Showing 69001 words to 72000 words out of 85226 words
na ajiye shi na d'auko tsintiya na fito na fara sharan bana ko kallon inda yake.
Ajiye pen din hannun shi yayi ya kwanta yana kallo na yana Kara jin nishad'i gani na cikin hawaye, da gangan ya kirkiro atishawa yayi kusan guda 3 sannan yace wai da gangan nake sharo mishi da kura har ya saka shi yin atishawa.
"Kina sharewa a hankali in kika sa na kara yi zan nuna miki true colour na" kaman in kurma ihu nake ji saboda takaici wani kura ne a parlour nan da za'a ce har ya saka mutum atishawa kawai dai salon wulakancin sa ne wannan na sani.
Ban kula shi na gama sharan ko Ina da mopping duk yana zaune ko motsawa baiyi ba, baya na duk ciwo yake min da yake ban saba aiki haka ba har zan wuce d'aki yace in dawo in d'aura girkin yanzu.
Cikin gunguni na wuce kitchen ina shiga na fara ja mishi Allah ya isa " wannan ai zallinci ne haka kawai ya sani sharan da tunda aka haife ni ban tab'a yin irin shi ba tunda gidan mu dai kowa b'angare shi yake sharewa amma dan mugunta yasa inyi wannan uban aikin, dani yake wallahi sai na rama" duk ni kad'ai nake ta masifa ta ina fere dankalin turawa dana gani an zuba su a cikin store.
Patatos omllet nayi na zubo mishi a plate na d'aura a kan tray na plastic mai dan Karan kyau na saka mishi spoon na fito dashi zuwa inda yake zaune kaman wani sarki na duka har kasa na ajiye mishi, wani abin takaici da wannan bawan Allah ya min yanda kika san kashi na ajiye mishi haka ya tsaya kallon abincin.
A kyamace ya d'auki spoon din ya sakuro kaman mai tsakuran kashi ya kai bakin shi, dama ina kallon shi ta gefen ido saboda inga wani reaction zaiyi domin na san karyan mutum ya kushe girki na koda banyi catering school ba Inna ta ba baya bace wajan girki, alaman mamaki na gani karara akan fuskar shi lokacin da abincin ya shiga bakin shi amma tsaban iyayi furzar da abincin yayi yana yamutsa fuska yace " meye wannan, tambayan ki nake meye wannan is this what u called food , muguwa wato so kike inci in mutu Allah kad'ai ya san abinda kika zuba a cik tsaban muguntai, common kwashe kayan ki nd leave my sight"
Duk a masifance yake min maganan , rai na kara baki yayi na rasa me zancen ko inyi mishi da zan huce nayi, kawai tattara kayana nayi na koma kitchen ban kula shi ba.
"What a mess" ina cikin had'a nawa abincin naji ihun shi daya kara firgita ni kamin in san me yake faruwa na gan shi a fusace a bakin kofan yace;
" lalle kin cika Yar rainin hankali ki gyara ko ina amma ki kasa gyara min d'aki?" Ya karasa yana zubo min ido tare da tare kofan kitchen din.
"Baka ce min harda d'akin ka ba shiyasa ban shiga ba".
"Oh sai na gaya miki sannan zaki gyara ko d'akin nawa ba acikin gidan yake ba?" Kamin in samu amsan bashi ya cigaba "wuce ki gyara min yanzu plus my bathroom"
Rufe plate din nayi nazo zan wuce na zata zai bar min kofan in fita ne sai naga matsawa kad'an yayi yace in wuce,ban san lokacin da na daga kai na kalle shi ba naga ya wqni kankantar da Lulu eyes din shi yana kallo na.
" Toh... Z...an ...wuce" nace mishi murya ta na rawa.
Na hana ki wucewa ne?" Ya tambaya Yana kara gyara tsayuwar shi, girgiza kai na kawai nayi ina maida shi kasa, da hannu ya min alama da inzo in wuce.
