Showing 9001 words to 12000 words out of 32935 words

Chapter 4 - KADDARATA

Start ads

11 Sep 2025

80

Middle Ads

kanina kayi kyau sosai"
knocking akayi yace "yes"
Ammi ce ta shigo sanye da alkyabban da bayan yake jan kasa, tasa hulan alkyabban akan gashinta da yasha gyara sannan tasa ɗankunne da abin goshi na gold, rike take da plate na flower a hanunta, saide fa fuskanta babu annuri ko kaɗan babu alaman murmushi, kaseem kallo ɗaya yayi mata ya kauda kai, hameed kuma ya zuba mata ido har ta karaso, tace "mai martaba yace mu fito tare an gama shirya komai kuma baƙi sun hallara"
kaseem yayi saurin sa kayanshi shadda maroon me masifan kyau, ya fesa turare sannan yasa hula maroon ya riko hanun hameed ɗin yace "muje"
tana bayansu suna gaba da plate ɗin flower a hanunta, suna fita su sultan da sukayi anko cikin maroon na shadda irin na ya kaseem ɗin suka zo suna mishi sannu, murmushin karfin hali kawai yake musu, minat da gudu ta sauko daga stair ɗin ɗakinsu tayi bala'in kyau cikin baƙin shadda irin wanda ammi tasa kafin tasa alkyabban, dogon riga ne fited gown sai red veil da tasa a gefen wuyanta, tace "wow yaya yarima kayi kyau"
murmushi yayi mata sannan ya fara kallon sama inda yake kin karan takalmi da kamshin turare, aneeta ce take takowa cikin tsoro ta damƙe karfen stair masha Allah tayi bala'in kyau cikin baƙin shadda, itama irin ɗinkin minat ne amma ya kama jikinta sosai hakan yasa take rufewa da red veil ɗin sabida bata saba sa kaya masu kama jiki ba, bata mantawa kullum mama cewa take kada ta rinƙa sa kaya masu kama jiki domin yanayin jikinta mai ɗaukan hankali ne, ya kasa ɗauke idonshi a kanta, kaseem da yake mishi magana yaga yana kallon waje ɗaya shima ya kalli inda yake kallo, murmushi yayi ya zuba mishi ido, har saida ta sauko kafin ya kauda kai daga kallonta, sai a lokacin ya kalli kaseem, da sauri ya sunkuyar da kai sabida kunyan kashe mishi ido da kaseem ɗin yayi, durkusawa tayi ta gaida kaseem ɗin tareda hameed ɗin, bai amsa ba ya ɗauke kai, ya kaseem ne ya amsa, ta gaida ammi ta amsa ba yabo ba fallasa, hanunta minat ta rike, kaseem da hameed ne a gaba su kuma suna bayansu, suna fita a falon suka fara taka red carpet ɗin da aka shimfiɗa me matukar kyau, duk bayi da dogarai suna tsaye a gefe gefe sun sasu a tsakiya kan red carpet ɗin, ammi ta mikawa ɗaya daga cikin bayin plate ɗin sannan ta fara watsa mishi flower, algaita ake hurawa tareda busa sarewa, masu kiɗin garaya suka fara, ana mishi kirari, da haka har suka isa inda zasuyi taron, makil mutane suka cika wajen, manya manyan mutane ne harma da kanana, mutanen gari dana nesa dana kusa duk sun hallara, tun daga nesa mai martaba ya fara murmushi ganin kyaun da hameed yayi, hankalinshi kwance yake idan ya mutu ya bar hameed ne zaiyi gadon sarauta hakan yasa yake gaggawan bashi wannan matsayin na yarima, har ya karaso ya durkusa kasa ya yiwa abi alaman gaisuwa, ɗagashi yayi ya zaunar dashi akan kujeran, flower aka watsa sannan aka tafa mishi domin ya zauna a kujeran yarima, su kaseem dasu ammi