Showing 45001 words to 48000 words out of 85226 words

Chapter 16 - BA SONTA NAKE BA

Start ads

20 Aug 2025

182

Middle Ads

kaman yanda mukayi magana tun kwanaki 3 da suka wuce amma na jika shiru, so yau ne deadline d'in kuma dole ne in cika alkawari na dana d'auka na samo maka mata a cikin 'ya'yan dangi".

"Kayi min afuwa Abba yanzu haka abinda nazo fad'a maka kenan na tarar kuna kallon wa'azi shiyasa na jira ku gama sai muyi magana" ya amsa yana wani sussunne kai.

"Okay sai yau kaga dama kazo min da zancen??

Hmm toh bakin alkalami ya bushe gobe zanje duk wacce tayi min itace matar ka insha Allah" Abba ya karasa hankalin sa kwance.

A rikice Zafar ya d'ago da kai ya rarrafo gaban Abba ya fara magana duk a rikice" Abba wallahi ba wai nayi biris da maganan ka bane na zata kace in kawo ta yau ne shiyasa nayi shiru, please Mom kisa baki wallahi maganan da nazo dashi yanzu kenan please Abba".

"Alhaji kayi mishi afuwa tunda bai fahimci abinda kake nufi ba sai yanzu ". Cewar Mom kenan da duk har yanayin ta ya canza.

"Hum kuma daina b'ata bakin ku kema kin san in nayi magana d'aya bana canza ta".

"Abba na sani wallahi na sani amma dan Allah kayi hakuri ba dan hali na ba" ya cigaba da magiya shida Mom Abba yana jin su bai kula su har sai da ya wana su son ran shi sannan ya ce;

"Ya isa haka naji sai ka kiyaye next time 'yar waye ne ka samo mana??"

Harshan sa har hard'ewa yake wajan bada amsa " sunan ta Zareefa a garin nan take 'yar Mallam....."

"Mallam kuma Zafar ?" Mom ta katse shi fuskar ta d'auke da matsanacin damuwa.

Kamin ya bata amsa Abba ya karb'e da cewa" ke yakewa bayani da zaki katse shi?

Meye laifi a auren 'yar Mallam, so kike kiji yace 'yar Alhaji ko 'yar governor or what?" Ya karasa fuskar shi na nuna bacin rai.

Cikin kwantar da murya Mom ta shiga bashi bashi hakuri bai amsa ba illa mikewa da yayi ya wuce sama tare da cewa Zafar ya biyo shi.

***********

Gwaggo Aisha da kawar ta Lantana suna tattaunawa cikin farinciki a cikin motar haya suna dawowa daga kauyen Manguno inda aka kai ta wajan wani boka.

Cikin annashuwa ta ce" gaskiya Lantana na jinjina miki dama kin san irin wajan nan.amma kika barni ina ta shan wahala kan kananan kwarin nan?"

Cikin fariya Lantana tayi wani dariya ta amsa da " A'i kenan ai ba nan kad'ai na sani ba wajaje dayawa na sani kin san duniyan nan sai da dan shige-shigen nan zaki kwacin kanki kuma ki wuce rainin miji ko kishiya.

Kin gan ni nan wallahi Mallam Ado sai abinda nace a gidan sa yake babu wanda ya isa ya tsallake magana ta har matan shi da yaran su".

"Kai kawata kina wuta ina bin ki da fetir har kinsa na fara hangowa ina juya Bintu da wannan fitsararriyar 'yar ta" cewar Gwaggo Aisha cikin jin dad'i.

"Ke dai kibi duk sharud'a daya kindaya miki kiga aiki da cikawa kasancewar aikin shi kaman yankan wuka yake.

"Ai dole ne in bi sharud'an nashi" da wannan tattaunawan har suka iso gida.

Sai bayan karfe 3 bacci yayi nasaran sace ni nan kan sallayan, kiran sallah farko Inna ta farka ta ganni kwance kan sallaya bata tashe ni ba tayi alwala ta fara nata nafilfilu kasan zuciyar ta kuwa tana mamakin kwanciya ta a nan.

