Showing 12001 words to 15000 words out of 32935 words

Chapter 5 - KADDARATA

Start ads

11 Sep 2025

71

Middle Ads

sanɗa ta sauka daga gadon ta manta ma da zancen hijabi kawai ta nufi hanya ta fita a ɗakin, cikin sanɗa take tafiya duk gidan duhu ne sabida an kashe wutan, wannan al'adansu ne idan zasuyi bacci su kashe wuta, cikin gudun tayi tuntuɓe ta zube a kasa kara zatayi tayi saurin rufe bakinta da hanu, tashi tayi zata tafi taji kamar ana bubbuga kofa da sauri ta kalli kofan da ake bubbugawa taga kofan ɗakin hameed ne kamar zata tafi sai kuma wani abu yace ta tsaya ta duba menene, a hankali ta buɗe kofan ta shiga, taka mutum tayi ta waro ido a firgice zata kwala ihu taga hameed kwance a kasa yana birgima, da sauri tace "hameed? meyasa sameka?"
hanunshi ya mika mata da sauri ta rike hanun, taɓa jikinshi tayi taji da zafi sosai, cikin tsoro ta taimaka mishi ya tashi, da kyar yake ciza baki yana runtse ido, takalmin data rike a hanu ta zubar ta zauna a bakin gadon ta taimaka mishi ya kwanta, tace "me yake damunka?"
hanunta ya rike a razane ta kalleshi ganin ya cusa hanunta a cikinshi, zata kwace hanun ya damƙe da nashi, shiru tayi jikinta yana rawa ta kasa ɗauke idonta akanshi, gani tayi yana lumshe ido tareda kara tura hanunta cikin jikinshi, fizge hanunta tayi cikin tsoro ta tashi zata gudu dan bata taɓa ganin abu haka ba a rayuwarta, fizgota yayi ta faɗo jikinshi baki ta buɗe zatayi ihu ya toshe bakin, waist beads nata da yaji ɗazu ya fara wasa dashi, ganin tana kanshi idanunta sun kara girma sosai ba kaɗan ba, kwace kanta take ya kara danneta a kanshi yana kara wasa da waist beads ɗin, da kyar ta samu ta zame hanunshi daga bakinta zatayi ihu ya haɗa bakinshi da nata, cikin tashin hankali take bugunshi da karfi tana hawaye, wuntsila kafafunta takeyi tana neman hanyan tsira, so yake yace mata ta nutsu babu abinda zaiyi mata amma babu bakin magana, tun tana iya fizgewa har jikinta yayi sanyi tayi shiru kawai tana jinshi, a hankali ya zame bakinshi daga nata, juyar da ita yayi ta kwanta a gefenshi numfashinshi ke sauka akan dogon wuyanta, hanunta ya rike wanda ta kasa ko ɗagawa yasa a maranshi yana shafawa, jikinta har yanzu bai daina rawa ba, kuka take yi sosai kuma ta kasa magana, saida taji yayi shiru kafin ta faki idonshi ta dira a gadon da gudu zata fita a ɗakin, baya tayi a razane ganin ya kaseem daya shigo yanzu, da waya a hanunshi, kallonta yayi sai yaga ta sunkuyar da kai jikinta yana rawa, kallon miss calls ɗin da hameed ɗin yayi ta mishi yayi yau bacci ne ya saceshi shiyasa baiji kiran ba, baiyi magana ba itama batace komai ba, yace "jeki"
raɓawa tayi ta gefenshi ta wuce a guje, kallon hameed daya lumshe ido kamar me bacci yayi, karasawa yayi ciki ya zauna a bakin gadon yana kare mishi kallo, lips nashi da sukayi pink sosai ya kara kallo sai kuma ya kalli kofan yace "tashi kasha magani"
make kafaɗa yayi alaman no, cikin tsawa yace "tashi mana"
tashi yayi yana yamutsa fuska, ya bashi ruwa da maganin yace "sha"
buɗe baki yayi yasha maganin yana rufe ido, kwanciya ya kuma yi yana kokarin rufe kanshi da blanket ganin yadda kaseem ɗin yake kallonshi, ya rike blanket ɗin yace "me kayi mata?"
shiru yayi yana turo karamin bakinshi, yace "me kayi mata nace?"
yasan bazai iya amsawa ba amma tsaban haushi yasa yake mishi tambayan, tsawa ya daka mishi yace "me kayi mata nace?"
a hankali ya ɗaura hanu akan lips nashi ya shafa, kaseem yace "kiss?"
gyaɗa kai yayi, yace "kenan ba zaka iya hakuri ba idan kana ji bakasha magani ba? shine har zakayi kokarin raping mace?"
girgiza kai yayi da sauri alaman ba raping nata yayi niya ba, tsaki yaja yace "hameed na rasa wani irin jaraba ne da kai sam bakada hakuri ko kaɗan bakasan a matsayin kanwarka take bane?"
kanshi kasa yaki yadda su haɗa ido, ya kara jan tsaki yace "to Allah ya shiryeka ko ni da nake yayanka na girmeka nesa ba kusa ba banada wannan masifan jaraban"
tafiya zaiyi ya rike mishi hanu, ya juyo yace "me kuma?"
lumshe ido yayi, tsaki yaja shifa ya fara gajiya da lamarin hameed sai shegen lumshe ido kamar mace, yace "me kake so?"
wayanshi ya karba ya fara typing, mika mishi yayi ya karanta (Aneeta nakeso)
da mamaki ya kalleshi yace "to ai ba matarka bace ba yadda za'ayi tazo ta kwana anan"
lumshe ido ya kuma yi ya kara typing (ka auramin ita)
murmushi yayi bayan ya karanta kawai ya fita daga ɗakin ya rufe, Aneeta nunfashi take saukewa da kyar bayan ta koma ɗakin ta laɓe a bayan minat, a mugun tsorace take da gidan da kaseem harma da hameed wanda ya mata abinda bata taɓa zaton zaiyi ba yau, kuka ta fara tace "aneeta kin shiga uku baki lalace ba"
minat da tayi kamar tana bacci dariya takeyi sosai sabida itace ma taje ta kira ya kaseem tunda ta fita taji karan kofa tabi bayanta har zuwa lokacin daya kaseem ya shiga ɗakin kafin ta dawo ta kwanta.

