Showing 15001 words to 18000 words out of 85226 words

Chapter 6 - BA SONTA NAKE BA

Start ads

20 Aug 2025

195

Middle Ads

p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ 🖊 *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.*

https://www.facebook.com/101594048306878?referrer=whatsapp


حَدَّثَنَا سَعِيدُ بْنُ مَنْصُورٍ وَقُتَيْبَةُ بْنُ سَعِيدٍ وَأَبُو كَامِلٍ الْجَحْدَرِيُّ وَاللَّفْظُ لِسَعِيدٍ قَالُوا حَدَّثَنَا أَبُو عَوَانَةَ عَنْ سِمَاكِ بْنِ حَرْبٍ عَنْ مُصْعَبِ بْنِ سَعْدٍ قَالَ دَخَلَ عَبْدُ اللَّهِ بْنُ عُمَرَ عَلَى ابْنِ عَامِرٍ يَعُودُهُ وَهُوَ مَرِيضٌ فَقَالَ أَلَا تَدْعُو اللَّهَ لِي يَا ابْنَ عُمَرَ؟ قَالَ إِنِّي سَمِعْتُ رَسُولَ اللَّهِ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ يَقُولُ لَا تُقْبَلُ صَلَاةٌ بِغَيْرِ طُهُورٍ وَلَا صَدَقَةٌ مِنْ غُلُولٍ وَكُنْتَ عَلَى الْبَصْرَةِ.

*It was narrated from Simak bin Harb, that Mus`ab bin Sa`d said: "`Abdullah bin `Umar came to visit Ibn `Amir when he was sick and he said: `Won`t you supplicate to Allah for me, O Ibn `Umar?` He said: `I heard the Messenger of Allah (s.a.w) say: "No Salat is accepted without Wudu` (purification), and no charity (is accepted) that comes from Ghulul," and you were the governor of Al-Basrah."`*

[ Sahih Muslim ]



*7*


Baban mu jikin sane yayi sanyi sosai, wai Bintu ce ta biya mishi bashi. Bayan duk abubuwa da yayi mata basu da misali bayan wa'yan da ya fifita duk suna tsaye babu wanda yayi gigin biya mishi alhalin suna dashi, more especially 'yar gaban goshin sa wato Gwaggo Aisha, ga Baffan mu duk suna wajen taya zai iya kallon idon ta nan gaba?.



"Amma Mallam Hassan ka cika mugu azzalumi,wato yanzu a baka kud'in da zaka biya ni shine ka rike ka maida ni d'an iska wato inyi in gama ko? Allah ma yasa a gaba na aka aiko da kud'in da shikenan sai ka cigaba da raina min hankali kana cewa babu" yana banbani ya matso kusa da Baban mu ya kwace kud'in a hannun sa ya fita yana," Allah ya so ka Mallam".



Da ido kowa ya bi bayan shi har ya ida ficewa, bai san cewa mamaki ne daya cakud'u da mutuwar jiki su suka hana shi bayar da kudin ba, bai kara kallon kowa a wajan ba ya koma d'akin shi ya zauna a bakin gado tare da rafka uban tagumi yana tunanin ta yayane zai shawo kan Bintu yaci dad'i kuma ya samu na kashewa, dubu biyu fa?.



Can shi kad'a ya saki murmushin jin dad'i alamun ya samu mafita kenan.



A waje kuwa Baban mu yana shiga d'akin sa Baffan mu shima ya bar wajan yana tab'e baki dan bai ga dalilin da zai saka ya biya mishi bashi ba, da ace wannan kud'in yayi amfani dasu wajan ciyar da iyalin shine zai iya biya amma tunda kansa kad'ai ya sani bai san hakkin daya rataya akan sa ba shi ya sani yaje can ya karata.



"Allah sarki Bintu Allah dai yasa ba mugun halin kema kika fara kaman sauran matan ba saboda mugun halin d'an uwana duk shi ya jefa iyalin shi cikin halaka" yana magana ne tare da shigewa b'angaren shi.



