Showing 18001 words to 21000 words out of 32935 words
rige suke wajen tambaya ammi tace "ya mutu?"
da mamaki dr ya kalleta yace "kinaso ya mutu ne?"
shiru tayi, ya kallesu su duka sannan yace "yana raye bai mutu ba amma yaji mummunan rauni"
hamdala kaseem yayi sannan ya ɗago kai ya share hawayen, farin ciki ya bayyana a fuskanshi yace "Alhmdllh hameed bai mutu ba"
shiga dakin yayi hameed yana kwance akan gadon hanunshi ɗauke da jini sun san jininshi kuma ya zubar da jini sosai, fuskanshi yayi fayau sosai, a hankali ya zauna a gefenshi ya rike hanunshi dake free, murza yatsunshi yake hawaye suna wanke mishi fuska yace "hameed kayi hakuri ka yafemin ban zama yaya na gari ba na zama yaya mara amfani a wajenka, kullum cikin ciwo kake baka taɓa samun kwanciyar hankali koda na kwana ɗaya bane"
shafa kanshi yayi yace "ka yafeni hameed"
shigowa sukayi aneeta ta tsaya a bakin kofan tayi shiru, kallonta kaseem yayi sai yaji ta bashi tausayi, yace "aneeta zoki zauna kusa da mijinki"
cikin jin kunya ta sunkuyar da kanta, tashi yayi yace "kizo"
a hankali tazo ta zauna kusa dashi, shiru tayi, kaseem yace "zaku iya tafiya gida idan yaso gobe saiku dawo zamu kwana da aneeta anan tare dashi"
duk sukayi shiru basason tafiya, yayi kamar bai taɓa dariya ba yace "kuje mana"
tashi sukayi ba dan sun so ba harda Ammi suka fita, kallon Aneeta yayi yace "kiyi hakuri da duk abinda yake faruwa sannan ki kula da mijinki ko sau ɗaya banaso ki tambayeshi abinda yake faruwa a wannan gidan, ko su meenat dasu sultan banso ki tambayi kowa, kici gaba da zama mutuniyar kirki kamar yadda kike"
a hankali tace "to ya kaseem insha Allah"
shiru yayi yana kallon hameed dake bacci, ya tashi yace "zanje office ina zuwa"
tace "to"
fita yayi, ta kalli hameed a ranta tace "meyasa baka mutu ba? nace me yasa baka mutu ba hameed?"
ta kalli jinin dake tafiya a jikinshi, fizge canulla ɗin hanunshi tayi ta bar jinin baya tafiya, murmushi tayi tace "ko kaɗan banso naga kana rayuwan farin ciki, so nake naga kullum kana kuka hameed, na tsaneka na tsani ƴan gudanku hameed na tsaneku"
rashin jinin dake jikinshi yasa jikinshi ya fara zafi, fizgewa ya fara yana neman karya gadon, tana ganin yadda yake jin zafin ciwon a jikinshi da yadda yake fizge jikinshi sabida rashin jini, tace "ka mutu hameed ka mutu mana hameed"
knocking akayi da sauri ta fara rike hanunshi tace "shigo"
ya kaseem ne ya shigo da juice a hanu, ya kalleta ya kalli hameed wurgar da juice ɗin yayi yazo yana rikeshi, yace "ya akayi jinin ya fita?"
tace "wallahi fizge fizge ya fara kuma na rasa yadda zan yi"
ganin tana kuka yace "karki damu babu abinda zai sameshi"
gyara mishi jinin yayi yana jin jini a jikinshi ya koma luf ya kwanta akan cinyarta.
shiru tayi tana kallonshi, juice ɗin kaseem ya mika mata yace "gashi kisha nasan rabonki da abinci tun safe"
girgiza kai tayi tace "bana jin yunwa, ba zan iya cin komai ba"
yace "ki daure kisha dan Allah"
shiru tayi tana girgiza kai hawaye yana wanke mata fuska, da kyar ya lallaɓata tasha kaɗan, a wajen tana zaune bacci ya ɗauketa.