Sai da aka fara sallah a sauran masallatai sannan ta tashe ni na fita nayi alwala nazo na kabbara sallah, ko azkar kasawa nayi saboda baccin dake cin ido na kara bingirewa nayi na cigaba abina anan Inna ta fahimci bacci bai ishe ni ba jiya cikin tausaya min ta kama 'yan aiyukan ta nan cikin d'akin ba tare da ta fita ba, bata kawo komai a zuciyan ta ba duk a zaton ta ban dawo dai-dai daga shock na rabuwa da Yaya na ba.

A wannan Gwaggo Aisha tayi bine-binne ta a mashigar kitchen d'in mu ta saka kujera a k'ofar d'akin ta tana jira mu fito mu tsallaka kaman yanda bokan ta yace.

Cikin ikon Allah Inna itama baccin ta koma tunda babu wani abu na azo a gani da zatayi, cikin bacci muka ji kaman ana tonon abu cikin k'asa, ko motsi banyi ba amma na farka sai Inna tace tayi karfin halin fitowa jin muryan maza kuma bakin murya ya cika gidan.

Maza tayani sun kai su biyar kowanne da abu a hannun shi yana tono Baban mu na tsaye daga gefe , kamin Inna ta bud'i baki tayi tambayi me yake faruwa suka ji muryan Gwaggo Aisha tana" kai! Kai!! Ku dakata me kukeyi haka?"

Duk suka juyo suna kallon ta duk ta had'a zufa sai wurwurga ido take, Baba ne ya bata amsa da " meye naki na ihu haka sai kace gidan ki ake tono,

Toh gini zanyi zan canza ginin gidan nan ya zama na zamani".....
[1/26, 7:12 AM] Golden Pen Writer's Assoc: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._

_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_

_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*

*_BA SONTA NAKE BA_*

✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍

https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/

*wΜΆΜΆΡ” Ξ±rΜΆΜΆΡ” Π²Ρ”Ξ±rΜΆΜΆΡ”rΜΆΜΆ'sΜΆΜΆ ΟƒfΜΆΜΆ sΜΆΜΆΟƒ gΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ*
*wΜΆΜΆΡ” wΜΆΜΆrΜΆΜΆΓ­tΜΆΜΆΡ” Ξ±sΜΆΜΆsΜΆΜΆΓ­dΜΆΜΆΓ­ΟƒuΜΆΜΆsΜΆΜΆlΜΆΜΆΡ‡ pΜΆΜΆΡ”rΜΆΜΆcΜΆΜΆΡ”Γ­vΜΆΜΆΡ” nΜΆΜΆΟƒ pΜΆΜΆΞ±Γ­nΜΆΜΆ,*
*sΜΆΜΆΟƒ mΜΆΜΆΞ±gΜΆΜΆΓ­cΜΆΜΆΞ±lΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ cΜΆΜΆrΜΆΜΆΡ”Ξ±tΜΆΜΆΓ­vΜΆΜΆΡ” gΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ* ✍ *,Π²Ρ”hΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ.Ξ± pΜΆΜΆrΜΆΜΆΟƒdΜΆΜΆuΜΆΜΆcΜΆΜΆtΜΆΜΆ ΟƒfΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆ*ΜΆ *,sΜΆΜΆΞ±vΜΆΜΆΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ, fΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆ Γ­tΜΆΜΆ wΜΆΜΆΓ­lΜΆΜΆlΜΆΜΆ* *cΜΆΜΆΞ±uΜΆΜΆsΜΆΜΆΡ” Ρ‡ΟƒuΜΆΜΆ nΜΆΜΆΟƒ pΜΆΜΆΞ±Γ­nΜΆΜΆ.*

*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*

Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.

*INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*

Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buΖ™ata namu daga farko.

Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana Ζ™ara mana Ζ™arfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.

*Bismillahir Rahmanir Raheem*

*21&22*

"Haba Mallam ba zaka bari mu d'an kimtsa ba gyara da sassafe haka?" Gwaggo Aisha ke fad'an haka cikin matukar tashin hankalin gani za'a saka ta wahalan banza.

