Showing 36001 words to 39000 words out of 87059 words
lafiya.”
“Ameen ya Rabbi. Sai na dawo Mama.”
Sai da Mama ta raka ta har bakin hanya ta shiga dan sahu sannan ta dawo. Sarat ce ta turo mata msg kan cewa tana bakin kamfani, abinda ya baiwa Zahara mamaki kenan, ganin ga komai sai Sarat tazo latti. Amsa mata tayi da gata nan isowa nan da mintuna. Amma ba ita ta iso ba sai bayan rabin awa, domin lokacin kowane mutum ya fito neman na abinci. Koda ta isa, har motocin sun zo, nan ta hangi Mr. Ammar, Sarat, Hajiya Hassana da kuma mijin ta. Saidai babu alamun Kamal amma motar sa na nan. Da sauri ta biya Mai Dan sahu ta fiddo jakar ta. Koda Sarat ta tsinkayo ta, ta tinkari inda take.
“Haba Zahara, me zaki yi da wannan karamar jakar? Ciki kika sa duka kayan ki? Ni kananan akwatina biyu nazo da su. Ba wanda yasan me zai faru a cen.”
“Kwana biyu kawai zamu yi a cen Sarat. Kuma aiki ne zai kai mu.”
“Ke kike ganin haka, amma ni holewa zan je. Oya muje sauran har sun iso.”
Bin bayanta Zahara tayi, tana gaishe da wanda ta gamu da su.
“Kokarin kiran ki nake yanzu.” Mr. Ammar ya cewa Zahara. “Tinda kin zo zamu iya tafiya. Ku shiga nan.”
“Ibrahim, kai da Sarat zaku shiga mota ta. Hajiya Hasana da mijin ta zata tafi. Shi kuma Kamal zai biyo bayan mu shi da Afnan.”
Zahara taso tambayar Sarat inda Kamal yake, amma bata samu damar hakan ba. Koda suka shiga motar, Mr. Ammar yayi mata key. Motar su Hajiya Hasana na bayan tasu. Ibrahim na gaba shi da Kamal. Zahara da Sarat kuwa na baya suna ta hira. Ko ince Sarat na ta zuba, Zahara na sauraron ta ba tare da tace kala ba. Amma koda Sarat tace mata, hankalin Mr. Ammar take son jawowa kanta. Lokacin ne Zahara tayi magana.
“Yana da budurwa, ya kamata ki daina yin hakan.”
“Ji wata magana.. ke da kanki kika ce ina burge shi. Kuma ma doguwar rigar da ya bani har yanzu tana nan. Bansan wani wasan kwaikwayon yake yi ba, amma na tabba yana bukatar na dan tunzura shi.”
Zahara a ranta tace wannan ma aikin Amriya ne. Bata san me yasa tayi hakan ba, amma dole ita zata gyara kuskuren.
“Bansan me yasa na fada miki hakan ba, amma bana tunanin Mr. Ammar yana jin wani abu a kanki...” Zahara ta fada mata cikin rada dan kar su Ammar su jita.
“Toh me yasa zai mini kyautar wannan tsadaddiyar rigar? Dakata Zahara, bansan me kike nufi ba, amma ba zan saurare ki ba. Ina son yin soyayya ta gaske da shi, dan haka babu abinda zakk fada min, ki sani.”
“Kuskus din me kuke yi ne haka yan mata?” Cewar Ibrahim da sigar wasa.
“A'a ba komai, mun dai kagu mu kai ne.” Cewar Sarat.
“Ah na gani, kar dai a manta aiki ne zai kai mu.”
“Eh, mun sani.” Sarat ta sake fada.
Duk wannan lokacin Mr. Ammar bai ce ko kala ba. Da alamu yana cikin yanayin da ya shiga ne kwanan nan kuma Zahara bata daina tunanin abinda ya faru da budurwar shi ba. Kuma idan Sarat ta shigo cikin labarin, wani hargitsi zata sake haifarwa.
(.....)
“Ke..Zahara..!”
Zahara taji ana girgiza ta cikin bacci. Sai da ta dauki lokaci kafin ta farka daga baccin da take. Bata ma san lokacin da bacci ya dauke ta ba. Sarat ce a kanta tana kokarin tashe ta.
“Ki tashi mun kusa karasawa.”
