Showing 66001 words to 69000 words out of 87059 words

Chapter 23 - AMRIYA HATSABIBIYAR ALJANA

Start ads

Ashar   

11 Aug 2025

423

Middle Ads

naso kar na sake tako ƙafata cikin gidan nan.” Cewar Ammar.

Daddy da tun dazu yayi nisa cikin tunani yace
“Ɗanki ne ke zargi na da aikata wani abu marar dadin faɗa, har kunya nake ji na furta hakan.”

“Afnan, kin rantse sai kin wargaza min iyali ko? Bayan kin je kin yi karuwancin ki waje shine kike son ni ki zo bata min sunan ahali ko? Me na faɗa miki a baya?”

“Kin san da zancen kenan?” Cewar Ammar da mamaki. “Kuma shine baki ce komai ba?”

“Saboda ƙarya take, kawai tana son wanke kanta ne ta hanyar ɓata nawa gidan. Ba zan yarda da wannan ba!” Cewar Mommy.

“Wai meke faruwa ne?” Kamal ya tambaya da muryarsa ta marasa lafiya.

“Ba komai ɗana, bari na sa nurse ya kai ka tsohon ɗakinka domin ka huta.” Cewar mahaifiyar tasu.

“Ba komai? Wannan mutumin da muke kallo a mahaifinmu shi ya yiwa Afnan fyaɗe.”

Da farko Kamal bai fahimci komai ba, amma da maganar ta rasa illahirin ƙwalwarsa, waro idanu yayi ya kalli Daddy ya kalli Ammar.

“Rufe min baki.” Cewar Hajiya Karima. “Kar na sake jin ka ƙara faɗar irin wannan shirmen ƙanzon ƙuregen da bakinka."

Afnan ɓoye fuskarta tayi da tafin hannuwanta a bayan Ammar. Shi kuwa Daddy gefe yake kallo ba tareda ɗaya daga cikinsu ya canki abinda yake tunani ba.

“Tsaya Ammar. Wannan fa ba ƙaramar magana bace. Na kasa fahimta, kayi min bayanin abinda ya faru.” Cewar Kamal.

Ammar ya fara bashi labarin duk abinda ya sani da kuma yanda yayi ya gane gaskiya. Lokacin da ya ƙare, Kamal ya kalli Afnan yace
“Afnan, dagaske ne abinda ya faɗa?”

Afnan bata ce komai ba na tsawon wasu mintuna.

“Dagaske ne abinda ya faɗa?” Kamal ya ƙara tambayar ta wannan karon gyaɗa kai tayi alamar eh.

Kunya ce sosai ta lulluɓe Kamal ya rasa me zai yi. Wannan ne na farko da yaji kunya na kasancewar shi ɗan wannan mutumin. Ya tabbatar da gaskiyar Afnan da Ammar, yana jin ina ma ace mafarki yake.

“Barin wannan maciya amanar zaka yi su zubar maka da mutunci?” Hajiya Karima ta juya kan mijinta da yayi shuru bai ce komai ba.

“Shikenan a ɗauka da gaske ne abinda ta faɗa, ina son ganin hujjoji. Idan naga hujjojin cewar mijina ne ya yiwa yarinyar nan fyaɗe ni da kaina zan kai ƙararshi."

“Bama bukatar nuna miki hujjah idan baki yarda ba shikenan. Bana bukatar taimakonki wajen yin wani abu. Amma jin cewa kinsan da wannan zancen baki faɗa mana komai ba na gane kin wuce yanda nake tunani. Koda na fahimci kin ƙirƙiri wani labari kawai dan ki kare daddy naji ina son barin gidan nan, na ƙara yin nesa da shi. Kuma ina son ku saurari sammacin kotu."

“Shikenan...” Cewar Daddy da ya dawo hayyacinsa.

