Showing 54001 words to 57000 words out of 87059 words

Chapter 19 - AMRIYA HATSABIBIYAR ALJANA

Start ads

Ashar   

11 Aug 2025

419

Middle Ads

ta samu sukuni da zuciyar ta.

Afnan tambayar kanta take, me Rakiya zata fada da yafi wannan muhimmanci.

“Ok, ina sauraron ki. Zo ki zauna.” Cewar Mommy.

Rakiya bata zauna ba, ta fara magana
“Na kasa hana kaina daga jin maganar da kuke yi, Hajiya kar kice na miki rashin kunya amma kinyi kuskure na ganin laifin Afnan...”

Afnan ba zata iya barin Rakiya ta fadi abinda take son fada ba.

“RAKIYA WANNAN BA ABINDA YA SHAFE KI BANE!”

“Fyade aka mata.” Rakiya ta fada.

Da sauri Hajiya Karima ta mike tsaye.

“Me kika ce?”

“A nan gidan hakan ke faruwa, tsawon shekaru.”

“RAKIYA IDAN KIKA SAKE FADAR WATA KALMA .." Cewar Afnan cikin tashin hankali.

“RUFEWA MUTANE BAKI.” Hajiya Karima ta dakawa Afnan tsawa.

Wannan ne karon farko da Hajiya Karima ta daga mata murya. Saidai Afnan ko a jikinta, abinda take so shine ta hana Rakiya magana.

“Ke kuma ina jinki, me kike son cewa ne?" Cewar Hajiya Karima ga Rakiya.

“Da farko, na dauka su biyun suna cin amanar ki ne amma daga karshe na gane yana tursasa ta ne yin abinda bata so. Naji tsoron fadar gaskiya kuma itama naga alamun tana tsoron tona masa asiri amma yanzu tunda hakan ta kasance ba zan iya rike bakina ba.”

“Wanene? Ammar? In dai shi ne ban yi mamaki ba !"

“Rakiya.. ki yiwa girman Allah.. kar ki yi haka. Kada ki bata mana rayuwa.” Cewar Afnan amma Rakiya bata da alamun yin shuru.

“Alhaji ne mijin ki.”

Dariya Hajiya Karima ta fara.. sosai take dariya ta yanda ta kasa tsayar da kanta.

“Kenan, bayan kin je kin gamo karuwancin ki waje, shine zaki zo ki sharracin mijina akan fyade ko? Kuma babban abun shine har da saka Rakiya cikin makircin ki. Lallai yarinya, bansan irin wannan sakayyar zan samu ga rikon ki ba. Bayan duk abinda nayi miki, bayan duk abinda shi yayi miki ki samu karfin halin zuwa ki ce min mijina yayi miki fyade."

“Mommy ni ban ce miki haka ba, kuma bansan dalilin da yasa Rakiya tace haka ba amma wallahi karya take."

“Kina tunanin Rakiya zata zo tayi wannan karyar ne ba tareda kin ce tayi ba?"

“Please Mommy ki yarda da ni, ban ce Rakiya tayi wani abu ba. Laifi na ne, ni naje waje nayi iskanci na kuma ga sakamakon da na samu. Ki yafe mini Mommy.”

Afnan sai rusar kuka take durkushe rike da kafar Mommy. Bata yi tunanin lamarin zai kwabe haka ba, a tsorace take sosai. Abinda take gudu shi yake shirin faruwa.

“Ki fice min daga gida Afnan, daga yau ni ba mahaifiyar ki bace. INA SON DUKA KU BIYUN KU BAR MIN GIDA."

“Ke Afnan, yau zaki koma gun asalin mahaifiyar ki, wata kila ita zata iya renon shegen da kike dauke dashi. Bayan duk abinda nayi miki : na kula da ke, na soki kamar yar da na haifa a cikina.. ke kuma ki rasa da me zaki saka min, sai ki shiryo wannan bakin sharrin dan ki raba min ahali. Wane buri kike son cimma? Me kike so? A baki kudi dan kiyi shuru? Na kasa fahimta..."

“Kar ki guje ni Mommy.. wallahi duk wannan ba gaskiya bane."

Kafa Hajiya Karima tasa ta ingije Afnan ta fadi kasa kafin ta bar falon tareda bangaje Rakiya. Da gudu Rakiya ta nufi Afnan da niyyar taimaka mata amma Afnan ta hana ta taba ta.

