Showing 1 words to 3000 words out of 85226 words

Chapter 1 - BA SONTA NAKE BA

Start ads

20 Aug 2025

167

Middle Ads


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

Compiled By Umar Dalha Funtua.

Copied By Ummee Yusuf.

[8/31, 6:05 PM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAKE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._



_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_


_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*


*_💃🏻NBA SONTA NAKE BA💃🏻



*✍✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾

*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*🖊
*w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ 🖊 *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.*


*~INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?~*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*


_Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samun wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook_. 👇


https://www.facebook.com/101594048306878?referrer=whatsapp


_Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana gwiwa a wajen rubutu._


*BA SONTA NAKE BA* littafi ne daya kunshi darrusa na yau da kullum,ina rokon Allah kaman yanda na fara lafiya yasa na gama lafiya.
Da fatan zaku bani hadin kai kaman yanda kuka saba.

حَدَّثَنَا يَحْيَى بْنُ يَحْيَى التَّمِيمِىُّ وَأَبُو بَكْرِ بْنُ أَبِى شَيْبَةَ وَمُحَمَّدُ بْنُ الْعَلاَءِ الْهَمْدَانِىُّ جَمِيعًا عَنْ أَبِى مُعَاوِيَةَ - وَاللَّفْظُ لِيَحْيَى أَخْبَرَنَا أَبُو مُعَاوِيَةَ - عَنِ الأَعْمَشِ عَنْ إِبْرَاهِيمَ عَنْ عَلْقَمَةَ قَالَ كُنْتُ أَمْشِى مَعَ عَبْدِ اللَّهِ بِمِنًى فَلَقِيَهُ عُثْمَانُ فَقَامَ مَعَهُ يُحَدِّثُهُ فَقَالَ لَهُ عُثْمَانُ يَا أَبَا عَبْدِ الرَّحْمَنِ أَلاَ نُزَوِّجُكَ جَارِيَةً شَابَّةً لَعَلَّهَا تُذَكِّرُكَ بَعْضَ مَا مَضَى مِنْ زَمَانِكَ. قَالَ فَقَالَ عَبْدُ اللَّهِ لَئِنْ قُلْتَ ذَاكَ لَقَدْ قَالَ لَنَا رَسُولُ اللَّهِ -صلى الله عليه وسلم- « يَا مَعْشَرَ الشَّبَابِ مَنِ اسْتَطَاعَ مِنْكُمُ الْبَاءَةَ فَلْيَتَزَوَّجْ فَإِنَّهُ أَغَضُّ لِلْبَصَرِ وَأَحْصَنُ لِلْفَرْجِ وَمَنْ لَمْ يَسْتَطِعْ فَعَلَيْهِ بِالصَّوْمِ فَإِنَّهُ لَهُ وِجَاءٌ ».

*It was narrated that `Alqamah said: "I was walking with Abdullah in Mina when he was met by Uthman. He stood and talked with him and Uthman said to him: `O Abu Abdur-ur-Rahman, shall we not marry you to a young girl who can remind you of the times past?` Abdullah said, `If that is what you are telling me, (let me tell you that) the Messenger of Allah (s.a.w) said to us: O young men, whoever among you can afford it, let him get married, for it is more effective in lowering the gaze and guarding one`s chastity. And whoever cannot afford it should fast, for it will be a shield for him."*


Sahih Muslim


*BISMILLAHI RAHMANIR RAHIM*



________Hmmmmm bansan ta ina zan fara baku labarin na da yake cukuikuiye ba *BA SON TA NAKE BA* wannan Kalmar da na saba ji kenan a gidan mu har zuwa gidan aure na, bari dai in fara muku daga d'an farko yanda zaku fi fahimta.


Suna na Fatima. Amma Inna ta na kira na da Zareefa a halin yanzu shekaru na basu fi 10 zuwa 11 ba muna shirye-shiryen rubuta common entrance a makarantan mu na boko sai dai yau tunda na shigo kuka nake sosai saboda cin mutuncin da akayi min yau har yayi yawa duk da ba yau aka fara min ba sai dai na yau d'in ya tsaya min a rai.


Uniforms aka zo dasu ana rabawa daga gwarzon Governor mu professor Babagana Umara Zullum, harda jaka wadda ya kunshi note books, tex books crayon pen da sauran tarkacen da d'alibi zai bukata gefe d'aya kuma ga sandal da socks amma aka tsallake ni wai dan ban biya 200 na PTA ba duk da kasancewar nafi kowa bukatan wa'yan nan kayan domin uniform d'ina ya gama yagalgalewa.


Basa tab'a ganewa Inna ta ina zata samu gudan 200 ta bani in kawo musu Ita da kyar take samo 30 da safe ta bani 20 in sayi alale wajan Maman Dije dake gidan mu 10 kuma ta bani a matsayin kud'in tara, toh a wannan halin 200 ba karamin kud'i bane a wajan mu.