“Ban gane shikenan ba? ƙoƙarin wargaza mu fa yake kuma kasan kamfanoni zasu durƙushe.” Cewar Mommy.
Ta ƙara da cewa
“Ina guje maka ranar da zaka san ainihin wacece wannan yarinyar, ranar zaka yi baƙin ciki. Zaka yi nadamar yiwa mahaifinka sharri da kuma juya mana baya da kayi. Kayi nadamar yarda da maganar wannan makirar, rayuwarka ta zama babu komai sai wahala..”

“Wahala ce a rayuwata tun lokacin da na gane abinda iyayena ke iya aikatawa, bana tunanin akwai wani baƙin ciki da yafi wannan. Ina fata adalci yayi halinsa."

“Ina fatan haka nima.." Daddy ya faɗa cen ƙasan maƙoshi. “Zan yi iya ƙoƙarina wajen dawo da mutuncina da ka zubar na yimin wannan mummunan sharrin. Ke kuma Afnan bansan me nayi miki ba da zaki saka min ta wannan hanyar. Bansan cewa sakamakon da zan samu na zamar miki uba da nayi ba shine sharrin fyaɗe.” Ya fada da ƙaramar murya ba tareda ya kalli kowanne daga cikinsu ba.

“Babu abinda kayi, baka buƙatar sai ka faɗa my love. Na yarda da kai, na yarda ba zaka taɓa aikata hakan ba. Allah yana tare da mu.”

Tashi Ammar yayi sannan ya taimakawa Afnan ta tashi.

“Ina fata wannan ne na ƙarshe da zan ganku cikin wannan gidan." Cewar Hajiya Karima.

“Kar ki damu Hajiya koda yunwa zata kashe ni ba zan ƙara saka ƙafata a gidan nan ba." Cewar Ammar kafin ya juya ya cema Kamal sai sun haɗu gidansa.

Kamal bai bashi amsa ba, domin babu wannan kwarin gwiwar a tattare da shi.

Koda suka fita daga gidan Afnan ta fashe da kuka.

“Bana son ka rabu da su saboda ni.” Cewar Afnan.

“Ban rabu da su ba saboda ke. Ki daina faɗar haka bana so. Ki daina kuka please. Idan da gaske kina son ki taimakamin wajen taimaka miki ya kamata ki daina ganin laifinki. Babu laifinki a cikin duk wannan."

“Eh amma..”

“A'a, babu amma. Komai zai yi daidai. Na tabbatar Kamal a ɓarinmu yake. Ba zamu kasance mu kaɗai ba.”

Haka aka yi koda Kamal ya samu sauki, ya nunawa su Ammar da yana tare da su. Makonni sun shuɗe kuma sun shigar da Alhaji Yusuf ƙara kotu. Cikin sa'a suka samu Rakiya yar aikin gidan tace zata bada shaida domin tasan abubuwa da dama. Lauyen Afnan din yace mata lauyen Daddy zai iya tsorata ta akan me yasa bata faɗa ba tun farko amma ya samar mata hanyar da zata bi ta bashi amsa mai kyau ba tare da an zarge ta ba.

A yanzu haka suna cikin haɗa ƙwaƙwaran file ne na shari'ar da za'a yi nan da wata huɗu.



(.......)


Kamal ne ke fama da yin wani zane da zai yiwa wani balarabe da zai bawa matarsa a matsayin kyauta na birthday ɗinta. Kamal yana ɓata lokaci sosai akan zanen dan ganin ya ƙawatu da kyau.

Amma wannan ranar, wani abu na damun Kamal. Yanzu yake tunanin kusan wasu watanni kenan rabon da yaga Zahara ko jin labarinta kuma abun mamakin bayada bukatar ji. Duk lokacin da ya ɗauki waya da niyyar kiranta sai ya manta kuma ba zai sake tunawa ba. Kuma abinda yafi bashi mamaki, baya jin kewarta ko kaɗan. Irin abinda yake ji game da ita duk ya ɓace, kamar ma hakan bai taɓa faruwa ba. Hakan na damun sa sosai domin yayi imani da soyayyar da yake yi mata. Ya kasa fahimtar meke faruwa kuma baya son sanin meke faruwan.