“Na sani ba wanda zai yarda da ni, shi yasa na bar sirrin a zuciya ta domin kare mutuncin wannan gidan amma gashi ke kin zo kin wargaza komai. Kin bata min rayuwa. Rakiya, da kin kyale ni naji da lamarin da kaina, Mommy zata ji haushi na ne amma ba zata taba korata ba. Amma yanzu.. kowa zai tsane ni, yan uwana.. kin raba ni da sauran farincikin da ya rage min.”

“Yanzu ne zaki samu yancin ki Afnan, nasan ba hurumi na bane kuma nayi katsalandan amma bana nadamar yin hakan. Ba wanda ya cancanci irin rayuwar da kika yi, ba zan iya bari su bata miki suna akan laifin da ba kece sila ba. Ki bata lokaci zata fahimta ko ba dade ko ba jima, idan ta cigaba da rufe ido akan laifin mijinta to bata cancanci zama mahaifiyar ki bane."

“BA KECE ZAKI FADA MIN WACCE TA CANCANCI ZAMA MAHAIFIYA TA BA. BA KECE ZAKI FADA MIN ABINDA YAKE MAI KYAU DA MARAR KYAU BA GARE NI. NAGODE DA RUGUJE MIN RAYUWA DA KIKA YI RAKIYA. KI RABU DA NI YANZU.”

Ba tareda ta sake jin kalma daya ba ta Rakiya, Afnan ta tashi tayi shigewarta daki. Rakiya tayi kokarin zuwa ta ga Hajiya Karima dan ta kara yi mata bayani amma bata ganta ba. Dakin Afnan ta nufa domin sake yi mata magana da kuma kokarin kara shawo kanta akan ta tsaya ta kwato yancin ta.

Koda ta karaso kofar dakin Afnan, tayi ta knocking amma Afnan bata bude ba. Hankalin ta ne ya tashi, ta shiga kwala kiran sunan Afnan amma bata amsa ba. Da iya karfin ta ta shiga dukan kofar har daga karshe ta bude. Saidai abinda ta gani ya sanya ta mutuwar tsaye. Afnan ta gani kwance hannun ta cikin jini, ta yanka hannun ta da reza. Kuma bata motsi.


(....)


A wannan rana, Khadija ta gaji da shariyar da Kamal yake mata. Tana kiran shi, tana tura masa da texte amma baya amsa mata. Dan haka ta yanke shawarar zuwa ta ganshi. Wajen karfe hudu taje gidan sa, tayi ta knocking amma bai bude ba. Tayi alkawarin ba zata bar wurin ba in har bata ga Kamal ba. Bayan wasu mintuna, taji sawun tafiya. Kamal ne ya bude kofa nan ta fahimci dalilin da yasa bai daukar wayarta.

Da alamu baida lafiya sosai domin tsayuwa ma bai iya yi da kyau, labbansa sun yi fari kal kuma idanun sa kamar zasu fito daga gurbin su. Hankalin Khadija ne ya tashi...

“Subhanallahi ! Me yake damun ka?” Ta tambaye shi tana shigowa da sauri cikin gidan. Rufe kofar tayi sannan ta taimaka masa dan tsayuwa duk da girma da nauyin shi. Bai ce komai ba ya barta ta taimaka mashi. Daki Khadija ta kaishi ta taimaka masa ya kwanta. Jan bargo Kamal yayi, ya rufe jikin sa.

“Tun yaushe kake rashin lafiya? Me yasa baka fada min ba?"

Bata jira jin amsar shi ba, ta ajiye jakar ta ta shiga kitchen neman basin na ruwa. Daya daga cikin towels din sa ta dauka ta jika, ta dora masa a kai domin rage zafin zazzabin da ke gare shi.

Ba a dau lokaci ba, Kamal yayi bacci. Kusa da shi ta tsaya har lokacin da ya farka. Da alamu yaji dan sauki.

“Kana jin yunwa ne?” Ta tambaye shi.

Gyada mata kai yayi.

Porridge ta hada masa sannan ta taimaka masa ya ci. Koda taga da alamun yaji sauki, ta fara magana
“Me yasa baka kira ni ba?”

“Ba wani abu bane babba.” Ya bata amsa. “Kawai yar gajiya ce.”

“Eh amma da ka kira ni lokacin da ka fara jin ciwo, da nazo kuma na raka ka asibiti.”

“Gaki nan ai.. kuma yanzun ma taimako na kike. Gashi har naji sauki.”

