har abada,
Sunkuma tabbatar Mata da wallahi bazata taba rainon cikinba a gidan bare haihuwarsa,
Idanma ta haifesa koko zasusa abasa yasha ya mutu su sun huta itama ta huta da renon 'dan da babu uba hakama shi kansa Dan ya huta da girma a duniya yatashi cikin gori da wulaqanci.
Masiface da tozarci Wanda ya haddasawa maqota sanin abinda tadawo dashi daga Lagos din suka ringa zuba Mata cikin fushi da bacin Rai,
Da yawa wasu sunshigo da sunan duba Inna Dan su tabbatarwa da idonsu cikin shege tayo daga zuwa Lagos....
Bata taba kukan Rashin mahaifintaba da Rashin Salisu kamar ayau datai wunin tsananin baqin ciki da danasanin tafiyarta Lagos sbd da agaban iyayenta cikin ya farfado da babu Wanda zaiyi Mata Wannan yankan qaunar.
Idanuwanta sunyi wani irin kumburi da Bata iya gani sosai.
Daddafawa tayi bayan tasamu dare yayi su Yaya Umar sunbar gidan ta shigo dakin da mahaifiyarta take ta zube gabanta Daqyar sbd tsananin azabar naquda.
Hawaye ne suka gangaro Mata takai hanunta dake rawa ahankali ta dafa na mahaifiyarta tareda rintse ido wasu hawayen na tsananta Mata gudu.
Kuka takeson yi ganin yanda mahaifiyarta ke numfashi ahankali alamar samun sauki saidai bazata kukanba Dan naqudarta tagama zuwa kusa,ta gyara zamanta da qyar tana hada wani irin zufan gaske tako Ina jikinta azababbiyar azaba takeji Dan haka ta damqe hannun mahaifiyarta da qarfi tana sake wani irin gurnanin Nishi tana Kiran sunayen Allah a azabance.
Inna na dakinta kwance zazzabi Mai tsananin gske ya kwantar da ita da wannan babbar masifar data kunno musu Kai Dan haka batasan meyake faruwa da hadizan ba.
Naquda Mai tsananin wuya da azaba takeyi gadan gadan
Tagama jiqewa sharkaf da zufa
hakama mama tuni tafara bude idanuwanta cikin tsananin ciwo,
Tanajin 'yarta na nakuda Kuma Mai wuya da azaba Amma babu abinda zata iya yimata hakama babu Wanda zai taimaka Mata...
Hawaye da 'dacin tausayin 'yartane ya gangaro gefen idonta
ta Dan motsa hanunta dana hadizan yake Kai ta kama hannun hadizar ahankali idanuwanta na zubowa da wasu hawayen masu zafin gaske.
Hadiza taji mamar Amma bazata iya magana ba ko juyowa takalleta saima wani wahalllen Nishin datake fitarwa tana fidda Rai ga rayuwa,.
Jin take da zata mutu agurin wannan naqudar data godewa Allah ta huta da Wannan rayuwar da babu komai acikinta sai qunci da damuwa.
Wani qaqqarfan Nishi ne yafara zuwar Mata Idanuwanta sukai jajir gumin na sake jiqota tako Ina...
Cikin dauriya da azaba tafara Addua sbd sanin adduar mace Mai naquda karbabbiyace inshallah.
"Ya Allah kaine masanin gaskiyata nida abinda zan Haifa,
Ya Allah ka albarki rayuwarsa ko rayuwarta Idan mace ce,
Allah ka tallafi rayuwar abinda zan Haifa ka datar dashi kyakkawar rayuwar kwanciyar hankali da nutsuwa.
Mahaifiyarta da 'danta Abdul take kokarin yiwa Addua Amma Ina mamar kawai tasamu damar rokarwa Allah sauki jariri ya kunno Kai Kuma adaidai lokacin mama Allah yabata ikon riqe hannunta kyau Dan sassauta Mata radadin datake ciki na kutsowar 'da ya fito ta jikinka.
Gabaki daya jaririn ya fado tareda sake lafiyayyan kukan jarirai ba kakkautawa.
Wani irin numfashi take saukewa da a wahalce tana Kai hannu inda jaririn yake ta dauko ta Dora jikinta.
