Showing 15001 words to 18000 words out of 32935 words

Chapter 6 - KADDARATA

Start ads

11 Sep 2025

74

Middle Ads

tace "muje to sabida me lalle zatazo da dare tayi miki"
tashi tayi jikinta dama ba a sake ba ta bita suka nufi ɗaki, gyara mata tulin gashin tayi sannan da dare akazo aka mata lalle me kyau.
kaya ammi ta siyo mata masu tsada da yawa da kuma kyau sannan ya kaseem yasa aka sauya ɗakin hameed aka kara ƙawatawa da kayan adonsu na sarauta, rana bata karya kamar yadda Abi yasa yaune auren yarima hameed da kuma Aneeta, gidan ya zama busy sai gudanar da biki ake tun yanzu da safe kafin ma a ɗaura, Aneeta tana ɗaki banda kuka babu abinda take yi, saida minat tayi da gaske kafin ta yadda tayi wanka ta fito akayi mata kwalliya me kyau, leshi fari da golding me masifan kyau tasa, fited gown ne ya kama jikinta sosai hakan yasa tasa babban mayafi, mutane sai shigowa suke suna tayata murna, ɓuya tayi dan batason mutane sosai, Amrah wacce take yawan rike waya tace "unty amarya kafin musa kayanmu kizo nayi miki hoto"
murmushi tayi tace "a,a ban iya hoto ba"
tace "please unty"
a hankali ta gyara mayafin ta tsaya me kyau tayi mata hoton, tace "wow kinyi bala'in kyau"
sawa tayi a status sannan ta kashe data a ranta tace "sai anjima zanga comment na mutane akan kyakkyawar matar yayana"
shiryawa suka fara saida sukayi kyau kafin suka fara hotuna duk a wayan Amrah.
Amrah ta zauna a bakin gadon kafin ta canja wani kayan tace bari ta duba watsapp, saura awa ɗaya a ɗaura aure domin an tafi sallan juma'a, message ta gani ya shigo mata voice ne amma da tsayi jin hayaniya a ɗakin yasa ta tashi ta shiga toilet playing tayi tana ji, jikinta ne ya fara rawa ta kara sawa a kunne tana ji ta kara maimaitawa, wayan Amnah ta kira kusan sau biyar bata ɗauka ba sai kuma ta kira wayan minat itama bata ɗauka ba, tsaban rawan da jikinta yake yi ta kasa fita a toilet ɗin, ji tayi ɗakin yayi shiru, fitowa tayi da kyar ta buɗe kofan ta tsaya tana kallon Aneeta wacce take kallonta tana murmushi tayi kyau cikin shaddan data sauya, gani tayi babu kowa a ɗakin sai ita tace "inasu... minat?"
taɓe baki tayi tace "sun fita ammi ta kirasu"
hanyan fita ta kama da sauri ta tsaya a gabanta, gabanta yana faɗuwa tace "meyasa kika tsaya a gabana? ki matsa min na wuce"
murmushin gefen baki tayi tace "naga kinamin wani kallo kin sanni ne?"
tace "ban sanki ba ki matsamin na wuce"
dariya tayi me sauti sannan ta kalli wayan dake hanunta, nuna kanta tayi tace "ANEETA LAWAN LAMBA nice nasan shine abinda aka faɗa miki kike ɓoyewa kinaso kije ki faɗawa su minat ko?"
jikinta yana rawa tace "meyasa kike shirin auren ya hameed?"
dariya tayi sosai sannan ta takaita dariyan fuskanta kamar wacce bata taɓa koda murmushi ba tace "zaki iya zuwa ki faɗawa kowa kamar yadda kikayi niyan tonamin asiri"
juyawa tayi zata fita saida ta bari ta kai bakin kofa kafin tasa igiyan dake gefenta ta harɗe kafanta dashi, waro ido tayi ta zube a kasa, baki ta buɗe zata kwala ihun azaba da raɗaɗi tanada tabbacin ta samu karaya a jikinta, toshe bakinta tayi tace "kina tsammanin bana ankare da ke ne? to ai tunda naga kin ɗaukeni hoto kinsa a status nasan akwai abinda zai faru, kuka naga kin shiga toilet ai nasan da akwai wata a kasa, inaso ki sani aneeta ba sakara bace ta san me takeyi kuma tasan takunta, ki sani wannan auren na shafe shekaru masu yawa ina neman hayan da zan samu a yishi bayan burina ya kusa cika baki isa ki rusamin arana ɗaya ba, da ki tonamin asiri gara na kasheki"
