Showing 51001 words to 54000 words out of 85226 words
yarda ta juyo ba balle ta amsa, Dan murmushi Maa tayi tana girgiza kai tare da mata addu'a Allah ya rage mata wannan zafin zuciyan.
Lokacin da ta dawo bacci ya d'an sace ni ban san ma ta dawo ba sai cikin bacci naji kaman kuka harda shashheka, a hankali na bud'e ido na dan tabbatarwa, bayan ta na gani tana ta kuka tsakanin da Allah wanda tun tasowa ta banga ko kwatanci sa tayi ba.
Tausayi da kaunar tane naji yana bin ko ina a cikin jinin jikina saboda na san duk a kaina ta tada hanklin ta kan auren da taji Baba yace zai min, banida zab'i dole in kwantar da hankali in nuna mata babu komai ta wajena ko zata samu natsuwa, wannan dalilin yasa naki fad'a mata tun farko kenan amma ba yanda zanyi dole ne ta sani.
D'an motsi nayi yanda zata ji, aiko nan da nan ta shiga share hawayen sannan ta d'an juyo sai taga ido na a rufe, bakin gado tazo ta zauna tana shafa min gashin kaina, jin ta daina kuka yasa na bud'e ido na kaman yanzu ne na tashi daga baccin.
Murmushi ta sakar min tace " bacci kika koma kenan?" Gyad'a kai na nayi nima ina maida mata martanin murmushin.
Ina ta jira inji ko zata min maganan auren amma naji tayi shiru sai jana take da hira tana bani labaran ban dariya, nima dan in kwantar mata da hankali yasa na saki raina nayi ta dariya amma can kasan raina cike ya tab da damuwa.
Bayan sallah magarib sai ga Abban Zafar da tawagar sa a kofar gidan mu Kuma sun taki sa'a Baba yana nan bai tafi ko ina ba, Baba duk ya rikice ya susuce ganin manyan masu kud'in garin maiduguri a kofar gidan sa kuma da sunan sun zo had'a zuri'a dashi.
Makotan mu biyu ya kira sannan ya kira Baban Dije wanda zance shi ya jagoranci komai ya hana Baban mu gudun kada ya kwafsa ko ya saki layi, hakan da yayi ya taimaka kuwa dan shi Abban Zafar tunda yaji ance Mallam ya zata Baban Mallamin ne da gaske.
Wata 2 ciff aka saka na biki mu aka rabu cikin mutunci bayan sun sauke carton carton na minti da chewing gum da goro na rabawa yan uwa, Abba yaja Baba gefe ya bashi check na wasu kud'ad'e kan yayi hidimar biki da gida sannan ya d'aura da basa bukatan a kaini koda cokali guda d'aya su zasu tanada min komai su kawai surka suke bukata.
Murna da Baba yake ji kaman ya daka tsalle amma ganin yanda Baban Dije ya kama kai yake musu magana shima hakan ya kwaikwaya har yayi mishi sallama ya shiga mota driver yaja suka tafi.
Muna zaune sai gani mukayi anata shigowa da kwalaye kaman za'a bud'e shago, kowa kallon kayan yake tare da neman karin bayani sai dai babu mai bamu, sai da aka gama shigowa da kayan tass sannan Baba ya shigo yana jan banban rigan shi a kasa cikin d'aga murya ya fara magana yanda kowa na gidan zai ji.
"Allahu yayi Allahu yayi!!! Ina kuke mutanen gidan nan kowa ya fito yaga abin arziki daya same mu, kayan saka rana ne na 'yar albarka, wata 2 kacal iyayen ango suka ce a saka dan suna bukatan ayi auren da wuri.
Ba wayan nan kayan kawai ba har takardan karb'an kud'i na banki sirikin nata ya bani sannan yace basa bukatan mu kai ta koda cokali su zasuyi mata komai...."
"Aaaaaaayyyyyyiiirrrrrrrr!!! Inna Asabe ce ta rangad'a wannan gud'a cikin farinciki tace" Masha Allah 'ya tayi goshi duk abubuwa daka lissafo duk na saka rana ne ina ga Allah ya nuna mana ranan auren ba magana....."