Kudin taran ma in na zo dashi sai in rasa abun saya dashi, gashi kiri-kiri ana mana girki a makaranta a rabawa kowa banda ni da ban san me na tare musu ba, bakin jinin Malamai prefect harda monitor nake dashi akan wannan 200 da bana kawowa yasa duk suke jin haushi na, ina ji ina gani za'a tsallake ni a hanani abincin nan wanda nake masa kallon kaman naman kaza suke ci sai randa suka ga dama suke bani bani, duk ranan da na samu ci nake kaman in had'a da hannu na.


Abinci ne da ake rabawa ko kwatankwacin sa babu a gidan mu, dan wata ran alale mai kwai da hanta ake rabawa wata ran kuma jallof d'in doya ko macroni ko kuma na shinkafa da wake yaji manja, toh ina mu ina cin wannan kayan dad'in a wannan gidan namu na yawa.


Abban mu matan shi 3, dan haka in gari ya waye kowa shi zai nemawa cinsa da 'ya'yan sa abinda zai ci babu ruwan Baban mu da d'aukan nauyin ahalin da Allah ya bashi duk ranan da Allah ya bashi zai sayo masara ko dawa a nika dayawa a rinka tuwo da daddare da safe da rana kuma kowa yaji da kan shi dan haka duk yayuna da kanne na wanda muke uba d'aya da cousins d'ina duk tallah suke dan rufin asiri amma ni Inna ta bata yarda da tallah ba duk da ni kad'ai ce wajan ta tana iya kokarin ta wajan ganin ta sauke duk wani nauyi daya rataya akan ta dai-dai karfin ta shiyasa kaf gidan mu babu masu zuwa boko ko islamiya sai ni kad'ai wanda 'yan gidan mu sukewa lak'abi da iyayi ne sai dare kuma muke zuwa makarantan Allo gaba d'ayan mu amma banda 'yan matan da suke tsayawa zance abin su.



Kona dawo makaranta wata rana babu abinda zanci in Inna bata samu wankau tayi ba sai dai ta tura ni gidan su da yake makotaka da namu inci duk abinda ya sauwaka a wajan kakata kasancewar suma kaman gidan namu suke babu wadata sai dai su basu da yawa kaman gidan mu,ranan da ta samu kud'in wankau kuma ta kan bani hamsin in sayi garau-garau nan wajan Gwaggo Aisha ta d'an yarfa min a roba dan mugunta ko mai da yajin kirki bata zuba min kuma in na fita waje na saya ya zama abin magana da habaice-habaice shiyasa ko zan fita saya a waje Inna ta ke hanani.



*BA SON TA NAKE BA* shine kullum Kalmar da Baban mu yake fad'awa Inna ta in wani abu ya faru a cikin gida kuma kayan takaici a gaban kowa yake fad'a mata hakan sauran matan gida suyi ta shewa ana kara habaice-habaice tun bani da wayo har nayi wayo na gane me hakan ke nufi kuma a bakin matan gidan mu na tsinta wai Kakana Abban Inna ta tsohon soja ne in ba'a biya su fensho ba wajan Baban mu yake neman rance har kudin suka taru ya kai Kakana ba zai iya biya ba wanda yasa dole ya bashi Inna ta shiyasa ko kad'an bamu isa mu d'aga murya kaman kowa a gidan ba,Inna ta in ba wani abu take ba kullum tana cikin d'akin ta dan matan duk sun had'e mata kai har yaran su duk raini suke mata sai wajan matan kanin Baban mu Maman Dije take samun sauki dan babu ruwanta da hargitsin gidan mu sai kishiyarta itama tana shiga cikin sauran matan Baban mu tana taya su wulakanta Inna ta.




Haka na fito daga cikin makarantan ina kukana na karin takaicin ma 'yar silifas da nake lallab'awa kuma nake shan bulalan rashin sandal akai ina zuwa bakin gate ya tsinke, ban tsaya neman leda dan gyarawa ba na rike a hannu na nufi titi ido rufe na manta da akwai motoci kan titin burina kawai in ganni a gida.



Karan takawan brick ne ya dawo dani hayyaci na, ganin mota ya nufo ni gadan-gadan yasa na rasa yanda zanyi saboda firgita nan na durkushe ina jiran ta Allah ta kasance min.


Motan daya ja brick Allah ya taimake ni bai kad'e ni ba amma motan bayan shi sai da ya fasa mishi danger, shima na bayan shi ya buga mishi a takaice dai motoci kusan 5 sukayi hatsari duk a dalilina, kuma duk abinda ake ina nan durkushen ban mike ba.



Wani wanda motan shi yafi na sauran bugawa ya fito a zuciye ya janyo ni yana bala'i yana zagina ya d'aga hannu zai yarfa min mari, ihu na yi na rufe fuska ta da d'ayan hannuna ina jiran saukan marin amma na ji shiru ina bud'e idona naga ashe mutane ne suka rike shi suna bashi hakuri, ina jin ya sake min hannu na kama hanyan gida da gudu dama tsakanin makarantan mu da gidan babu wani nisa sosai.