suna kujeran gaba gaba, gomna aka bawa waje ya fara jawabi, daga nan Abi yayi magana cikin nutsuwa, karɓan sandan hanunshi yayi ya aje a gefe sannan ya kalli sabon sandan da aka bawa gomna wanda dashi zasuyi amfani wajen mikawa hameed wannan girman na yarima, ɓare tsadadden sandan gomna yayi a leda sannan yazo gaban hameed ya tsaya Abi ya tashi shima yasa hanu akan sandan zasu mika mishi, hameed ganin baiwa rike da plate da kuma wuta kaɗan akai, ya zuba mata ido, jikinshi ne ya fara rawa, Abi ganin haka yace "relax hameed babu abinda zai sameka"
baya baya ya fara yana waro manyan idanunshi, girgiza kai ya fara kamar sabon mahaukaci, da sauri ya bige sandan zai gudu, ya kaseem dake zaune da gudu ya tashi yazo ya rikeshi, a kunnenshi yace "hameed ka nutsu cikin mutane muke"
girgiza kai ya fara yana kwace jikinshi daga na kaseem ɗin, fizge fizge ya fara yana nuna wutan, mutanen wajen kowa ya fara tsorata ganin halin daya shiga, take zufa ya jiƙa goshinshi, ya kaseem ya kankameshi sosai yana hanashi fizgewan, Aneeta da mamaki take kallonsu sai kuma ta kalli minat tace "me yake faruwa dashi haka?"
share hawaye minat tayi tace "baya son ganin wuta ko kaɗan ne, kuma...."
kuka ne yaci karfinta ta kasa karasa maganan, a hankali ta janyota jiki tana shafa bayanta alaman tayi hakuri, idonta akan hameed daya kasa nutsuwa zuwa yanzu kaseem yanaso ya gagara control nashi, ga mutane da suka fara tashi zasu tafi sabida abin ya fara worst, a hankali ta saki minat ɗin ta tashi, wajen taje zuwa yanzu ya fara kaiwa kaseem duka a kirji, cikin sanyinta ta rike hanunshi dake dukan kaseem ɗin, ɗago jajayen idanunshi yayi yana kallonta, addu'a ta fara yi mishi a hanun, ji yayi jikinshi yayi nauyi, kaseem ganin ya ɗan nutsu ya fara sauke ajiyan zuciya, cikin sanyinta take addu'a tana tofa mishi, a hankali kaseem ya sakeshi tana rike da hanunshi, ji tayi ya faɗa jikinta ya kanƙameta kamar zai maidata cikinshi, bata damu ba taci gaba da karanta addu'o'i masu karfi tana tofa mishi a kunne da kuma kanshi, saida yayi shiru kamar wanda yayi bacci kafin ta tofa addu'a a hanu sannan ta zameshi daga jikinta ta shafa mishi a fuska, kallon baiwar dake rike da plate da wuta a kai wanda ta zuba turaren wuta tayi, da hanu tayi mata alaman ta tafi da wutan a wajen, tafiya tayi da wutan, a hankali ya dawo hayyacinshi ya kalli inda wutan yake yaga babu, kallonta yayi tayi mishi murmushi tace "babu wuta ka koma ka zauna"
a hankali ya koma ya zauna yana kallonta, ya kaseem ya share zufa yace "ya Allah"
gomna wanda ya ɓuya a bayan kujera ganin ya daina abinda yake ya fito yana neman sandan daya wurgar a gefe, ɗauka yayi yazo sarki ya tashi ya rike shima har idonshi yayi ja saboda halin da ɗanshi ya shiga, bashi sandan sukayi sannan sarki yace "YARIMA HAMEED"
tafi akayi kowa yana murna, murmushi jabeer yayi yana tafa mishi, kowa ya shaida shine yarima, hulan kanshi aka cire sannan gomna ya ɗaura mishi rawanin sarauta nan take ya kara zama me kwarjini na musamman, tafa mishi ammi sukayi, da haka aka gama taron.

