Showing 39001 words to 42000 words out of 87059 words
yin kuskure, dan haka ka nuna mata tayi kuskure, kuma auren da zaka yi rusa ka zai yi, ba wai farin ciki ba.”
Ya saurari duk abinda ta fada. Dagowa yayi ya kalle ta bayan ta gama.
“Nayi mamaki... Wannan ne karo na farko da kika yi magana mai tsawo kuma babu gargada. Ina tunanin sai na shirya walima domin wannan.” Ya fada yana dariya. “I knew that on the beyond your fragile and shy appearance hides a very thoughtful and intelligent woman. Nagode sosai da wannan shawarwarin naki Zahara, kina da gaskiya kuma zan yi iya kokari na ganin nayi yanda kika ce. I feel a lot.. better now.”
Sosai bata jin dadin ganin sa a wannan yanayin.
“It's normal...” Ta bashi amsa a takaice.
“Ya kamata mu je mu kwanta, kar tashi da wuri yayi wahala gobe. Ina so da an gama meeting din zamu hau hanyar gida.. dan haka ku zama cikin shiri.”
“Ok, Allah ya kaimu.”
Direct daki ta koma, ta tarar da Sarat sai baccin ta take, ita kuwa sai da ta rage kayan jikin ta, domin taji dadin baccin. Bata jima ba bacci ya dauke ta. Ji tayi kamar kwanan mintuna biyar tayi kafin gari ya waye. Kwaramniyar da Sarat ce ke yi ya tashe ta, tuni ita har ta shirya. Bata yi mata magana ba, kawai kallon ta tayi kafin ta fice daga dakin. Da sauri ta tashi ta shirya kafin tayi latti. Ganin bata zo da kaya masu yawa ba, shirya su bai dau lokaci gare ta ba. Wucewa tayi dakin da suke meeting, cikin sa'a kuwa bata rasa komai ba game da meeting din. Hajiya Hasana da mijin ta Elh Nuhu basu kai da karasowa ba. Saidai Mr. Ammar, Sarat da kuma Ibrahim. Sai da suka jira na kamar mintuna talatin kafin bakin su zo. Wannan karon Kamal yana nan, kuma dashi aka yi meeting din. Zahara iya kokarin ta take ganin basu hada idanu ba.
Shi kuwa akai akai yana satar kallon ta amma ita bata yi gangancin hada ido dashi ba. Bayan bakin sun tafi, Mr. Ammar ya basu mintuna ashirin dan su shirya kayan su. Zahara kuwa daman a shirye take, dan haka sai ta wuce direct cikin mota.
“Baki jima ba.” Mr. Ammar yace mata bayan ta shiga cikin motar.
“Daman ba wasu kaya ba gare ni.” Zahara ta bashi amsa.
“Ai da kin tafi tare da Kamal, har ya tafi mintuna goma da suka wuce, shi da Afnan. Taso ta tsaya amma shi yanada ayyukan da zai yi cen gida.”
“Ah...ok..”
“Kin samu yin magana dashi da safe?”
Tana shirin bashi amsa sai ga Ibrahim yazo da kullum fuskar sa dauke da murmushi.
“Wai me Sarat take yi ne?” Mr. Ammar ya tambaye ta.
“Mai yiyuwa bata karasa shiryawa bane, bari naje na dubota.”
“No kar ki damu, bari naje nayi mata magana. Bata lokacin ya isa haka."
Zahara bata tunanin hakan tunani ne mai kyau amma bata da wani excuse da zata hana shi tafiya.
Bayan Mr. Ammar ya tafi, Ibrahim ya shiga motar, ya zauna mazaunin gaba. Bayan sun gaisa. Yace
“In tambaye ki?” Ya fada tareda juyowa yana fuskantar Zahara.
“Ina jinka.”
“Kawar ki, tana da saurayi?”
“Wa Sarat?”
“Eh.”
“Uhm, gaskiya ban sani ba. Dan bama irin wannan zancen da ita amma zaka iya tambayar ta.”
“No, bana tunanin zan iya yi mata wannan maganar, please kema kar kiyi mata.”
“Ok, kar ka damu.”
A BANGAREN AMMAR
Da hanzari ya shiga cikin hotel din, daya daga cikin ma'aikatan ce ta taso da sauri ta tarbe shi.
“Kayi mantuwa ne Mr. Ammar?”