Ban iya tsayawa a ko ina ba saboda zafin rana da yake kona min kafa ina shigowa Hajara na fita da katon tire da aka jera mata robobi da aka zuba garau-garau hamsin hamsin a ciki, ni dai ban san ya akayi ba kawai sai gani nayi munyi karo kayan kan ta sun zube kamin kice kwabo almajirai sun fara wawaso nima ganin haka na wawasushi roba 2 na kama ci dama na kwaso yunwa ta na fitan hankali.




Ihu Hajara ta fasa tana "Wayyoo Gwaggo zo ki gani zo kiga abinda Zareefa tayi min" jin an ambaci suna na yasa matan gidan da yaran su lekowa dukan su, ni kuwa ko a jikina ina gefe sai zabga loma nake yau na samu shinkafa da wake daya ji mai da yaji har roba 2.


Salati manyan suka fara suna bina da kallo yanda baki na yayi nasha-nasha da mai,Gwaggo Aisha da fitowar ta kenan tace" kan uba ke Hajara meke faruwa ya akayi kika min b'arin abinci haka?"



"Wallahi Gwaggo kin gan ta nan Zareefa ce ina fita ta shigo a guje ta ture ni har nayi barin, kuma tun kamin almajirai su zo ita ta fara wawason min abinci" Hajara ta karasa tana harara ta yanda nake ta sud'e roba dan ban san ma sunayi ba sam.



Wani maka da Gwaggo ta kai min a gadon baya ban san lokacin da na saki roban na gatsare tare da fasa ihun azaba ba, wuyan matattacen uniform d'ina ta kama ta jani zuwa ciki tana" lalle na yarda wannan 'ya ta gado mugunta, hasada da tsiya yo banda tsiya yanda kuke ke da uwar ki baku da allura a cikin d'akin shine ta koya miki yanda zaki na yi min barna kina jawo min asara??


Ke Bintu koki fito wallahi kabo na ba zaiyi ciwon kai ba duk inda zaki shiga ki fita sai kin bani kudina yanzu kuma wallahi ba sai anjima ba, ki fito na ce ".



Kallon yanda wuyan uniform d'ina yake kara yagewa yasa nace" Gwaggo ki sake min uniform d'ina kinga kina kara......" Ban samu karasawa ba sakamakon buge min baki da tayi tana huci tace" inifon din banza inifon din wofi ke iskanci uwar taki take koya miki ko boko shegiya yarinya duk wani gantali kin iya wai an likawa boko da baida baki"



"Ni ai abin nasu dariya yake sakani haka masu bokon suke ko akan su aka fara oho, dubi kiga ko takarda d'aya bata dashi balle fensir,ko da uwar me take rubutun?" Cewar Inna Asabe.




Inna ta duk tana jinsu amma ko lekowa bata yi ba balle ta tanka musu, hayaniya sosai ya kaure a gidan mu harda mokota masu zugi sai yi suke harda masu cewa a gaban su ma abin ya faru, dole yasa Inna ta fitowa daga d'aki jin abin yaki ci yaki cinyewa.



"Yauwa daddawa uwar zaman d'aki dole ai yau ki fito azo a biyani kud'ina naira dubu daya da dari biyu ciff wallahi ko biyar d'ina ba zaiyi ciwo ba".



Dariya suka fara suna " keko Aisha ina wannan taga har dubu da dari biyu sai dai in 'yar zata sai da ta biya ki" ko kuma kije wajan tsohon soja" wani tsohon soja sai dai ayi sata" ire-iren kalamai da suke jifan Inna ta dashi kenan.



Kaman yanda ta saba bata kula kowa ba ta koma cikin d'akin ta sai gata ta fito da dubu d'aya da dari biyu ciff da Gwaggo Aisha ta ambata ta mika mata babu kunya ta sake min riga ta karb'e kudin tana lissafi tana mamakin ina Inna ta ta samu wannan kud'i ita da burin ta yau sai ta wulakan tamu yanda taga dama amma cikin ikon Allah ta biya.



Duk watsewa suka yi cike da mamaki wasu ko cewa suke dama bar raina mutum baka san sirrin sa ba.



Ana cika min rigata na shigo d'aki ina kallon wuyan rigata na ce, "Inna dubi fa yanda ta maida min wuyan rigata gobe ya zanyi in tafi makaranta?"



Inna da ta had'a rai sosai ta ce, "ba wuyan riga ya kamata kiyiwa kuka ba, gobe kika ce za'a rufe karb'an kud'in common entrance ko?"


Gyad'a mata kai nayi ina cire kayana.



"Toh kud'in da nayi wata 3 da wani abu ina tara miki na common entrance d'in su na bada a maimakon abincin mutane da kika zubda, gobe ma in kin taso daga makaranta kada ki rinka kula da gaban ki".




Yawan comments yawan typing.
[8/31, 6:05 PM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._



_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_


_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```


*_And now_*


*_💃🏻UWANI💃🏻



*✍✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾

*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*🖊
*w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ 🖊 *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.*


*Addu'a Ga Wanda ka zage shi:*

Manzon

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login