"Aikin banza aikin wofi kowa yaga dama zaiyi ai tunda abin shige-shige ne" Gwaggo Aisha ta katse ta, Inna Asabe dai bata kula ta sai shewa suke da Allah ya sanya albarka suke da Mama Dije.
Tashin hankali sosai na shiga da ganin kayan da muka maganan Baba duk da na san da zancen, kokarin dannewa nake saboda kada in karawa Inna tashin hankali amma na kasa daurewa,kuka na fashe dashi sosai har jikina yana rawa na shiga d'aki da gudu na fad'a kan gado ina mai cigaba da kuka mai tsuma zuciyan mai sauraro.
.
Jiki a sanyaye Inna ta biyo baya na ta zauna a gefena ta kura min ido itama idon ta na cikowa da hawaye amma ta hana su zubowa, tana rayawa a ranta inama zata iya dakatar da wannan auren da tuni ta dakatar da wanne zan ji cikin lokaci d'aya na had'u da jarrabawan rayuwa ga rad'ad'in rabuwa da Yaya na bai bar ni ba ace kuma ga auren da bamu san daga ina ya fito ba.
Sai dai bata da zab'i dole ne ta karfafa min guiwa inyiwa mahaifina biyayya kaman yanda itama tayiwa nata mahaifin, gyara zama tayi tana gyaran murya sannan ta fara magana cikin rarrashi" wani lokacin kuka bashi ne waraka ba ga matsaloli na rayuwar mu ba,sai dai mu kanji sauki da rad'ad'in da zuciyoyin mu suka tsinci kan su a ciki dan haka ba zan hana ki kuka ba kiyi Zareefa kema ko zaki ji sauki.
A al'adance da kuma addinin musulunci ya bawa mahaifi daman zab'awa 'yar shi miji daya ga ya dace da ita bi ma'ana ya yarda da addinin shi da kuma tarbiyan shi dan haka kada kiyiwa mahaifin ki mummunan fahimta domin ba zai tab'a Kai ki inda zaki wulakan ta ba kuma albarkacin biyayya da kikayi mana Allah zai saka miki da mafi alkhairi ko kuma da abinda baki tab'a zato ba balle tsammani.
Abu d'aya da nake son ki tuna wannan auren ko dan Abdulbasit ya kamata ki rike shi da hannu bibbiyu saboda na san duk inda yake zai ji cewa za'a miki aure,kn ga kuwa kin nuna mishi zaki iha rayuwa ko babu shi sannan zai fahimci cewa kina da masoya ba shi kad'ai ne gare ki ba".
Tun ina kuka kasa-kasa har na daina nayi shiru ina sauraron kalaman Inna, ya zanyi dole ne inyi biyayya in aure shi tunda ya biyo ta hannun Baba, baya ga haka in nace bana son shi waye nake dashi a yanzu, wanda na taso da son shi tun ban san kaina ba ya guje ni ya watsa min kasa a ido I don't have choice rather than accept this man domin na gama soyayya a rayuwata zuciya ta ta rufe kofa tayi ban kwana da soyayya harb abada.
Sanyi sosai Inna taji a ranta na ganin kalamanta sunyi tasiri a kaina har na daina kukan sai ajiyan zuciya da nake akai-akai, matsowa nayi jikin ta sosai tare da d'aura kaina a kan cinyar ta na saka hannaye na duka biyu na rungumo kwankwason ta, itama tasa hannu ta dama tana shafa min gashin kaina na fara magana a hankali kaman mai rad'a.
" Inna ku iyaye nane biyayya a gare ku ya zama wajibi a gare ni, kukan da kika ga inayi ba dan auren da Baba yace zai min bane kawai na tuna da Yaya nane" na karasa wasu sabbin hawayen na zubo min na tausayin kai na, na fad'i haka ne dan in kwantarwa Inna hankali ba wai da gaske ba.
Cikin jin dad'in kalamai na Inna ta kara rungumo ni jikin ta tana shafa kaina tare saka min albarka da addu'oin gamawa da duniya lafiya.