"Wani irin kimtsawa sai kace daga kofar ki aka fara, ki bari in aka zo kofar ki sai ki kawo korafin naki" Baban mu ya amsa a dakile.

"Ni ba wani abu nake nufi ba naga safiya ce kuma ai ko ita Bintun zata so a bar ta ta d'aura abin karyawa ita da 'yar ta, ko ba haka ba Bintu?" A zuciyar ta kuwa tana ta addu'an Allah yasa Inna ta amince da abinda ta fad'a a fasa tonon sai bayan mun shiga kitchen d'in mu munyi girki, kamin nan mun sallake abubuwan da ta binne shiyasa dama ta zab'i binnewa a kofar kitchen d'in mu sanin ba wanda zai taka wajan sai mu.

"A'a in ta nine bakomai suyi aikin su, ba zamu rasa yanda zamuyi ba, wannan ai abin farinciki ne kuma cigaba ne muma zamu zama 'yan gayu" Inna ta amsa tana dariya sauran mutane da suke wajan suma dariyan sukayi suka cigaba da aikin su ba tare da sun lura da halin da sun lura da halin da Gwaggo Aisha ta shiga ba.

Afujajjan ta shiga d'akinta sai safa da marwa take duk ta had'a zufa ta kasa zama sai neman hanyar da zata dakatar dasu take amma kasan zuciyar ta kuwa gargad'i take mata na kar ta tsauwala har ta tonawa kanta asiri cikin mutane, da wannan shawaran ta nemi waje ta zauna sai karkad'a kafa take tana sharce gumi,Hajara tana ankare da ita amma taki tanka mata.

Ni kuwa tunda naji Baba yace ginin zamani za'a yiwa gidan mu na kasa ko daga yatsa na sannan kuma na tabbatar da zancen bawan Allah nan na jiya gaskiya ne kenan in ba haka ba ina Baba yaga kud'in ginin zamani,

"Ya Allah ka dube ni ka fidda ni cikin wannan fitinan" nace cikin raina.

Basuyi wani nisa ba suka fara tono tsirkullen Gwaggo Aisha, cikin mamaki suka tsaya cirko-cirko suna kare musu kallo an rasa mai magana cikin su.

"Mu cigaba da aikin mu mana" cewar d'aya daga cikin su.

"Kaman yaya mu cigaba bayan wannan abubuwa da muka tono,kamata yayi a sanarwa mai gidan sai ya san matakin da zai d'auka" nan duk sukayi na'am da shawaran nan suka tura karamin cikin su kiran Baba.

"Innalillahi wa inna ilahi rajiun" shine Kalmar da Inna ta samu daman maimaitawa fitowar ta kenan daga bayan gida taga sun tara tsirkullen a gefe suna ta tattaunawa akai.

Kasa wucewa tayi tana mamakin me ya kawo layu da guraye kofan kitchen d'in ta, fargaba fal a zuciyar ta na kada ace itace ta binne su,har Baba iso wajan tana tsaye sai ambaton sunan Allah take.

"Wannan ai ba wani abin tada hankali bane, ta yiwu tun na kakanin mune sune zasu iya ajiye irin wayan nan abubuwan su jima haka kasa haka" cewar Baba kenan cikin rashin d'aukan abin da muhimanci.

"A'a wayanan tsurkullen basu dad'e a kasa ba ta, da gani kwananan aka binne su" cewar d'aya daga cikin su.

"Matsalaha daya ne shine a k'ona su kurmus in ma mai shi da wata manufa ya binne toh zai zo da sauki"

Inna da jikin ta yayi sanyi sosai barin ma irin kallon tuhuma da taga Baba na aiko mata da shi yasa duk taji ba dad'i, tana jin anyi maganan konawa yasa cikin sauri ta wuce d'aki ta d'auko ashana a cikin drowern d'aki inda take ajiyewa in ta sayo kwali.

Kamin ta fito har sun tara su a gefe sun zuba kalanzir suna neman ashana, Baban mu ta mikawa ta koma gefe ta tsaya babu b'ata lokaci wanda ya karba ya ketta ashana bayan yayi addu'oi nan da nan kuwa wuta ya kama ya fara ci bakin hayaki na tashi a jiki kaman ana kona taya.