kowa sai zuwa yake yana gaisawa da hameed tareda mishi congratulations, saide yayi murmushi ya gyaɗa kai da haka har taro ya watse, cikin gida suka koma su duka, kaseem wanda jininshi yake tafasa yana kallonsu da tsananin ɓacin rai akan fuskanshi yace "wallahi ban taɓa rantsuwan karya ba wannan abinda ya faru set up ne"
Ammi wacce take huci tace "set up kamar yaya kaseem? baka ganin turaren wuta ta kawo?"
idonshi sunyi jajur yace "turaren wuta? waya sata? dama ana kawo turaren wuta wajen naɗi ne?"
tace "to kaseem wa kake zargi?"
itama tayi maganan ranta yana tafasa kamat idanunta zasu zubo waje, kallonta yake babu ko kyaftawa yace "koma wa nake zargi babu ruwanki kuma na rantse idan har na tabbatar da wanda ya shirya wannan abin wallahi sai na hukunta meshi koma waye shi"
da ihu yake maganan kamar zai fasa gidan, fita yayi daga ɗakin, hameed ya zube kan kujera yana rike kanshi ya tsani tashin hankali, ya tsani ihu jininshi hawa yake idan ana hakan, babu jimawa kaseem ya shigo hanunshi rike dana baiwar data kai wutan wajen yana janta kamar zai cire hanunta daga jikinta, wurgi yayi da ita a falon ya nunata da yatsa, jijiyoyin kanshi sun tashi yace "na rantse da Allah, na rantse da ubangijin daya halicci sammai da kassai idan har baki gayamin waye ya saki wannan aikin ba saina kasheki"
Aneeta dafa kirji tayi jin abinda ya faɗa tayi baya a tsorace, bakin baiwar ya fara rawa, ya taka hanunta dake kasa yace "zaki gayamin ko ba zaki faɗa ba?"
rufe ido ammi dasu minat sukayi ganin yadda ya taka hanun babu tausayi, ihu tayi ya sauke mata marin da yasa tayi shiru sabida azaba ya kara taka hanun wannan karon idanunsa kamar zasu zubo kasa yace "zaki faɗa ko saina kashe ki?"
jikinta yana rawa ta kalli Ammi, da sauri Ammi ta juya baya, ya kalli inda take kallo ya kara taka hanunta wannan karon saida ya fara jini yace "zaki faɗa ko kuma?"
ganin ba zata faɗa ba ya cire kafanshi daga hanunta a fusace ya haura stair da mugun gudu ɗakinshi ya shiga babu jimawa ya fito da bindiga karami a hanunshi, waro ido hameed yayi, sultan ya ɗaura hanu aka zaiyi ihu yasa hanu a baki ya toshe, Aneeta fitsari ne kawai bata yi ba, duk hantar cikinta ya kaɗa, batasan time ɗin data kankame hanun minat ba, tunda take bata taɓa ganin me zuciya idan ranshi ya ɓaci kamar kaseem ba, nunata yayi da bindigan yace "idan na irga uku baki faɗa ba wallahi saina harbeki"
jikinta yana rawa tace "zan faɗa"
duk suka kalleta a tsorace kenan da gaske sata akayi?
yace "ɗaya...biyu...."
tace "A..."
kafin ta karasa ammi ganin yace "three"
taje da gudu zata buge bindigan ba tareda ya cire hanu ba bindigan ya tashi take goshin baiwar ya fashe da bullet ɗin daya fasa mata har ƙwaƙwalwa, tsit ɗakin yayi babu wanda ya kara koda numfashi me kyau, bindigan rike a hanunshi ita kuma ammi tasa hanu a baki ta rufe idanunta a waje, Aneeta kuma fitsarin da take rikewa ji tayi kamar ma ya zubo, minat kuma tasa hanu aka ta kasa fasa ihun, hameed rufe ido yayi tareda kunnenshi ya toshe, Abi daya shigo yanzu ya kasa maida kofan ya rufe, jikin hameed ya fara rawa ganin ya jabeer baiyi dana sanin abinda yayi ba domin ko gezau baiyi ba bale yaje ya duba ko tana raye ko ta mutu, sunfi minti goma sha biyar a haka, da kyar ammi taja kafarta da yayi nauyi taje inda take kwance tana kiran sunanta "A'isha? Aisha?"
da ihu kamar zata fasa gidan tace "A'ishaaaa?"
kanta ta ɗaura akan ruwan cikinta tana kuka, ɗago jajayen idanunta tayi tana kallon kaseem da har yanzu yake rike da bindiga, cikin ihu tace "meyasa ka kashe ta?"
murmushin gefen baki yayi yace "na kasheta? ko kuma kika kashe ta ba? ai da gangan kikazo kika bige bindigan sabida nayi harbi ban saniba"
tana kallonshi da mugun mamaki har ta karaso wajenshi, hanu tasa ta shaƙe wuyanshi tace "akan me zan kasheta? me zaisa na kasheta?"
tureta yayi yace "sabida bakyaso ta faɗi wanda ya sata"
tace "kana nufin ni kake zargin na sata taje da wuta wajen naɗin hameed ɗana sabida ya fita hayyacinshi? ɗana dana san ganin wuta yana iyasa ya rasa rayuwarshi?"
yace "kin damu da rayuwarshi ko mutuwanshi ne?"
kara shake wuyanshi tayi tace "kaseem kana nufin nice nasa taje da wuta?"
yace "idan bake bace me yasa kika kashe ta? sannan kalman A ba Ammi yake nufi ba?"
tureshi tayi ta kwala ihu cikin tashin hankali tace "kaseem ni kaɗai ce me farin suna da A a wannnan gidan? ni kaɗaice?"