******************
A kwana a tashi babu wuya a wajan Rabbi Izzati, mun cinye wata d'aya cikin watanni 2 da aka saka na bikina kuma gini da Baban mu yake yayi nisa sa dan har an gamawa Inna bangaren ta,2 bedroom da babban parlour sai kitchen da store sosai ginin yayi kyau, yanzu bangaren Inna Asabe da Gwaggo Aisha ake yi.
Maryam ta dage sai rawan kai take akan bikin ni bata san haushi ma take bani ba, duk wasu frnds d'in mu na makaranta ta sanar dasu sai shirye-shiryen su suke ni dai na kawao na mujiya na zuba musu.
A bangaren Zafar ma hakan take dan shi cewa yayi babu wani biki da zaayi sai ranan da zai auri love of his life sannan zasu sha bukukuwa ba biki bama.
Sadiq ne yace bai isa ba dole ne su sha biki in ya tashi yin wancan yayi abinda ya ga dama, yaso yayi jayayya amma ganin yanda Abba da Mom suka dage suna shirye-shiryen auren yasa yaja bakin shi yayyi shiru tare da zuba musu ido ya san in har zai cigaba da nuna halin ko in kula asirin shi zai iya tonuwa.
Akwai wata mata daga sudan take ta kware wajan gyaran amare Inna ta nemo kuma wai dole sai kaje gidan ta da farko ta ganki sannan zata duba gyaran daya dace da fatar ki,sun gama magana da Inna saura wai ta tura ni ta ganni, ba dan naso ba Inna tasa na kira Maryam a waya kan tazo ta rakani.
Da washe gari kuwa tazo muka tafi gidan nata da yake can Shokari, koda muka je gidan ta cike yake da matan aure harda sabin amare ana tayi musu aiki dan harda 'yan mata masu taya ta tana biyan su.
Tarba na musamman akay mana a babban parlour ta inda take sauke bakin ta na musamman,bamu dad'e da zama ba tazo wajan mu bayan mun gaishe ta cikin girmamawa itama ta amsa mana cikin kulawa sannan ta fara aikin ta wato rubuta duk kayakin da zasu dace da fatana da kuma gashi na sannan ta sallame kan cewa sai next week zan fara zuwa, godiya mukayi mata muka fito zuwa gida.
A gajiye tibis muka dawo kasancewar Anguwan nata da nisa sosai da namu, mun shigo layin mu kenan wata had'add'iyar mota baka wuluk tazo zata fita mu Kuma muna shiga kaman ance min dago kanki ina d'agawa na tsaya cak tare da dafe kirji na da hannu biyu ina zaro ido waje duk at da same time bakina na rawa nace " YAYA NAAA..."
[1/26, 7:14 AM] Golden Pen Writer's Assoc: π¦πΉπ¦πΉπ¦πΉπ¦πΉ
π¦πΉπ¦πΉπ¦πΉ
π¦πΉπ¦πΉ
π¦πΉ
π¦
*BA SONTA NAkE BA*
π¦
π¦πΉ
π¦πΉπ¦πΉ
π¦πΉπ¦πΉπ¦πΉ
π¦πΉπ¦πΉπ¦πΉπ¦πΉ
_A story about love and sacrifice._
_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_
_*From The Fantastic Writer of*_
```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```
*_And now_*
*_BA SONTA NAKE BA_*
β *β GΜΎOΜΎLΜΎDΜΎEΜΎNΜΎ PΜΎEΜΎNΜΎ WΜΎRΜΎIΜΎTΜΎEΜΎRΜΎSΜΎ AΜΎSΜΎSΜΎOΜΎCΜΎIΜΎAΜΎTΜΎIΜΎOΜΎNΜΎ* ββ
https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/
*wΜΆΜΆΡ Ξ±rΜΆΜΆΡ Π²ΡΞ±rΜΆΜΆΡrΜΆΜΆ'sΜΆΜΆ ΟfΜΆΜΆ sΜΆΜΆΟ gΜΆΜΆΟlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡnΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡnΜΆΜΆ*
*wΜΆΜΆΡ wΜΆΜΆrΜΆΜΆΓtΜΆΜΆΡ Ξ±sΜΆΜΆsΜΆΜΆΓdΜΆΜΆΓΟuΜΆΜΆsΜΆΜΆlΜΆΜΆΡ pΜΆΜΆΡrΜΆΜΆcΜΆΜΆΡΓvΜΆΜΆΡ nΜΆΜΆΟ pΜΆΜΆΞ±ΓnΜΆΜΆ,*
