Showing 63001 words to 66000 words out of 87059 words
taqi ta daina takura ta, ta kan cewa kanta ya kamata tayi rayuwa da abinda take da yanzu sannan ta bar gobe ta tsara kanta. Kuma tana ganin cigaba cikin alakar daga sex-friend zuwa sex-friend da kuma confident kuma tana fata nan kusa alakar ta fi haka. Ta zamo macen da tafi kowa farin ciki.
Gashi bata sani ba idan zata iya jurar yace mata alakar su ba zata wuce fiye da hakan ba.
Muryar sa ce ta dawo da ita daga duniyar tunani.
“Tunanin me kike?”
“Ah ba komai.”
“Kin tabbatar?” Ya tambaye ta.
“Eh kar ka damu. Maganar ma me muke yi ma?"
“Kin tambaye ni abinda nake son na ci ni kuwa nace miki bani jin yunwa.”
“Ah ban ji abinda ka fada ba."
“Ai na gani, akwai abinda ke damun ki ne? Me yasa naga hankalin ki na wani wurin daban?"
“Kawai na gaji ne, amma babu komai."
“Toh zo ki kwanta." Ya fada yana bude mata hannuwan sa yanda zata iya shiga. Hakan kuwa tayi babu musu.
Dariya yayi lokacin da tayi wani abu kamar mage yayin da taji dumin jikin sa da ya yi mata dadi.
Haka suka tsaya na tsayin wasu mintuna, har bacci ya fara daukan Sarat lokacin da muryar sa ta tashe ta.
“Ki shirya mu je Niamey, iya mu biyu kawai."
Cikin bacci taji maganar amma sai da taji kamar ta daka tsallen murna.
“Da gaske kake?" Ta fada tare da dago kanta tana kallon sa cikin ido.
“Eh sosai, ina son muje cen domin mu dan huta. Naga alamun gajiya a tattare da ke. Kuma nima ina son na dan sha iska da wannan abubuwan da suke faruwa da ni kwana biyun nan."
“Naji dadi sosai da wannan labari. Yanda baka zato.” Ta fada cike da nuna jin dadin ta a fili.
“Cool, toh ki shirya wannan weekend din."
Kwanaki na gaba, Sarat cikin farin ciki take sosai. Babu abinda yake iya bata mata rai. Gidan gyaren jiki taje, aka darje ta kamar wata amarya. Kusan suman farin ciki tayi lokacin da Ammar ya bata credit card din sa domin ta siyi duk abinda take so ai kuwa bata yi kasa a gwiwa ba. Ta siyo dogayen riguna, skirts, kayan bacci, takalma da sarkoki. Ta dinga jin ta tamkar wata princess.
Ranar juma'a suka hau jirgi cikin kankanin lokaci sai gasu babban birnin Niamey, suka sauka a wani kayataccen five star hotel. Hutawa suka yi har zuwa gobe da yamma da ya nemi da su fita zuwa restaurant. Dan haka Sarat ta cancara kwalliya kamar wata jarumar Hollywood. Bata tabbatar da hadewar ta ba sai da taga irin kallon da Ammar yake mata. Ba iya shi kadai ba, lokacin da suka zo restaurant, idanu suka yi ca a kanta hakan yasa ta kara jin ajinta ya karu.
Da fari komai na tafiya daidai, daya daga cikin ma'aikatan restaurant din yayi musu jagora zuwa table din da Ammar yayi reservation. Suna hira cikin nishadi kafin Sarat ta lura hankalin Ammar yana wani gu daban. Ya daina sauraron ta kuma bai daina kallon bayan ta ba. Dan ganin me ya daukar masa da hankali Sarat ta juya nan taga Salmah tsohuwar budurwar sa.
Salmah ce tare da wani saurayi kuma da alamu itama ta gansu. Kallon Sarat take ba tare da Sarat ta fahimci ma'anar kallon ba. Kafin ma Sarat ta kai ga gane meke faruwa, taji Ammar ya janyo ta tare da hade bakunan su na tsayin wasu mintuna. Irin kiss din da bai taba yi mata ba a baya.
Sarat ba sakarya bace domin tasan duk wannan abun da yayi dan ya ba tsohuwar budurwar sa haushi ne. Kuma ta tabbatar ba coincidence bane idan sun hadu duka nan.
Haushi ne ya kama Sarat amma tayi kamar ba komai. Ta qi barin duk wani emotion ya bayyana da Ammar zai gane ta harbo jirgin sa.
