Showing 78001 words to 81000 words out of 85226 words
zauna a nesa sai kace wata bakuwa,cike da jin nauyin su na matso na zauna ina Kara gaishe ta ganin bata wani amsa min ba.
Sama-sama ta amsa min tana kokarin fara serving din mijin ta amma sai ya dakatar da ita yana mai cewa " dakata mana da zuba abincin nan, ga surkuwar mu ta kawo mana kayan dad'i shi ya kamata muci yau ki maida naki gefe sai wata rana" ya karasa suna dariya shida Zafar ni dai murmushi kawai nayi na kasa dago da kai.
Yake kawai Mum tayi tare da maida warmers din ta rufe zuciyar ta na kuna ta yaya zata kwashi lokaci tayi mishi girki amma wai dan yaga nawa yace ba zai ci ba, bata musa shi ba ta jawo basket din ta fara cire warmers da suke ciki , tana bud'ewa kuwa kamshi duk ya cika parlorn na girkin dana man shanu.
Ranta duk babu dad'i haka ta zuba mishi abincin ta ajiye a gaban shi tana shirin rufe su yace mata " ya zaki rufe baki diba ba?"
" Zan diba ba rufewa nake ba" ta bashi amsa ta jawo plate gaban ta ta zuba malmala kwaya d'aya tak ta zuba miya kaman bata so ko mai kyankyamin abincin ta kai baki a ba zata sai da ta lumshe ido, dan abincin yayi mata wani irin dad'i domin batayi tsammanin zata ji abincin haka a tunanin ta tunda ni 'yar talakawa ce ban iya komai ba.
Zafar da yake kallon duk drama dake faruwa ya saki murmushi domin shi shaida ne in ta girki ne bani da ta 2, Abba sai santi yake ta zubawa wai ya akayi na san yana son abincin gargajiya, ashe wai dole su daina ganin Zafar wajan neman abinci a gida bayan cika baki da yayi ta musu a baya ko mata 4 be dashi abincin Mom d'in shi kad'ai zai ci.
Mom tana ji bata ce uffan ba koda suka gama Abba cewa a ajiye mishi snacks din nashi ne shi kad'ai, Mom sai tabe baki take tare da jin haushi Abba yana tsinka su a gaban wannan jinjirar yana abu kaman bai tab'a cin abinci mai dadi ba, ni kuwa duk farincikin ya lullube ni ganin yanda Abba yake ta yabon girki na dan ni nayi ne kawai banyi zaton zasu ci ba balle in samu irin wannan yabon.
Tattare kayan Mom ta fara Nima nayi saurin mikewa dan in taimaka mata amma cikin tsare gida tace in bar su, duk sai naji jiki na yayi wani irin sanyi na kasa komawa in zaunan, muryan Abba naji yana min magana yace " zo nan ki zauna daughter akwai hirar mu ta musamman dake" ya karasa yana nuna min gefen sa da hannu.
Da kyar na ja kafafu na zauna a inda ya nuna min yayi kasa da murya yace " kyale uwar nan taku haka take bata son in tana aikin mijin ta wani ya saka hannu wai ladan ta zai ragu shiyasa bata barin masu aiki suyi sai ita da kan ta" ban san lokacin da murmushi ya kwace min ba dan salon da yayi maganan dole ne yasa mutum dariya.
Zafar dake d'ayan gefen shima dariyan yayi dan ko shi baiji dad'in abinda Mom din nashi tayi ba amma yanzu daya ga Abba yana min barkwanci sai yaji hankalin shi ya kwanta kuma yaji dadi har cikin ran shi.
Wani envelope mai dan girma da yake kan kujeran bayan shi ya d'auko ya miko min yace " ga wannan tukuici ne daga gare ni kan yanda kika bada gudumawa wannan stubborned son nawa ya koma gentle boy".
Kasa karb'a nayi sai bin foldern nake da ido ina imagining what could be inside? Zafaar da yake sauraron mu ya b'ata fuska cikin shagwaba yace" Abba pls mana".
"Kwarai hakane my daughter ki karb'a Mana" yace ganin na kasa karb'a, hannu na rawa na saka na amsa tare da cewa " nagode Abba Allah ya kara girma da daukaka" Ameen my daughter" ya amsa min cikin jin dad'in addu'an da nayi mishi.