A d'akin Gwaggo Aisha kuwa tunda aka cinnawa layun nata wuta ta fara ganin d'akin na juya mata ga wani zafi-zafi da take ji a jikin ta kaman ana hura mata wuta, tun tana iya daurewa har abin yafi karfin ta ta fara ihu tana birgima a tsakiyar d'aki.

Sharewa nayi kaman banji ba dan nima ina fama da nawa matsololin inda zan samu daman ihun nima da nayi ko zanji sauki cikin raina.

Tsaki naja ina mikewa tsaye da d'an sauran kuzarin daya rage min na fita saboda yanda naji ihun yaki tsayawa kuma kana ji kasan wanda yake yana cikin mamuyacin hali.

Kus-kus na tarar masu aikin nayi ban kula su ba nayi wucewa ta zuwa d'akin Gwaggo Aisha da zan iya kirga shiga ta ciki tunda aka haife ni.

Da gudu na karasa nima ina kokarin rike ta kaman yanda naga Inna da Hajara sukayi Inna sai tofa mata addu'oi take, ban tsaya b'ata lokaci ba nima na fara taya ta muka cigaba da tofa mata har ta daina birgima sai jikin ta da yake rawa sosai, tuni Baban mu ya fice abin shi zuwa d'akin shi ya bar mu da ita.

Mun Kai good 30 mins muna yi mata sannan ta dawo hayyacin ta sai ajiyan zuciya take a kai- akai hawaye na bin gefen fuskan ta amma koda wasa bata bud'e ido ba, ganin taji sauki yasa Inna mikewa tacewa Hajara ta lullub'a mata abin rufuwa da alamu ta samu bacci, amsawa tayi da toh tare da mana godiya muka fito zuwa d'akin mu Inna bata zauna ba ta d'auki dubu d'aya ta bawa Ibrahim kan ya sayo mana abin karyawa a waje.

Tunda ta bada sakon ta dawo d'aki ta zauna shiru na san shirun nata baya rasa nasaba da abinda ya faru a safiyar yau, ba Inna da take shekaru ba ko ni nan na fahimci abinda ya faru da Kuma musababbin ta.

Allah sarki Inna ta kamin ka samu mai irin zuciyar ta a wannan zamnin sai an tona, tsab ta gane komai amma taje tayi mata addu'a, da wata ce sai dai ta mutu ko nice nan Yasin ko kurar da ya debo ki ba zan kallah balle har in nema miki waraka barin ki zanyi ki girbi abinda kika shuka.

Shi kuwa Baban mu akwai shi da kyaluwa ba kasafai kake gane mishi ba in ba harkan kud'i bane, ko ya fahinmci abinda ya faru ko bai fahimta ba oho.

*************

A b'angaren Zafar kuma yau cikin farinciki ya tashi ko ba komai ya ragewa kan shi tention da kuma fad'an Abban shi, ba komai yake kara mishi nishad'i ba kaman in ya tuno da hiran shi da Abban shi jiya a kaina.

Murmushi ya kara saki lokacin da ya tuna Abba shi yace" ina matukar alfahari da kai ka birge ni sosai da ka tashi neman aure baka nema cikin 'ya'yan masu kud'i ba ka nema a irin gidan da nake son in samu sirka,

Naji dad'i da baka bi halin mahaifiyar ka ba na wajan kin talaka, da mai kud'i da talaka duka Allah ne yayi mu saboda hikimomin shi ba yayi hakan bane dan baya son su ba.

Ina son ka auna da kanka ka gani a nan ne zaka gane hikiman ubangiji da nake fad'a maka, misali ace duniyan gaba d'aya babu talaka ya kake ganin zai kasance ko kuma ace duka talakawa ne babu mai kud'i, ka fahimta?" Ya tambaya yana kallon yanda ya natsu yana sauraron shi.

Gyad'a kai Zafar yayi a hankali kan shi a kasa da sai yanzu da Abba ya fad'a mishi ya gane dole talaka yana bukatan mai kud'i haka Kuma mai kud'i yana bukatan talaka a rayuwar shi.