“Mene..?” Zahara ta fada cikin yanayin bacci.
Tashi tayi daga jikin Sarat tana murza idanun ta dan ta gani da kyau. Gyara gyalen ta tayi, tana kokarin dawo da natsuwar ta.
“Zahara sai kace kasa." Cewar Ibrahim. “Kinsan kira nawa nayi miki dan ki tashi, amma kamar wacce tayi doguwar suma. Injin dai kin samu yin mafarki mai dadi?”
Murmushi kawai Zahara tayi ba tare da ta bashi amsa ba. A lokacin Mr. Ammar yana faka motar a bakin wani hostel. Kyakyawan wuri ne sosai, da ya dauki hankalin Zahara ta yanda bata jin duk wani sauti dake kewaye da ita. Kyan wurin yasa taji tana son daukar hoto. Da sauri ta fiddo wayar da Kamal ya ara mata ta shiga daukar wurin hotuna da video.”
“Wow Zahara, a ina kika samu wannan wayar? Mu gani.” Cewar Sarat tare da warce wayar daga hannun Zahara. Saidai cikin rashin sa'a wayar ta fadi kasa. Gaban Zahara ne ya fadi. Da sauri ta duka ta dauko wayar. Saidai wayar duk ta kwankwatse.
“Wayyo Allah.. I'm very sorry Zahara. Wlh ba da gangan nayi ba."
Wayar tana aiki duk da faduwar da tayi, saidai Zahara bata san ya zata yi wajen biyan mai wayar ba. Ko albashin ta na shekara guda ba zai isa ba.
“I'm very sorry. Dan Allah Zahara. In ga wayar.” Sarat fada.
Amma Zahara bata bata amsa ba, tayi gaba ba tare da tace komai ba. Tayi alkawarin kula da wannan wayar. Me zai ce game da ita kenan yanzu?
Su Hajiya Hasana suka karaso daidai lokacin. Mr. Ammar yayi wani waje sai gashi ya dawo bayan wasu mintuna. Ya fada musu ma'aikatan hotel din zasu zo su gwadawa kowa dakin da zai zauna. Zahara tayi tunanin zasu jira Kamal ne, amma Mr. Ammar bai ce komai ba. Dan haka suka wuce domin hutawa. Zahara santin kyawun wurin kawai take. Zuwan ta na farko kenan irin wannan kyakyawan wurin. Haka ma Sarat tana ta surutun ta game da kyan wurin. Koda suka karasa dakin da aka basu. Sarat tayi tsalle bisa gado.
“Wow wurin nan ba karamin kyau gare shi ba, da har ya fara sa ina jin wani yanayi. Yi tunani a ce ni matar Mr. Ammar ce? Ba bukatar sai nayi aiki, zan kasance kullum a makale da shi. Zan zama tauraruwa a kasar nan.”
Ba tare da Zahara ta tanka ta ba, ta cigaba
“Kina dage min kai ne saboda na fashe miki waya? Nace miki kiyi hakuri, to me kuma kike so?"
“Bar zancen Sarat." Zahara ta fada a sanyaye.
“Wa ya baki wayar? Ba irin wacce zaki iya siye da kudin ki bace, ki cewa wanda ya siya miki da ya gyara miki ko ya sauya miki."
Zahara bata ma san dalilin da yasa take sauraron duk wannan shirmen da Sarat take fada ba. Bathroom ta shiga tayi wanka. Sun samu kamar hutun awa biyu, kafin Mr. Ammar ya kira su domin suyi summarazing abinda zasu yi gobe. A wani private room suka hadu, kowa yazo banda Kamal da kanwar su.
Mr. Ammar ya fara magana, yayi musu bayanin abinda yake son yi da wanda su zasu yi.
Meeting din sai da kwashi kusan awa uku kafin su kare. Bayan nan, aka kawo musu abinci da abin sha.
Zahara ta mayar da hankali akan abinda aka zuba mata, lokacin da aka bude kofa. Tayi tunanin ko ma'aikatan hotel din ne, amma katuwar muryar Kamal tasa ta gane ba ma'aikatan bane. Shine da kanshi, a bayan ta shi da Afnan.
Afnan sai da ta zagaya table din ta gaishe da kowa kafin ta zauna kusa da dan uwan ta. Shi kuwa Kamal kusa da Zahara ya zauna, alhali table din babba ne kuma akwai wuraren zama. Zahara bata yi gangancin dago kai ba.