“No, madam kar ki damu. Just nazo duba abinda ma'aikaciya ta ke yi ne.”
“Ah ok, ko na sa daya daga cikin mutanen mu ya raka ka? idan kana so.”
“A'a ba bukata, ba zan dauki lokaci ba.”
“Ok, a fito lafiya.”
Murmushi yayi mata sannan ya shiga lifter. Dakin da su Sarat din suke yana saman nashi ne. Zuwa yayi ya konkwasa.
“Sarat? Ke kadai fa muke jira.”
Shuru bai ji an amsa ba. Cigaba yayi da konkwasawa har ya fara gajiya, amma bata bude ba. Number ta ya kira, yaji a kashe. Har yana shirin juyawa ya koma wajen ma'aikatan, yaji an bude kofar. Sarat ce gaban sa, daga ita sai rigar bacci wacce da ita da babu duk daya. Kasa motsawa Ammar yayi, haka kuma ya kasa dauke idanun sa a kanta.
Kamar rakumi da akala, ta janyo shi zuwa cikin dakin tare da rufe kofa. Tura shi tayi jikin bango, ta wani shige jikin shi.
Hakan babu kyau, ka kuma ci amanar Salmah. Wani bangare na zuciyar sa ne ke ta yi masa gargadi.
Kar ka damu ai ka wahala Ammar kuma Salmah bata bukatar ka yanzu. Dayan bangare na zuciyar sa marar kyau ya shiga ingiza shi.
Haka bangarorin biyu na zuciyar sa suka shiga dambe, a yayin da ita kuma Sarat bata yi magana ba, ta shiga sumbatar shi...a wuyan sa.. a kirjin sa.. a cikin sa.. a ko'ina na jikin sa. Jin hannayen ta yake na yi masa yawo ko'ina a jiki. Yayi iya kokarin sa ganin ya bar dakin, amma sha'awar ta ta baibaiye shi...
“Stop Sarat.. ya kamata mu tafi..” Ya hada iya kuzarin sa wajen fadar kalmomin nan. Ita kuma kamar ya kara tunzura ta, ta yage rigar da ke jikin ta, sai gata ta koma babu komai jikin ta. Hakan kuwa da tayi yayi tasiri gare shi, bai yi wata-wata ba ya tura ta bisa gado tare da haye ruwan cikin ta... Daga nan mai aukuwa.. ta auku.
A BANGAREN SU ZAHARA KUWA
“Awa daya fa kenan, Mr. Ammar bai dawo ba.. gaskiya akwai abinda ke faruwa.” Cewar Ibrahim yana ta kokarin kiran ogan su, amma tana ta ringing ba'a dauka.
“Oh kin gan shi nan ma.” Ya fada lokacin da ya hango Mr. Ammar din.
Ta window Zahara ta hango shi dauke da akwatunan Sarat. Saka su yayi a boot, kafin ya zagayo ya shigar motar. Tare da ce musu
“Tana gyaren kayan ta ne, shi ne na tsaya taya ta dan tayi sauri. Gata nan zuwa.”
“Ah, mun yi tunanin ko wani abun ne ya faru.”
“Wani abu kamar me?” Mr. Ammar ya fada a dan harzuke.
“Toh nima ban sani ba dai.” Cewar Ibrahim.
“Kana da matsala kai..”
Bayan wasu yan mintuna, Sarat tazo tana ta faman washe hakora.
“Sorry na bata muku lokaci. Kayan ne suna da yawa. Da naji maganar Zahara nazo da yan kadan.”
Zahara bata yi magana ba, bata san dalili ba amma tana ji a jikin ta akwai abinda ya faru tsakanin Sarat da Mr. Ammar. Bata gasgata hakan ba, sai da suna kan hanya, Sarat ke ce mata :
“Kina shanawar ki da yayan boss, nima wannan karon lokacin shanawa ta ne !!”
“Me kike nufi da hakan?”
“A'a komai, zan yi kamar ke. Nima sirri ne.”
No.. bayan duk maganar da suka yi jiya, Mr. Ammar ba zai fara wata alaka da Sarat ba, hakan baida wata ma'ana. Ta tabbatar Sarat, ta fada mata hakan ne domin tayi magana... Tana fata ace hakan ne.