Tafiya na fara yi kaman wacce take tsoron taka kqsa ba dan komai ba sai dan sanin in zan wuce sai jikina ya gogi nashi, karkata jiki na nayi sosai yanda ba zai hadu da nashi ba, na ko yi sa'a dan ko bai hadun ba har na kusa fita naga ya saka hannuwan shi duka 2 ya tare kofan ya zama banida daman fita Kuma banida daman komawa ciki.
"Ni kike guduwa da wani kazamin jikin ki, ni banyi kyaman zaki had'a jikina da naki ba sai kece zakiyi?" Jikin na karkarwa kawai yake tsaban tsoro ban tab'a samun kusanci da d'a namiji kaman haka ba sai yau so ban san ya zan kwatanta muku halin da na shiga ba a wannan likacin.
Sai da yaga ya gama tsoratani sannan ya bani hanya, haba kaman in kifa haka na fara sauri na shiga d'akin na maida kofa na rufe na jingina a jikin kofan ina maida numfashi, sai da na dawo hayyaci na sannan na tsaya kallon d'akin ko ina fes yake a gyara kaman d'akin mace sai kamshi ke tashi, ajiyar zuciya nayi na wuce bathroom din shima dai fes yake.
Haka dai na had'a ruwan omo da hypo na goge ko ina na bayin nan ya kara kyalli da walwali, sai da na tabbatar komai yayi na bude kofa na fito.
A razane na koma baya ganin shi tsaye a bakin kofan daga shi sai dogon wando ya cire rigan jikin shi, rab'awa nayi na wuce shi Kuma ya shigah har zai rufe kofa naji shi yana cewa in tabbatar na gama gyaran d'akin ya fito.
Da toh na amsa mishi yana shiga na fara gyara mishi gado da jera pillows sannan na fara mopping din d'akin inda babu carpet, har na gama zan fita wata zuciyar ta zuga ni da yanzu shikenan ba abinda zanyi in rama yaci bulus kenan??
Bakin kofan bathroom din na dawo hankali na zubar da ruwan omo kad'an yanda ba zai iya ganewa ba na fita da sauri ina addu'an Allah yasa ya taka wajan da na huta takaici da ya guma min yau.
Jikin kofan na d'aura kunne na na tsaya jiran fitowan shi, aiko ban dad'e da tsayuwa ba naji karan fad'uwa muryan shi da karfi yace " ouch my back" haba da gudu na koma daki Ina dariyan mugunta raina fari kal.
[6/16, 9:19 PM] Golden Pen Writers Associ: π¦πΉπ¦πΉπ¦πΉπ¦πΉ
π¦πΉπ¦πΉπ¦πΉ
π¦πΉπ¦πΉ
π¦πΉ
π¦
*BA SONTA NAkE BA*
π¦
π¦πΉ
π¦πΉπ¦πΉ
π¦πΉπ¦πΉπ¦πΉ
π¦πΉπ¦πΉπ¦πΉπ¦πΉ
_A story about love and sacrifice._
_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_
_*From The Fantastic Writer of*_
```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```
*_And now_*
*_BA SONTA NAKE BA_*
β *β GΜΎOΜΎLΜΎDΜΎEΜΎNΜΎ PΜΎEΜΎNΜΎ WΜΎRΜΎIΜΎTΜΎEΜΎRΜΎSΜΎ AΜΎSΜΎSΜΎOΜΎCΜΎIΜΎAΜΎTΜΎIΜΎOΜΎNΜΎ* ββ
https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/
*wΜΆΜΆΡ Ξ±rΜΆΜΆΡ Π²ΡΞ±rΜΆΜΆΡrΜΆΜΆ'sΜΆΜΆ ΟfΜΆΜΆ sΜΆΜΆΟ gΜΆΜΆΟlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡnΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡnΜΆΜΆ*
*wΜΆΜΆΡ wΜΆΜΆrΜΆΜΆΓtΜΆΜΆΡ Ξ±sΜΆΜΆsΜΆΜΆΓdΜΆΜΆΓΟuΜΆΜΆsΜΆΜΆlΜΆΜΆΡ pΜΆΜΆΡrΜΆΜΆcΜΆΜΆΡΓvΜΆΜΆΡ nΜΆΜΆΟ pΜΆΜΆΞ±ΓnΜΆΜΆ,*