Ta gane hakan ne ya kawo shi Niamey lokacin da suka koma daki. Shuru yayi kuma yaki ya kalle ta duk da masifaffar rigar da saka. Ranar Sunday suka baro Niamey ba tare da sun yi komai ba, idan nace «Komai» ina nufin asalin komai. Ko fita ma basu yi ba, shi da yayi mata alkawarin dream weekend.
Taki ta yarda da hakan, amma cikin kanta hargitsi ne sosai, yanzu ta tabbatar Ammar yana tare da ita ne kawai dan rage lokaci, kafin ya dawo da tsohuwar budurwar sa.
Amma zata cigaba da biye masa a hakan, har lokacin da zata fahimtar da shi ba zata bari ya subuce mata ba.
Saidai cikin rashin sa'a, ranar lahadi da dare zuwa karfe goma, suna tsaka da action suka ji ana knocking kofa. Mamaki Sarat tayi domin babu wanda take tsumayin zuwan sa a wannan lokacin. Da sauri ta saka kayan ta, ta bar Ammar kwance tare da rufo kofar dakin sannan ta kauda duk wani abu da zai nuna akwai wani a gidan bayan ita.
Zuwa tayi ta bude kofar, nan tayi arba da mahaifiyar ta. Jiki ne ya shiga yi mata bari domin ba taba zaton mahaifiyar ta zata zo a daidai wannan lokacin ba. Sosai take cikin shocking ta yanda ta kasa furta ko kalma daya.
“Ni bani hanya in wuce, ko kuwa kara shanya ni zaki yi a nan?"
“Mami me kuma kike yi nan?”
Ture ta mahaifiyar tata tayi tare da kutsa kai cikin falon.
“Kamar ya me nake yi nan? Nazo ganin ki ne tunda ke ko ganin kiran wayar ki ma wahala yake."
“Amma kinsan aiki nake 24 hours. Ina cikin hutawa ne domin gobe sauko zan yi wajen aiki."
“Sai kuma me?" Cewar mahaifiyar ta. “Kora ta zaki yi ne saboda kawai a gajiye kike? Me yake damun ki ne? Ko kin canza uwa ne?"
“Wace irin tambaya ce wannan Mami? Ni ban ce ke ba mahaifiyata ba ce, kawai dai a gajiye nake."
“Koma dai meye sai na tsay...”
Wayar Ammar ce tayi ringing cikin daki da yasa kiris ran Sarat ya fita daga jikin ta.
“Meye wannan?” Mahaifiyarta ta tambaye ta.
“Oh..wayata ce. Na manta ban saka ta a silence ba." Sarat ta fada duk a rikice.
“Yaushe wayar ki ta fara irin wannan ringing? Sakarya kika dauke ni ko me?"
“Na canza ringtone ne, wannan yana burge ni ne sosai."
Sarat ta shararo wannan karyar. Saidai ba banza Mami take mahaifiyar ta ba. Dandanan take gane karya take yi.
Fiddo wayarta mahaifiyar Sarat tayi, ta shiga latsawa cikin kankanin lokaci sai ga wayar Sarat na ringing.
“Waya biyu gare ni yanzu." Cewar Sarat.
Saidai mahaifiyar Sarat bata tsaya kula ta ba, ta tashi ta nufi dakin Sarat. Sarat bata yi kokarin hana ta ba, domin hakan zai kara kwadaitawa mahaifiyar ta son shiga dakin.
A lokacin babu irin addu'ar da Sarat bata karanto ba domin tasan yau kashinta ya bushe.
A BANGAREN ZAHARA
“Na tabbatar kece kike tunanin haka." Cewar Maryam.
“Ba mahaukaciya bace ni. Duk lokacin da zamu hadu sai ya fadi rashin lafiya kuma ina yin nesa da shi zai dawo cikin koshin lafiya. Ina ganin ni ce ke saka shi rashin lafiya."
“Na fada miki Zahara wannan tunanin ki ne kawai. Ta yaya zaki iya bayanin kece ke saka shi rashin lafiya duk lokacin da kuka hadu? Nasan yana sonki amma ba irin wanda zai sa ya fadi rashin lafiya da ya ganki ba.” Maryam ta fada da sigar wasa dan ta kwantarwa da yar uwarta kuma kawarta hankali, saidai hankalin Zahara nesa yake da kwanciya.
“Maryam ina ji a jikina wani mummunan abu ne ke faruwa."
“Subhanallahi Zahara, ki daina fadar haka. Kin cika tunani da yawa, shi yasa har kin fara irin wannan zancen. Kawai ki ce baida lafiya ne kuma insha Allahu zai samu sauki.”