Ta gasgata hakan da kyau.. bayan wasu kwanaki da dawowar su, ta fara lura da wasu abubuwa tsakanin Sarat da ogan su. A duk lokacin da suka hadu, tana ganin yanda suke kallon juna. A ranta tace wannan shi ne yake kira da fada akan masoyiyar sa? Dole tayi wani abu kafin ayi nisa. Duk wannan ta dalilin ta ne, zata taimaka masa ganin ya dawo kan hanyar daidai. Haka Sarat ya kamata ta fahimci Mr. Ammar yana cikin bakin cikin rabuwa da masoyiyar sa ne, shi yasa yake kula ta ba wai dan yana sonta ba.
A yayin da Zahara ke kokarin shawo kan Sarat amma taki ta saurare ta, a ranar bayan ta dawo gida daga aiki wajen shidda na yamma, cike da mamaki wa zata tarar in ba Kamal ba zaune a falon su.
[03/03 à 05:18] ASHTAR: AMRIYA
(Hatsabibiyar Aljana)
Love 💞 and Horror ☠️ story 📖
By Malik al-Ashtar 🖋
For more novels https://bit.ly/3Egdy1m
On wattpad : https://www.wattpad.com/story/270492485
CHAPTER 16
⚖ HOME OF QUALITIE'S WRITERS ASSOCIATION 📚
Rabon da Khadija taji irin wannan kuncin zuciyar, tun ranar da iyayen ta suka rabu. A lokacin tana da shekaru 15 dan haka tana fahimtar duk abinda ke faruwa. Kunci ba komai bane akan halin da ta shiga kwanakin da biyo bayan mutuwar auren iyayen ta. Yau gashi ta sake tsintar kanta cikin yanayin, kuma tsoro da fargaba ne suka dabaibaye ta na gudun abinda zai faru nan gaba..lokutan bakin ciki.. nadama da kuma wahala. Bata taba tunanin Kamal zai yi mata irin haka ba. Ta kawo tunani iri-iri na dalilin da yasa Kamal ke gudun ta, amma bata taba kawowa saboda Zahara bane.
Dafa bango tayi domin taimakawa kafafuwan ta da suka kasa daukan ta. Kamal shima bai ji dadin ganin zanen Zahara da tayi ba, bayan abinda Ammar ya fada masa. Ya kara tabbatar masa gaskiyar cewa Khadija tana son shi. Ba wani kwararre bane shi wajen gane irin haka. Amma yanzu da yasan gaskiya, lamarin ya ida cabewa. Ta yaya zai iya sanar da ita baya jin abinda take ji ba tare da ya cutar da ita ba? Kuma tashin hankalin yanzu, ta ga hoton Zahara dole zata so yayi mata cikakken bayani.
Kamal kokarin yanda zai yi ya tattara kalaman da zai yi amfani da su wajen yiwa Khadija bayani yake. Matsawa yayi kusa da ita, ita kuma tayi tsalle tayi baya tare da hadewa da bango.
“Kar ka matso kusa da ni, ta yaya ka iya yin haka? Me ke ga wannan yarinyar da kuke ta rawar kafa a kanta?”
“Maganar me kike?” Kamal ya tambaye ta. “Baki san me kike fada ba Khadija, bansan me aka fada miki ba, amma kin yi kuskure. Ba abinda kike tunani bane.”
“Nasan me nake fada, saboda yarinyar nan Ammar da Salmah suka rabu. Fada min ba soyayya kake da ita ba... Fada mini please.”
“Ba soyayya nake da ita ba, amma a shirye nake idan ta amince da ni. Babu wani bashi da kika biyo ni Khadija, rayuwa ta ce. Idan kina tunanin ta dalilin ta ne kawar ki da Ammar suka rabu good, ba zan tilasta ki ba ki karya ta kanki amma ba ke zaki fada min abinda zan yi ba.”
Khadija ji tayi tamkar an caka mata wuka a kirji. Taji numfashi na kokarin ya gagare ta. Dafe daidai zuciyar ta tayi tana tambayar kanta idan da gaske wanda ke gaban ta best friend dinta ne Kamal.
“Dan Allah ce da ni mummunan mafarki nake. Na tabbatar mafarki nake.. fada min please.”
Kamal yaji ba dadi na ganin halin da ta shiga. Amma bata da yancin shiga rayuwar shi. Ya tsani a dinga shiga sha'anin sa, kuma ba yau hakan zai canza ba. Ko mahaifiyar shi ta daina shiga harkokin sa.. domin bai bata dama ba.