Gwaggo Aisha da Inna Asabe duk sun kasa barin wajen suna tsaye a wajan kaman wanda aka dasa su kowacce da irin tunanin da take a zuciyar ta saboda Abin ya mugun daure musu kai sosai ita da duk gidan itace wacce bata dashi amma yanzu ta dara kowa a gidan.



Gwaggo Aisha fargaban ta d'aya shine kada Inna tazo ta kwace mata matsayi a wajan Baban mu domin ta san halin shi tsab zai iya juya mata baya dama saboda tafi kowa kud'i a gidan yake fifita ta, kai dole ne tayi wani abu akai dan ba zata tab'a zuba ido Inna ta ta kwace mata ba.



Da washe gari ina dawo daga makaranta a nesa na hango motan Abdulbasit a k'ofar gidan mu, aiko da gudu na karaso wajan motan cike da murna dan yanzu na daina tsoro tunda Innata da kanta take cewa inje mu gaisa bayan haka ga kayan dad'i da kullum in zai zo yake kawo min, yana zaune a ciki motan amma kafafun shi a waje hankalin shi yana kan wayar shi ban san me yake dan dannawa ba.


"Sannu da zuwa Yaya na" na fad'a da d'an karfi bayan na karasa kusa dashi,a d'an razane ya d'ago sai kuma ya saki murmushin sa mai kyau da baya barin fuskan sa.


"Har kin tsorata ni saura kad'an in ruga da gudu" ya ce yana dariya.



Nima dariyan na kyakyale dashi sannan na ce," toh ya zakayi da motan ka in ka gudu ka barta?"



"Sai in bar miki ita ki rink'a zuwa makaranta dashi" toh ai ban iya yanda ake tukawa ba" na fad'a a shagwab'e.



"Kada ki damu zan koya miki, kije ki cewa Aunty zan shigo mu gaisa".



Da toh na amsa sannan na juya na shige gida da sauri na, su Hajara duk sun tafi tallah iyayen nasu ma ban gan su ba da alamu duk sun fita.



Inna tana k'ofar d'aki tana shara na shigo da sallama ta amsa tana yi min sannu da zuwa,ciki na shige na ajiye jaka ta sannan na kara fitowa na ce mata," Inna Yaya yazo yana waje yace zai shigo ku gaisa".


"Ciki nan zai shigo yace?" Ta tambaya da alamun tsoro da damuwa akan fuskan ta, gyad'a mata kai nayi ina kallon duk yanda ta zama wani iri.



"Toh ya shigo" ta ce tana komawa d'aki ni kuma na fita waje na sanar dashi kan ya shigo, a bakin k'ofan d'aki muka tadda Inna zaune cikin tagumi amma tana ganin mu ta saki ran ta tana mishi sannu da zuwa.



Kallon gidan namu yake tare da nazarin sa,har k'asa ya duka suka gaisa da Inna a mutunce tare da bata hakurin rashin zuwan sa akai-akai kaman yanda yayi mata alkawari, nuna mishi tayi babu komai kana ta d'aura dayi mishi godiya tare da addu'oin gamawa da duniya lafiya.



Cikin jin dad'i yake amsawa da Ameen sannan ya mike yace zai wuce dai-dai lokacin kuma iska mai karfi ya d'aga d'an yalolon labulen mu karaf idon sa sai a d'akin mu da ko arzikin leda babu sai siminti dasu ghana must gon mu a gefe.


Tare muka fito dashi har zuwa wajan motan sa ya ciro manyan jakuna na shopping daya saba kawo mana ya mik'a min sannan ya kara da kud'i masu yawa yace in bawa Inna ince ta sayi carpet na tsakar d'aki dasu gado.



Cikin tsananin murna na dawo cikin gida da kaya niki-niki sannan na nunawa Inna kud'in daya bata tare da fad'a mata abinda yace tayi dasu.



