Showing 42001 words to 45000 words out of 85226 words
kurma ihun murna sai dai ba hali cikin sauri har muryan shi na rawa yace" kai amma yaro yaro ne meye na wani sai an tambaye ni, bayan babu inda zan je kullum ina gida. Ko yau suke so su zo ina jiran su kaji?".
"Toh Baba nagode, mu zamu tafi" yace tare da mikewa ya kara ciro wasu bundles d'in ya zubar da su a gaban Baba sannan ya mike har suka fita daga compound d'in Baba bai dawo daga suman ganin makudan kud'ad'e daya tafi ba.
Sun hau kan hanya ba tare da Sadiq ya kalle shi ba yace " Zafar it's wrong, it's totally wrong".
"And who are you to say so?" Zafar ya tambaye sh yana kara cin magani, Sadiq bai kara ce mishi uffan ba sai ma kara maida hankalin shi da yayi kan tukin da yake.
A nan asibiti kuwa Gwaggo Aisha kasa zaune ta kasa tsaye sai jujjuya ido take wai me yake shirin faruwa ne, bata gama da wancan ba kuma ace ga wani ya bullo? Ita abinda yafi d'aga mata hankali shine ita 'yan matan ta basa samun masu kud'i sai ni, shi wannan kam bayan mai kud'in ne kuma gashi balarabe.
"Wallahi ba zata tsabu ba wai bindiga a ruwa wannan karan sai ta raba ni da komai na jin dad'in rayuwa ko da duk abinda ta mallaka zasu kare ba zata tab'a zuba ido Bintu da 'yar ta su kasance fiye da ita da yaran ta ba.
Kaman wacce aka tsikare ta da allura muka ga zuruf ta mike fuuu tayi waje kaman wata kububuwa,da ido kowa ya bi ta dan tunda su Zafar suka fita babu wanda yayi magana cikin d'akin kowa da kalan tunanin da yake a cikin zuciyar shi.
Tashin hankali da Gwaggo Aisha ta tarar a waje yasa taji kaman ta kurma ihu dan bakinciki, akan idon ta Zafar ya yiwa Baba kyautan makudan kud'ad'e suka shiga mota su dashi kad'ai ta kalla ta san cewa kud'in sa ya wuce duka tunanin ta.
Ganin Baban mu ya hangame baki ya kasa dawowa hayyacin sa tunda yaga ruwan kud'i ya kara tunzura ta, ta taho a fusace ta cikin d'aga murya tace "kai Mallam meye haka?" sai a sannan yaja doguwar ajiyan zuciya ya juyo ya kalle ta,ba tare da yace mata ci kanki ba ya kwashi kud'add'en sa yayi gaba abin shi.
Sosai Gwaggo Aisha ta shak'a wato ya mai da ita mahaukaciya ko? Zasu gani zata nuna musu ainihin true colors d'in ta zasu san da ita suke zancen, sai matsayin ta na da ya dawo ta cigaba da mulkan gidan baki d'aya.
Bayan fitan Gwaggo Aisha Inna abu da Hajara suka mike sukayi mana sallama tare da yi min Allah kara sauki suka fita, cikin sauri Inna tabi bayan su dan basu kud'in mota d'akin ya kasance daga ni sai Maryam da Maa da ta juya mana baya ta kwanta da alamu dai tayi bacci.
"Ni fa na kasa yarda Yaya na zai min haka, saboda yana matukar so na Maryam wallahi yana so na" na karasa ina fashewa da sabon kuka.
Gyad'a kai kawai Maryam ta iya yi min tana share hawaye itama saboda ta shiga duhu sosai a yanda muke matukar son junan mu ace ya juya min baya lokaci d'aya, tabbas babban al'amari ne zai iya raba mu , addu'an ta Allah ya daidaita tsakanin mu.
"Kiyi hakuri Zareefa ko wani tsanani yana tare da sauki, mu cigaba da addu'a insha Allah komai zai daidaita" ban iya bata amsa ba sai kuka da nake ina jin zuciya ta na min wani irin suya.