*sΜΆΜΆΟ mΜΆΜΆΞ±gΜΆΜΆΓcΜΆΜΆΞ±lΜΆΜΆ ΟuΜΆΜΆrΜΆΜΆ cΜΆΜΆrΜΆΜΆΡΞ±tΜΆΜΆΓvΜΆΜΆΡ gΜΆΜΆΟlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡnΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡnΜΆΜΆ* β *,Π²ΡhΜΆΜΆΟlΜΆΜΆdΜΆΜΆ ΟuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ.Ξ± pΜΆΜΆrΜΆΜΆΟdΜΆΜΆuΜΆΜΆcΜΆΜΆtΜΆΜΆ ΟfΜΆΜΆ ΟuΜΆΜΆrΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡnΜΆ*ΜΆ *,sΜΆΜΆΞ±vΜΆΜΆΟuΜΆΜΆrΜΆΜΆ ΟuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ, fΜΆΜΆΟrΜΆΜΆ ΓtΜΆΜΆ wΜΆΜΆΓlΜΆΜΆlΜΆΜΆ* *cΜΆΜΆΞ±uΜΆΜΆsΜΆΜΆΡ ΡΟuΜΆΜΆ nΜΆΜΆΟ pΜΆΜΆΞ±ΓnΜΆΜΆ.*
*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*
Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.
*INA MASOYAN LITATTAFAN ΖUNGIYAR GOLDEN PEN?*
*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ΖARE!.*
Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buΖata namu daga farko.
Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana Ζara mana Ζarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.
*Bismillahir Rahmanir Raheem*
*35&36*
Zaune take kan sallaya da carbi a hannunta tana ja a hankali tare da kurawa waje d'aya ido,kallo d'aya zaka mata ka gane tana cikin damuwa kullum cikin wannan yanayi take tunda aka fitar dani daga gidan sai dai in damuwar yayi mata yawa,sai tayi nafila tana kai kukanta wajan mai kowa mai komai kan Allah ya bamu zaman lafiya mai d'aurewa.
'Yan biki duk sun watse tun ranan yini saboda an riga da an daina zaman bakwai sai dai gobe ne satin auran kuma a goben uwa take zuwa ganin d'akin 'yar ta amma ita tana ganin ba zata je ba hakan zai fi mata kwanciya hankali bata son taje ta ganni cikin wani yanayi ko kuma cikin tashin hankali hakan zai tsaya mata a rai ya hana ta sukuni, ta yanke shawaran zamanta a gida ta bini da addu'oi samun zaman lafiya.
Tana cikin zancen zuci baba yayi sallama ya shigo,sallamar nashi ne ya katse ta ta juyo tana kallon shi tare da amsawa a hankali tana bin shi da kallo yanda ya sauya zaka ce wani hamshakin mai kud'i ne,duk mamaki ya cika ta dan zata iya cewa tunda bikin nan yazo sai yau ta saka shi a ido saboda taga bashi da niyyan yin komai ya zauna akan abinda Abban Zafar yace na cewa kada suyi min komai su zasu yin min.
A lokacin ta nemi su zauna suyi magana ta fahimta bai kamata su sake musu komai ba kaman wacce bata da gata koda kayan d'aki daya ne ya kamata suyi min gudun gori watarana amma yaki sauraronta sam,wai tunda sunce abari a bari kawai itama tunda ta lura da takun shi ta fita harkan shi tayi duk abinda Allah ya hore mata dana 'yan uwa da abokan arziki cikin ikon Allah kuma asiri ya rufu.
Zama yayi a kan kujera ya d'auki remote ya kara volume na TV data rage,kaman ta share shi sai kuma taga koma yaya ne shine gaba da ita,tashi tayi ta kowa mishi ruwan sanyi da snacks na biki ta ajiye a gaban shi ta gaida shi tana zama a gefen shi.