Ya kan ji a duk lokacin da yaso ya nemi sanin me yasa yake sauyawa game da Zahara wani abu na hana shi kuma sai ya tilasta shi mayar da hankali ga wani abun daban.

A ɓangare ɗaya kuma rayuwa sai yiwa Khadija daɗi take. Kowace rana da zata wuce, tana jin ƙara samun kusanci da Kamal take. Bai iya kwana biyu ba tare da yaji labarinta ba, kullum ciki son ganinta yake da son jin muryarta. Har ya nemi da Khadija ta kwana a gidanshi, abinda bai taɓa yi ba a baya kuma yake nadamar aikata shi. Saidai ita Khadija hakan da ya nema bai wani dameta ba.

A wannan daren, sha'awa ta rufewa Kamal idanu. Ya nunawa Khadija adadin yanda take jan hankalinsa. Sun aikata a ko'ina, a falo, cikin kitchen, cikin ɗaki har cikin bathroom ma.

Washe gari, Khadija tayi sauko wajen aiki. Fuskarta cike da annuri kamar wacce aka yiwa albishir da gidan aljanna. Tana cikin murna domin burinta ya cika, Kamal ya kamu da sonta. Me kuma zata nema bayan wannan? Komai ya tafi da sauri ta yanda har yau ta kasa yarda. Abu ɗaya ya rage mata yanzu shine AURE !



(.....)


“Ba dai haka zaki zauna ba, har sai kin ƙarar da hawayenki akan wannan mutumin?" Cewar Maryam tare da dauke pillow din da ta jefawa Zahara.

Komawa Zahara tayi gefen gado tareda share Maryam dake ta faman masifa domin da alamu ta saba.

“Zahara! Wai kina saurare na kuwa? Ki daina wani abu kamar yarinyar ki tashi! Ba zaki ɓata watanni kina kuka akan mutumin da bai damu da ke ba. Ki tuna ajinki mana..”

Wani sabon baƙin ciki ne ya mamaye Zahara, taji kamar Maryam ta caka mata wuƙa amma kuma tasan gaskiya ta faɗa. Kamal bai damu da ita ba.

“Ya isa haka, yanzu ki tashi ki shirya ki je wajen aiki kamar yanda kike yi a baya kafin ki haɗu da shi. Kina tayar da hankalin kowa."

“Idan da kin san yanda nake ji.."

“Ki yarda da ni, nasan abinda kike ji fiye da kowa.” Maryam ta bata amsa cikin sanyin murya wannan karon. “Ba zaki cigaba da cutar da kanki ba alhali shi yana cen yana sheƙe ayarsa wa ya sani."

“Nasan wannan nisan da nayi da shi shine mafita. Nice silar duk wani hali da yake ciki. Wata kila hakan ne yafi. Amma ba zan iya hana kaina tunaninsa ba.. nayi kewarsa sosai har yasa ina jin zafi. Ina jin ciwo sosai Maryam.”

“Bansan me zan ce miki ba.” Cewar Maryam. “I'm really Sorry.. kinsan wani abu? Ni zan je in ganshi.” Maryam ta faɗa tare da saukowa da sauri daga bisa gadon.

“What? A'a!" Cewar Zahara. “Kar kiyi hakan."

“Saboda me? Kawai ina son gane dalilin da yasa yake miki...”

“A'a..a'a..a'a.." Zahara ta katse ta. “Bana son sanin komai.. please kar ki aikata hakan.”

“Toh ni dai ina son sanin meke faruwa kuma yanzu zan je. Ai nasan gidan nashi.”

Maryam ɗaukar gyalenta da takalminta tayi da sauri ta fice daga ɗakin kawar tata. Tashi Zahara tayi domin taro Maryam da tuni ta daɗe da fita daga gidan.

TO BE CONTINUED...