hanu ta haɗa tana rokonta alaman dan Allah ta kyaleta ba zata faɗawa kowa, bakinta ta ɗaure sannan ta sauko da sabon akwatin ta juye kayan a kasa, sata tayi cikin akwatin bayan ta rufe hancinta da bakinta ta ɗaureta ta kulle akwatin ta yadda ko motsi ba zata iya ba bale asan akwai mutum, kallon kofan bayan tayi sannan ta fara jan akwatin, zata fita dashi taji karan kafan mutum, da sauri ta saki akwatin ta kwanta a gado kamar me bacci, minat ce ta shigo tana cewa "laaa unty Aneeta bacci yanzu? ki tashi dan Allah an ɗaura aure yanzu ki fito ayi hotuna gasu Abi a falo"
kamar me bacci taki tashi, bubbugata tayi da sauri ta buɗe ido aɗan firgice tace "na'am"
dariya tayi tace "amarya amma tana bacci ran aurenta? kizo muje ayi hoto"
murza ido tayi sannan tace "to"
sauka zatayi a gadon tace "tsaya na gyara miki makeup ɗin"
gyara mata tayi sannan ta kara mata sabon ɗauri suka fita tare, juyowa tayi ta kalli akwatin sannan ta tura kofan gau, Amrah ta kasa motsi tana jinsu amma babu halin magana, tun tana iya numfashi da kyar har numfashin yazo ya gagareta.
hotuna suka fara Amnah wacce tayi kyau da ankon da sukayi da Amrah ta tsaya a gefen Aneeta akayi hoton tace "ina Amrah ne? tazo ayi hoto"
meenat tace "wallahi ban ganta ba may be ta fita"
Amnah tace "no babu inda taje kin san Amrah bata son yawo"
meenat tace "eh kuma fa hakane bari na dubata a ɗakin Ammi ko tana can"
dubata tayi bata ganta ba ta dawo tace "babu ita muyi hoton may be tana shiri"
cigaba sukayi da hotonsu, har yamma ya fara babu Amrah, amnah zuciyanta ya fara tsinkewa domin wayan Amrah akwai caji kuma ta kira taji a kashe, meenat tace "ki kwantar da hankalinki kin san da ba zata ɓata a wannan fadan ba ko?"
Aneeta fakan idonsu tayi ta koma ɗakin taja akwatin ta fita dashi, jim kaɗan ta dawo tana gyara mayafin tace "naje fesa turare"
Amnah wacce ta damu sosai tace "gaskiya na tsorata amrah bata yawo kuma wayanta a kashe bayan tasa caji?"
meenat ma ta fara damuwa, Ammi data zo yanzu daga fada fuskanta da yanayin damuwa tace "wallahi babu ita nasa an duba ko ina"
Amnah ta ɗaura hanu aka tace "na shiga uku na lalace ina Amrah ta shiga?"
Aneeta ta rike ta tace "karki damu za'a ganta"
hameed wanda ya shigo cikin damuwa tareda su sultan fuskokinsu kaɗai ya isa ya nuna halin da suke ciki, ammi tace "an ganta?"
duk sukace "A,a"
itama ammi zuwa yanzu ta gama tsorata tace "na shiga uku Amrah ina kike?"
kafin ta rufe baki sukaji faɗowan abu daga saman silin, a mugun tsorace sukayi baya ganin Amrah ce ta faɗo kasa kan tiles, jini ne ya fara bin tiles ɗin bakinta ɗaure da ɗankwalin kanta hanunta ma a ɗaure idonta a rufe alaman bata raye tun da jimawa.
Ammi duhu take gani ta zama kamar makauniya sai tattaɓa hanya take, zubewa kasa tayi, da rarrafe ta isa wajen zata taɓata ya kaseem yace "dakata ammi kar kiyi saurin taɓata bari a kira police, a rufe gidan babu me fita sai an gwada hanun kowa"
gaban aneeta yayi wani irin mummunan faɗuwa ji tayi kirjinta kamar zai fashe tsaban tsinkewan rai, ganin kowa ya tsaya babu wanda ya taɓa gawan an fara rufe kofofin gidan ta kalli Amrah dake kwance sannan ta rufe ido, faɗuwa tayi a kanta kamar ta suma, ganin haka kaseem ya dafa kai yace "wayyo Allah shikenan aneeta ta taɓa ta"
Ammi ganin haka ta rungume Amrah kawai ta fara ihu, Amnah kam tana tsaye tana bin kowa da kallo, da masu ihu da masu kuka ita kam batasan ma me take yi ba, tasan dai kawai ta kasa ɗauke idonta daga kan ƴar uwarta abin alfaharinta wato Amrah.