Mitsinar Zahara, Sarat tayi a kafa sannan ta rada mata a kunne
“Ina jin kanshin turaren sa har nan. Hadadden guy ne, naso in gwada da shi inda ba miskili bane.”
“Let me eat please.” Zahara tace mata.
“Ai sai kiyi ta yi.” Sarat ta fada tare da jan dan guntun tsaki.
Hira a wurin ta barke. Har Mr. Ammar da yake a kame sai gashi yana dan kokarin magana da Sarat, ita kuwa abinda take so kenan. Sai kuma Zahara da ta mayar da hankali kan plate din ta, ko ince tayi kamar hankalin ta na ga plate alhali duk a takure take ganin Kamal na kusa da ita, da shima ba magana yake ba sai sauraro.
Zuwa wani dan lokaci, Zahara taji kafar sa ta hade da tata. Dan zabura tayi, tare da bashi hakuri domin tayi tunanin ko ba da gangan yayi ba. Bai ce komai ba, ya shiga zubawa kanshi abinci. Lokacin da ya shafi hannun ta domin ya dauki gishiri, nan ta gane dazun ma da gangan yayi.
Abun sa fa ya fara yawa, Zahara har ta fara da nasanin sakar masa fuska. Yana tunanin ita irin yan matan nan ne? Sai yanzu take jin haushin amsar wayar shi da taimakon ta da yayi. Ta tabbatar tun ranar da ta kwana gidan shi, yake tunanin ita yarinya ce mai sauki kuma zai iya samun damar ko me yake so da ita. Dole ma ta taka masa birki tun kan yayi nisa.
“Please zamu iya yin magana?” Zahara ta tambaye shi ba tare ta bari sauran sun jiwo ta ba.
Da mamaki ya kalle ta kafin ya amince. Tashi tayi daga kujerar ta tare da neman uziri ga sauran. Fita tayi waje tana jiran shi. Bayan wasu yan mintuna shima ya fito.
Nufar wani lambu dake cikin hotel din tayi, yana biye da ita a baya. Kafin su karaso cikin lambu Zahara ta tattara duk wani kuzarin ta, amma koda ya kasance daga ita sai shi sai duk kuzarin ya bace. Shi kuwa kallon ta yake da dan guntun murmushin sa. Zahara kuwa takaici ne na rashin tattaro kalaman da zata yi amfani da su wajen bayyana masa abinda take ji.
Yanke shawarar ta fara da mai muhimmanci tayi. Ta ciro fasashiyar wayar shi ta miko masa.
“Na kayar da ita ba da gangan ba amma zan biya ka. Ina son ka fada min nawa ne screen din ta yake, zan yi iya kokari na ganin na gyara maka ita.”
Kallon wayar yayi kafin ya kalle ta.
“Kin samu wata sabuwar wayar ne?” Ya tambaye ta ba tare da ya karbi wayar ba.
“No, but I don't need your help anymore. Ina jin kana tunanin ni yarinya ce mai sauki, wacce zaka iya yin yanda kake so da ita. A shekaru ka girme mini, amma ba hakan ya nuna zaka juya ni ba ta sauki. Idan saboda na kwana a gidan ka ne kuma ka taimaka min shi yasa kake min haka, toh ka sani ba dan naso hakan ta faru ba. Abinda ya faru a daren nan, babu inda zan je ne da ya wuce wajen ka. Kuma ma zai iya yiyuwa baka yarda da labarin da na baka game da Amriya ba...”
[03/03 à 05:18] ASHTAR: AMRIYA
(Hatsabibiyar Aljana)
Love 💞 and Horror ☠️ story 📖
By Malik al-Ashtar 🖋
For more novels https://bit.ly/3Egdy1m
On wattpad : https://www.wattpad.com/story/270492485
CHAPTER 14
⚖ HOME OF QUALITIE'S WRITERS ASSOCIATION 📚
“Ki daina motsowa haba Zahara, idan baki jin bacci. Zaki iya tashi ki samu wani abun kiyi.” Cewar Sarat cikin muryar bacci.