Karb'a Inna tayi ta ajiye gefe ba tace komai ba dan yanzu zuciyar ta ta fara amincewa dashi sannan ta fara sabawa da lamarin sa.


Ni kuwa duk na k'ogu ta bud'e kayan domin na san duk tsaraba nane a ciki, tana bud'ewa kuwa sune ice cream da sauran kayan dad'i sai kaza gasassu biyu,ice cream na na d'auka na koma gefe na fara sha domin ni yafi min kaza sau dubu.



Da washe gari Inna ta sayo mana carpet d'in mu maroon mai d'an karan kyau harda katifan mu da sabon labule, murna a waje na ba'a magana muma munyi katifa kaman sauran 'yan gidan mu, a ranan da kyar Inna ta kirani waje domin tarewa nayi akan katifan.



A wannan rana mun ga hasada kiri-kiri a wajan matan gidan mu, Gwaggo Aisha tafi kowa shiga tashin hankali sai zage-zage take babu wanda ya kula ta sai 'yan koron tane suke taya ta.



Babu abinda zan cewa Allah sai Alhamdullilahi saboda rayuwar mu ta canza sosai yanzu muci mai kyau mu sha mai kyau mu kwanta a waje mai kyau hatta suturar da muke sakawa ya canza albarkacin Abdulbasit.



Mu muna nan zaune zuciya d'aya ashe bamu sani ba Gwaggo Aisha ta saka ana tayi mata bincike ta ina muke samun kud'i har rayuwar mu ta canza muka zama zara a cikin su.



Bata sha wahalan samun cewa wani saurayi mai kud'i ne yake taimaka mana ba, daga wannan rana ta saka ido sosai tana jiran zuwan shi,cikin ikon Allah duk lokacin da zai zo bata nan sai dai taji labarin yau yazo ya tafi.



A wannan lokacin Gwaggo Aisha duk yawon ta daina fita muka ga tayi a gida take wuni haka Hajara ma ta daina zuwa tallah kullum suna gida,ni na d'auka cewa sun daina tallah ne ashe wai ta gaji da kullum sai ta dawo daga gantalin ta taji cewa yazo har ya tafi shiyasa suka daina fita kullum hanya suke kallo suna jiran zuwan shi.



Sun kai kwana biyar da shiga kullen nasu Abdulbasit yazo yanzu mun saba sosai ni dashi dan har tambaya ta yake abubuwa da nake so, ni kuwa in kirgo mishi in zai dawo ya kawo min.



Ranan ma haka ya kawo min sautu da nayi mishi na kayan kwalliya shi kuma ya sayo min masu tsadan gaske kaman wata budurwa da kuma kayan makulashe daya zame masa jiki kullum zai zo sai ya kawo min, bayan ya gama zolaya ta na gama kuka na muka shirya na kwashi kayana na zan shiga ciki bayan nima na saba kullum in yazo sai na zolaye shi da in d'an b'uda murya ince," sannu da zuwa Yaya naaa".



Sai ya juyo a d'an razane yace," kin tsorata ni zaki sa in fita a guce" sai inyi ta kyalkyalan dariya.


A zaure na tarar da Hajara tana tsaye sai lek'e take ta sha kwalliyan ta na 'yan tallah fuska ya sha make up har yayi over.



Tana gani na ta had'a rai ta tsaya ni kuwa da hankali na na kuruciya ban kawo komai a raina ba nayi shigewa ta ciki, tana ganin na shiga ta fito da saurin ta zuwa wajan shi domin har ya shiga motan shi ya tayar saura yaja.



"Assalamu alaikum barka da war haka ya kyakkyawan d'an saurayi".



Fasa jan motan yayi ya tsaya kallon ta da wani irin fuska sannan ya ce," meke tafe dake?".



Juya ido tayi mishi irin na jan hankalin nan sannan ta ce," haba yanzu har sai nayi maka bayanin abinda yake tafe dani,me budurwa zata nema a wajan saurayi? Koda yake bari in fito in fad'a maka yanda zaka gane.