Readers na daina jin ra'ayoyinku gameda wannan labari. Ya kamata ku fito domin labari ya fara nisa nasan duk kuna nan kun yi likimo. 😇
[03/03 à 05:18] ASHTAR: AMRIYA
(Hatsabibiyar Aljana)

Love 💞 and Horror ☠️ story 📖

By Malik al-Ashtar 🖋

CHAPTER 26


I just published Amriyar Hatsabibiyar Aljana Chapter 26 of my story “AMRIYA Hatsabibiyar Aljana”

http://www.ashblogg.com.ng/2022/02/amriya-hatsabibiyar-aljana-chapter-26.html


“Sai an wuce asibiti gidansa yake ko kuwa kafin a kai? Ina tunanin na ɗan manta takamaimai inda gidan yake.” Maryam ta cewa Zahara da sigar wasa.

Zahara gyara ɗakin da ta duk yamutse tayi, ita kuwa Maryam ta zauna bakin gado tana kallonta.

“Well, ina ga kinada gaskiya, ba shawara ce mai kyau ba zuwa gidan Kamal koda kuwa ina son zuwa. Bansan me zan ce masa ba, kuma nasan lamarin ne zan ƙara dagulewa maimakon inyi gyara.” Cewar Maryam.

“Naji daɗi da kika gane hakan, ban son yayi tunanin ni marar yawo ce da ba zan iya mantawa da komai ba, na cigaba da harkar gabana. Ina son cigaba da rayuwata kamar baya, wacce nake yi kafin in san shi.” Cewar Zahara.

“Ba rashin wayo bane gareki, ke mutum ce shi yasa. Wannan ce wahalar soyayyarki ta farko, kuma kinada ƴancin yin kuka. Amma kinada gaskiya, yanada kyau kiyi gaba, ki ƙara sanin wasu sabbin abubuwan rayuwa. Saidai ba zai yiwu na barki ki koma rayuwarki ta baya ba, a'a wannan ba yiyuwa bane. Zahara lokaci yayi da zaki zauna kiyi tunani akan ƙarancin yardarki. Ya kamata mu nemo wata hanyar canza hakan.”

“Ba abu bane da za'a iya zancawa, yau ko gobe." Cewar Zahara.

“Haka ne, amma ke babu wani ƙoƙari da kike yi. Zan kama miki amma kece zaki yi aikin mafi muhimmanci.”

“Eh na sani Maryam, ki yarda da ni, ina son na canza."

“Toh, yanzu mu ɗan fita. Mu je muci wani abun a waje."

“Ina?”

“Suprise ne!”

“Idan mijinki ya kira fa?"

“Bah what? Ni ba prisoner shi bace, ina zuwa inda nake so. Essential shine nasan inda nake saka ƙafata. Ya yarda da ni kuma yasan adadin yanda nake sonsa.” Maryam ta faɗa tana murmushi.

“Mtsw sannu Romeo da Juliet. Well.. ina son fita amma na gaji ba zan iya ba.” Zahara ta faɗa tareda komawa bisa gado tayi kwanciyarta.

Ba tareda ta shirya ba taji Maryam ta janyo ta daga bisa gadon, sai gata ta faɗo ƙasa.

“Wayyoo karya ni kike son yi ko me? Da fa na karya hannu.”

“Hannun naki ya karye ne?” Maryam ta tambaye ta.

“Ina tunanin bai karye ba amma...”

“Good, tashi kiyi wanka, ni zan fiddo miki kayan da zaki saka.”

“Hum ban yarda da ke ba, idan basu mini ba, ba zan saka ba."

“Ban damu da ra'ayinki ba, oya je kiyi wanka sai wari kike!”

“Nan fa ƙarya kike yarinya.” Zahara ta fada tareda tashi daga ƙasa.

“Ki je kiyi wanka ki daina wannan surutun dan Allah!” Cewar Maryam tareda jefawa Zahara pillow.

“Zan je dan Allah, daina ɗaga murya.” Zahara ta faɗa tareda shigewa bathroom kafin Maryam ta tashi gidan.