*sΜΆΜΆΟ mΜΆΜΆΞ±gΜΆΜΆΓcΜΆΜΆΞ±lΜΆΜΆ ΟuΜΆΜΆrΜΆΜΆ cΜΆΜΆrΜΆΜΆΡΞ±tΜΆΜΆΓvΜΆΜΆΡ gΜΆΜΆΟlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡnΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡnΜΆΜΆ* β *,Π²ΡhΜΆΜΆΟlΜΆΜΆdΜΆΜΆ ΟuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ.Ξ± pΜΆΜΆrΜΆΜΆΟdΜΆΜΆuΜΆΜΆcΜΆΜΆtΜΆΜΆ ΟfΜΆΜΆ ΟuΜΆΜΆrΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡnΜΆ*ΜΆ *,sΜΆΜΆΞ±vΜΆΜΆΟuΜΆΜΆrΜΆΜΆ ΟuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ, fΜΆΜΆΟrΜΆΜΆ ΓtΜΆΜΆ wΜΆΜΆΓlΜΆΜΆlΜΆΜΆ* *cΜΆΜΆΞ±uΜΆΜΆsΜΆΜΆΡ ΡΟuΜΆΜΆ nΜΆΜΆΟ pΜΆΜΆΞ±ΓnΜΆΜΆ.*
*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*
Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.
*INA MASOYAN LITATTAFAN ΖUNGIYAR GOLDEN PEN?*
*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ΖARE!.*
Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buΖata namu daga farko.
Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana Ζara mana Ζarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.
*Bismillahir Rahmanir Raheem*
*25&26*
Yanda ka san statue haka na tsaya ko motsi na kasa yi sai motan nabi da kallo da idanuwana kaman zasu zazzago kasa ga kuma zuciya ta na ta lugude kaman zai faso kirji na ya fito.
" What's wrong with you Zareefa daga ganin mota sai kice ga Yayan ki, ke duk wulakanci da mutumin nan yayi miki ashe baki cire shi a ranki ba har kina tunanin zai dawo gare ki Kuma ga dukkan alamu zaki karb'e shi da hannu bibbiyu kenan...."
"Maryam shi na gani fa ba imagination bane" na katse ta da muryar tausayi.
"What ever, zo muje ga Inna can da kaya a hannu zata shiga gida muje mu taimaka mata ba wannan surutu mara kan gado ba" tana magana ne tare da jan hannu na muka fara tafiya ina waiwayen baya ko zan ga motan zai dawo amma har muka shiga gida banga ko kalar motan ba, kamin mu karasa Inna har ta riga mu shiga gida.
A parlour muka iske ta zaune tana kallo babu lodin kaya da muka ga ta shigo dasu, zama mukayi muma anan Maryam tana yi mata bayqni akan zuwan mu gidan mai gyaran amma hankalin ta yana kai na ganin nayi shiru na zama wani iri ba kaman yanda muka fita ba.
"Ke kuma lafiyan ki kuwa ana magana kinyi wani zuru dake?" Kaina na mayar kasa ina kokuwa da hawayen da naji suna son zubowa, harara Maryam ta b'alla min tana muskudawa sannan ta bawa Inna amsa.
"Kyale ta Inna ni takaici ma ya hanani kula ta, muna shigowa layin nan wai kawai dan taga mota ya wuce kin ga yanda ta daskare waje d'aya wai taga wannan mayaudarin da kyar fa naja ta muka biyo bayan ki lokacin kina shiga gida ga kaya a hannun ki nace muzo mu taya ki".
"Ban san meyasa taki sakawa ranta dangana ba ko kin manta aure zakiyi, haka zaki je gida wani kina wanna shirmen da shashanci? Ki kama kanki daga irin haka na gaya miki" Inna take dad'in haka cikin fushi ba tare da ta bawa Maryam amsar tambayar ta ba, nima hakuri na shiga bata ina cewa na daina ba zan sake ba Maryam tana taya ni sai da muka ga ta sauko sannan muka bari.