Tana da gaskiya, Zahara ta kasa daina juyi bisa gado, tun lokacin da suka kwanta. Ta yaya zata iya bacci? Bayan abinda ya fada mata. A lokacin shishigin Sarat ne ya kwace ta. Tazo a daidai lokacin da Kamal yace yana son ya auri Zahara.
Zahara taji kamar ta kurma ihu domin ya fitar da ita daga yanayin da take ciki. A lokacin bata san me zata yi ba, ko amsar da zata bashi. Juyawa tayi, tayi tafiyar ta ba tare da tace dashi komai ba, saidai koda suka koma daki ta fara jin haushin kanta na kin tsayawa. Domin akwai akwai tambayoyi da dama da take son amsoshin su.
A lokacin hanyar daga lambun hotel din zuwa dakin da suka sauka, ba karamin tsayi yayi mata ba. Domin tasan idanun Kamal na kanta ga kuma tarin tambayoyin da Sarat take mata.
“Soyayya kuke? Amma munafuka ce ke Zahara !! Bani labari, ta yaya kuka fara soyayya ??”
“Stop please.” Zahara ta fada da sa ran ko Sarat zata yi shuru amma kamar ta manta wacece Sarat.
“Kin hanani kutsa kaina gurin Boss, ashe ke da yayan shi kike soyayya. Amma kar ki damu na fahimce ki, ba wanda zai iya tsallake charm din su. Abun mamakin, yanda kika yi, kika iya shiga wurin shi, duk da miskilancin sa. Come on Zahara, fada mini meye sirrin?”
Haka Sarat tayi ta maganganun ta, ba tare da Zahara ta tanka ta ba, dolen ta tayi shuru da ta gaji. Zahara na tunanin ma Sarat fushi tayi, amma ita wannan ba shi bane a gaban ta.
“Zahara kina takura min, kin hana ni bacci.” Sarat ta sake maimaitawa alhali ita Zahara juwa kwanciyar ta ne tayi wannan karon ba tare da tayi wani kwakwaran motsi ba.
Tashi Zahara tayi daga kan gadon, ta fito ta kofar bayan hotel din. Sanyin da ake dan rurawa yayi mata dadi. Nadamar kin zuwa da Kur'anin ta take. Domin ta lura lokaci ne mai kyau yanzu na karatu da nazari. Idan da tayi hakan kuwa, da ta samu dan sauki har ta iya yanke shawara mai kyau. Domin a halin yanzu, a cikin confusion take. Ta yaya zai iya zuwa a gaban ta yace yana son ya aure ta, alhali basu wani san juna ba. Wannan hujja ce da ke nuna ya dauke ta sakarya, yana tunanin zata yarda da wannan shirmen? Ita kuma yanzu take kara jin haushin kanta, na da bata jefa masa wayar shi ba.
“Kema kin kasa baccin koh?”
Muryar Mr. Ammar ce ta dawo da ita daga duniyar tunani. Yana zaune bisa daya daga bencinan dake cikin lambun hotel din. Tayi nisa sosai a cikin tunanin har yasa bata lura da shi ba a wurin. Murmushi tayi masa, amma babu tabbacin yaga murmushin da yake akwai dan duhu a wurin.
“Ko zaki taya ni zama ne?” Ya tambaye ta.
Bata yi gardama ba taje ta zauna kusa da shi. Hirar aiki suka fara, hakan kuwa yasa ta dan manta halin da take ciki shima haka domin ya nuna mata bayan wasu mintuna.
“Ban yi tunanin haka ba, amma hirar aiki da muke yi a wannan lokacin ya dan yaye mini damuwar da nake ciki.”
“Nima hakan.” Cewar Zahara.
“Da gaske?” Ya fada. “Wani abu na damun ki ne?”
Ba zata iya fada masa abinda ke faruwa tsakanin ta da dan uwan sa ba.
“Dalilin brother na ne koh?” Ya tambaye ta.
Ta yaya ya sani? Yanda ta waro idanu cike da mamaki ne ya bashi dariya. Sai da yayi dariya mai isar sa kafin yace
“Idan da kinga yanda fuskar ki tayi, da sai cikin ki yayi ciwo dan dariya.”
“Ta yaya.. yaya aka yi kasan da wannan zancen?”
“Shi ya fada min.” Ya fada da dan murmushi.
Zahara ta rasa me zata yi tsabar kunyar sa da ta kama ta.