Muryan Abba yaji ya cigaba da magana " babu wanda yafi wani sai wanda ya mutu ya samu aljanna, kana nan duniya kana taka mutum saboda kai kana da shi shi kuma talaka baka sani ba kila a wajan Allah yafi ka daraja, dan haka ka cigaba da rike mutane da kyakkyawan zuciya zaka ga amfanin haka duniya da kiyama".

Shi dai Zafar duk mamaki ya hana shi sakat yaushe rabon da su zauna da Abban shi har suyi magana mai tsayi cikin lumana haka, tun kafin zuwan sa abroad karatu, tunda ya dawo da sabbin halayen sa na shan minti kuwa suka daina shan inuwa d'aya tare.

"Kana da kud'i a account d'inka?" Ya karajin muryan Abba ya katse mishi zancen zuci yake.

"Eh akwai Abba ba za'a rasa ba" ya amsa a sanyaye kaman mutumin kirki.

"Ok bari zuwa anjima ko gobe zanyi maka transfer ko kad'an ne kada sirkata ta nemi wani abu kace mata babu" yace yana dariya.

Shima dariyan yayi yana kara sadda Kai kasa.

Cikin wani irin kwarin guiwa ya nufi part d'in iyayen nashi bayan yayi wanka ya sha gayun shi kaman kullum sai kamshin tsadaddaun turaruka yake, tsab'anin da in Abba yana gari da kyar yake iya zuwa saboda ya san in yaje ma ba zasu kwashe da dad'i ba.

Da sallama ya shiga parlour amma babu kowa sai masu aiki da suke kai kawo, kowa na aikin da yake gaban shi, zama yayi kan d'aya daga cikin royal cussion d'in da suka lamushe kusan set 2 ya d'auki remote yana canza channel zuwa aljazeera sports yaji motsin saukowan su.

Ajiye remote d'in yayi ya mike tsaye ya tarbe su basu tsaya anan ba direct dinning suka wuce kowa yaja kujera ya zauna banda Mom da sai da tayi serving din su sannan ta zauna suka fara cin abinci

Basu dad'e da farawa ba Zafar yaga alert na zunzurutun kud'i har 10 million cikin tsananin murna bai san lokacin daya durkusa jiki na rawa har kasa ya fara godiya yana" Abba naga sako nagode Allah ya kara girma da nisan kwana" ba dan komai ba Abba yafi shekara rabon shi daya bashi kud'i sai dai Mom ce ke bashi a cewar shi ba zai bashi kudin shi yaje yana shashanci dasu ba.

Abba kuma ya kalli Mom da take bin tilon d'an nata da kallon mamaki yace" da fatan kin fahimci abinda nake nuna miki kika kasa fahimta kinga tun kamin ayi auren ta fara canza mana shi ina ga Kuma anyi auren?"

"Oh yanzu duk sun d'auka wannan village girl d'in ce ta canza ni..."

Muryan Mom yaji tana cewa" na fahimta Alhaji ya tabbatar da alkhairi"

"Ameen Ameen addu'an ki yake bukata dama, Kai kuma a yau d'in nan ka cewa 'yar Mallam gobe zamu je mu tsaida magana da Baban ta"

Murmushi da bai shirya bane ya kwace mishi jin sunan da Abba ya kira ni dashi wai 'yar Mallam.

"Ja'iri ji duk wannan washe bakin dan nace gobe zamu je ne, ina ga inda aka daura auren Kuma ya zakayi?"

Dariya yayi kawai yana ficewa ya nufi part d'in shi yana kara dariyan sunan da kuma na Abban shi da yake ganin auren soyayya zaiyi bai san auren contract zaiyi ba.

Direct bedroom d'in shi ya wuce yana cigaba da dariyan shi yayi dialing no Sadiq , saida ya gama ringing kamn zai katse sannan ya daga yana cewa " meye ya faru??"

" Hey Ni ba fad'a yasa na kira ka ba, I just called dan in fad'a maka gobe Abba zai je nema min auren 'Yar Mallam" ya karasa yana dariyan da sai da yasa Sadiq ya cire wayan a kunnen shi ya

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login