haka har tayi kwana biyu a gidan bata yadda ta fito idan yana falo shima bai damu ba yasan idan ta gaji zata fito da kanta, a rana na uku minat ce ta sata dole ta fito sanye take da bakin dogon riga tayi kyau sosai fuskanta ya kara yin haske da kyau, zama tayi a kujeran dinning ta gaida Abi sannan ta gaida Ammi dasu kaseem, harda sultan ta gaishe sannan ta saci kallon hameed dake cin abinci bai ko kalli inda take ba, a hankali tace "ina kwana"
gyaɗa kai kawai yayi kamar ma baisan da ita ba, kaseem ya kalleshi sannan ya kalleta yaci gaba da shan tea, mai martaba daya gama yace "Alhmdllh, Aneeta"
da sauri tace "na'am Abi"
yace "zan haɗa aurenki da hameed"
ba ita ba har ammi da minat saida suka kaɗu da jin maganan, da kallo ammi ta bishi, kaseem yasan da maganan shiyasa bai damu ba, aneeta cikin bashi girma tace "to Abi"
yace "kina sonshi?"
shiru tayi tana kallon hameed dake cin abinci bai kalleta ba, yace "kina sanshi?"
wasa take da yatsun hanunta a hankali ta gyaɗa kai, murmushi sultan yayi yace "wow abu yayi kyau"
tashi Abi yayi yace "juma'a me zuwa aurenku saura kwana biyar kenan"
tafiya zaiyi ammi tace "mai martaba"
tsayawa yayi yana kallonta, tace "kamata a tabbatar tana sanshi kada a cutar da ɗaya"
yace "gashi ta amsa shima da kanshi yace yana sonta"
tana kallonshi tace "amma ai batasan komai ba"
mai martaba ya ɓata rai kamar bai taɓa dariya ba, tace "ni ba zan bari a cutar da mutum ba, ya kamata tasan cewar Abdulhameed ya taɓa aure...."
wani irin tsawa kaseem ya daka mata, shiru tayi tana kallonshi yace "ko sau ɗaya ko sau ɗaya ki zama...."
tace "karka kuskura ka gayamin magana kaseem sabida kafin kowa sanin abinda yake faruwa, sannan kai kanka kasan cutarwa ne ayi aure da ɓoye ɓoye"
cikin haushi da ɓacin rai da yake ciki yace "me amfanin tuna baya?"
tace "sabida kasan duk bamu aikata mai kyau ba?"
yace "kece dai amma ni..."
tace "amma kai me? kai mutumin kirki ne kaseem? bakayi komai ba? kafi kowa sanin auren hameed ba karamin tashin hankali zai tono ba kafi kowa sanin irin masifa da bala'in da za'a shiga matukar hameed ya samu sarautan yarima kuma yayi aure kafi kowa sanin abinda zai faru..."
buga kujeran yayi kamar zai ɓalla, saida abincin dinning ɗin duk suka zube, yana kallon cikin idonta yace "me zai faru? me zai faru nace idan hakan ya faru?"
dariyan bakin ciki tayi wanda kana gani kasan ba har cikin ranta tayi ba, tace "ina fatan baka manta cewar ABDULHAKEEM bai mutu ba yana raye......"
kamar zai fasa kunnuwansu yace "ya mutu zuwa yanzu ya mutu a inda yake baya raye"
itama kamar zata fasa kunnuwansu tace "Abdulhakeem...."
ihun da aneeta tayi yasa suka kalleta babu shiri, tana rike da hameed daya yanka jijiyan hanunshi yana zubar da jini kamar jikin jikinshi zai kare, ammi ce ta kwala ihu taje da gudu zata taɓashi kaseem yace "stay away from my brother"
yayi maganan cikin tsananin ɓacin rai, kasa taɓa hameed ɗin tayi sai rawa da jikinta yake, kaseem yana hawaye yace "idan ya mutu shikenan? duk zaku huta idan ya mutu?"
zama yayi akan kujera ya harɗe hanu a kirji yace "to shikenan Aneeta barshi ya mutu, watakila komai ya dawo daidai idan Abdulhameed ya mutu"
yana maganan yana hawaye me zafi, yace "amma ki sani"
ya nuna ammi yace "wallahi idan Abdulhameed ya mutu ko Abdulhakeem bai mutu ba saina kasheshi nayi alkawari"