Juya baya yayi yace "ke take nufi"
cikin zafi da raɗaɗin rai tace "Abi shine sarki Abdallah ba A bane? Aminat itace minat ba A bace? Abdulhameed shima ba A bane? ko kuma wannan bakuwar da kuka kawo itama ba Aneeta bace A ce ko ba A ba?"
da ihu tace "kaima ba A bane? ko ka manta asalin sunanka Alkaseem ne?"
shima da ihun kamar zai fasa ɗakin yace "sunana ba Alkaseem bane sunana kaseem ne"
tana kallon cikin idonshi tace "ba zaka taɓa canjawa tuwo suna ba kaseem sunanka na gaskiya shine Alkaseem"
jikinshi yana rawa yace "karki kara kirana da Alkaseem"
tana huci tace "idan kuma na kara fa me zakayi? me zakayi Alkaseem"
ganin yana nufota Abi wanda ya gama sankarewa a wajen yace "kaseem!!!"
tsayawa yayi yana huci, yace "ko taku ɗaya idan ka kara zan tsine maka"
bai kara ko taku ɗaya ba kawai ya juya baya, ammi tana kuka tace "kowa ya manta da baya, nice kaɗai ake ganin laifina kowa ya manta da abinda ya aikata a baya, wallahi tallahi saina tona"
sultan yace "please ammi dan Allah kiyi shiru"
tace "nayi shiru sultan? nayi shiru ana zargina? bayan kowa abin zargi ne a gidannan, har an manta farin sunan kowa nice kaɗai aka tuna nawa? ko kun manta wanda yake kulle a bayan gidannan shima ba A....."
kujeran da hameed yake zaune akai ya ɗaga da karfi ya buga da kasa jin abinda ya faɗa, duk suka kalleshi a firgice, huci yake yi jikinshi yana wani irin rawa yana kallon ammi da idanunshi da suka rikiɗe suka koma jajur, take ya canja daga hameed ya koma asalin Abdulhameed, ammi ɓuya tayi a bayan sultan ganin yadda kujaran ya karye ga kuma hanunshi daya dunƙule yana huci sosai kamar zaki.

