Showing 75001 words to 78000 words out of 85226 words

Chapter 26 - BA SONTA NAKE BA

Start ads

20 Aug 2025

188

Middle Ads

amsa nayi nayi ko zan samu haske amma ban samu ba, tagumi na zuba kawai na zauna shiru can naji zuciya ta na azalzala ta kan in leka inga ko yana cin abincin?

Cikin sand'a na iso bakin kofan na leka ta bulin makulli, laptop din naga ya ture gefe yana ta kwasan gara harda lumshe ido alamun abincin yana mishi dad'i, rufe baki nayi da tafin hannuna kada dariyan da nake rikewa ya fito fili ya ji ni.

Ina kallon shi ya cinye abincin tas ya kora da juice sannan ya tattara kayan ka Kai su kitchen yazo ya zauna ya cigaba da aikin da yake yi a laptop din, ni ko sai da naga ya gyara komai ya zauna sannan na fito nayi hanyan kitchen ba tare da na kalli inda yake ba .

Da ido ya bini har na shige yana tunanin me zai fad'a wanda zai kare kan shi kan cewa ba shine yaci abincin ba, har na fito bai samu wata gamshasshiyar magana da zai gaya min in gamsu ba.

Tafiya nake a hankali ina kallon shi da alaman tambaya akan fuskata na waye ya cinye abincin?

Cikin kame-kame ya fara magaa " hey look don't think negative dan ko yunwa zata kashe ni banga abinda zai saka inci wancan jagwalgwalon ba I just gave it to the driver suka cinye ya dawo da...." Kasa karasawa yayi ya tsaya kallon yanda nake ta gyad'a mishi kai tare da murmushin rainin hankali.

"Meye kika wani zuba min ido kina dariya kaman wanda ke miki karya?". Saurin girgiza kai na nayi Ina danne dariya da yake son kufce min.

A fusace ya tashi yayi kaina yana " dariya kike min ni zaki maida mahaukaci?"

Aiko Ina ganin ya mike na kwasa a guce ina sakin dariyan da na danne na shige bangare na gudu ban tsaya a parlour ba na wuce daki na fad'a kan gado Ina dariya sosai .

Shima daya biyo ni da gudu bai san lokacin da ya saki murmushi har hakoran sa suka fito ba ya girgiza kai yana " lallai yarinya nan ta fara raina ni".

Nagode da addu'oin ku Allah ya bar zumunci nd Alhmdlh jiki na yayi sauki sosai .
[6/16, 9:21 PM] Golden Pen Writers Associ: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._

_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_

_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*

*_BA SONTA NAKE BA_*

✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍

https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/

*wΜΆΜΆΡ” Ξ±rΜΆΜΆΡ” Π²Ρ”Ξ±rΜΆΜΆΡ”rΜΆΜΆ'sΜΆΜΆ ΟƒfΜΆΜΆ sΜΆΜΆΟƒ gΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ*
*wΜΆΜΆΡ” wΜΆΜΆrΜΆΜΆΓ­tΜΆΜΆΡ” Ξ±sΜΆΜΆsΜΆΜΆΓ­dΜΆΜΆΓ­ΟƒuΜΆΜΆsΜΆΜΆlΜΆΜΆΡ‡ pΜΆΜΆΡ”rΜΆΜΆcΜΆΜΆΡ”Γ­vΜΆΜΆΡ” nΜΆΜΆΟƒ pΜΆΜΆΞ±Γ­nΜΆΜΆ,*
*sΜΆΜΆΟƒ mΜΆΜΆΞ±gΜΆΜΆΓ­cΜΆΜΆΞ±lΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ cΜΆΜΆrΜΆΜΆΡ”Ξ±tΜΆΜΆΓ­vΜΆΜΆΡ” gΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ* ✍ *,Π²Ρ”hΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ.Ξ± pΜΆΜΆrΜΆΜΆΟƒdΜΆΜΆuΜΆΜΆcΜΆΜΆtΜΆΜΆ ΟƒfΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆ*ΜΆ *,sΜΆΜΆΞ±vΜΆΜΆΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ, fΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆ Γ­tΜΆΜΆ wΜΆΜΆΓ­lΜΆΜΆlΜΆΜΆ* *cΜΆΜΆΞ±uΜΆΜΆsΜΆΜΆΡ” Ρ‡ΟƒuΜΆΜΆ nΜΆΜΆΟƒ pΜΆΜΆΞ±Γ­nΜΆΜΆ.*

*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*

Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.

*INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*

Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buΖ™ata namu daga farko.

Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana Ζ™ara mana Ζ™arfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.

*Bismillahir Rahmanir Raheem*

Assalamu alaikum yan uwa da fatan munyi sallah lafiya, Allah ya karb'i ibadun mu ya nuna mana na gaba Ameeen.