Muna cikin haka Mom ta dawo ta zauna hankalin ta da imanin ta duk suna kan abinda ke hannu na wondering ya akayi yazo hannu na, ganin irin kallon da take min yasa Abba ya maimaita mata abinda ya faru tare da ce mata " saura kema ya kamata ki kawo taki gudumawar"
Dama ance in talaka ya rabe ka in ba kayi sa'a ba toh kaima sai ka talauce, if not ya zaayî ya d'auko takardun company shi na buga ledodi dugurungum ya bada kyautan shi ma yar mitsitsiyar yarinya? Duk a cikin zuciyar ta take wannan maganan amma a zahiri kuma sai ta kirkiro murmushi tace" lalle Alhaji kana ji da wannan surkuwar tamu sai dai ai ko ni ban kara komai ba nakan ma ya wadatar kyautan company fa ai ya wuce wasa" ta karasa zuciyar ta na suya.
"Company? Ni Zareefa aka bawa kyautan company?" Na tambayi kaina da kaina hawaye na kokarin zubo min amma na shanye ina kara kasa da kai.
" Ga complimentary card dina daughter duk private numbers dina suna jiki a duk lokacin da yayi miki ba daidai ba ko kina bukatan wani abu kada kiji nauyi ki Kira ni Kai tsaye ki fad'a min kinji ko?"
Yanzu Kam sai da hawayen yayi nasaran zubo min nayi saurin saka gefen gyale na goge na saka hannu na amsa kamin in samu bakin magana naji muryan Mom da ta kasa hakuri tace " kaima dai Alhaji sai kace kaga wani alamun rashin zaman lafiya a tare dasu ko Kuma wacce bata da iya..."
Wani kallon ki shiga hankalin ki da Abba yayi mata yasa ta had'iye sauran zancen nata tare da kawar da kai gefe, saida ya maye fuskar shi da murmushi sannan yace " ta riga da ta shigo wannan family dan haka muma iyayen tane ko kin manta ita zata haifo mana magajin gidan nan a gaba?"
A razane take kallon Abban Jin wannan furucin da yayi me yake nufi kenan, duk shekarun da ta b'ata tare da shi ya tashi a tutan babu? Lallai ko sai ta kara tsayawa da kafafun ta ko ayi mata tsakiyar da ba ruwa. Amma a zahiri sai ta gyara fuskarta da nemo aron murmushi da ya tsaya mata a iya leb'e tace " hakane Alhaji Allah ya kara bud'i".
Gaba d'ayan su suka amsa da "Ameen " daga nan Abba da Zafar ne kad'ai suka cigaba da hiran su game da business daya yake taya shi a gida ,zuwa kusan karfe 10 Zafar yace zamu tafi Abba yana ta saka mana albarka ita kuma Mom cewa kawai mu gaida da gida.
Ga mamaki na har muka shiga mota bai kara hantara ta ba saima murmushi da yake ta faman sakewa shi kad'ai yana tukin sa cikin kwanciyar hankali ni kuma zuciya ta tana wani waje daban Ina rike da complementary card din Abba ina ayyana abubuwa da yawa a raina.
[6/16, 9:22 PM] Golden Pen Writers Associ: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
_A story about love and sacrifice._
_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_
_*From The Fantastic Writer of*_
```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```
*_And now_*
*_BA SONTA NAKE BA_*
*INNALILLAHI Wa INNA ILAIHI RAJI'UN
Muna taya 'yar uwar mu PRINCESS FATIMA MAZADU na babban rashi da tayi wato yayan ta HRH. ALH ABUBAKAR MUHAMMAD KWAIRANGA ( SARKIN FUNAKAYE) UBANGIJI ALLAH ya jikan shi da rahama yasa mutuwa hutu ce a gare shi AMEEEN*
✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍
https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/
*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*
*w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.*
*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*
Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.
*INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?*
*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*
Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko.
Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.
*Bismillahir Rahmanir Raheem*
*41&42*
Bakomai ne yake raina ba sai yanda zan rama zalunci da yayi min, domin na yarda da maganan Yesmin da take fada min na cewa yana matukar tsoron Abban shi saboda nima gauce yanzu ba jiyau ba, ya wani natsu sai abubuwan mutanen kirki yake alhali kuwa mugu ne na bugawa a jarida.