zata taɓashi cikin tashin hankali ya kara daka tsawan da yasa jikin aneeta fara rawa yace "don't dare touch him Ammi"
cak ta tsaya, mai martaba kirjinshi ya rike yana jin jiri, kasa tim ya faɗi kaseem yana kallonsu babu abinda yayi sai naɗe hanu da yayi a kirji, yana kallon sultan dasu fadeel suna ihu, masu tsaro ne suka shigo jin ihu da wani irin tsawa kaseem yace su fita, jikinsu yana rawa suka fita, aneeta tana ganin jini yaki tsayawa ta sauke kanshi daga cinyarta daya gama ɓaci taje gaban kaseem ɗin ta durkusa, kafanshi ta rike cikin tashin hankali tace "dan girman Allah ya kaseem dan girman Allah ka taimaki hameed idan ya mutu ban san yadda zanyi ba, dan Allah ka taimakeshi jininshi yana gab da karewa"
ɗauke kai yayi ya juya yana kallon gefe yace "Aneeta ki barshi ya mutu"
ganin ba zai kulata ba taje da gudu ta cire ɗankwalin kanta ta ɗaure hanunshi dake jinin gam, janshi tayi a kasan zuwa kan sofa, kankara ta ɗauko a fridge tazo da gudu kamar mahaukaciya manna mishi tayi a hanun sabida ya daskarar da jini, tayi sa'a jinin ya daina gudu sosai ya ɗan tsaya, ta sauke kanshi daga cinyarta ta ɗaura akan sofan ta haura sama da gudu, first-aid-box ta ɗauko da sauri ta dawo ta ciro audiga da bandage kamar yadda taga anayi ta fara dressing ciwon, cikin sa'a Allah ya taimaketa hanun ya daina jini, tashi tayi ta fita ta kira driver taje asibiti, yaki shigowa da kanta ta ɗagashi ta fita dashi, sai nishi take sabida wahala, a mota suka tafi asibitin ya kaseem ɗin, suna ganinshi suka fara taimakonshi da gaggawa, Allah yasa suka ɗinke ciwon, yana kwance akan gadon tana zaune a gefenshi ta haɗa kanta da jikin gadon tana kuka, a hankali ya buɗe ido yana jin sautin kukanta, ji tayi ya rungume waist nata ya manna kanshi da bayanta, shiru tayi ta share hawayen, a hankali ta juyo gaba ɗaya ta yadda zaiji daɗin hugging ɗinta, a hankali ya matso sosai ya manna kanshi da kirjinta yayi shiru, shafa kanshi tayi cikin jin daɗi tace "Alhmdllh baka mutu ba na gode Allah"
murmushi taga yayi, hanunta ya rike yana kara cusawa a kanshi, cikin farin ciki taci gaba da wasa da gashinshi, lumshe idonshi kawai yayi.
turo kofan akayi ya kaseem ne ya kasa zama duk yadda yaso ya bari hameed ya mutu ya kasa yin hakan, da sauri ta ture kanshi yaki sakinta sai daɗa kanƙameta da yake, cikin jin kunya tace "sannu ya kaseem"
hawaye yake yi yana jin kunyan haɗa ido da kaninshi da ɓacin rai ya hanashi taimakonshi yace "ke zan yiwa sannu aneeta gaskiya sai yanzu hankalina ya kara kwanciya idan kika yadda kika aureshi zanfi samun nutsuwa"
a hankali tace "karka damu babu abinda zai hanani auren yarima hameed saide idan kaine ka hana ko kuma shi yace bayaso"
yace "na gode"
kallon hameed daya lumshe ido a jikinta yayi sai kuma ya kalli hanun dake ɗaure da bandage, yace "sannu hameed"
gyaɗa kai kawai yayi yana kara kanƙame waist na Aneeta, tureshi takeyi ta kasa sakin jikinta duk a takure take, ganin haka kaseem yace "ina zuwa"
fita yayi, da sauri tace "baka ganin ya kaseem ne?"
shiru yayi mata, sun wuni a hospital ɗin sai dare kafin kaseem yazo yace su tafi, tafiya sukayi suna shiga gida kaseem yace "sultan ya jikin Abi?"
yace "da sauki ammi tana can wajenshi"
yace "Allah kara mishi sauki"
sukace "ameen"
sukace "sorry ya hameed"
lumshe ido kawai yayi ya wuce ɗakinshi.