Bayan mun huta mun ci abincin da Inna ta ajiye mana sannan Maryam ta wuce gida tare da cewa sai munyi waya.
Tun daga wannan rana suka kara kaimin shirye-shirye da suke Inna ta ta zama busy sosai these days sai fita sayayya suke da Maman Dije wata rana Kuma da Inna Asabe, Gwaggo Aisha ce dai ko kallo basu ishe ta saima yad'a habaice-habaice da take.
A haka satin da matan tace zan fara zuwa gyara ya zagayo na fara zuwa wajan gyaran a motan su Maryam wanda Mamanta ce ta d'auki nauyin hakan kullum driver zai zo ya d'auke ni in mun gama zuwa yamma kuma waya kawai zanyi yaje ya maido ni gida kasancewar tace ba'a son ina shiga rana saboda zai maida aikin baya.
***************
A gidan su Zafar suma ba karamin shiri suke ba abinka da masu kud'i an gyara mana gidan da zamu zauna duk da sabon gini ne sai da suka Kara da d'an gyare gyare,kayan da za'a saka na cikin wannan gida Abban Zafar ne yayi order su daga kasar waje haka ma kayan lefe na suma duk a kasar waje suka had'o su, shi dai yana gefe yana kallon su yana jin ina zai iya hana su ko kuma inama zai iya fad'a musu gaskiya cewa auren da zaiyi temporary ce ba permanent ba su daina kashe kud'in su amma hakan ba mai yiwuwa bane dan yayi Imani Abban shi yaji abinda ya shirya suna iya batawa na har abada.
Sadiq kuwa in ka ganshi zaka zata shine angon kan yanda ya kasa ya tsare komai yana tafiya daidai, baya ko neman shawaran Zafar yake abinsa shi kad'ai ko Kuma suyi da sauran friends d'in su saboda ko ya nema baram-baram suke rabuwa dan haka suma suka ajiye shi a gefe suke abinda ya dace.
Ana saura kwana goma bikin duk an gama komai a gidan nasu had'a dasu cards da kayan da zamu saka na duk event d'in sun kammala sai bikin kawai suke jira.
Da yamma Mom ta kira shi a waya kan ya same ta a part d'in su, amsawa yayi da toh dama ba wani abu yake ba dan haka ya mike ya fita zuwa amsa kiran nata.
A parlour ya iske su kusan su biyar da Aunty's d'insa wasu ta bangaren Mom wasu kuma ta bangaren Abba sun baza uban kaya a gaban su suna ta kallo.
Gaishe su yayi ya koma gefe ya zauna yana yan dane-dane da wayar shi.
"Ya kuma zaka zauna a nesa, oya come closer kayan amaryar ka ne zo ka duba in akwai abinda baiyi ba sai a canza ko" Mom tace mishi hakan.
" No Mom ba sai na duba ba duk abinda kukayi daidai ne" yace yana kara gyara zama alamun bashida niyyan motsawa bare tashi.
"Kema dai Yaya da son jan magana kike, wannan lefen nayi Imani ko gidan governor zamu iya kaiwa without fargaba balle Kuma wannan 'yar talakawan" cewar wata kanwar Mom da suke kira da Aunty Hauwa dama tana takaicin Zafar daya tashi aure bai nema a cikin 'yan uwa ba yaje ya jajib'o musu 'yar talakawa.
"Hmmmmm" Mom tace tana tabe baki alamun maganan yayi mata dad'i.
"Ai babu zancen duk abinda akayi dadidai ne kai kafi mu sanin matar ka da abinda take so da Kuma abinda zaiyi mata kyau dan haka kazo ka duba nace maka" Aunty Falmata ke fad'in haka babu alamun wasa kan fuskar ta.
Da yake ya san halin ta bata da sauki sam kusan halin su d'aya da Abban shi shiyasa yake matukar shakkar ta, ba musu ya taso yazo ya tsugunna gaban kayan ya fara dubawa kaman da gaske bayan kawai d'agawa yake yana ajiyewa ,su Kuma kannen Mom da ita kanta sai tab'e baki suke na jin takaicin wai sai ya duba.
Yana yi yana kallon