Amsawa yayi sannan ya d'an sha ruwan da ta kawo mishi yana kare mata kallo yana murmushi yace"kinga yanda kika dawo kaman kece Amaryar gaya min menene sirrin?" murmushi kad'an tayi bata ce komai ba wai yau ita yake fad'awa haka ya manta duk munanan kalamai da yake furta mata da kuma aurar dani ga wanda ba son sa nake ba..........
"Tunanin 'yar albarka kike ne ,nima nan kullum sai nayi tunanin ta a raina toh ya za'ayi dole ne kiyi hakuri kuma kiyi murna tunda tana gidan hutu" yace yana gyara zama
"Yauwa ni abinda ya kawo ni daban, kin gan ni nan wallahi bikin nan ya cinye min duka kud'ad'en hannu na shine nace bari inzo ki bani wani abu na san 'yar ki na aiko miki tunda maganan da nayi ta jaddada mata kenan daren da za'a Kai ta gidan ta cewa kada ta kuskura ta zauna shiru duk dabarun da zatayi tayi ta rinka turo mana gida mu rinka shan maikon tare, in ma bata turo ba na san tana kan tarawa ne kema na san ki adana balle kuma kin samu makudan kud'i a bikin nan d'an gutsoro min rabo kamin 'yar albarka ta aiko mana" ya karasa yana washe baki.
Takaici ne ya kawowa Inna har wuya ya hana ta magana tir da mai irin halin sa irin nasihar da yayiwa 'yarsa da zata shiga gidan miji kenan, wai har sai yaushe zai canza sai yaushe ne zai gane gaskiya?
" Abin haushi ma kin ga banida number sirkin nawa ai da kai tsaye zan Kira shi muyi magana ta fah....." Cikin sauri Inna ta katse shi tana " haba Mallam yin hakan ba girman mu bane zai iya raina mu ka bari tunda dai ka fad'awa ita Zareefan zata aiko su ne da zaran ta samu"
"Ji wani zance wai ba girman mu bane, yo wani girma talaka yake da ita in banda abinki menene a ciki dan Mai kud'i ya raina talaka."
" Babu komai ba komai bane Amma ka bari in an kwana 2 da kaina zan karb'o maka numbern nashi a wajan ta kaga daga nan zaka iya magana dashi kai tsaye a duk lokacin da kake so" tana gama dad'in haka ta mike zuwa cikin bedroom dinta ta d'auko mishi bunch na dubu daya wato dubu dari kenan ta kawo mishi.
"Ka rike wannan zuwa wani lokacin ko?"
" Ai shiyasa nake son ki ke d'in ta daban ce" yace yana ta washe baki ya mike ya fice daga parlour ba tare da ya jira amsar ta ba.
Dabas Inna ta koma ta zauna tana nazari inko hakane tana da aiki babba a gaban ta ba zata tab'a bari ya zubar min da kima a gidan miji ba dole ta mike tsaye akan shi sannan ta dage da addu'a Allah ya shirye shi ya gane gaskiya.
***********************
Tundaga wannan rana ban kara ganin kowa a gidan da sunan ziyara ba daga ni sai shi, duk aikin da yace inyi kullum da sassafe nake yi kamin ya fito na tsabtace ko ina na saka turaren wuta abincin sa kuwa bana fashi ina ajiye mishi a kan table in koma d'aki in kulle kaina duk da akwai lokacin da ya same ni yace in daina ajiye mishi wannan jagwalgwalo na dan yafi karfin ci kullum masu aiki yake bawa, ban kula shi ba na cigaba da ajiyewa dan jiki na ya bani shi yake cinyewa ya fake da masu aiki, d'akin shi ne dai ban kara gigin lekawa ba balle ince zan share.
Duk wannan kokarin da nake bai hanawa in 'yan rashin mutuncin nashi suka motsa ya sauke su a kaina, ina dai daurewa bana nuna mishi rauni na sai na koma daki nake cin kuka na in more duk rayuwar gidan ya ishe ni.
Yau tunda na farka nake ta murna saboda a yau za'ayi yinin bakwai kuma a gidan nan za'a yi shi kaman yanda al'ada yake, babban farinciki na harda Inna za'a zo shima iyayen shi zasu zo a hadu gaba daya asan juna a kara karfafa zumunci.