“Hakan saukin fada gare shi, idan ba'a san abinda ke faruwa ba."
“A kan me kike magana?” Maryam ta tambaye ta tana ajiye kofin tea dinta a kan center table.
“Ban sani ba, idan fa.."
“A'a kar ma ki fara, kar ki min maganar sihiri dan ni ban yarda da irin wannan abubuwan ba."
“Aljana ta taba shiga jiki na Maryam."
“Ba zan ce karya kike yi ba ! Dan haka dan Allah kar ki sa in fada. Yanzu mu je ki raka ni kasuwa kafin mijina ya dawo. Karfe nawa zaki je ki ga Kamal din?"
“Ban sani ba.. bana son zuwa.. ko kuma ince ba zan iya ba."
Ajiyar zuciya Maryam tayi.
“Me kike son yi kenan?"
Kallon ta Zahara tayi.
“Komai.. bansan me zan yi ba, kuma hakan ba karamin damuna yake ba."
Zahara ta kasa daina tunanin Amriya, amma kuma tana ganin mawuyaci ne Amriya ta sake dawowa. Shafa layar dake hannun ta tayi tare da kallon Maryam da itama take kallon ta.
A ranta tace ina ma zata iya nemo wannan tsohon.
“Tunanin me kike yi?" Cewar Mayarm.
“Komai, tashi muje kasuwar."
Kasuwa suka je, bayan sun yi siyayya Zahara ta kama mata suka sanya kayan bayan mota kafin Maryam ta kaita gidan Kamal. Tana son ta ganshi domin ta yi masa bayanin abinda take tunani, ta tabbatar shima irin tunanin yake amma yaki ya fada mata dan kar ta tashi hankalin ta.
Knocking kofar gidan tayi, kafin ta ji sautin tafiya na zuwa, ta gane Khadija ce. Zahara a ranta tace tana amfani da rashin lafiyar Kamal domin kara samun kusanci da shi, tinda ita Zahara babu abinda zata iya.
Zahara na tunanin Kamal ya yiwa Khadija zancen domin tana bude kofa ta hau Zahara da balbalin bala'i.
“Kin zo ne ki karasa shi ko me? Me yasa kika zo bayan kinsan kina sanya shi rashin lafiya?"
Zahara bata tsaya sauraron ta ba, ta wuce kai tsaye cikin gidan. Dakin saurayin nata ta nufa ta tarar da shi zaune yana cin abinci. Da alamu yana cikin koshin lafiya.
Murmushi yayi mata koda ya ganta. Ita ma ta mayar masa da martani saidai ita nata kamar yake tayi.
“Yanzu nake shirin kiran ki." Yace da ita.
“Gani nazo amma zan iya dawowa wani lokacin idan kana so." Tace da shi.
Daidai lokacin Khadija ta shigo.
“Bar mu dan Allah muyi magana Khadija.”
“Amma.." Tayi kokarin musawa amma ta juya ta fita sakamakon wani kallo da Kamal ya watsa mata.
Koda Khadija ta fita, Kamal ya budewa Zahara hannuwan sa alamar tazo.
“Amma...ka..san.."
“I miss you so much.. I just want to..”
Bai kasara maganar da yake son fada ba, ya shiga yin tari kamar wanda aka shake. Zahara duk ta bi ta rikice, tana son taimaka masa amma bata san me zata yi ba. Tarin da Kamal yake yi ne ya janyo hankalin Khadija ta fado dakin da sauri tare da wata mata a bayan ta. Koda suka karaso Zahara ta gane Hajiya Karima ce mahaifiyar Kamal.
“Mommy kin ga abinda nake fada miki ko? Yarinyar nan mayya ce, duk lokacin da ta kusanci inda yake sai ya kwanta rashin lafiya. Lafiya lau fa, yake yanzu yake cewa zai dan fita yaga gari. Na fada miki muguwa ce." Cewar Khadija tana ture Zahara domin zuwa kusa da abokin ta.
Wani mugun kallo Mahaifiyar Kamal ta yiwa Zahara kafin ta fiddo wayarta. Hannuwan ta na rawa ta kira ambulance.
“Fice min daga nan yanzu, bana son kara ganin ki kusa da dana." Hajiya Karima ta cewa Zahara bayan ta gama wayar.
Cike da jin kunyar tsintar kanta a tsakanin mutanen nan, Zahara ta fita da gudu daga gidan. A ranta tana cewa suna da gaskiya, laifin ta ne idan baida lafiya.
Idan tayi nesa da shi, ba zai kara cutuwa ba.