“Listen Khadija, you are my best friend... kin fi kowa sanin ko ni waye. Kin san cewa ba zan bibiyi abinda bani da ra'ayi a kan...”
Katse shi tayi
“Ni ba best friend din ka bace, ban taba daukan kaina a wannan matsayin ba kuma kaima kasan da haka. Kasan cewa ina matukar sonka, kana tunanin zan zauna banda saurayi alhali ina da masu sona. Ban kula samari ne saboda ina hango kaina a matsayin matar ka.”
Kamal kara tunkarar inda take yayi, amma ta kara danganewa da bango da iya karfin ta.
“A'a.. bani bukatar wata tausayawar ka, kuma ka sani ba zan taba hakura da kai ba. Na rasa shekaru da dama na rayuwa ta ta 'ya mace saboda kai, bana tunanin zan yafe maka wannan. Ina son ka fada min komai game da yarinyar nan.”
Kamal yayi kamar bai gane me take nufi ba, sun dade tare amma bai taba ganin wannan dayan fuskar tata ba. Khadija ta kasance mai nutsuwa da tunani.
“Eh, ka jini da kyau Kamal. Na cancanci sanin ko iya wannan ne.”
“Baki biya ta bashin komai Khadija, i'm sorry amma ni ban taba yi miki wani alkawari ba. Ba lallai zan san abinda kike ji ba game da ni idan baki fada min ba yau. Ba laifi na bane kuma kinsan da hakan.”
“Nima ba laifi na bane idan sakarcin ka ya hana ka gane na haukace a kanka. Ina yin duk wani abinda kace nayi. Dan Allah Kamal...nasan tsakanin ka da ita pass attraction ne kawai...mun san juna tsawon shekaru...ba zaka ce baka jin sona ko kadan a zuciyar ka ba. Please kar ka min haka.”
Wannan karon Khadija hannun Kamal ta rike a hankali... domin fahimtar da shi adadin yanda take son shi, adadin yanda take tsoron rabuwa da shi.
“Hakan ba sauki ke gare shi ba gare ni nima, ban so hakan ta kasance ba tsakanin mu. Khadija ke mace ce mai kyau, mai hankali da ilimi you deserve wanda zai so ki ya kuma kula da ke. I feel something for her duk da bamu dade da sanin juna ba. I would never lie about my feelings, ba zan taba cewa ba ina son ki, dan na faranta miki. Wannan ba hali bane.”
Ba tare da ta saki hannun sa ba, ta durkushe kasa tare da fashewa da kuka. Kamal yayi kokarin dago ta amma taki.
“No..no..i can't accept it...i can't accept it..i can't...”
“Please Khadija be reasonable and kiyi kokarin fahimta ta. Kinga muje.. in maida ke gida.”
“A'a... ba zan taba fahimtar wannan zabin da ka yiwa kanka ba. Yarinya ce fa ita, bata san komai ba game da rayuwa, bata ma wani sanka ba. Da me ta fini? Me take da wanda bani da shi? Wannan zabin da kayi baka yi tunani ba, kuma ni zan ganar da kai. Wannan munafukar ta jefe ka ne kamar yanda ta yiwa Ammar, na tabbatar har da wasu mazan ma. Tana nuna ita saliha ce, ni kuma nasan ba haka bane.”
“Ya isa haka Khadija, wannan ba halin ki bane. Ba haka na sanki ba... Kuma saboda kyan halin ki ne nake son abotar mu.”
“Ba ruwa na, a yanzu nothing is going right.. Ko na birge ka ko kar na birge ka hakan bai dame ni ba! Kawai na fadi abinda nake tunani a kanta. Gara ka bude idanun ka ka gane wacece ita kafin ayi nisa.”
“Je ki dauki jakar ki, muje in kaiki gida.” Kamal ya fada a yayin da ita kuma ta mike tsaye tana kakkabe jikin ta.
“Ba sai ka kaini ba nasan hanya.”
Saidai Kamal bai kula ta ba, ya shiga dakin sa ya canzo kaya dan ya maida ta gida. Fitowa yayi da key din motar shi, ya taimaka mata ta saka takalmin ta ba tare da ta daina rusar kuka ba.
(....)
A BANGAREN HAJIYA KARIMA DA ELH YUSUF
“Alhaji ina tunanin sai ka sa baki cikin lamarin Afnan.”