Har muka karaso gida ko ci kan ki bai kara ce min ba nima na share shi na wuce d'aki na, kayan jiki na na fara ragewa sannan na shiga na watsa ruwa na fito nayi shirin bacci na kwanta amma sai na kasa samun baccin, tunanin wannan company da Abba ya bani shi ya fad'o min a rai toh ni ya zanyi da companyn nan? kawai bari in bari in an kwana 2 sai in fad'awa Inna inji me zata ce.
Lumshe ido nayi da niyyan bacci haka kawai Yaya na ya fad'o min a rai, ko a wni hali yake ciki, ko meyasa ya guje ni??
Tunanin hakan da nayi yasa na fara hawaye sosai harda shasshek'a dan ji nayi abin ya dawo min sabo fil zuciya ta sai kuna yake, duk halin da nake ciki a yanzu shine sila da bai guje ni ba da wannan mugun ko kallo na ba zai samu daman yi ba balle har in shigo gidan shi.
A wannan dare da kyar na samu bacci ya d'auke ni mai cike da mafarkai kala-kala.
Ko dana farka da safiyan nan sai naji duk raina a cunkushe yake fuskata babu walwala sam, iya d'aki da parlor na kawai na share nayi kwaciya ta ko kitchen banida niyyan lekawa balle inyi batun girki.
Zuwa kaman karfe 10 naji yunwa na neman hallaka ni dole yasa na fito main parlour na had'a tea mai kauri akan dining na d'auki mug d'ina da niyyan komawa d'aki naga mutum a zaune yana waya ko kallon inda yake banyi ba nayi wucewa ta na bar shi baki bud'e cike da mamakin abinda nayi yake bi na da kallo har na shige.
"Toh wai me ya hau kan yarinyan nan yau? Zaman da nayi anan ya kusa 1 hr ina jiran inga ta girka wani abu in samu inyi breakfast in fita shine taki yin komai saima tea da ta had'a ta wuce ko gaishe ni batayi ba, ko dai ta gane bana iya cin abincin kowa yanzu sai nata?" Zafar kenan shi kad'ai yana sumbatun sa a cikin ran shi.
Zuruf ya mike yana cewa naga kwana 2 yana d'an sake min shiyasa na fara kawo mishi raini bari ya shiga ya gyara min zama, yana maganan ne tare da nufan d'aki na.
Hankali kwance nake sipping tea na naga mutum ya shigo min babu sallama sai wani had'a fuska yake wai shi ala dole zai tsoratani.
"Ke tsaban kin raina mutane shine har zaki shigo ki fita ba zaki gaida mutane ba?" Ya fad'a cikin tsawa.
Sai da na turo baki na dan kalle shi na watsar nace" ni dai banga mutane ba,mutum daya na gani a parlorn".
Mamakin da yake fuskar shi kasa boyuwa yayi yana bina da wani irin kallo, had'iye abin shi yayi ya Kara wani tsare gida yace" ohk in ma mutum dayan kika gani ba zaki gaida shi ba kenan, nd what do you mean by ki shiga daki ki zauna shan tea sauran mutanen gidan ba zakiyi musu girki bane?"
Sai da na kuma kurban tea na hankali kwance sannan na bashi amsa " I don't feel like cooking today"
"What!! Ni kike fad'awa u don't feel like cooking, kin ga ina bin ki a hankali shiyasa ko jira ni ina zuwa zaki min bayanin yanda ya dace" yana fad'an haka ya fuce fuuu kaman zai tashi sama, tab'e baki nayi na raka shi da ido wai ni zai rainawa hankali wai mutanen gidan me zasu ci, yace min dai me zai ci?.
No Abba da tun jiya nayi saving a wayata na kira na saka a handsfree na ajiye kusa da ni muna gaisawa Ina karasa shan shayi na daya rage ya shigo dakin a zafaffe da belt a hannun shi har zai bud'i baki yayi magana jin muryan Abban shi yasa yayi tsit yana zare ido, kallon up nd down na mishi ina murmushi Abba yace" da fatan kin tashi lafiya my daughter"
Kara kwantar da murya nayi sannan na amsa mishi da" yau na tashi da jiri da amai da zazzab'i Abba ko tashi bana iya yi shine na nemi alfarman ba zan iya shiga kitchen ba yau amma yake ta min fad'a"
"Mene! Yana ina, ki bashi wayar in yana kusa" Abba ya karasa a d'an zafaffe.