_jiddah ce....✍️_
08144818849
[20/08, 2:11 am] Shuraihu Usman: 🌸🌸🌸🌸🌸
*ƘADDARA TA*
🌸🌸🌸🌸🌸


Na
*Jiddah S Mapi*


*Chapter 6*


~Har aka fara shirye shiryen bikin babu wanda ya kara ɗago maganan, aneeta kam batama fita su zauna bale magana yayi nisa, kwance take akan gado dare ne kowa na bacci banda ita da take da tarin tambayoyi dayawa a kanta amma ta rasa wa zata yiwa, minat bata bata amsa koda ta mata tanbayan, shiru tayi sanye take da kayan bacci me kyau dogon riga silk, kasancewar silk yasa yake mannewa a jikinta sosai duk shape nata suka bayyana, net ne a wuyan rigan hakan yasa saman kirjinta da yake fari tas ya fito sosai, gashinta dake cikin net ta cire net ɗin sabida zafi sosai takeji, ishi ma ta fara ji, a hankali ta kunna wutan ɗakin ta sauke fararen santala santalan kafafunta, fita tayi daga ɗakin tana hamma ga bacci a idonta amma ta kasa yinshi ga ishi har gani take kamar ba zata isa wajen fridge ɗin tasha ruwa ba, wutan a kashe yake, sauka tayi ta buɗe fridge ɗin bayan ta kunna wutan, kashe wutan tayi ta haura stair ta buɗe ruwan zata fara sha, ji tayi an fizge goran, ihu zatayi ya toshe bakinta ya mannata da jikin bangon, idanunta kamar zasu zubo tsaban firgita, bakinshi yasa a wuyanta yayi mata sassanyar kiss, ta hanyan numfashinshi ta gane shi, ajiyan zuciya ta sauke, hanunta ya rike yana murzawa a hankali kuma yake kissing wuyanta, tureshi tayi tace "ka tsorata ni yarima"
murmushi me sauti yayi sannan ya kara mannata jikin bangon ta yadda ba zata iya kwacewa ba, jin kiss ɗin yayi yawa tace "sakeni bacci nakeji"
kin sakinta yayi, hanu taji yana sawa ta kasan riganta da sauri tace "kai yarima ka kyaleni"
bakinshi ya haɗa da nata ta yadda ba zatayi magana ba, yadda yaso yakeyi da jikinta sai numfashi yake saukewa a hankali yana samun wani kyakkyawan nutsuwan da rabonshi dashi ya jima, idan yana tare da ita ji yake kamar ya mallaki komai na duniya na jin daɗi, tafiya take da imaninshi musamman idan tasa kayan da yake kama jikinta, hanunshi taji a bayanta yana pressing duk yadda tayi ta kwace ya hanata saima kara mannata yake da bangon kamar zai shige jikinta, so much pleasure yake samu idan yana taɓa jikinta, kaseem da ya tashi cikin bacci sabida ishi ya buɗe fridge nashi baiga ruwa ba sai drinks tsaki yaja yasa slippers ɗinshi ya fita, kunna wutan yayi zai sauka ya gansu, da sauri hameed ya saketa, kamar zatayi kuka ganin ya kaseem a ranta tace "na shiga uku nikam asirina ya gama tonuwa a wajen ya kaseem"
hararan hameed tayi sannan ta juya kamar munafuka ta wuce ɗaki da goran ruwan a hanunta, kallonshi yayi baiyi magana ba ya wuce ya ɗau ruwan ya buɗe yana sha, har yanzu yana tsaye a wajen yana wasa da yatsunshi kanshi a kasa kamar munafuki, aje sauran ruwan yayi ya kama hanya kawai zai tafi, rike hanunshi yayi ya juyo yana kallonshi, hanu biyu yasa ya rike kunnenshi kanshi kasa alaman sorry, tsaki kawai yaja yace "wuce kaje ka kwanta"