BANGAREN KHADIJA


Khadija na tunanin ciki ne da ita. Bata da wani ƙonƙonto akan hakan. Tun bayan wasu makonni, take jin alamar symptoms na mai ciki. Tana yawan jin kasala, ga yawan fitsari duk bayan mintuna goma alhali da tana iya riƙewa na yini guda bata yi fitsari ba. Da farko ta fara tunanin ita ce ke sa hakan a ranta, amma mamanta suka fara yi mata ciwo, da safe ƙwarnahi bai rabuwa da ita. Kuma wannan safiyar bayan ƙwarnahi sai ga yawan jiri. Ba coincidence bane idan hakan ya faru.

“Karɓi je kiyi gwajin." ƙawarta Sa'adiya tace mata.

Karɓa tayi ta sauka daga kan gadon ta nufi ban ɗaki.

Khadija karɓar test pregnant ɗin tayi. Murna ce da damuwa suka cakuɗe mata wuri ɗaya. Bata san takamaimai me take ji ba. Ta so irin wannan ya biyo bayan aurenta da masoyinta Kamal amma ƙaddara ta ɓullo mata ta wani wurin daban. Yanzu bata sani ba idan ya dace ta damu domin bata san ya Kamal zai ji ba. Tasan Kamal ba zai taɓa musa cewa ba nashi bane. Tambayar shine jin zai yi amanna da cikin kuma ya zamar masa uba?

Tambayoyi ne da dama cikin kanta.

Gwajin kuwa ya nuna bata yi kuskure ba tana dauke da cikin Kamal.

Fitowa tayi daga cikin ban ɗakin. Sa'adiya da ke faman jiranta ta warce test pregnant ɗin daga hannun Khadija. Lokacin da taga result din ta juya gun ƙawarta tareda rungumeta.

Khadija cikin kuka tace mata :
“Zan je na faɗawa Kamal, zan je wajenshi yanzu."

“Bansan me zan ce miki ba, amma ki kwantar da hankalinki nasan Kamal ba zai taɓa barinki ba. Amma ina baki shawara da ki bari har gobe sai ki je wajenshi kafin nan kin samu nutsuwa."

“Kinada gaskiya.” Khadija ta bata amsa tana goge hawaye. “Zan kwanta yanzu, domin ina buƙatar hutu."

“Me kike ji yanzu?” Sa'adiya ta tambaye ta tana mai taimaka mata dan ta zauna bisa gado.

“Ban sani ba, a halin yanzu komai confusion ne.”

“Yaro a kullum albarka ce daga gun ubangiji. Kuma kin jima kina son ɗa, duk da ba irin wannan hanyar ba amma abinda ya faru ya riga ya faru. Kuma abu na karshe da nake son faɗa miki ko ba komai yanzu ke da Kamal kun zama ɗaya har abada."

Khadija tayi nisa cikin tunani, ƙawarta tanada gaskiya wannan cikin zai ƙara haɗa soyayyarta ne da masoyinta.

“Ni ina ga cikin ba komai zai kawo miki ba face alkhairi nan gaba. Bayan kin haihu, wata ƙila Kamal ya aure ki. Kin ga kin samu abinda kike so da jimawa. Dan haka ki daina yiwa kanki wasu dubban tambayoyi.”

“Shikenan, may be kinada gaskiya. Bari na ɗan huta."

“Ok, nima bari naje na haɗa dinner. Kafin nan zaki iya yin baccinki.”

Sa'adiya ta bar ɗakin bayan ta taimakawa Khadija ta kwanta. Ta rufe mata rabin jikinta da bargo kafin ta kashe mata wutar ɗakin.

Duk da tayi alƙawarin ba zata yi ba, Khadija bata daina tunanin rayuwarta nan gaba da wannan cikin ba. Bayan ɓata awowi tana tunani daga ƙarshe bacci ya ɗauke ta.

Saidai bata sani ba, baccin nata shima ba wurin hutu bane.