_Jiddah Ce....✍️_
08144818849
[20/08, 2:11 am] Shuraihu Usman: 🌸🌸🌸🌸🌸
*ƘADDARA TA*
🌸🌸🌸🌸🌸


Na
*Jiddah S Mapi*


*Chapter 7*


~Jikin kaseem yana rawa yace "Innalillahi wa inna ilaihiraji'un me yake faruwa?"
hameed ma jikinshi rawa yake sai kallonsu yake ya kasa yin komai, minat kallon Amnah tayi yadda ta bushe a tsaye, da sauri taje ta riketa cikin tashin hankali tace "kija numfashi amnah"
girgiza kai tayi alaman ba zata iya ba, tace "Amnah kija numfashi"
girgiza kai kawai take ta kasa magana, meenat da karfi tace "ya kaseem Amnah fa bata numfashi"
da sauri yazo ya riketa, wani irin rikeshi tayi ta kwala ihun daya amsa gidan gaba ɗaya, mai martaba wanda ya shigo yanzu ya zuba musu ido ya kasa cewa komai sai zufa da yake, Amnah da Ammi ihu kawai suke meenat tana tayasu, cikin kuka tace "Amrah meya kawomu? Amrah tarefa mukazo meyasa zaki tafi ki barni?"
hameed ɗaga Aneeta dake kwance yayi ya ɗaurata akan sofa, ruwa ya ɗibo ya watsa mata, da sauri ta buɗe ido tana kallon shi, kallon Amrah dake kwance tayi sai kuma ta rungumeshi tana kuka tace "wa yayi haka? waye ya kashe ta ranan aurenmu ayi kisa hameed? hameed na fara tsorata da wannan gidan wallahi akwai wani abinda yake faruwa"
mai martaba ne yayi karfin halin yin magana yace "ayi jana'iza kada a ɓata lokaci"
kaseem yace "Abi a bari ayi bincike"
Ammi dake kuka idonta ya jika da hawaye tace "kaseem a birneta babu wani bincike da za'ayi a bari sai an birneta komai ma za'ayi sai ayi daga baya"
yace "sabida bakiso a gano wanda ya kasheta?"
da mamaki ta kalleshi sai kuma ta share hawayen tace "banaso kuma? me kake nufi kaseem?"
murmushin gefen baki yayi yace "ai kinfi kowa sanin me nake nufi..."
a fusace ta mike tana kallonshi da tsananin ɓacin rai akan fuskanta tace "me kake nufi kaseem? kana zargin zan iya kashe ƴar kanwata? ko kana nufin zan bada goyon baya a kasheta?"
shima yana huci yace "to meyasa zaki hana?"
cikin raɗaɗin mutuwan Amrah da haushin maganan da yakeyi tace "sabida nice na saba kisa? ko ka manta kaine...."
mai martaba a tsawace yace "ya isa haka!!! nace ya isa haka!!! wai meyasa kullum ba zaku faɗi alkhairi bane? meyasa kullum cikin zargin juna kuke? maimakon ku maida hankali akan mutuwan da akayi ayi bincike me kyau domin a hukunta wanda yayi amma kuna wannan banzan maganan mara am....."
rike kirjinshi yayi yana salati jin wani zafi da kirjinshi yake, idonshi ya rufe kasa ya faɗi da mugun gudu hameed yazo ya rikeshi, kallon kaseem dake tsaye yayi ya kalli jakadiya sannan ya nuna mata kofa alaman ta buɗe mutane su fita, da sauri tace "to yarima"
zuwa tayi ta buɗe kofan mutane suka fara fita, saida ya tabbatar mai martaba ya farfaɗo kafin hankalinshi ya ɗan kwanta.