"Hmmm ni ban san su Ya Sadiq me ya kawo su nan ba abin ya daure min kai" cikin sauri na d'ago da kaina ina duban ta dama tambayoyin dake cin raina kenan su waye su, kuma menene dalilin zuwan su har asibiti duba ni ba dan ni dai ban san su ba.
"Ai na zata wajan ki suka zo " na fad'a da dashassiyar murya ta.
Girgiza kai ta shiga yi kana tace " ko d'aya, na shirya ina shirin zuwa duba ki kiran Ya Sadiq ya shigo bayan na d'aga mun gaisa yake tambaya ta labarin ki shine fa nace mishi nima yanzu zan zo duba ki anyi admitting d'in ki a Kanem Hospital, sai naji yace suma gasu nan zuwa in sun iso zai kira waya ta in shigo da su. Ni dai da toh na bi shi ina mamakin ya akayi ya samu number ta".
Ido kawai na zuba mata ina sauraron ta itama tace haka toh ni kuma in ce me kenan.
"D'ayan kuma shine Zafar Baban shi multi millionaire ne maybe ma zaki san shi sunan shi....."
Saurin katse ta nayi nace" bana bukatan ji koma shi d'an wanene wannan damuwar shi ce nima ki bar ni inji da nawa damuwar".
Shigowan Inna yasa muka bar zancen ta cigaba da bani baki, cikin dabara ta zubo min pepper soup na kayan cikin rago da ta kawo min naci ba laifi da yake tana ta Jana da hiran Yaya na sai gashi na d'an ware muna hira.
Sai kusan azahar sannan Maryam tayi mana sallama ta tafi, a takaice sai da nayi kwana 2 a asibiti sannan aka sallame mu.
Cikin kwanaki 3 nan da nayi a asibiti kullum ido na yana kan hanya wai ko zanga Yaya na yazo duba ni yace min wasa yake amma shiru kuma kullum cikin gwada layi shi nake amma ko sau d'aya bai tab'a shiga ba.
Cikin kwanaki 3 nan da mukayi a asibiti abubuwa da yawa sun faru cikin su kuwa yanda Zafar ya bi ya shiga jikin Baban mu yayi amfani da son abin duniya na Baban mu ya saye shi tsaf har yayi mishi alkawarin bani da wani miji a duniya sai shi, hakan kuwa ba karamin dad'i yayi mishi ba dan ya san yanzu bashi da matsala ta ko Ina .
Da yamma muka dawo gida nan da nan gidan ya cika da makota da basu samu daman zuwa asibiti duba ni ba suka shigo suna min ya jiki, har mutanen suka watse Gwaggo Aisha bata shigo ba dama rabon ta da asibitin tun ranan da suka je duba ni dukkan su daga nan bamu kara ganin ta ba sai Inna Asabe ce mai zuwa ita da Hajara, Jameela kam tunda aka kwa tar dani bamu ga keyar ta ba balle kuma yanzu kila ma bata gidan ta fita wannan gantalin nata.
Zafar da Sadiq sai da suka kusan samun tsab'ani a kaina wai lalle sai Sadiq yazo ya same ni ya min bayanin auren shi kuma yace ba da shi ba wannan dan wallahi in ya kuskura ya turo shi wajena ce mishi zaiyi sona yake kaman rayuwar shi shiyasa ya turo shi in taimaka inji tausayin shi in aure shi.
Wannan magana da Sadiq yayi ba karamin tunzura Zafar yayi ba wai kaman shi za'a ce wai k'aramar yarinya mara class mara kyau wacce yake ganin in ba dan takurar Abban shi ba ko a mai wanke-wanke gidan shi ba zai d'auke ni ba balle ace wai sona yake Allah ya kiyaye.
Cikin fushi yaja motan shi yayi hanyan gidan mu dan dole ayi ta ta kare saboda yau ne deadline da Abban shi ya bashi, shi kuma Sadiq yayi hakane dan yaje da kan shi saboda gaba yake jiye mishi amma shi sam baya gani.
Ina zaune kan sallaya dana idar da sallah isha'i nayi zuru ina tunanin ta yaya zan iya rayuwa ba tare da Yaya na ba, shine komai nawa na taso da soyayyar sa cikin jinin jikina duk wata rayuwa da shi na tsara yanzu rana tsaka ace ya rabu dani, to ya zanyi da rayuwata?