_jiddah ce...✍️_
08144818849
[20/08, 2:11 am] Shuraihu Usman: 🌸🌸🌸🌸🌸
*ƘADDARA TA*
🌸🌸🌸🌸🌸
Na
*Jiddah S Mapi*
*Chapter 8*
~Sunyi kwana biyar a asibiti kafin aka sallamesu, da kyar yake takawa sabida ciwon da yake cikinshi, wajen jeep ɗin dake fake suka nufa tareda ya kaseem da yayi kyau cikin yadi maroon, Aneeta kuma sunye take da hijab peach color tayi kyau sosai tasa mayafin a kanta bayan tasa hula me kyau baƙi, tana rike dashi yana takawa a hankali har ya shiga motan, itama shiga tayi sannan ya kaseem ya shiga, driver ne yaja suka tafi, koda suka isa gida a hankali yake tafiyan har aka kaishi ɗaki, kwanciya yayi akan gadon yayi shiru yana kallon Aneeta dake kallonshi, gira ya ɗaga mata alaman ya akayi?
murmushi tayi ta kauda kai, zata tafi yaja hanunta ta faɗo kanshi, rungumeta yayi sosai yana sauke ajiyan zuciya, shiru tayi a jikinshi har zuwa lokacin daya fara shafa duk jikinta, duk wani taɓata da yayi ji take kamar wuta ne yake taɓa mata jiki, bakinshi zai haɗa da nata tayi saurin tashi ta bar wajen, binta yayi da kallo, sultan ne ya shigo yace "yaya yarima a kawo maka abinci?"
gyaɗa kai yayi, yace "to"
fita yayi jim kaɗan yazo da abinci yace "tashi na baka"
tashi yayi ya zauna, jallof rice ɗin ya fara bashi yana ci cikin nutsuwa, fitowa tayi daga toilet ta karɓi plate ɗin tace "karka damu zan bashi"
kallonta yayi shifa gabanshi yana faɗuwa idan yana kallonta ya rasa dalili, tace "tashi mana sultan zan bashi da kaina"
a hankali ya tashi ba dan yaso ba, bashi ta fara, sultan ya fita daga ɗakin, fadeel yaga yanayin sanyin jikinshi yace "ya akayi sultan?"
yayi tsaki kaɗan yace "wallahi haka kawai hankalina yaki kwanciya da Anti Aneeta musamman idan tana tare da ya hameed sai naji gabana yana faɗuwa"
caraf a kunnen Ammi wacce ta fito daga ɗaki, kallon sultan tayi, ashe ba ita kaɗai bace takejin haka akan aneetan shima yana ji, idan taga aneeta gabanta yana faɗuwa, idan tana tare da hameed sai taji bugun zuciyarta yana karuwa, tana kallonsu har fadeel ya dafa wuyanshi suka tafi yana cewa "ka kwantar da hankalinka babu wani abu mara kyau da zatayi mishi kasan tana masifan sonshi"
fitowa Aneeta tayi da plate ɗin a hanunta ido huɗu sukayi da Ammi, murmushi tayi mata tace "sannu ammi"
bata amsa mata ba kuma bata daina kallonta ba, taɓe baki tayi ta wuce taje ta aje plate ɗin ta dawo ta shiga ɗakin ta rufe.
meenat wacce taga duk abinda ya faru tazo wajen ammi ta riketa, tace "ammi me yake faruwa ne?"
girgiza kai tayi tace "ba komai meenat"
tace "ammi amma kamar naga kina yiwa anty Aneeta wani irin kallo kuma naga ya sultan ma kamar jikinshi a mace da ita"
ammi taja numfashi sannan tace "meenat wallahi na kasa nutsuwa da wannan yarinyar haka kawai banason ganinta kusa da hameed"
tace "comon ammi babu komai fa kawai dai kinsa abu ne a ranki"
tace "to amma meenat"
tace "amma me ammi muje please ki huta kin gaji sosai"
shiru tayi suka tafi, meenat kallon kofan ɗakin tayi itama haka kawai taji kamar akwai abu a kasa, itama ta kasa nutsuwa da aneeta tunda Amrah ta mutu, sannan tunda akayi aurensu da hameed sai taga kamar ta canja duk da tana ɓoyewa amma ta lura da hakan.
sharewa kawai tayi.
zaune suke a dinning daka anan ne suke haɗuwa su duka harda Abi, abinci sukeci da hameed wanda yake cin abincin a hankali yake kallon matarshi, murmushi yake idan sun haɗa ido, meenat tace "Abi zanso naje nima naga wani kasan saudiya kawai na taɓa zuwa gaskiya zanso naje wata kasar kuma"
murmushi yayi yace "shikenan meenat zaɓi kasar da kikeson zuwa hutunki"
tace "turkey"
aneeta ta sauke cup na tea da take sha tace "me zakiyi a turkey? akwai sanyi sosai acan gara kije cairo yafi daɗi sabida babu sanyi sosai kuma babu za..."