har aka fita da Amrah kanwarta Amnah bata cikin hayyacinta, gidan ya zama shiru babu me magana, amnah tana zaune a gefen meenat da ammi tayi tagumi har hawayenta sun tsaya yanzu sai kukan zuci take, Aneeta kuma tunda ta faɗa zazzaɓi ya kamata tana ɗaki kwance, kaseem ne ya shigo sanye da jallabiya yayi shirin kwanciya amma yace bari ya dubasu, da sallama ya shiga sannan ya zauna a kusa dasu yace "sannu Amnah"
a hankali tace "yawwa yaya"
yayi shiru har na ɗan lokaci, cikin nutsuwanshi yace "dama akwai wanda suke gaba ne?"
girgiza kai tayi sannan cikin muryanta daya dishe tace "ko ɗaya Amrah batada abokin gaba, maganan bakinta ma baida yawa kaima ka sani, bata fiye shiga harkan kowa ba..."
kuka ta kara fashewa dashi, yace "kiyi hakuri na san zafin da kikeji Amnah kiyi hakuri kuma na miki alkwari saina samo wanda ya aikata wannan mummunan abin"
yayi magana yana kallon ammi, itama kallonshi tayi, tun daga kasa suke jiyo karan buga kofa, sunan Amnah ake kira babu kakkautawa, Amnah dake zaune tashi tayi farat tace "Dady ne"
tare suka fita yana tsaye sanye da babban riga da alama daga tafiya ya dawo hulanshi ya cire ya wurgar jijiyoyin kanshi sun tashi, hameed dake ɗakin Abi yana bashi malt yaji hayaniya da sauri ya kalli Abi sannan ya kalli kofa, tashi yayi ya fita Abi yabi bayanshi, Aneeta dake zaune akan stool tana kallon kanta a madubi taji hayaniya murmushi tayi ta shafa fuskanta da yayi jajur sabida kukan karya da tayi, rigan bacci ne a jikinta milk color ya bala'in karɓan jikinta, murmushi tayi tace "haka nakeson ji, ko kaɗan banason ganin gidannan babu tashin hankali, ko kaɗan banaso naga ana zaman lafiya a wannan gidan, idan ana hayaniya da tashin hankali ji nake kamar na zuba ruwa a kasa nash"
tashi tayi tana kallon jikinta da kayan baccin ya matukar karɓanta, hijabi tasa dogo har kasa sannan tace "bara naje naga me yake faruwa"
fita tayi ta maida fuskanta kalan tausayi, tana ciza baki kamar mara lafiyan gaske, dadyn Amnah cikin tsananin fushi yaje yaja hanunta yace "ko kwana ɗaya ba zaki kara a wannan gidan ba, saida na faɗa muku keda Amrah wannan ba gidan zuwa bane, na faɗa muku har mahaifiyarku ta mutu bata magana da wannan matar duk da uwa ɗaya uba ɗaya suke amma kunki jina, saida kuka zo Amnah gashi yanzu sun kashe ƴar uwarki"
Ammi tace "amma salisu daka bari ta kwana idan yaso zuwa gobe...."
cikin masifa da zafin mutuwar ƴarshi yace "gobe? gobe fa kikace, to nasan me zai faru da ita da darennan idan ta kwana? wannan gidan naku da yake ɗauke da mummunan tarihi an gaya miki ban san komai bane? kuma wallahi ku sani ƴata ba zata mutu a banza ba, na rantse da Allah saina ɗau fansa, ke kuma....."
ya nuna ammi jikinshi har yana rawa, Abi wanda ya gama cika yace "an gaya mata itace tayi kisan da zaka zo kana gaya mata bakaken maganganu?"
ya kalli Abi da idanunsa da sukayi jajur yace "a cikin gidannan waye baya kisa?"
kaseem wanda shima ranshi ya gama ɓaci yace "ka daina yi mana kuɗin goro ai laifin wani ba zai shafi wani ba"
jan hanun Amnah dake kuka yayi yace "muje babu ke babu su daga yau ba zasu sake ganinki ba kema kin rabu dasu"
meenat tana kuka tace "dady dan Allah kada kayi haka dan Allah ka barta mu zauna tare, ka barta mu ɗibe mata kewan ƴar uwarta data mutu, dady yanzu haka Allah ne kaɗai yasan zafin da Amnah take ji dady kada kayi haka"
yace "meenat na gommace Amnah ta mutu yau a gidana sabida zafin mutuwan Amrah data kwana a wannan ƙazamin gidan naku"
fita yayi da ita tana tirjewa tana cewa "dady ka bari na kwana anan"
suna fita kaseem ya kalli ammi dake rusa kuka yana huci yace "mutum ɗaya ba zai ɓata mana suna ba nasan wanda yayi wannan kisan"
Aneeta saida jinta da ganinta suka ɗauke na lokaci, yana kallon Ammi yace "kema kin sani hakeem ne zai iya wannan mummunan kisan..."
tace "ya isheka kaseem ya isheka nace"
jikinshi yana rawa yace "meyasa zaki danne gaskiya? meyasa zaki ɓoye abinda yake a bayyane? hakeem shine ya kashe Amrah"
marin data ɗaukeshi dashi yasa yayi shiru yana kallonta hanunshi dafe da kuncinshi, ta nunashi da yatsa tace "inaso ka san nice na haifeka kaseem ba kai ka haifeni ba, kaseem zan iya yin komai idan ka kara sa sunan hakeem a cikin abinda yake faruwa a gidannan"
murmushin da yafi kuka ciwo yayi sannan yace "okay kina nufin hakeem baida laifi?"
tace "hakeem baida laifi kuma ko za'a kasheni ba zan taɓa yadda cewar yanada laifi ba"
yace "to waye me laifi?"
hameed dake tsaye ta nuna tace "hameed shine babban me laifi, yarima hameed shine da laifi ba yarima hakeem ba"
hameed dake tsaye ya kalleta da manyan idanunshi a hankali ya fara yin baya jin abinda ta faɗa, Aneeta dake tsaye ta kasa karasowa ta zuba mishi ido tana gani jikinshi yana rawa, showglass dake cike da turare ya buɗe, kwalban turare ya ɗauka sannan ya fasa, aneeta tana tsaye tana kallonshi murmushi take a ranta tana kallo yadda kwalban yayi tsini, ganin hankalinsu baya kanshi sunata faɗa tsakaninsu yasa itama bata ankarar dasu ba domin so take taga gawanshi kwance baya motsi hakan zaisa taji ranta yayi sanyi hakan zaisa ta yafewa kanta, daɓa kwalban yayi a cikinshi, tana kallonshi har ya faɗi kasa jini ya fara bin tiles, sai a lokacin tayi wani irin ihu tareda kiran sunanshi ammi da kaseem waɗanda suka kai karshe wajen fushi suka juyo a tare suna kallon hameed dake kwance hanunshi akan cikinshi jini ya ɓata inda yake kwance idonshi a rufe da alama ya mutu.