Daqyar ta bude idonta dakyau ta Dan daga kafar jaririn taga 'ya mace ce
Take wasu hawayen suka gangaro Mata masu dumi,
Duk da hakan ta godewa Allah daya Bata abinda ta haifar Amma taso namijine sbd zaifi samun qwarin zuciyar fuskantar zunde da qalubalan maganar da zaa ringa binsa dasu na Kalmar 'da Mara uba.
Kukan jaririyar ne ya karade gida tako Ina
A gigice Inna ta taso ta fado dakin tana Kiran sunan hadiza.
Da mamaki da tausayi take kallon hadizar tana cewa"
Hadiza ke kadai Kika haihu acikin wannan halin?
Komawa tayi da hanzari ta dauko sabuwar Reza a dakinta tazo ta yanke cibin jaririyar tana kallon fuskar Yar da fitilar hannunta.
Bata iya cewa komaiba sbd batasan Mai zata fada ba,
Rayuwarsu cikin Rana daya Allah ya juya musu akalarta inda yaso dan haka take fatar Allah yabasu ikon cinye Wannan jarabawar.
Ruwan zafi ta Dora acikin tsakar dare tazo ta karba karba Yar ta wanke tas
Ta juyewa hadizar sauran ruwan itama ta lallaba taje tayo wanka tadawo.
Sauran tafasasshen ruwan hadiza ta karba Tasha sosai sbd babu abinci babu komai.
Komawa sukayi suka zauna jigum jigum babu Mai cewa qala.
Hadizar zaune take bakin shimfidar mama Idanuwanta dake kumbure ta zubawa jaririyar tana kallo duk da acikin duhune Bata ganin komai.
Hannu mahaifiyarta taji akan kafadarta
Ta juyo ahankali idanuwanta na Mata nauyi da radadi ta kalla maman cikin duhu ta bude Baki jikinta matuqar sanyaye muryarta a shaqe tace"
Mama 'ya mace ce na Haifa.
Wani sanyayyan numfashin da Baya fita sosai maman tasaki tareda janye hannunta kan hadizar ta bude Baki daqyar cikin yanayi na majinyaci Mai tsananin Jin jiki ta Kira sunan Hadizar.
##MAMUH#
#ZAFAFABIYAR#
#LOVE#
#ROMANCE#
#INAYA A MAJEED#
#AYSHATOUH#
[10/15, 3:51 PM] Mariyamah: *_INAYAH_*
_Mamuhgee_
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
5
Daqyar ta iya furta
"Hadiza Allah zai zama gatanki,
Allah zai raya Miki 'yarki cikin Aminci inshallah.
Allah ya Raya zuriarki ya sanyawa zuriarki albarka kinji¿
Hakama halima ki kula da ita tamkar uwar data dauki cikinki ta haifeki sbd dagani harku har abada bamuda abinda zamu saka Mata dashi akan halacci da kaunarta garemu,
Batada kowa saiku ku sauke nauyin uwa mahaifiya akanta kinji hadiza.
kasa kuka tayi sbd yanda zuciyarta taso tsayawa cak daga bugawa da sanyin kalaman mahaifiyarta,
Tunda mutuwa ta dauki mijinta Bata taba samun kyakkawar kalamiba daya taba zuciyarta sai yau da mahaifiyarta ta furta matasu adaidai lokacinda duniya da kowa ya juya Mata baya ana gudunta akan abinda daya sameta.
Cikin rawar murya dake son bayyanarda kukan dake kokarin yiwa kansa iso tace"
Mama kin yarda da bazan taba aikata abinda ake zargina dashiba???
Mamar Bata iya mgna ba saidai gyara kanta tayi ahankali tana rufe Idanuwanta dake lumshewa da kansu...
Kalmar shahada take kokarin furtawa a kakkarye
Hadizar naji ta tabbatarwa da kanta rasuwa mamar zatayi
Cikin sanyi da qarfin zuciya ta Bata sauran Kalmar shahadar
Cikin saa maman ta karba ta qarasa daqyar sbd Rai dayazo gangar fita.