Muryan kani na Ibrahim naji yana cewa Inna ta daya tarar a waje wai ana sallama da Zareefa.
Ban tsaya jin me Inna tace mishi ba na fita da sauri kaman zan had'a da gudu, a zuciya ta ina haba na sani mana shima ba zai iya rayuwa babu ni ba na san dama wasa yake min.
Murmushin dana fito da shi a fuska tace ta b'ace bat ganin wanda ban tab'a zato ba tsaye a kofar gidan mu.
[1/26, 7:08 AM] Golden Pen Writer's Assoc: π¦πΉπ¦πΉπ¦πΉπ¦πΉ
π¦πΉπ¦πΉπ¦πΉ
π¦πΉπ¦πΉ
π¦πΉ
π¦
*BA SONTA NAkE BA*
π¦
π¦πΉ
π¦πΉπ¦πΉ
π¦πΉπ¦πΉπ¦πΉ
π¦πΉπ¦πΉπ¦πΉπ¦πΉ
_A story about love and sacrifice._
_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_
_*From The Fantastic Writer of*_
```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```
*_And now_*
*_BA SONTA NAKE BA_*
β *β GΜΎOΜΎLΜΎDΜΎEΜΎNΜΎ PΜΎEΜΎNΜΎ WΜΎRΜΎIΜΎTΜΎEΜΎRΜΎSΜΎ AΜΎSΜΎSΜΎOΜΎCΜΎIΜΎAΜΎTΜΎIΜΎOΜΎNΜΎ* ββ
https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/
*wΜΆΜΆΡ Ξ±rΜΆΜΆΡ Π²ΡΞ±rΜΆΜΆΡrΜΆΜΆ'sΜΆΜΆ ΟfΜΆΜΆ sΜΆΜΆΟ gΜΆΜΆΟlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡnΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡnΜΆΜΆ*
*wΜΆΜΆΡ wΜΆΜΆrΜΆΜΆΓtΜΆΜΆΡ Ξ±sΜΆΜΆsΜΆΜΆΓdΜΆΜΆΓΟuΜΆΜΆsΜΆΜΆlΜΆΜΆΡ pΜΆΜΆΡrΜΆΜΆcΜΆΜΆΡΓvΜΆΜΆΡ nΜΆΜΆΟ pΜΆΜΆΞ±ΓnΜΆΜΆ,*
*sΜΆΜΆΟ mΜΆΜΆΞ±gΜΆΜΆΓcΜΆΜΆΞ±lΜΆΜΆ ΟuΜΆΜΆrΜΆΜΆ cΜΆΜΆrΜΆΜΆΡΞ±tΜΆΜΆΓvΜΆΜΆΡ gΜΆΜΆΟlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡnΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡnΜΆΜΆ* β *,Π²ΡhΜΆΜΆΟlΜΆΜΆdΜΆΜΆ ΟuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ.Ξ± pΜΆΜΆrΜΆΜΆΟdΜΆΜΆuΜΆΜΆcΜΆΜΆtΜΆΜΆ ΟfΜΆΜΆ ΟuΜΆΜΆrΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡnΜΆ*ΜΆ *,sΜΆΜΆΞ±vΜΆΜΆΟuΜΆΜΆrΜΆΜΆ ΟuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ, fΜΆΜΆΟrΜΆΜΆ ΓtΜΆΜΆ wΜΆΜΆΓlΜΆΜΆlΜΆΜΆ* *cΜΆΜΆΞ±uΜΆΜΆsΜΆΜΆΡ ΡΟuΜΆΜΆ nΜΆΜΆΟ pΜΆΜΆΞ±ΓnΜΆΜΆ.*
*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*
Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.
*INA MASOYAN LITATTAFAN ΖUNGIYAR GOLDEN PEN?*
*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ΖARE!.*
Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buΖata namu daga farko.
Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana Ζara mana Ζarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.