*39&40*

"kada abinda kika gani ya tayar miki da hankali domin matan masu kud'in nan haka suke sun fi son 'ya'yan su su auri 'ya'yan masu kud'i kamar su, bakomai yasa kika ga tana mana wannan kallon ba sai dan sanin mu talakwa ne.

Idan muka cigaba da yi musu addu'a sannan kuma ita Zareefa zata iya samo soyayya surukan ta wajan dagewa da kyautata musu tare da yi musu zallar biyayya" Maa ce take fad'awa Inna cikin kwantar mata da hankali.

"Hmmmm hakane Maa har hankali na ya kwanta da tunda na dawo na kasa sukuni domin na san yanda wannan matsalar take" Inna ta amsawa mahafiyar ta cikin sanyin murya..

" Ki kara kwantar da hankalin ki saboda mun yarda da tarbiyan da muka bata ba zata tab'a yin abinda zai b'ata sunan ta ko na gidan ku ba" Maa ta kara tabbatar mata nan dai ta daura da shawarwari da hira masu sanyaya zuciya sai ga Inna da tazo mata wani cikin damuwa da sanyi jiki ta ware suna ta hira harda kyalkyalan dariya.

Bayan kwana 2 Gwwggo Aisha ta had'a duk wasu 'yan kud'ad'e da suke hannun ta tare da sayar da wasu kayayyakin ta saboda ta samu isassun kud'in zuwa wajan boka, dama haka take duk tabi ta sayar da abinda take dasu dan ko dakin Inna Asabe yafi nata kyan gani domin ita ta fawwalawa Allah lamarin ta ta rungumi sana'an ta kuma alhmdlh tana samu daidai gwargwado domin tana sayan kayan daki da kadan kadan tana gyara dakin ta.

Sun je wajan bokan ita da lantana da yake can jejin Goshe ko tsoro basa ji na yanda hanyoyin maiduguri suka lalace, sunyi sa'a sun same shi ya basu magani amma yace a abinci za'a zuba mishi na kwana 3 in dai har yaci abincin toh zai min wani irin tsana da bashi da iyaka ya min koran kare a gidan shi.

Wani kullin maganin ya Kara miko musu yace shi wannan kuma a turare zasu saka Hajara ta rinka shafawa a duk lokacin da zata je kusa da shi , in har ya shaki kamshin toh shikenan an wuce gurin zata zama itace mace kad'ai a rayuwar shi ko uwar shi ba zai kara tuna ta ba.

Cikin tsananin farincikin samun nasara ta dawo gida ta labartawa Hajara yanda sukayi da boka, nan kuwa ta hau murna kaman da gaske harda su rawanta wai ta kusa samun miji balarabe.

***************

Kaman yanda ya saba kullum sai yaje ya gaida iyayen nashi yauma ya isa gidan nasu akan lokaci domin ya samu Abban shi a gida bai fita ba, cikin girmamawa ya isa gare shi ya zauna wajan kafafun shi sannan ya gaishe shi yana daura kan shi kan kafar Abba.

Cike da so da kaunar tilon d'an nashi ya amsa yana mai shafa gashin kan shi, dan yanzu sosai suke shiri ba kaman da ba da kullum suke cikin rigima kan hallayyar shi ganin yayi auren yasa yake ganin ya natsu sosai.

"Ina 'yata tana lafiya ko?" Abba ya tambaya bayan ya amsa gaisuwan nashi.

"Tana nan lafiya Abba tace ma in gaishe ku" ya bashi amsa yana wani tsunne Kai kaman da gaske.

"A'a ni gaisuwan nan ta ishe ni hakan nan tunda taki zuwa mu ganta koda yake bata da laifi kai ne kake mana rowan ta ko Hajiya?" Ya karasa yana maida hankalin sa kan Mom da take saukowa yanzu.

Sai da ta tab'e baki ganin dukkan su basa kallon ta sannan ta kirkiro murmushi tare da karasawa gare su ta zauna kusa da Abban tana mai cewa " babu batun rowa ririta amaryar sa yake" ta karasa tana dariya kaman da gaske.

Dariyan suma sukayi suka cigaba da hiran su har zuwa wani lokaci sannan ya mike yace zai tafi

"Ya maganan da mukayi da kai sai yaushe zaka fara fitowa office?" Abba ya dakatar da shi.

"Sai nan da 2 months" yace yana sosa keya, dariya suka mishi Abba yana " ja'iri wata 2 ai kaman kwana 2 ne yanzu zai zo ya wuce, amma ka tabbatar ka kawo min 'yata mun gaisa".

Mom da duk haushi ya cika ta na me yasa Abba yake son gani na ta bud'i baki zatayi magana yayi saurin dakatar da ita wajan daga mata hannu ba dan taso ba tayi shiru tana gani har Zafar din ya fice zuciyar shi fari tass dama abinda yasa yace sai bayan wata 2 zai fara aiki kamin nan ya gama da chapter na ya Zama free man zaiyi abinda yake so.