saurin yin shiru tayi ganin yadda duk suke kallonta bata sani ba ashe tayi ɓarin zanje, meenat da mamaki take kallonta sai kuma tace "ya akayi kika sani? keda kikace baki taɓa fita ko wani gari ba bale wata ƙasa?"
gabanta ya fara faɗuwa da sauri ta kalli ammi wacce ta aje spoon tana kallonta tana jiran amsa, tace "a tv na gani ai, film na kalla ranan naga an faɗa"
sultan yace "wani film?"
ruɗewa tayi domin ta rasa amsan da zata bayar, tace "to ai ba zan iya rike sunan film ɗin ba sabida da turanci ne kuma bana jin turanci"
meenat tace "kuma kikaji me suke cewa a film ɗin har kikaji sunce kasar turkey da sanyi?"
tace "to ai naga suna saka rigan sanyi su kuma..."
kaseem ne yace "ya isa haka"
shiru tayi meenat kuma ta fara binta da kallo haka Ammi, hameed yana gamawa ya tashi ya tafi ɗaki.
itama Aneeta bata jira yau ta gama duka ba ta tashi ta tafi, da kallo meenat ta bita.
tun daga ranan bata kara yadda tayi suɓul da baka ba, yau weekend ne suna zaune a falo su duka banda hameed dake bacci a ɗaki, meenat ce kwance akan sofa tana chatting, tace "yanzu zasusa favorite film ɗina bara na kashe data nayi kallo"
sunan jarumai aka fara nunata tana rike da wayan taji Aneeta tace "michael marrone, ashe kina kallon film ɗinshi wannan film ɗin After marriage ne ko?"
kallon da meenat take mata yasa tayi saurin rufe baki, meenat zuwa yanzu ta gane karya take yi akan abubuwa da dama domin yadda take kiran sunan abu kamar tanada masaniya sosai a kai, shakku ta fara a kanta, batayi magana ba kawai ta kawar da kai tana kallon tv, a zahiri kallo take amma a zuciyarta tana kara kallon Aneeta ne, a hankali tace "ya zama dole nasa ido sosai a kanta"
saida aka gama film ɗin ta musu saida safe ta tafi ɗaki, ta rufe kofan ta jingina da jikin kofan tayi shiru, a hankali ta lumshe ido ta buɗe tace "wacece wannan?"
zata wuce ciki taga sim a gefen gado, da sauri tace "sim ɗin waye?"
ɗauka tayi tana kallo, sai kuma tace "ba nawa bane, ko dai na Amnah ne?"
shiru tayi tana tunani sai kuma tace "no Amnah batada sim biyu saide Amrah itace take canja sim"
da sauri tace "wannan na Amrah ne"
da sauri ta buɗe wayarta tasa sim ɗin a ciki, dubawa ta fara taga sunayen duk yawanci a bakin Amrah takejin sunan, numbern Amnah taga tayi saving da blood sis, tace "tabbas wannan sim ɗin Amrah ne"
barin sim ɗin tayi a wayarta ta kwanta ta fara bacci.
Aneeta kwance take itada hameed ya rungumeta sosai yana bacci cikin kwanciyan hankali, so take ta samu waje tayi waya amma tana tsoron kada a kamata, a hankali ta cire hanunshi daga jikinta kunna wuta tayi taga karfe biyu na dare cikin sanɗa ta buɗe drower ta ɗau waya karami data ɓoye fita tayi daga ɗakin cikin sanɗa take tafiya, tsayawa tayi a jikin bango ta fara kunna wayan saida ya kunnu zata kira taji karan tafiyan mutum, da sauri ta rufe baki tana waro ido, sanye yake da bakin kaya ya rufe fuska kofan jabeer taga ya buɗe, fasa kiran wayan tayi a hankali ta fara bin bayanshi, tsayawa tayi a baya taga ya ɗaga hulan, alluran da ake yiwa hameed kullum taga ya ɗauka ya juyo dashi, zaro manyan idanunta tayi ganin sultan ne ya canja alluran ya ɗau original ɗin ya kalli kaseem dake bacci cikin kwanciyan hankali sannan ya juya zai tafi, da sauri ta ɓuya a bayan kofa, fita yayi ya rufe kofan, yana fita itama ta fita cikin sanɗa tana mugun mamakin me zaisa sultan ya canja allura?