“Baki da damuwa akan wannan, ba zan takurawa rayuwar ku ba. Kawai dai kin dan tashi hankalin ki ne, shi kuwa brother na wannan ne karon farko da naga ya kula budurwa.”
Sunkuyar da kai kawai ta iya yi, domin bata san amsar da zata bashi ba.
“Yayi min bayanin shakkun da kike da game da gaskiyar abinda ya fada miki. Ba wani kwararre bane shi a wannan fannin amma ina tabbatar miki ba zai bayyana miki hakan ba idan ba gaske yake ba. Ban kuma ce kiyi saurin yarda da shi ba, ba tare da kin samarwa kanki amsoshin tambayoyin ki ba. Dan uwa na ne shi, amma ba hakan zai sa na bari ya cutar da ke ba. Idan akwai matsala, ni ne na farko da zan nesanta ki da shi.”
“Ba fa soyayya muke ba... kuma bani da tabbacin irin hakan zata faru a tsakanin mu.”
Dariya Mr. Ammar yayi.
“Ok, kar dai ki tursasa kanki kan abinda baki da ra'ayin shi. Ki fada masa gaskiyar baki bukatar kasancewa da shi, idan da gaske hakan ne a ranki.”
Matsalar ba wai Zahara bace, saidai shi Kamal din. Ba wai bata son shi bane, kawai bata san ko zata iya yarda da shi bane, ta shiga, kai kasa ko a'a. Tana tsoron shiga fagen da bata da masaniya, ta fara soyayyar da zata da ita. Tana da rauni a wannan fannin, cin amana ko rabuwa ta bazata, suna iya yi mata illar da zata iya rasa ranta. Amma idan da gaske auren ta yake son yi? Shin ya dace ta amince? Tana son amincewa, domin addinin ta yayi mata hani kan duk wata alaka da saurayi kafin aure. Idan da gaske yana son auren ta, kamata yayi su samu lokaci su san juna kafin auren.
“Kar ki takura kanki.” Cewar Ammar. “Har yanzu kina da lokaci a gaban ki. Kiyi abinda kike ganin daidai ne. Kar kiyi abubuwan da kika san zaki zo kina dana sani. Ni gani nan... Ban ma san ko zan iya auren matar da nake so ba. Amma ba zan yi kasa a gwiwa ba, zan yi iya kokari na ganin ban yi nadama ba a rayuwa ta. Kuma koda wata rana, ya tabbata na rasa ta. Toh zan san na fafata da iya jiki da ruhi na a kanta.”
Zahara a ranta tace, mai yiyuwa wannan shine lokacin da zata fada masa abinda ya faru. Amma ko hakan zai canza wani abu? Ko ba komai ta samu salama da zuciyar ta amma bata tunanin zai fahimci zancen. Ko kuma kamata yayi ta karfafa masa gwiwa wajen ganin ya dawo da masoyiyar sa.
“Mahaifiya ta na son na auri yar kawar ta domin wani buri nasu na daban...”
“Ban sani ba ko... ya dace na shiga abinda ba ruwa na. Amma ina ganin rayuwar ka ce, ya kamata kayi fada domin wacce kake so. Kayi duk wani abinda ya dace na ganin ka dawo da ita. Na tabbatar ita ma abinda take so kenan.”
Murmushi yayi, murmushi da bai kai zuciya ba.
“A halin yanzu ba wanda ta tsana kama ta.”
“Ina ganin kawai tana cikin bacin rai ne. Bansan komai ba game da hakan amma ina tunanin ba zai yiwu mu iya tsanar wanda muka ce muna so na tsawon shekaru ba, koda wannan mutumin ya cutar da mu. Tana kokarin ta tilasta kanta ne akan ta tsane ka domin yayewa kanta damuwar da take ciki, amma karya kawai take wa kanta. Kayi fada kuma kar kayi nadamar hakan. Kayi iya kokarin ka na ganin ka shawo kan mahaifiyar ka. Ka fahimtar da ita cewa kaima cikakken mutum ne, mai buri da ganin ya gina rayuwar sa mai kyau. Domin kowace mahaifiya farin cikin danta shine nata, tana tunanin wacce ta zaba maka ita ta dace da kai. Amma kaima ka nuna mata, baka yi zaban banza ba. Dukan mu mutane ne, kuma muna