Ina kif-kifta ido kaman da gaske nace " gashi nan Abba" tare da mika mishi wayan, sai a lokacin ya dawo hayyacin sa ya saka hannu ya karb'a yana min mugun kallo, ni kuwa ko a jikina saima murmushin mugunta dana bi shi da ita.
"Assalamu alaikum Abba barka da safiya" yace cikin sanyin murya.
" Wa'alaikum salam son me nake ji haka kada ka kasance cikin mazan da basa kyautatawa iyalin su mana kayi koyi da manzan Allah dan ya kasance mai kyautatawa iyalan sa,ko kaga haka muke da Momyn ka?" Bai iya bude ya bashi amsa sai girgiza kai da yayi kaman yana gaban Abban.
"Kada in kuma jin irin haka try to be a good husband ok, nd get something for her tayi breakfast". Insha Allah Abba" ya amsa cikin sanyin murya sannan ya katse kiran.
Ina jira inga ko zai hau kaina da wannan masifan nashi amma ga mamamki na sai ajiye min wayan yayi ba tare da yace komai ba ya fita daga dakin, murmushin nasara nayi tare da gyra kwanciya ta kan kujera na d'auko wayata na shiga watsApp.
Bayan fitan shi kaman da minti 30 sai gashi ya kara shigowa da sallama da wasu shopping bags a hannun shi ya ajiye min harda na pharmacy a ciki da alamu magani ya sayo.
"Ga breakfast dinki da drugs ki sha bayan kin gama nd pls next time in baki da lafiya let me know" yana gama magana ya fita, ni abin ma sai naji shi wani bambarakwai wai yau Zafar ne yake min magana a nitse babu tsawa harda wani pls? Hmmm tab na yarda da maganan Yasmin da tace yana bala'in tsoron Abban shi daga waya sau 1 har ya sauya.
But sai nake jin kaman ban kyauta ba da na had'a shi da mahaifin shi har yayi mishi fad'a, wani bangare na zuciya ta na kara ingizani cewa sai me ai shima lokacin da yake takura ni bai tausaya min ba.
Bud'e ledan eatary nayi naga manyan package na take away guda 2 na farko cike da chips da kwai sai na biyun kuma cike yake da pepped chicken sai kamshi suke ba b'ata lokaci na d'iba na fara ci ina zuba santi,sai da nayi nak sannan na tattara sauran na kai kitchen ban gan shi a parlorn ba ban kuma bi ta kan shi ba nazo na cigaba da charting na.
******************
Washe garin ranan da suka dawo daga wajan boka Gwaggo Aisha tasa Hajara wanka da sassafe ta shirya wai ta taho gida na su fara aiwatar da kudurin su tunda wuri, bata musa mata ba ta shirya tsab tayi kwalliyar ta cikin doguwar rigar ta na atampa daya amshe ta sosai,tana bari tayi breakfast kamin ta fita amma ta hana ta tace in azo nan gidana taci.
Haka ta fito wajan 8 da wani abu ba tayi nisa da gidan namu ba ta samu kwata ta jefa maganin a ciki tayi wucewar ta, bata son zuwa gidan da sassafe haka ta san duk yanda akayi kila ko farkawa daga bacci bamuyi ba, tunda ta shigo anguwan da nake ta fara jan kafa dan bata san kowa a anguwan ba da ta shiga ta dan ja lokaci har sai Zafar din ya fita kamin ta shigo.
Dole haka ta karaso kofar gidan tayi knocking mai gadi yazo ya bud'e mata kofan ta shigo daga ciki sannan ta gaishe shi cikin girmamawa da yake ya dan manyan ta, amsa mata yayi cikin kulawa kasancewar yaji dad'in yanda ta gaida shin.
"Dan Allah Baba masu gidan sun tashi kuwa?" Ta tambaya shi lokacin yana shirin komawa dakin shi.
"Gaskiya bana jin sun tashi dan sai kusan goma sannan muke kin motsin farkawan su" ya amsa mata.
" Toh dan Allah zan zauna a nan kamin su farka" tace tana nuna mishi wasu kujerun roba da suke can gefe cikin furanni.
"Toh toh shikenan ki zauna sai sun fito" yace yana shigewa dakin shi, karasawa tayi ga kujerun ta zauna tana ajiyar zuciya samun relief ta ciro wayar ta daga cikin jaka ta fara game dan ya rage mata zaman kad'aici, ya ko taimaka matan dan bata san lokacin da taja a wajan zaune ba hankalin ta duk