Gaban alhajin ne ya fadi. Zufa ce ta fara kare masa, ya shiga kokarin boye tsoron da ya bayyana a fuskar sa dan kar matar shi ta gani. Dan gyaran murya yayi sannan yace
“Saboda me? Meke faruwa da Afnan din?”
“Ban sani ba, ina lura da ita yanzu bata son shiga mutane. Ina tunanin akwai abinda ke damun ta da taki ta fada min. Nayi iya kokarina jin meke damun ta amma sai tace ba komai, ni kuwa nasan karya take min."
“Ba yarinya bace ita, ki daina daga hankalin ki. Idan tace miki lafiya lau take, to lafiya take.”
“Ko kana ganin bata jin dadin zama da mu ne? Ka ganin na barta ta koma wajen iyayen ta?”
“Kina daga hankalin ki ne a banza, akwai matsalar da tafi wannan a yanzu wacce ya kamata mu warware, ta auren Ammar.”
Alhaji satar kallon matar sa yayi dan ganin ko zata manta da zancen Afnan kuma da alama yayi nasarar yin hakan. Yanayin matar sa ya sauya daga damuwar halin da Afnan ke ciki zuwa bacin rai.
“Yarinta har yanzu ke damun Ammar, da zai san dalilin da yasa muke yi masa duk wannan ba."
“Daina nuna karfi a kansa, ki sake kokarin yi ganar da shi. Nima zan yi masa magana.”
“Kana da gaskiya, zan sake yi masa magana in gani. Idan bai sauya ba dole zan yi ta karfin."
Alhaji ya daina jin me matar sa take fada, tunanin yanda zai fitar da Afnan kasar waje yake kafin ta sa matar shi ta fahimci wani abu. Yasan Hajiya Karima, bata taba karaya ba idan tana son sanin wani abu. Gara ta tafi kafin ta tona masa asiri.
Yasan abinda yake yi ba daidai bane, amma ba yanda za'a yi ya iya hana kanshi. Yarinyar nan tana tuna masa da matar sa lokacin da suna matasa. Matar shi a lokacin kyawawa ce ga diri mai daukar hankali, a lokacin maza rububin ta suke amma ita ta kyankyashe tace sai shi. Suka yi aure cike da son junan su, amma shekaru na shudewa sonta da sha'awar ta suka fara raguwar masa. Sai gashi yau a jikin Afnan yana ganin matar da ya fada soyayyar ta a baya. Yana bala'in sha'awar ta.. sosai ta yanda idan ya ganta sai yaji kamar ya yage kayan jikin sa yaje ya dauke ta.
Yasan Afnan ta tsane shi, hakan ne kuma ke kara sa yaji yana sonta... Shine na farko da ya fara sanin ta a 'ya mace, hakan yasa yake bata duk abinda yasan tana so. Yana siyo mata abubuwa masu tsada in har basu fi karfin arzikin sa ba. Amma ba zai bari wannan makauniyar sha'awar ta kaishi ga faduwa ba. Dole ya fidda ta kasar waje, zai yi mata maganar yau da yama idan kuwa taki amincewa. To fah zai yi abinda ba zai so aikatawa ba.
(.......)
Kwanaki na shudewa amma yanayin Khadija ya kasa daidaituwa, wutar tsanar Zahara na kara ruruwa a cikin zuciyar ta. Kamar mai shafar aljanu.
Hankalin Salmah ya tashi, ganin yanda kawar ta bakin ciki da damuwa na son suyi mata illa kuma babu abinda ta iya yi. Sai yanzu take fahimtar abinda Khadijar ta dinga ji lokacin da itama ta bata da Ammar.
Tana ganin yadda kullum kawar ta ke sauya... Har ta fara kasa gane ta.. bata cin komai sannan tafi son kulle kanta cikin daki. Ta daina zuwa wajen aiki kuma abinda yafi dagawa Salmah shine Khadija ta daina sallah.
Wata rana, ta shirya tayi kwalliya da har ta sa Salmah jin dadi da tunanin ko kawar tata ta fara dawowa daidai. Amma da tace mata zata je wajen Ammar ne tayi masa maganar Zahara, Salmah ta fahimci babu abinda ya rage na halin da Khadijar take ciki.
“Kada kiyi haka Khadija, zaki batawa Kamal rai ne kawai. Kuma ba lallai bane ta