*Bismillahir Rahmanir Raheem*
*19 & 20*
Ina fitowa na ga ya ajiye motan sa a inda ya saba ajiyewa yana sanye da kaftani na farar shadda ya d'aura waya a kunne yana magana, farinciki naji kamar ya kashe ni Yayana ya dawo gare ni wayyoo ni.
Da gudu na Ζarasa ta bayan shi saboda farinciki ya rufe min ido nayi abinda ban tab'a yi ba wato ina zuwa banyi wata-wata ba na rungume shi ta baya ina sauke tagwayen ajiyan zuciya cikin muryan kuka na fara magana ;
" Yaya naaaaa ni na san ba zaka iya ba dole zaka dawo gare ni i know u truly love me idon ka kad'ai nake kallo in gane hakan"". Cak ya tsaya ya kasa juyowa kuma ya daina wayan mun kusan minti 1 a haka ya juyo tare da banbare ni a jikin shi ya watsar a gefe yace;
"Yuck how disgusting baki da hankali ne daga gani na zaki wani zo kiyi huging na haka ko ance miki irin samarin nan naki ne marasa kan gado?" Yanayi yana watsa min wani kallon kaskanci, muryan da naji kad'ai yasa gaba na fad'uwa dan wannan dai ba muryan Yaya na bane amma kuma na san mai muryan sai dai a sani na da tunani na babu abinda zai kawo shi gidan mu.
Cikin fargaba na d'aga ido na dan tabbatarwa kai na cewa bashi bane, amma me ina dagowa idona sai cikin nashi da yake aiko min da munanan sakonni.
D'auke nawa idon nayi cikin second d'aya ganin wanda ban tab'a zato balle tsamani ba a kofar gidan mu, na had'iye wani bushashan yawu da ya tsaya min a makoshi sai yanzu na lura da yanayin shigar sa tsayin sa fatan jikin sa komai daban dana Yaya na.
Kara d'agowa nayi naga yana min wani kallo kaman yaga kashi , cike da jin haushin kaina kama hanya zan shiga gida garin murnanan zuwan Yaya bada kaina.
Gaba na yasha yana wani kumbura fuska kaman ni na jawo shi gidan namu yace;
"Nasan yanzu gurgun tunanin ki ya baki cewa wajan ki nazo ko? well I don't have much time but to say I have a contract with you"
"Contract!?" Naji baki na ya furta cikin mamaki ba tare da na shirya ba, shi kuwa murmushin gefen baki yayi yana like father like daughter" shi a zaton sa duk son abin duniya yasa na amsa mishi lokaci d'aya bai san cewa mamaki ne ya kama ni ba.
"Yeah contract marriage kuma if possible ba zai wuce 1 to 2 months ba zakiyi tafiyan ki nd zan iya baki daga 100 millions zuwa sama kuma kada ki d'auka wai zaman ma'auran gaske zamuyi, no zanyi haka ne kawai dan in fita daga mess d'in da Abba na yake son jefa ni ciki" a garance ya cigaba da tambaya ta nawa zai bani.
Juyowa nayi ina fuskar shi da kyau duk da ina jin yanda zuciya ta take bugawa kaman ya fito saboda tsaban kwarjini da yayi min dan sosai yake cika min ido amma dole ne in nuna mishi mu mata daraja ne damu kud'i bai isa ya saye mu ba.
"Hmmm ikon Allah , naji ni mai gurguwar tunani ce, kai kuma wannan tunanin naka me zan kira ta dashi miskini ko nakashasshe?
"Anyway bari in fada maka ko duniya da abinda yake ciki zaka mallaka min toh ni Zareefa na fi karfin wannan kazami ko haramtaccen rayuwa da kazo min dashi sai dai ka kara gaba kila ka samu wata gantalalliya da zata amince maka amma ba ni ba"
Ina gama maganata na rab'a ta gefen shi zan wuce zuwa cikin gida naji an finciko ni ta baya tare da d'aga hannu zai yarfa min mari kuma ya fasa ya dungule hannun ya kaiwa iska naushi yace;
Damn u ! Who do u think u re ? Da har zaki bud'i baki ki fad'a min magana son ranki, I don't blame you baki san wanene ni ba da ko wuka aka d'aura miki a wuya u will not have d guts to do it.