Ni kuwa bayan wannan incident daya faru tsakanin mu wanda ya kasa barin kwakwalwata bamu kara zama waje daya dashi ba sai dai da naji motsin shi zan l'eko in kare mishi kallo sometimes yana cin abinci sometimes kuma yana wannan danne- dannen shi a laptop, ni dai har yau ban san me yasa bana gajia da kallon shi ba.

Yau tunda na tashi na gama aiki na zauna ina duba wani littafin Hadisi cikin litattafai na islamiya, wannan mayen kamshin nashi shi ya fara min sallama, wani irin zillo zuciya ta yayi kaman zai fad'o kasa jin wannan sassayan muryan yana cewa " ki shirya anjima da daddare zamu je ki gaida su Abba, nd saura in muka je kada ki kama kan ki kije kiyi ta musu kauyanci ki da kika saba kiga yanda zan tsaba miki ".

Maimakon inji haushi ni dariya ma ya bani dan haka ban san lokacin da na saki wani kayataccen murmushi ba, wai nice zanyi mishi kauyanci ko ce mishi akayi daga kauye nake oho.

Cike da takaici yake kallon yanda na sunkuyar da kai kasa ina murmushi, shifa wannan sabon dabi'a da na samu haushi yake bashi da duk abinda zaiyi min ko ya fad'a min baya bani haushi balle in nuna ko inyi kuka, in ya ganni ina kuka wani dad'i yake ji na musamman amma da yanzu bana nuna jin haushi sai yaji duk haushi ya kara cika shi.

Cike da tsana ta ya hamb'are ya fice yana" duk abinda za'a mata sai ta zauna tanawa mutane dariya, mayya kawai ni dai ba zaki cinye ni ba" yana magana yana mai ficewa daga parlourn.

Tashi nayi na karkad'e jikina still murmushin bai bar fuskata ba wai nice mayya hmmmm.

Tunda yace zamu je gaida iyayen shi duk sai na kasa zaune na kasa tsaye ina tunanin me zan kai musu da zan burge su, abinka da masu kud'in nan ba komai zaka musu kayi gwanin ta ba.

Duk tunani na ya tsaya ne kan girki, toh in banda girkin me nake dashi da zan kai musu, kitchen na shiga nayi tsaye ina tunanin what should I cook? Wai meye nawa da zan takura kai na kan sai na musu gwanin ta kwana 2 nan mantawa da nake cewa auren temporary nake zai iya sallama ta at any time tunda yanzu mun bawa wata d'aya baya, saurin kawar da wannan tunanin nayi saboda yanzu na tsani in tuno da hakan a cikin raina.

Tunani na ya tsaya ne kan inyi musu abincin gargajiya maybe zasu fi son ci, ina da garin ndalayi da aka had'o min cikin gara ban tab'a amfani da shi ba,yau shi na d'auko na daura tukunya mai dan girma da ruwa dai-dai yanda nake so.

Kamin ruwan ya tafasa na gyara kayan miyana na daura miyan a gefe, miyar kubewa danya da yaji zallar naman rago sannan na tuka tuwo bayan na wadata ruwan daya tafasa da man gyad'a, sabuwar warmers da ban tab'a amfani da su ba na ciro na zuba abincin a ciki bayan nayi malmala masu kyau sannan na Kara bin man su da man shanu na rufe.

Ganin akwai sauran time yasa nayi samosa da meat πŸ₯§ suma nayi package din su a wasu containers masu kyau, duk na jera su a cikin yalwataccen basket sannan na lullub'e saman da tumakasa mai kyau na fito da shi kan dinning sannan na wuce dan shiryawa.

Cikin atamfa super fari tas da adon flowers blue na shirya kaina na zauna na dan yi make-up dina sama-sama harda kashe d'auri duk da Ina jin ana kiraye-kirayen sallah magarib ban dakata ba saboda ina fashin sallah, jewelries da na saka duka pure gold ne hakan sai ya kara haskani nayi kyau sosai abina .

Sai da na gama kwalliya na sannan na tuna ashe ban ci abincin ba, fitowa nayi kitchen na zuba rabo na a plate shima na zuba mishi komai da nayi harda su snacks din dan a tunani na ba lalle bane yaci abincin gargajiyan da na girka.

Ina cikin cin abinci na naji motsin ya shigo Kuma na tabbata yana dinning yana kwasan gara sai dai shegen girman kan shi yasa ba zai tab'a admitting cewa yana ci ba sai dai yace masu gadi yake bawa.