_Jiddah Ce...✍️_
08144818849
[20/08, 2:11 am] Shuraihu Usman: 🌸🌸🌸🌸🌸
*ƘADDARA TA*
🌸🌸🌸🌸🌸


Na
*Jiddah S Mapi*


*Chapter 5*


~Babu abinda yake cin ranshi kamar maganan dake bakinshi wanda ba zai iya faɗanshi ba, Abi ganin haka yazo da sauri zai taɓashi yayi baya yana girgiza kai alaman baison kowa ya taɓashi, Abi yace "hameed dan Allah kayi hakuri"
juyawa yayi a fusace yaje wajen kaseem, bindigan ya kwace ya saita kanshi, waro ido kaseem yayi ganin yana huci yana shirin harba bindigan, Aneeta cikin tashin hankalin da tunda mama da baba suka haifeta bata taɓa gani ba tace "dan Allah kada ka kashe kanka dan Allah"
ya kaseem yace "hameed kada kayi wannan kuskuren wallahi idan ka kashe kanka shima saina kashe shi"
hawaye ne suka fara wanke mishi fuska ga magana amma babu bakin faɗa, ganin da gaske yake kaseem ya buɗe drower dake bayanshi kusa da tv, ciro bindiga yayi ya nufi waje, a kiɗime ammi tace "kaseem ina zakaje?"
juyowa yayi ya kalli hameed yace "kina ganin idan hameed ya mutu zan kyaleshi ne? kafin ya kashe kanshi saide su mutu a tare"
hameed bindigan yasa hanu a kunaman ya harba, Aneeta da tazo da gudu ta rungumeshi ta wurgar da bindigan gefe kafanta bullet ɗin ya sama, kara tayi cikin azaba ta kanƙame hameed da suka zube kasa tare, akanshi ta faɗi hakan yasa ya rike waist nata sosai idonshi a rufe, jigidan dake waist ɗinta yaji hanunshi a kai, cikin kuka tace "kafata"
kaseem ne ya wurgar da bindigan yazo da gudu ya ɗagata yana duba kafarta dake jini, ammi hawaye ta share tace "shikenan tunda nice yanzu abin zargi kowa ya manta da laifinshi wanda aka lulluɓe sabida muninshi kafin ku kashe junanku ni bari na kashe kaina"
Abbi dake tsaye yana jin kanshi da nauyi ya lumshe ido a wahale ya buɗe yana kallonta ta ɗau bindigan, sultan ne yaje ya rungumeta ya kwace bindigan yayi wurgi dashi, tace "sultan mutuwana shine alkhairi, sultan komai baya tafiya daidai komai baya gyaruwa sai daɗa ɓaci yake, sultan watakila idan na mutu komai zai daidaita"
kanƙameta yayi yana shafa bayanta yace "shiru ammi"
kuka take yi, kaseem ne ya rike aneeta ta zauna akan sofa tana ciza baki cikin hawaye, ɗaki ya koma ya ɗauko kayan aiki yazo ya fara cire mata bullet ɗin, tashi hameed yayi ya zauna a gefe yayi shiru yana kallon yadda take ciza baki tana rufe ido, cire mata yayi, rikeshi tayi tana ihun zafi, minat tace "sorry"
shima cikin sanyin murya yace "sorry"
saida ya tabbatar jinin ya tsaya kafin yayi dressing wajen, a hankali ya tashi yana kallonta zubewa kasa yayi ya haɗa hanu biyu yace "thank you, na gode sosai da kika ceci rayuwar hameed na gode"
raba hanunshi tayi tace "ka daina min godiya ba kunce mun zama ƴan uwa ba?"
cikin kuka yace "na gode"
tace "ka daina yafi karfin komai a wajena kune kuka taimakeni kuma zan iya taimakonku a koda yaushe matukar zan iya"
a hankali ya tashi, Abi waya ya kira babu jimawa wasu maza suka shigo gawan ya nuna musu cikin bala'in ciwon kai da nauyin da kanshi yayi yace "kuje ku binneta ku ɓoyewa kowa kada kowa ya sani"
amintattunshi ne suna iya ɓoye komai wanda ya shafeshi matukar yace musu su ɓoye koda baice su ɓoye bama ɓoyewa suke bale yace su ɓoye, fita da ita sukayi ta kofan baya, aneeta binsu tayi da kallo har suka fita suka rufe kofan, bata taɓa sanin akwai kofa a wajen ba sai yau da taga sun buɗe domin ɓoye sirri, tashi hameed yayi ya fara tafiya fadeel ne ya rikeshi yace "yaya bari na kaika ɗaki"
ɗakin ya kaishi ya zauna kawai akan gado yayi shiru, fita yayi, minat ce ta taimakawa Aneeta suka tafi ɗaki, ammi ma sultan ya kaita ɗaki, abi yana rike da kanshi ya wuce fada, har zazzaɓi yake ji baisan meyasa ba kullum lamarin gidanshi ɓaci yake, babu abinda yake tafiya daidai.

Aneeta tana kwance tana kallon minat tana kuka, shiru tayi dan ta kasa gane meke faruwa a gidan, cikin sanyin murya tace "kiyi hakuri ki daina kuka komai yayi zafi zaiyi sanyi Insha Allah"
share hawaye tayi tace "babu abinda zaiyi sanyi a wannan gidan babu shi aneeta komai kara lalacewa zaiyi babu abinda zai dawo daidai"
shiru tayi tana kallonta, sai kuma tace "amma kada nayi shishigi waye ya kaseem yace zai kashe?"
shiru tayi kamar ba zata amsa ba sai kuma tace "wani ne"
tace "wanene shi?"
girgiza kai tayi tace "wannan sirrin gidan sarautarmu ce, wannan sirrin babu wanda ya sani sai mu kaɗai ƴan gidannan kuma alƙawari ne babu wanda zaiji"
tace "to shikenan Allah ya daidaita komai kiyi ta addu'a"
tace "insha Allah"
duk yadda taso tayi bacci ta kasa abinda ya faru yau ya tsaya mata a wuya data rufe ido yarinyar take gani a kwance, kenan suna iya kisa kuma su kwana lafiya? tsoron gidan ma ta fara fitsari takeji amma ta kasa tashi taje tayi haka take kwance data motsa kaɗan sai taga kamar zasu harbeta itama, kuma tasan babu abinda zai faru idan ta mutu, tashi tayi tace "anya aneeta ba zaki nemawa kanki hanya ba? anya ba gudu zakiyi ki bar gidannan ba?"
kallon minat dake bacci tayi sai kuma ta kalli kofa, cikin

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login