“Eh amma me zai faru idan da ban zo ba? Nasan da ka kira ni idan da bamu samu matsala ba a baya, nazo ne na fada maka na amince da abinda ka yanke. Ina son ka kasance cikin farin ciki kai da Zahara, nasan matsayi na. Nasan mu biyu babu komai tsakanin mu bayan abota.. dan haka ina son komai ya dawo kamar baya. Ka min alkawari.."

“Nayi miki alkawari." Kamal ya bata amsa.

“Yauwa, yanzu ina son ka shirya zamu je asibiti."

“Mene? Na fada miki na samu sauki. Bana son zuwa asibitin nan."

“Ba ruwa na.” Cewar Khadija. “Duk da haka sai mun je domin kara tabbatarwa."

Yayin da Khadija ke kokarin shawo kan Kamal domin su je asibiti, a bangaren Zahara na tunanin me yasa Kamal ya daina kula ta. Tayi kewar shi sosai ta yanda ko aiki ta kasa yi da kyau. Dan haka ta yanke shawarar zuwa ganin shi idan ta tashi daga aiki domin ko a waya bata samun shi. Ba halin sa bane bacewa na tsawon makonni babu labari. Har saida ta fara tunanin idan ba yayi niyyar raina mata hankali bane. Kuma ya ki kiranta ne saboda ya gaji da ita. Saidai da sauri ta kawar da wannan tunanin daga zuciyar ta, domin kullum Kamal cikin tabbatar mata yake. Bai dace ta dinga bari irin wannan tunanin na zo mata ba.

Tana sauka daga aiki, ta tsayar da dan sahu domin zuwa ganin Kamal. Tana zuwa kofar gidan, tayi knocking. Murmushi take har kunne duk da damuwar da take ciki, da kaguwar son ganin sa.

Saidai a maimakon Kamal wata matashiyar mata ce ta bude mata.. kyakyawar mata. Zahara tambayar kanta take wacece wannan kuma me take yi nan.

“Ah Zahara, kina lafiya?”

Ya aka yi ta sanni? Cewar Zahara a zuciyar ta.

“Lafiya lau.” Duk da haka ta amsa mata cikin ladabi.

“Kamal kike nema? Yana ciki, zaki iya shigowa. Daman shirin tafiya nake, shi ne ya kira ni bai dan jin dadi jikin sa ne. Ayya na cika ki da surutu, ni sunana Khadija, ni best friend din sa ce.”

Zahara ji tayi kishi ya turnuke ta, tana cen tana ta damuwa, bai yi komai ba dan ganin yanda take, bai ko kirata ba dan ta taimaka masa amma yana da karfin jiki da lokacin da zai dauki waya ya kira wannan yarinyar.

Dogon numfashi ta ja kafin ta tuna wautar ta ta tsayawa kishi alhali Kamal baida lafiya.

“Ya jikin nasa?” Zahara ta tambaye ta.

“Da sauki, kar ki damu na kula da shi da kyau har ya samu sauki. Ba zaki shigo ba?”

Zahara nunawa tayi bata lura da murmushin munafuncin da matar ke mata ba. Bata ma san ina tasan sunan ta ba.

“Nasan Kamal yayi mata zance na, wata kila tare suke zaunawa suna min dariya." Wani bangare dake cunkushe da kishi na zuciyar ta ne ke rada mata hakan.

Iya kokari take ganin ta boye damuwar ta, amma ga banza domin duk wanda ya kalle ta zai gane tsantsar kishi shimfide a fuskar ta.

“Ba zaki shigo ba?” Khadija ta sake maimaitawa.

“A'a." Cewar Zahara. “Gida zan wuce.”

“Ok, zan fada masa kin biyo. Na tabbatar zai kira.."

Ba tareda ta jira jin sauran abinda Khadija zata fada ba, Zahara ta juya tayi tafiyar ta.


[03/03 à 05:18] ASHTAR: AMRIYA
(Hatsabibiyar Aljana)

Love 💞 and Horror ☠️ story 📖

By Malik al-Ashtar 🖋

For more novels https://bit.ly/3Egdy1m

On wattpad : https://www.wattpad.com/story/270492485

CHAPTER 21

⚖ HOME OF QUALITIE'S WRITERS ASSOCIATION 📚


Komawa Khadija tayi ciki tana murmushi tare da tambayar Kamal ko zata kara tsayawa domin taya shi hira.

“Waye yazo?” Kamal ya tambaye ta.