a hankali ya tafi zuwa ɗaki, kaseem ɗinne ya rufe mishi kofa yace "bad boy"
Aneeta saida tayi hawayen kunya share hawayen tayi tace "yanzu zai rinka min wani kallo ko?"
da kanta take tambayan kanta, tace "ba zan kara fita ba wallahi bale na haɗa ido da ya kaseem"
da kyar ta samu tayi bacci.
washe gari kin fitowa tayi tana kwance a ɗaki, jin hayaniya a waje yasa tayi saurin tashi domin leka meke faruwa, gani tayi wasu ƴammata guda biyu sun shigo da trolley ɗinsu, sunyi masifan kyau suna kama da alama yaya da kanwa ne, murmushi tayi jin ammi tace "oyoyo yarana yaushe a kasa?"
karamar tace "jiya muka dawo momy tace mana auren ya hameed jibi shiyasa mukazo sai an gama zamu koma school next week"
cikin jin daɗi minat ta rungumesu tace "gaskiya aurennan zaimin daɗi tunda kuna nan, muje ciki"
ammi sai farin ciki take, dakinsu suka shiga tana ganinsu ta fara murmushi kamar ta sansu, ɗayar tace "itace amaryar ya hameed?"
minat tace "yes itace"
murmushi tayi tace "wow she's beautiful"
minat tace "unty Aneeta waɗannan yaran kanwar momy ne amma ta rasu tun da jimawa a hanun dadynsu suke suna karatu a kasar cyprus yanzu ma hutu suka samu ya haɗu da aurenku"
murmushi tayi ta buɗe musu hanu suka rungumeta tace "ya sunanku?"
karamar tace "ni sunana Amnah ita kuma Amrah"
tace "masha Allah sannunku da zuwa"
sakin jiki sukayi suka fara hira kamar dama sun san juna, zuwa sukayi suka gaida me martaba sannan suka dawo suka zauna a falon, ganin babu aneeta minat taje ta kirata fitowa tayi ba dan taso ba suka fara hiran tare, sultan ne ya shigo tareda fadeel da gudu sukaje suka rungumesu cikin jin daɗin ganinsu yace "amnah da Amrah yaushe kukazo?"
sukace "ɗazu"
zama sukayi a falon suka suka fara hira, aneeta ma tana ɗan hira itama tare da ita suke yi, kaseem ne ya shigo da uniform a jikinshi yace "suwa nakejin muryansu kamar ƴan kauyen nan"
dariya sukayi shima sukayi hugging nashi, Aneeta sunkuyar da kanta tayi tana jin mugun kunyanshi, murmushi yayi yace "Amarya harda ke aketa surutun?"
a hankali tace "eh"
janta yayi da hira har ta saki jiki.
hameed bacci yake a ɗaki sai can ya tashi yana sanye da jallabiya ya fito yana murza ido yana yatsine fuska tareda turo bakinshi cikin shagwaɓan ɗaya same mishi jiki, ganinsu Amrah yayi musu smiling sannan ya musu alaman welcome, shi tsoronshi suke shiyasa basa sakewa sosai idan yana waje, kallon Aneeta yayi tayi saurin ɗauke kai tana tuna abinda yayi mata ranan, smiling me kyau yayi sannan ya kalli ya kaseem dake danna waya, ji yayi hankalinshi ya kwanta ganin ya kaseem lafiya lau yana smiling da alama abinda yake a waya me muhimmanci ne.

Minat tace "unty aneeta zamu gyara miki kanki ko?"
gyaɗa kai tayi,

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login