Naga kana wahalar da kanka akan wancan 'yar karamar yarinya, bayan gani na had'a duk abinda kake nema zan saka ka farinciki domin babu abinda zaka nema a waje na ka rasa" ta karasa tana kara matsowa jikin motan tana girgiza mishi kirji.




Kallon takaici da kyama ya bita dashi sannan ya ce," pls matsa min ka jikin mota kada kisa min k'azanta a jiki".



Kasa matsawa tayi ta tsaya da idanuwa a waje tana kallon shi dan tunda take ba'a tab'a ci mata mutunci haka ba duk yanda taci kwalliya nan yace wai zata shafawa motan shi k'azanta , a firgice ta koma baya jin ya fisgi motan da matukar gudu saura kad'an ya take mata k'afa ya tafi ya bar ta a wajan.



Da hawaye shame-shame ta shigo gida tun daga bakin kofa ta fara ihu tana magana," ni Gwaggo wallahi baki ga wulakaci......" Da hannu Gwaggo Aisha tayi mata alama da tayi shiru, kama hannun ta tayi suka shige d'aki.



A kwana a tashi ba wuya a wajan Allah dan yanzu har munyi exam na third term muna hutu in mun koma kuma zamu shiga j.s.s 2.



Ranan nan muna wasa a k'ofar gida da kawaye na 'yan mak'otan mu naga Baban mu yana dawo wa gida ban kula ba dan shima ba kulanin yake ba kuma ya tsani in kula shi dan ma yanzu da sauki naga ya rage tsana da yake nuna min.



Bulala naga ya d'auka yayi kaina gadan-gadan zai zane ni bansan hawa ba ban san sauk'a ba, da gudu na kwasa nayi cikin gida ban tsaya a tsakar gidan ba na wuce d'akin mu sanin cewa baya tab'a biyo ni, Inna tana raba gasassun kaji da Abdulbasit ya kawo na fad'a d'akin ina haki.


Inna barin abinda take tayi ta kama min fad'an waye na tsokono zan fad'o mata d'aki haka?



"Inna wallahi ba tsokana nayi ba muna wasa ne sai naga Baban mu....." Had'iye sauran maganan nayi ganin Baban ya d'aga labule ya shigo, bani ba har Inna sai da ta zaro ido tana kallon shi da matukar mamaki.



"Ke yanzu Bintu haka ake tarbiyan 'ya mace yarinya ta fara girma amma ki bar ta tana wasa a waje sai kace namiji" yana maganan ne idon shi na yawo a d'akin har ya sauk'a kan kajin da suke gaban inna, mukut ya had'iye yawu tare da tsura musu ido shiri.



"Toh Mallam ayi hakuri insha Allah za'a kiyaye gaba" tana gama fad'an haka ta ture tiren da kajin suke ciki gefe tare da rufewa da wani tiren.





*Albishirinku mata masu son kamshi da gyara ga dama ta samu zamu fara classes na koyar da turaren wuta kala-kala humra shima in different colors dilke gyaran amarya man gashi nd lots more kada ko yarda a baki labarai akan 300 kacal zaki zama pro na kan ki, duk mai bukata ta tuntubi wannan no 08172724281 sai mun ji ku*.
[9/8, 5:01 PM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._



_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_


_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*


*_BA SONTA NAKE BA_*



*✍✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾

*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*🖊
*w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ 🖊 *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.*

*Abin da ake fada idan za a yanka dabba, ko za a soke ta.*

بِسْمِ اللهِ واللهُ أَكْبَرُ اللَّهُمَّ مِنْكَ ولَكَ اللَّهُمَّ تَقَبَّلْ مِنِّي.

Bismil-lah wallahu akbar, allahumma minka walak, allahumma taqabbal minnee.