Kada gani na a kofar gidan ku yasa ki d'auki kan ki kaman wata mace u re nothing yes I mean nothing, ba duniya da abinda suke ciki zan bayar ba amma Baban ki yace min ko gobe inzo zai d'aura min aure dake nazo nan na fad'a miki ne cus na san ba lalle bane su fad'a miki irin auren da zakiyi but for now at least kin san irin auren da zakiyi, as for me I don't have time for cheap girls like u".
Yana gama maganan shi fad'a motan shi yaja shi a d'ari ya fita daga layin mu tare da bad'e ni da kurar motan ya tafi abin shi.
Ni kuwa ko kafata na kasa d'agawa a wajan ba wai maganganun shi ne suka b'ata min rai ba illa sunan Baban mu daya ambata a cikin maganan shi ya jefa ni cikin tashin hankali mara misaltuwa.
Na san Baban mu tun ina k'arama akan kud'in Baban mu ba abinda ba zai aikata ba koda akan dubu d'ari ne zai amince balle yaji million d'ari, " Na shiga uku" nace hawaye na ambaliya a fuskata.
Nafi minti 5 tsaye a wajan ina hawaye sannan na goge fuska ta da hijabi na,naja kafafu na da sukayi min nauyi zuwa cikin gida.
Allah ya so ni babu kowa a tsakar gidan duk suna d'akunan su sai hayaniyar su daya cika ko Ina kai tsaye na wuce d'akin mu, da sallama na shiga d'akin ban tadda Inna ba ina zaton ta zaga bayi ne.
Ban tsaya bata lokaci ba na haye gado na kwanta ko hijabin dake jikina ban cire ba gudun kada Inna tazo ta same ni cikin sabon tashin hankali dan ban san wani bayani zanyi mata ba.
Tunani na zurfafa a ciki na yanda rayuwa take neman juya min baya ina 'yar k'arama ta koda yake Allah ba bawan sa da baya jarabta babba ko karami mace ko namiji, ni na san ina cikin jarrabawan ubangiji nane, yau na dawo daga asibiti wanda tashin hankali yaja min kwanciya can kuma gashi yanzu ga wata fitinan da kwanciya asibitin ma ba zai min maganin ta ba.
Ina ji Inna ta shigo tana min magana nayi likimo kaman mai bacci saboda bana son ta tambaye ni waye yazo, jin wanene ko meya zo dashi babu abinda zai kara mata illah tashin hankali.
Addu'oin bacci tayi ta shafa nima ta shafa min ta kwanta a gefe na taja mana bargo ba tafi 15 mins da kwanciya ba naji tayi bacci, a zuciya ta nace Allah sarki Inna ta dana fad'a miki halin da nake ciki yanzu na tabbata da baki samu daman runtsawa ba.
Har karfe d'ayan dare tayi ido na babu alamun bacci, cikin tsand'a na sauka daga kan gadon na fita na d'auro alwala na fara kai kuka na ga Rabbil Izzatti shine kad'ai madogara na.
****************
Zafar har ya isa gida zuciyar shi bai bar tafasa ba har kaman shi wannan yarinyan zata dubi cikin idon shi ta fad'a mishi abinda taga dama " bull shit" yace yana dukan stairin shi da karfi kaman shi ya mishi lafin.
Yana zuwa gida kai tsaye part d'in iyayen shi ya wuce, a kofan parlour ya tsaya ya gyara fuskan shi kaman he is in good mood saboda baya so su fahimci halin da yake ciki.
Da sallama ya shiga parlour suna zaune suna kallon wa'azi a Sunna TV da Sheikh Aminu Daurawa da yake , amsa mishi sukayi duka ya karaso ya zauna kan lallausan rug dake parlour ya gaishe su suka amsa mishi cikin kulawa daga nan yaja bakin shi yayi shiru shima ya maida hankalin shi kan wa'azin.
Kusan mint 10 wa'azin ya kare dama yazo karshe , remote Abban shi ya d'auka ya rage volume d'in TV sannan ya kalli inda Zafar yake zaune yace;
"Ina ta zuba ido ka kawo min wacce kake so