Irin gyaran da nayiwa gidan yau na musamman ne tun 7:30 na shirya cikin wata hadaddiyar shadda ta blue dinkin doguwar riga yasha zubi har kasa, duk da ban iya wani d'aurin kirki ba na kokarta nayi yanda zan iya kuma cikin ikon Allah yayi kyau sosai sai na kara zama Amarya sak, duk d'auki ya hana ni sukuni sai kallon time nake ina jin lokaci baya tafiya, ina zaune ina ta kallon agogo naji an murd'a handle din kofan parlour cike da murna da d'auki na mike na tafi da gudu dan in rungume duk wacce ta fara zuwa, da gudu na kwasa nayi kofan sai dai kamin in karasa naja wani wawan briki na tsaya a tsoroce tare da mayar da kai na kasa.
Shiru banji yayi min magana ba Kuma banji alamun ya tafi ba, ina ta ayyanawa a rai na kila ya tafi ne in ba tafiya yayi ba me zai tsayar dashi anan? Hakan da na saka a raina yasa na dago da kaina karaf ido na a cikin nashi yana min wani kallo da ni dai ban san fassaran shi ba, mayar da kai nayi na shiga gulman shi a zuciya ta mutum sai shegen fadin ran tsiya da iyayi....
"Meye na gaya miki last time akan gidan nan?" Muryan shi ya katse min gulman shi da nake.
"Kace in rika share gidan nan kullum...."
"And then?" Ya katse ni tun kamin in karasa.
"Ina yi kuma harda girki" daki na fa?" Ya kara katse ni.
Harga Allah bai zata da gangan na zubar da ruwa ya fad'i ba a wancan ranan Kuma yaji dad'in gyaran da nayi mishi shiyasa ya biyo ni, ni kuma a tunani na ya sani shiyasa naki shiga d'akin kada ya kama ni na San halin shi na cin zali.
"Kayi hakuri zan rinka gyarawa " na bashi amsa cikin sanyin murya.
"Better " yace tare da juyawa ya fita nabi shi da ido har ya b'ace min dan yayi min masifan kyau cikin riga armless da wando 3 quater duka farare ne tass anr rubuta Gucci da manyan harufa da bakin fenti a gaban rigan mutum yana ganin well builded body shi a zahiri ga gashi kwance luf a fatan jikin shi kaman wani balarabe.
Kofan na rufe na dawo na zauna jiki na duk a mace me yasa kwanan man nake jin wannan yanayin in muna zaune waje daya kuma duk abinda yake yanzu birge ni yake ba kaman da danake jin haushin shi ba.
9:00 am dot Yasmeen da kannen ta 2 suka zo cikin farinciki na taro su bamu zauna a babban parlour ba naja zuwa nawa muka zauna naja karamin kanin ta da ba zai wuce 7 years ba ina tambayan shi ya sunan shi? Dan Allah ya daura min son k'ananan yara ko dan babu a d'akin mu ne oho.
"Muhsin " ya amsa min da karamin muryan shi mai dad'i, murmushi nayi nace " sunan ka mai dad'i".
"Aunty Amarya kin gan mu da sassafe ko, wlh muhsin ne ya takura mana tunda ya farka daga bacci yana ta kuka shi lalle sai an kawo shi nan shine fa da ya ishi Momy da fitina tace muzo kamin ta karaso" Yasmeen ta katse ni da murmushi a fuskar ta..
"Ni ai Muhsin ya burge ni ina zaune ni kad'ai kaman mayya gashi na samu abokanen hira, kema kince zaki dawo ban Kara ganin kafar ki ba tun ranan da kika fice daga gidan nan" na bata amsa ina dan dariya.
"Cab ai Momy ce ta hani ni zuwa wai zan zo in takura ku" ta karasa itama tana dariyan.
Kawar da wannan maganan nayi na kawo wata hirar daban nake tambayar ta ya matakin karatun ta yake, ta amsa min da zata rubuta jamb