kiran wayan da batayi ba kenan ta koma ɗaki taga hameed ya buɗe ido yana kallonta, tasan da tambaya sosai a ranshi amma ba zai iya furtawa ba, a hankali ta kwanta ta rungumeshi tace "na fita shan ruwa ne kasan na saba da shan ruwan dare"
shafa kanta yayi sannan ya mata kiss a forehead ya kara rungumeta ya lumshe ido, a ranta har yanzu ta kasa gane me yasa sultan zaiyi haka?
tana ganinshi ta cikin dim light yana bacci like innocent baby boy, yadda yake turo baki kamar karamin yaro da ake shayarwa, shafa kanshi tayi a hankali ta fara shafa sajenshi, da sauri ta ɗauke hanunta daga jikinshi ta rufe ido tana cewa "bai kamata ba, bai kamata ba sam Aneeta"
matsawa tayi daga jikinshi tace "ba wannan ya kawoki ba aneeta abinda ya kawoki daban kada kiyi kuskuren da ba zaki yafewa kanki ba aneeta"
pillow ta ɗauka ta rungume, zuciyanta yana tafasa tana jin zafi a ranta.
washe gari breakfast sukeyi Aneeta tayi kyau cikin baƙin kaya, akan ferfesun da take sha idonta yake bata yadda ta kalli kowa ba domin bata bacci idonta kamar na ƴar kwaya ya zama tsaban baccin da takeji, kaseem yana sanye da uniform cikin sauri yake cin abincin saida ya ɗan koshi yace "thank god, tashi hameed nayi maka alluranka sauri nake"
ya ɓata rai sabida baison kalman allura, yace "oya tashi"
badan yaso ba yaga yaja ruwan alluran, idanunta masu cike da bacci ta kalli sultan, baiko kalli inda suke alluran ba, zai mishi tace "ka tabbata alluran bs fake bane?"
jikin sultan ne ya fara rawa, tana kallon cikin idon sultan tace "ina nufin ka tabbata ba'a canja ba?"
cokalin hanun sultan ne ya faɗi, abincin yabi kanshi take ya fara tari, Ammi da meenat sai kallonta suke yadda take jujjuya cokalin tana magana da kwarewa cikin rashin tsoro, kaseem murmushi yayi yace "nifa babban dr ne aneeta sabida mijinki ya samu lafiya kikeso a samu allura me kyau ko?"
murmushin gefen baki tayi har yanzu idonta akan sultan tace "so nake ya samu lafiya ya kaseem amma ka kara duba alluran kada watarana a canja"
gama mishi yayi yace "good boy yanzu ba gashi an gama ba?"
kwanciya yayi a wajen kan sofa, shifa idan anyi mishi alluran maimakon yaji sauki sai yaji jikinshi yana zafi kuma bacci me nauyi mara daɗi saiya ɗaukeshi, bayan ya tashi sai yaji jikinshi yana ciwo kullum haka yake fama, amma ya kaseem ya nace da alluran kuma baison ɓacin ranshi shiyasa yake yadda.
tashi tayi daga wajen ta wuce ɗaki ba tareda ta gama ci ba, ido ta rufe tace "no ba zan bari wani ya kashe hameed ba nice ya kamata na kashe shi da hannuna"
tayi maganan tana kallon dogayen hannayenta.
meenat school ta tafi, bayan ta dawo ta gama aikinta sannan ta zauna a falon tareda su Aneeta kamar kullum suna hira
kiran wayan meenat akayi ta duba taga sim ɗin Amrah da tasa ake kira da sabon number, ajewa tayi bata amsa ba, aka kara kira ta amsa tace "hello"
muryan mace taji tace "Amrah inata kiranki ba zaki ɗauka ba? yau na dawo nigeria naga tun ranan baki kara hawa online ba, ina fatan yanzu kin gane wacece ita, na faɗa miki Aneeta babu wanda bai santa ba a gidanmu"
da sauri ta tashi ta wuce ɗakinta, tace "ki nutsu baiwar Allah wannan ba Amrah bace Amrah ta mutu amma wannan ƴar uwarta ce meenat"
tana jin yarinyar ta kwala ihu tace "ta mutu? ko kuma ta kasheta ko?"
meenat cikin ruɗewa tace "wacece?"
tace "Aneeta lawan lamba"
dafa kirji meenat tayi ta zaro idanu a razane tace "Aneeta lawan lamba?"