Meenat hanu ta ɗora a kanta tana ihu, kaseem da sultan da kuma fadeel tare sukaje suka ɗaukashi jikin kaseem yana rawa yama rasa wani taimako zai iya mishi kawai yace "mu tafi hospital"
tare suka fita dashi a hanunsu Aneeta da meenat suka bisu a baya, ammi itama binsu tayi, a mota ɗaya babba suka tafi asibiti a cikin daren da yayi nisa basu sani ba, babu mutane dayawa akan titin sabida dare yayi sosai ba kaɗan ba, banda kuka babu abinda aneeta take yi, tana cewa "dan Allah kada ka mutu ka barni hameed dan Allah ka buɗe idonka kada ka mutu ka bar marainiyar matarka"
a hankali meenat ta rungumeta tana bubbuga bayanta tareda kwantar mata da hankali, shiru tayi a ranta tace "inama ace ya mutu, inama ace da gawanshi muke tafiya"
suna shiga asibiti kaseem ya fito babu takalmi a ƙafarshi ya ɗaukeshi, shiga ciki yayi dashi duk masu aikin night sukayo kanshi suna bashi taimakon gaggawa, jikin kaseem banda rawa babu abinda yake yi, gani yake hameed ya riga ya mutu tun kafin suzo asibitin, zama yayi akan dakali ya rike kanshi da hanunshi, kukan da bai shirya ba ya fashe dashi, sultan dake safa da marwa ya kasa zaune ya kasa tsaye yazo ya durkusa a gabanshi, rungumeshi yayi yana bashi hakuri yayi shiru.
Aneeta a bakin kofan ta tsaya kamar zata shiga kofan da aka rufe tana kuka tana addu'a, Ammi kam tsaban tashin hankali bin kowa kawai take da kallo kamar kanta ya taɓu.

Aneeta cikin ranta tana addu'a tace "Allah kasa ya mutu ya rabbi kasa baya raye"
a fili kuma cewa tace "Allah kada kasa hameed ya mutu ya barni dana sani da banyi wannan auren ba matukar zai kawo tashin hankali"
Ammi da jikinta ya gana sanyi tace "saida nace kada ayi wannan auren nasan babu mu babu kwanciyan hankali matukar hameed ya samu yarima kuma yayi aure amma sunki jina, kowa baya jin maganata"
kuka take yi sosai, bayan lokaci dayawa suka buɗe kofan, har rige

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login