Wata masifar a rayuwa fin karfin wata masifar take,
Idanuwanta da zuciyarta ne suka bushe Mata alokaci daya
Saidai wani irin gagarumin nauyi daya tokale zuciyarta ya tsaya a maqoshinta.
Hannnunta na cikin na mahaifiyarta ta cika,
Rintse idanuwanta tayi ahankali tana Jin nauyin Kirjin nata na tsananta
Ta miqe tsaye ahankali tareda aje jaririyarta a gefe ta matsa gurin inna dake qudundune gefe tana Nishin azababben zazzabi takai hannu ta tada ita tareda Kiran sunanta ahankali cikin sanyi tace"
Inna ki tashi Allah ya karbi ran mama...
Wani mugun yunquri Inna tayi tana tashi zaune idanuwanta a waje ta kalli inda mamar take tana qara hasken fitilarta tace"
Aishatu ta rasu kikace hadiza?
Yanzu nabarta akwance fa tana numfashi.
Miqewa tsaye tayi ta nufi maman hankali tashe tana cewa"
Ya akai kikasan ta rasu ne tunda ba ganewa zakiyiba.
Gaban gawar maman ta tsaya tana Kiran sunanta muryarta na rawa cikin firgici.
Data tabbatarda Aishatun ta rasu ficewa tayi daga dakin ta zauna tsakar gida tana rusa wani irin kuka Mai rauni.
Tun tanada shekara goma Sha uku Malam ya aurota daga qauyensu kasancewarta marainiya itada qanwarta Indo yazo ya kawosu Mama lokacin itama batafi shekara goma Sha biyarba ya hadasu suka zauna lafiya harya aurar da Indo itama.
Lafiya kalau sukai rayuwa da mama tamkar yaya da qanwa haka suka zauna harsukai wayo mamar ta hayayyafa su kabiru har manyanci da tsufa yakamasu suna zaune lafiya,
Basu qara kaunar juna na mutunta junaba saida malam ya rasu ya barsu
Ita Inna Batada kowa sai mama da 'yayan mamar da itace tayi renon kowannensu harya girma.
Yau aishatu ta tafi tabarta da tsananin kewa da kadaici adaidai lokacinda 'yayanta suke tsaka da rikicin da zai rabasu har abada Idan ba Allah ne ya kawo dauki ba.
Koda aka fito sallar asuba tuni su Yaya Umar da malam kabiru suka iso sbd Inna ta buga musu da 'yar qaramar wayarsu da hadiza ta siya musu tun kafin zuwanta Lagos wadda da ita take waya dasu.
Hadiza na zaune gefe cikin dakin da jaririyarta a dunqule suka shigo babu Wanda ya kalla inda take sukaiwa gawar mahaifiyarsu Addua suka fice Dan fara shirye shiryen jana'izarta da sauransu.
Jaririyarta data Kira da sunan AYSHATUH daidai bayan rasuwar mahaifiyarta sai baccinta takeyi sanyeda kayan sanyi farare tas data zakulo daga kayanta data Bari Nan gida tun kafin tafiyarta,
Kayan tun na Abdul ne Dan haka sun Mata yawa sosai amma tunda babu wani kayan haka ta Sanya Mata su.
Jamaar anguwa da koina sunji labarin rasuwar Mama Dan haka mutane sukaita shigowa cikeda alhini.
Tana dakin itadai Bata fitoba da jaririyarta sbd mutane zasu iya zunde duk da rasuwar da akai mata tasani
Dan haka ta kame kanta a daki Bata fitoba har akaiwa mamar wanka da sitira ta matso tayi Mata Addua aka
Dauketa aka tafi da ita.
Duk yanda taso kuka takasa zuciyarta ta bushe ta kafe da tsagwaron qunci da baqin ciki.
Saida Yan gaisuwa suka rage tana daki tafito taje tayi wanka da tafasasshen ruwan da Inna ta Dora Mata tana gurin wankan jaririyarta tayita kuka
Nan take Yan zaman gaisuwar suka fara yi da ita.
Haka tafito bandaki Takoma daki Bata Kuma fitowaba,
Wankanba itace tayiwa jaririyar da kanta sbd inna na cikin Yan gaisuwa.
Har dare Bata fitoba tana daki
Saidai taci abinci data fidda kudi tabawa innar aka siyo musu sukaci da daddare.