tace "tabbas nasan itace ta kasheta"
faɗa mata duk yadda sukayi tayi sannan tana kuka tace "ashe mutuwa tayi"
meenat cikin tashin hankali tace "dan Allah ki faɗamin inda zamu haɗu yau da dare inason ki faɗamin komai"
tace "kece ƴar sarki da take bani labari kullum?"
tace "nice"
tace "shikenan zanzo da dare amma kisan yadda zaki fita kada ki nuna mata kin gano komai kawai ki sameni a bakin titin kwaltan farko zan jiraki"
tace "kamar karfe nawa?"
tace "karfe goma sha biyu sabida banso kowa ya sani"
tace "to na gode me sunanki?"
tace "sunana fauza"
"na gode fauza"
kashe wayan tayi ta zauna a bakin gado tana maimaita kalman Innalillahi wa inna ilaihiraji'un, da kyar ta saisaita kanta ta fito, Aneeta ta kalla sai kuma ta mata murmushi tace "Anty Aneeta ki gyaramin gashina"
tace "zauna"
a tsorace ta zauna amma bata nuna mata ba, har dare tana bin komai a hankali sannan bata nunawa kowa komai ba, kallon agogo take bacci yaki ɗaukanta har karfe sha biyu kafin tasa dogon hijabi ta fita cikin sanɗa, cikin sanɗa ta fita a gidan tana sauri har taje bakin titin, gani tayi babu ita, kiran wayanta tayi taji a kashe, hankalinta ne ya kara tashi tace "fauza kizo mana ina kike?"
jiranta tayi babu ita babu dalilinta, saida ta gaji ga dare ya gama yin nisa kafin ta koma gida jikinta a mugun mace, ɗakinta ta shiga ta zauna kawai tana addu'a a fili da haka har gari ya waye batayi bacci ba, tana zaune akan sallaya tana addu'a, saida ta gama ta fito waje cikin uniform na school, kallon kofansu hameed tayi tsaban tsinkewan zuciya har ta rame.
knocking akayi a hankali tace "ana zuwa"
zuwa tayi ta buɗe kofan, gani tayi ɗaya daga cikin masu aiki ne namiji rike da katon ghana most go yace "Allah ya taimaki ƴar sarki meenat wannan sakon ance na kawo miki naki ne"
ta kalleshi ta kuma kalli sakon da yace, tace "waye?"
yace "nima ban sanshi ba amma yace a kawo miki fuskanshi rufe yake"
tace "to na gode"
ɗauka zatayi taji da nauyi, gabanta yana faɗuwa taja zuwa ciki da kyar, buɗewa tayi dan ganin me aciki, idonta kamar zasu zubo bakinta yana rawa kamar yadda jikinta yake rawa ta kwala ihu tace "ya kaseem? ya hameed? ku fito, ku tainakeni"
hameed ne ya fara fitowa, sannan sauran suka biyo bayanshi kallonta suke yadda take tsaye jikinta yana rawa ta kasa barin wajen, Ammi wacce itama ta gama ruɗewa da ganin ƴarta haka taje domin gani, ihu ta kwala tace "gawa"
hameed da kaseem sunzo a tare, kaseem ne ya kalla yaga kyakkyawar budurwa ce kwance yaga takadda a gefe, ɗauka yayi yaga an rubuta FAUZA da manyan harufa, kallon meenat yayi yace "fauza wacece ita? meyasa aka kawota nan?"
tana girgiza kai tace "ban sani ba yaya"
aneeta tana kallo ta rike hameed jikinta yana rawa cike da mugun tsoro tace "gawa hameed ba zan iya kallo ba a ɗauke anan"
ɓoye fuskanta take a jikinshi, mai martaba ganin abinda yake faruwa yace "kada kowa ya sani aje a binneta tunda bamu santa ba"
har yanzu jikin meenat bai daina rawa ba, fita da ita akayi, ammi tace "wai me yake faruwa ne damu?"
shiru suka zauna school ɗin da meenat bataje ba kenan, haka ta wuni da zazzaɓi da masifan ciwon kai, har dare tana kwance a ɗaki cikin bargo ta kasa fitowa, tunani ta fara, sai kuma ta tuna jiya data dawo kamar taji karan motsin buɗe kofa kuma tasan ba kofan ya kaseem bane, da sauri tace "Aneeta ya zama dole na bincike ta yanzu ma"
sauka tayi daga gadon ta fita a ɗakin, tana fita taga ta fito cikin sanɗa ta nufi kitchen, bin bayanta tayi taga tana tsaye ta juya baya a kitchen ɗin tana