Cikin bacci, Khadija ta tsinci kanta ƙofar gidan Amriya. Ta tuna haɗuwarsu ta farko a nan. Kallon baƙaƙen busassun fulawowin da suka kewaye gidan take. Wanda hakan koda yaushe ke sa mata tsoro. Wannan karon bata jira sai ta shiga ciki ba kafin ta ga Amriya. Jin alamunta tayi a bayanta. Ba zata taɓa sabawa da sauyawar temperature ɗin jikinta ba idan Amriya na ga wuri.

Shafa kafaɗarta Amriya tayi da ya sanya ta zabura amma tayi saurin daidaita nutsuwarta domin kar ta nunawa Amriya ta tsorata. Kallonta Khadija tayi wannan karon cikin ido. Amriya na da idanu mafi kyawo a duniya ko kuma ince Khadija bata taɓa ganin wani da kyawun idanu irin Amriya ba. A duk lokacin da ta haɗa ido da ita sai taji komai na jikinta ya daina motsi, ta kasa kallon wani wurin.

“Kar ki tsorata." Amriya ta raɗawa Khadija a kunne kafin ta kama hannunta.

Kamar da ƙyaftawar ido suka bayyana cikin wani ɗaki na jariri da wani ƙaton madubi gaban ɗan gado na jariri. Kyakkyawan ɗaki ne sosai kuma mai girma da yasa Khadija taji ta zama ƴar ƙarama a ciki.

Tuni ta sani kenan? Khadija ta raya a zuciyarta.

“Ba dai kina tunanin ki ɓoye min ba?” Amriya ta faɗa.

“A'a..nima..ban daɗe da sani ba. Bansan inada ciki..”

“Munada ciki dai zaki ce." Cewar Amriya. “Ni ce keda ciki...ba ke ba.”

“Kamar yaya?”

Khadija ta faɗa tareda juyowa ta kalli Amriya amma Amriya ta ɓace kuma ɗakin babyn da yake duka fari ya sauya launi zuwa ja.. jini ya bayyana ko'ina a jikin bango, a ƙasa, a jikin labulaye har ma bisa ɗan gadon jaririn. Khadija ji tayi ƙafafunta sun kasa ɗaukanta. Bata yi aune ba tayi wata muguwar faɗuwa ƙasa sai kuma ga Amriya ta bayyana cikin madubi.

“Kina tunanin idan bani nan, Kamal zai kwanta da ke? Duk wannan da kika ga ya faru saboda ina cikin jikinki ne. Ni yaji yana sha'awa, shi yasa har hakan ta faru. Duk wannan sha'awar da kika ga ya nuna a kanki a wannan daren, saboda ina wurin ne. Ni yake so ba wai ke ba."

“Ƙarya kike, maƙaryaciya ce ke!” Cewar Khadija.

Ɗakin ne ya fara wani girgiza, ƙwan fitilar dake ɗakin ya fashe kuma kujerar dake kallon ɗan gadon jariri ta juyo da ƙarfi tana fuskantar Khadija.

“Bana jin daɗi idan bil'adama na zagina. Amma ke ba zan yi miki komai ba domin kina ɗauke da ɗana. Zan cigaba da kulawa da ke har lokacin da zaki haife shi.

Khadija da ƙaraji tace
“ƊANA NE NI KAƊAI KINA JINA? KUMA BA ZAN TAƁA BARI KI ƘWACE MIN SHI BA.” Ta faɗa cikin ɓacin rai.

“Kina tunanin kinada zaɓi?” Amriya tace da ita kafin ta ɓace a jikin madubin.

Jariri ne ya bayyana gaban Khadija da ya kusa sa zuciyarta bugawa. Jaririn da fuskar Kamal amma baida wani abu na mutane, ko ƙafafunsa ba'a gani.

“Ranar da zaki haihu, lokacin da likitoci zasu ga jini a maimakon jariri, a ranar zaki gasgata da nawa ne."

Ƙwalla ƙara Khadija tayi ta yi. Jaririn ya ɓace sai ga Amriya ta bayyana wannan karon da ƙaton ciki a jikinta. Durkushewa Khadija tayi ƙasa wannan karon babu abinda ta

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login