“Zahara ce.”

Da mamaki Kamal ya kalle ta jin Zahara tazo har gida neman shi. Gashi daman ya jima rabon shi da ita sakamakon halin da gidan su yake ciki ga kuma zanen da wani kamfani na kasar Malaysia suka bashi da zai gama shi da gaggawa. Ga kuma rashin lafiyar da yake fama da ita kwana biyu. Yayi kewar ta sosai, yana da tunanin da ya samu sauki yaje gidan su. Sai gashi cikin sa'a tazo, ba karamin dadi yaji ba.

“Tana ina? Ce mata ta shigo."

“A'a tayi tafiyar ta."

“Kamar ya ta tafi?”

“Na fada mata kana nan kuma tana iya shigowa amma tace min wucewa zata yi. Nasan ko sauri take.”

“A'a, ba gaskiya bane abinda kike fada. Idan da tana sauri ne ba zata zo nan ba. Kuma koda tazo nan ba zata ki shigowa ba. Me kika ce mata?”

“A'a komai kawai nace mata baka da lafiya ne kuma ni ke kula da kai.”

“Me kake yi haka? Me yasa ka tashi?” Ta tambaye shi tana mai nufo shi da sauri shi kuwa yana kokarin sauka daga bisa gadon da kyar.

“Tambayar ka nake, ina zaka je?”

“Zan je na ganta ne, na tabbatar tayi wani tunani ne a kanmu.”.

“Kamar ya tayi wani tunani, bata yarda da kai bane ko me? Baka da karfin jikin da zaka fita yanzu, ka kira ta wani lokacin sai ka yi mata bayanin babu wani abu tsakanin mu. Ni zan iya zuwa na ganta saboda kai.”

“No, kar ki damu nafi son naje da kaina.”

Cikin wardrobe din sa ya bincika ya dauko bakin jeans da t-shirt ita ma baka. Duk da yana jin babu kwari jikin sa amma dole sai yaje domin baya son Zahara tayi wani tunani. Haka Zahara take, dandanan karamin abu ya juya mata tunani. Ya fada a ransa. Baya son tayi tunanin yana wasa da hankalin ta ne idan ba haka ba zai sha wuya kafin ya sake samun yardar ta. Sai da aka dauki lokaci sosai kafin ta fara sakewa da shi. Ba zai so ya rasa komai ba saboda yar karamar rashin fahimta.

“Toh ni zan tuka ka, please kar ka tafi a haka. Zan damu.”

“Da gaske kina son taimaka min?" Ya tambaye ta.

“Yes of course, ni fa na tambaye ka."

“Ki kula min gidan, ba zan jima ba zan dawo. Nayi miki alkawari.”

“Amma.."

“Please kar ki ce komai, ba jimawa ba zan yi.”

Ya fada kafin ya saka takalmin sa. Duk da abinda yace mata sai da ta taimaka masa ya shiga mota. Tayar da motar yayi da tabbacin Zahara gida ta wuce. Wajen karfe tara ne na dare, baya tunanin tana wajen aiki. Duk da haka yayi kokarin kiran ta a waya amma tana ta ringing ba'a daga ba. Kuma ya tabbatar da gangan taki daga kiran.

Yasan hakan zata faru. Ba zai ga laifin ta ba. Har yanzu akwai kuruciya a tattare da ita, idan tasa abu a kanta yana wahala a iya canza mata ra'ayi. Hakan yana dan bata masa rai amma yana iya kokarin sa ganin ya fahimce ta.

Yarinya ce kyakyawa da hankali amma tana da karancin yarda. Tana tsoron kar ace yana tare da ita ne kawai dan yayi wasa da hankalin ta domin tana ganin bata kai ajin da zai yi soyayya da ita ba kuma zai iya samun wata fiye da ita. Ba wai ita ce ta fada masa ba, shi da kan sa ne ya karance ta.

Yana kusan kaiwa gidan su, ya sake kiranta domin ta fito amma bata daga ba. Gashi kuma ba zai iya shiga gidan su ba a wannan lokacin, domin zai iya kara hassala ta. Daga karshe yanke shawarar yi mata text yayi.

“Slm Zahara, ina kofar gidan ku. Ina son ganin ki dan muyi magana. Bani da lafiya amma zan jira kofar gidan ku har lokacin da kika ji kina son fitowa ki ganni.”