Washe gari take anguwa da jamaa suka dauka cewar haihuwar cikin shegen datai shine ya kashe mama da baqin ciki
Dan haka Take masifar gidan takuma tashi da daddare harta kwanta su malam kabiru suka shiga shida Yaya Umar sukace wlh saita bar gidan da 'yarta bazata rena 'yar datai sanadin mutuwar mahaifiyarsuba adakin mahaifiyar tasu.
Tunda mama ta rasu zuciyarta ta kafe Dan haka ta tashi ta hau tattara kayanta.
Kallonta Inna tayi tana cewa
"Ina Zaki ki barni hadiza?
Wasu siraren hawayen tsananin tausayin Inna ne suka gangaro Mata.
Inna abar tausayice tako Ina sbd barinta tamkar watsar da itane ga duniya Dan kuwa su Yaya Umar Basu tallafi mahaifiyarsu data kawosu duniyaba tanada Rai tayaya zasu iya tallafar rayuwar Inna da batada kowa batada komai...
To Amma ya zatai tunda ankoreta ita kanta,
Kuma ita kanta zataso tafiyar sbd yanda ake zundenta da qyamatarta da yarta tareda jifanta da alkaba'i daban daban akan itace tayi sanadin mutuwar mahaifiyarta.
Tana kuka ta tattara kayanta tabar gidan cikeda baqin ciki da quncin Rashin ganinta Abdul daya koma hannun hajiyarsu Salisu sbd jinyar da mama keyi Inna Batada lokacin kulawa dashi.
Inna kam itama kukanta daukewa yayi bayan tafiyar hadizar da sunaji suna gani su malam Umar ana gaman zaman gaisuwa ya Roshe dakin mama ya hade da wanda yafara ginawa cikin gidan ya fake da sunan zai kawowa Inna abokiyar zamane sbd kadaici.
Barin Hadiza gida ya rusa rayuwar Inna da ita kanta hadizar wadda batasan Ina ta nufaba.
ALLAH YA ZAMA GATAN MARAYA A DUK INDA YAKE..AMIN
**************
_March 2002_
_7:26am_
Kokarin saka Mata pink safa a qananun qafafunta yakeyi Yana dan sake waiwayawa yana kallon wajen dakin nasu dan duba yanayin garin dakeda hadari sosai Wanda tun bayan sallar asuba yaketa haduwa.
Ganin yanda duk tabi ta lafe masa tamkar Mara lfy yasashi dagowa ya kalli kyakkawar qaramar fuskarta dake kallonsa da idanuwanta dako yaushe zai kaita makarantar raino sai tayi wannna qyuyar wadda tun batai wayo hakaba takeda ita.
Batasan kowaba bayan mahaifin nata da a duniya batada kowa bayanshi Kuma Bata yarda da kowa sai shi din sai uwar renonta yagana wadda take kira da Ummey.
Cikin idanuwanta dasuka Dan Yi Kaman zatai hawaye ya kalla ya saki ajiyar zuciya ahankali Yana janyota jikinsa cikin lallausan muryarsa me zallan nutsuwa ya furta
_"INAYA.._
Hawayene suka fara gangaro Mata ta girgiza kai ahankali cikin Rashin budewar harshenta sosai tace"
_ABBI..._
cikin kulawa ya hanata fadar abinda yasan rigimace kawai zatayi sbd batason zuwa
Kuma ya saba da hakan tunda yafara kaita kullum saitai masa wannna rigimar.
Share Mata hawayenta yayi tareda miqewa tsaye ya dauki Yar jakar takardar dayake saka Mata robar ruwan pure daya dayake juye Mata a empty robar Coke sai fanke da kosan matar kofar gidansu daake soyawa na siyarwa.
Daukarta yayi ya riqe jakar a dayan hannunsa suka fito ya janyo kofar dakin tareda Sanya padlock dinsa ya rufe kofar dakin nasa ya juya ya nufi hanyar kofar ficewa.
Dukkanin jamaar gidan hayar dasuke gidan kusan kowa yafito Yana hada hadarsa a qatoton tsakar.
Da damarsu dasukaci karo da fitowarsa da mugun kallo suka bisa