Da sunan Allah, kuma Allah ne Mafi Girma. Ya Allah! (wannan dabba) daga gare Ka take, kuma mallakarka ce. Ya Allah! Ka karba daga gare ni.


*~INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?~*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*


_Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samun wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook_. 👇


https://www.facebook.com/101594048306878?referrer=whatsapp


_Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu._


*8*


Karasa shigowa d'akin Baba yayi tare da yiwa kan shi masauki kan katifan mu yana kallon rufaffen tiren ya ce," haba Bintu yanzu iya abinda zaki ce kenan, Fateema ta fara girma sai da saka ido sosai fa".




Cike da mamakin furucin sa ta ce," naji Mallam za'a kiyaye gaba insha Allah" a zuciyar ta kuwa bata daina mamakin wannan sabon al'amarin ba domin ita dai tunda take a gidan bata tab'a ganin ya damu da 'ya'yan matan shi da yake so ba balle 'yar ta da kullum sai ya tsaya a tsakar gida yace ba son su yake ba



shiru ne ya biyo baya a d'akin,ni ina can bayan Inna ta saboda tsoron bulala duk da ya ajiye ta tuntuni naki fitowa, ita kuma Inna al'ajabin me ya zaunar dashi har yanzu a d'akin take gashi tana so ta gama rabon kazan in kaiwa wayan da take bawa kullum.




Mun kai minti kusan ashirin muna zaune shiru babu mai magana shi ya gaji da zaman kurame da muke ya d'an gyara zama yana kallon tiren ta gefen ido ya ce," naga kaman aiki kike Bintu dana shigo ko, toh ki karasa abin ki mana, in ta nine babu matsala Wallahi".



"Haba Mallam ba haka bane na riga da na gama ne shiyasa". Ta amsa mishi.



"Kin gama, me kika gama?" Ya tambaya tare da kafe tiren da ido.



"Rabo nake kuma na gama saura in bawa Zareefa ta kai" Inna ta amsa mishi cikin k'osawa da zaman nashi a d'akin.



"Toh su waye kuma zaki aikawa?"


"Maman Dije da Maa saboda sunyi yawa ga Zareefa ba ci take ba shiyasa nake aika musu".



"Ikon Allah amma Bintu kina da abin mamaki, ya za'ayi ki aikawa wasu alhalin ga 'yan gida nan, ko kin manta da nine?"




Cike da takaicin halin sa ta girgiza mishi kai sannan ta d'auko wani d'an gutsuri kad'an ta mika mishi jiki na rawa ya karb'a ya fara ci yana," kai amma Bintu baki da dama yanzu haka kike cin dad'i kuma ki manta uban 'yar ki?"



Ita yanzu inna halin nashi tsoro ya fara bata ya za'ayi kana magidanci mai iyali baka damu da ka samu ka kawo musu ba sai dai in ka gani a wajan su jiki na rawa ka karb'a, dubi yanda yanzu jiki na rawa yake neman a bashi kaza bai damu da tambayan a ina kika samu ba, sata ko maita ko karuwanci duk kiyi in dai zaki bashi to kece ma 'yar gaban goshin sa.




"Dama da yunwa na shigo kin ganni nan har wani juwa nake gani, Allah yasa da akwai abinci d'akin nan" yace yana faman tsid'e yatsu.



Girgiza kai Inna tayi sannan ta ce," babu abinci Mallam ba muyi girki ba sai...."



"Inna ki bashi nawa da kika ajiye min yaci dan ni nasha ice cream ba zan ci ba". Na katsewa Inna hanzari.



"Yauwa 'yar albarka, Allah sarki yarinya mai tausayin Baban ta" Abba yace cikin jin dad'i yana washe baki.



Inna tsuke fuska tayi tana jin kaman ta kamo ni tayi ta kirb'a sai yau ya san dasu a gidan a baya in ta aika mishi abinci kora ta yake hmmmm sai yau, ba dan taso ba ta tashi ta d'auko mishi hadaddiyar warmer sabuwa

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login