Tura mata msg din yayi, bayan wasu yan mintuna aka nuna masa ta buda amma babu alamar fitowar ta. Ya fahimci lallai tayi fushi sosai, ya yanke shawarar sake tura mata wani text.

“Nasan abubuwa da dama na yi miki yawo a kai, ki zo ni zan miki bayanin komai. Bana son barin ki a duhu.”

“Idan baki zo ba, ni zan shigo cikin gidan naku."

Bayan kamar mintuna biyu sai gata ta maido masa.
“Gani nan zuwa."

Bai ji dadin barazanar shigowa gidan su da yayi mata ba amma ita ta ja, kuma hakan yayi aiki domin bayan wasu mintuna ta sake yi masa Text tana tambayar sa inda yake. Fada mata yayi wurin da yayi parking. Bayan wasu mintuna sai gata tazo.

Bude kofar motar tayi, bayan ta shigo ta maida murfin motar ta rufe da karfi. Bata taba yin irin haka ba.

“Ina wuni?” Tace masa.

“Me yasa kika tafi?" Ya tambaye ta kai tsaye.

“Babu wani dalilin zuwa na cen."

“Toh kenan kin je ne dan ki ga kofar gidan ki dawo?”

“Bakuwa na tarar gare ka, bana son takura maka ne.” Ta fada da kaushin muryar da ya fara tunanin anya kuwa Zahara ce


“Wa ya fada miki ina son bakuntar ta? Nafi son taki sau dubu."


“Amma ai kai ka kirata. Ina nan tsawon weeks babu labari kuma ace bakada lafiya amma shi ne ita ka kira.”

“Da farko, da farko dai ba ni na kira ta ba. Sannan abinda yasa kika ji ni shuru ayyuka ne suka min yawa, ta yanda baki tsammani. Sannan wata matsala da ta taso a family na ga kuma kaina kamar zaya fashe. Amma na rantse miki kullum cikin tunanin ki nake. Sannan kinsan adadin yanda kike da muhimmanci gare ni, har abada ba zaki taba takura min ba...Naso ace kin zo kin ganni na tabbatar hakan zai mini dadi.”

“Toh amma wannan matar tace min...”

Katse ta yayi.

“We don't care about what she said. Ki daina sauraron abinda mutane ke cewa Zahara, ba zai kawo miki komai ba na alkhairi. Wannan matar friend ce kawai, a koda yaushe tana nan domin ni amma babu komai bayan wannan.”

“Kalle ni nan Zahara." Yace da ita.

A hankali ta juyo ta kalle shi.

“Yaushe zaki fahimci adadin yanda nake jin ki a zuciya ta? Idan da wani ne ba zan zo nan ba, bani da lafiya sosai Zahara Kuma bana tunanin zan iya mayar da kaina gida yanzu.”

“Na cika son kaina da yawa. Mugun kishi ya rufe ni har yasa ban damu da halin da kake ciki ba. I'm really sorry, ban yi tunani bane.”

“That's my Zahara ! "
Murmushi tayi tare da sunkuyar da kai.

“Ya jikin naka? Me yake damun ka yanzu?”

“Ni ban ma sani ba. Ina da zazzabi kuma ga matsananciyar gajiya amma duk wannan bashi ne gabana ba, abinda nake so shine ki yarda da ni, ko me zai faru ina so ki kira ni ko ki zo ki ganni muyi magana domin ba yara bane mu.”

“Ina son nima ka dinga fada min matsalolin ka, ka dinga neman shawara ta. Yayin da kuma ba zan iya nemar maka mafita ba, zan kasance ko dan na saurare ka.” Ta fada mishi ba tareda ta sauke idanunta ba.

Murmushi Kamal yayi ganin sun daidaita wannan matsalar, kuma yana ganin takun farko ne na alakar su. Yana son yarda ta shiga tsakanin su mai karfi kafin ta amince ta aure shi. Daman ya riga da ya fada mata ranar da taji ta amince da shi, zai zo ya nemi auren ta.

“I'm really happy Zahara..idan da kin sani. Nayi tsoron ki nade kanki kuma ki daina yarda da ni.” Ya fada yana mai kara matsowa inda take.

“Nima nayi farin ciki da muka daidaita hakan, da ba zan iya bacci ba yau." Ta fada a takure ganin yanda yake kusa da ita sosai.

Da murmushi a fuskar sa, ya shiga matso da kanshi zuwa nata, hankalin sa na kan kyawawan lips din ta. Ya daina

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login