Muryan shi ne ya katse ni yana in fito mu tafi, sai da na kara shafe jikina da humra mai dad'in kamshi na yafa mayafi blue mai dan girma na saka takalmi flat shima blue da poss din sa wanda wayata ce kawai a ciki sannan na fito hannu na dayan d'auke da plate din da na gama cin abinci, a tsaye na same shi shima ya shirya cikin kananan kaya riga ash color da wandon jeans fari sol.

Ta gefen ido na kalli kan table din ga mamaki na tass ya cinye abincin ko tab'a su snacks din baiyi ba, fasa shiga kitchen din nayi na tsaya na tattara kan table din na wuce dasu Ina kallon shi ta gefen ido dariya na cina ganin yanda ya wani tsare gida wai shi ala dole ba shine yaci ba.

Naso in tsaya in wanke plates da muka bata sai dai gudun masifan shi yasa na bari kan sai mun dawo, koda na fito shi har ya fice nima ban tsaya b'ata lokaci ba na d'auki basket da na jera abincin a ciki nabi bayan shi, a dan tsorace na isa ga motan da yake ciki duk da kasan zuciya ta cike yake da farincikin yau zan fita in ga gari dan tunda aka shigo dani cikin gidan nan ko bakin gate ban tab'a lekawa ba.

Koda na iso bakin motan sai nayi tsaye na rasa ya zanyi in shiga kada in shiga baya yace na maida shi driver sannan ina gudun shiga gaba yace na raina shi, shahada nayi na bude gidan gaban na shiga ganin ko inda nake bai kalla ba saima mayar da kan shi da yayi yana duba wani abu a cikin locker, sai da na zauna sannan na mayar da murfin na rufe tare da neman inda zan ajiye basket d'in.

Basket d'in hannu nawa yabi da kallo kaman zaiyi magana ko me ya tuna oho naga kuma ya mayar da kanshi gefe tare da jan motan muka fita a gidan ba tare da ya Kara kallo na ba.

Shiru cikin motan kaman babu mutane a ciki har muka iso wani tangamemen gida wanda ko ta waje kasan masu gidan sun jiku da naira, horn d'aya kawai yayi sai ga mai gadi ya taho da gudu ya zuge mana gate muka kutsa kai cikin hadadden gidan, baki sake nake bin gidan da kallo ashe da gaskiyan shi da yake cewa kada na mishi kyauyanci.

Talle min baki dana sake yayi da yatsa yana harara ta yace" wato baki yarda da abinda na gaya miki ba ko?" Yace yana jefa min mugun kallo, b'ata fuska nayi ina shafa baki na dan ba karya naji zafi sosai.

Bai bi ta kaina ba saima bud'e motan da yayi ya fita abin shi, shiri na saita natsuwa ta na bud'e murfin motan nabi bayan shi ganin yana son bace min, tun kamin mu karasa ma'aikatan gidan nasu suke ta durkusawa har kasa suna kawo mana gaisuwa amma maimakon ya tsaya ya amsa gaisuwan cikin mutunci sai dai kawai inga ya daga musu hannu ya wuce abinshi a zuciya ta nace wato shi ko ina yake sai ya nuna wannan girman kan nashi.

Wata mata ce ta karaso gaba na cikin sauri zata karb'i basket din hannu na nace mata ta bar shi amma ta nace sai na bata,ni kuwa ganin zata kusan sa'a da Inna ta yasa naki sake mata, dago kan da zanyi naga ashe bai shiga ba ni yake jira wani mugun kallo ya watsa min mai kama da warning yasa na sake mata basket d'in babu shiri na karaso inda yake jira na.

Hannayen mu ya tsarke waje d'aya sannan yayi sallama muka shiga cikin parlorn ,ashe abin kallon na ciki banga komai ba, ban san yanda zan kwatanta muku ba amma gidan yafi gaban had'uwa da kyar na shanye kauyanci na wannan karon na daina kalle-kalle na kalli gaba na, a can tsakiyan parlour Abba ne da Mom zaune kan wani lallausan rug sun saka warmers a gaba da alamu abinci suke shirin ci muka zo.

Abba fuskar shi d'auke da fara'a ta musamman yake amsa sallaman yayin da Mom Kuma baka gane yanayin da take ciki gata nan dai fuskan nan nata ba yabo ba fallasa, sau d'aya kawai na dago daga nan ban kara gigin d'agawa ba saboda kunya duk ya gama lullub'e ni yanda muka shigo hannun mu sarke nayi ta kiciniyan kwacewa amma bai bani daman hakan ba.

Kusa da Mom matan nan ta duka har kasa ta ajiye basket din sannan ta fice, sai da muka zo tsakiyan parlorn sannan ya sake min hannu ya karasa kusa da Abban shi ya zauna yana zuba musu shagwaba kaman karamin yaro suna biye mishi.

Ni dai daga dan nesa dasu na tsugunna Kai na a kasa na fara gaishe su, cike da kulawa Abba ya amsa yana in karaso kusa Mom in zauna mana ya zan

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login