BANGAREN SARAT DA AMMAR
“Me ya kai ka zuwa nan a wannan lokacin? Baku da gida ne ko me? Kana tunanin tarbiya ce mai kyau mace da namiji babu aure tsakanin su, su kadaice cikin daki daya?”
“Kiyi hakuri dan Allah Hajiya, insha Allahu hakan ba zai sake faruwa ba." Cewar Ammar.
“Idan har da gaske kana son 'yata kazo ka nemi aurenta mana."
Kallon Sarat Ammar yayi itama ta kalle shi. Tana kuka kasa-kasa tana rokon sa da idanu.
“Zan yi tunani insha Allahu Hajiya.”
“Na baka nan da gobe kayi tunani, idan ba zaka aure ta ba kar ka sake zuwa nan kana zubar mata da mutunci. Ka jini ko?"
“Naji Hajiya."
“Shikenan, zaka iya tafiya ina son yin magana da 'yata."
Yaso tsayawa domin dafawa Sarat amma mahaifiyar ta, cikin fushi take sosai ta yanda babu abinda zai iya yi.
“Ni ne da laifi, kiyi kokarin fahimtar ta dan Allah."
“Inyi kokarin fahimtar ta kamar yaya? Kana nufin ban baiwa 'yata tarbiya ba ko me? Kar ka shiga abinda babu ruwan ka.”
Hakuri ya kara bata kafin ya dauki jacket din sa ya bar gidan.
Ina ma zai iya auren Sarat din. Shi abinda yasa yazo gun Sarat gudun auren ne yayi kuma ba zai so ya sake fadawa wata chakwakiyar ba.
Bai bata lokaci ba yayi tsinke gidan sa, da shigar sa yaji kamshin soyayyun kaji ya bade masa hanci. Afnan ce yau ma ta sake hada girki mai dadi. Wanke hannu yayi da niyyar cin abinci.
Dakin da Afnan take ya leka dan yi mata godiya da girkin da tayi amma ya tarar tana bacci.
Shi ma yana bukatar hutun domin kwana biyu baya samun bacci sosai. Tun lokacin da Salmah ta fara yawo da sabon saurayin ta, ya daina samun sukuni. Yayi kokarin shima ya manta da ita amma hakan da ciwo ba zai iya ba.
Ganin ta tare da wani ba karamin kunci yake shiga ba. Ya yarda yayi amfani da Sarat dan ya sa Salmah kishi amma ya lura ita ko a jikin ta : hakan yasa ya fara tunanin dama cen bata taba son sa ba.
(....)
Washe gari, yayi sauko wajen aiki. Ya hadu da Sarat tace masa tana son yin magana da shi. Ya jira ta duka yinin ranar amma bata zo ba. Daga baya ne ta kira shi tace tana son suyi maganar ne wajen kamfani. Yana kokarin tafiya sai ga likitan Afnan Dr. Abdallah yazo.
Sam Ammar ya manta da likitan zai zo yau, kuma Zahara bata tuna masa ba. Ya lura kwana biyu bata yin aikin ta da kyau, yana son yayi magana da ita domin ba zai yiwu aiki ya cigaba a haka ba.
Bayan Dr. Abdallah ya shigo suka gaisa, Mr. Ammar yayi masa tayin wurin zama.
“Thanks. Sorry kan makarar da nayi. Ayyuka ne suka min yawa a hospital." Cewar D. Abdallah.
“Kar ka damu, nima ayyuka sun min yawa anan. Ko zaka sha wani abu ne?”
“A'a nagode, nazo ne ina son muyi wata magana mai muhimmanci."
“Ok ina sauraron ka."
“Magana ce akan kanwar ka. Kamar yanda na fada maka, ta yarda tayi min magana. Kuma nayi iya kokari wajen ganin na taimaka mata.”
Gyada kai Ammar yayi alamar gamsuwa.
“Abubuwan da nake tattaunawa da patients sirri ne da bana fitarwa, amma idan an aikata wani crime ya zama dole na fada domin a dauki mataki na gaggawa akan criminel din.”
“Ban fahimta ba. Me kake son fada? Wani crime aka aikata?” Ammar ya tambayi Doctor hankali a tashe.
“Abinda nake kokarin fada maka yanzu baida dadin ji amma ya zama dole ka sani.”
“Please Doctor ka fada ina sauraron ka."
“Mahaifinku shi ya yiwa kanwar ku fyade.. kuma ba sau daya ba. Idan baka dauki mataki ba ni zan je da kaina na kai karar sa wurin yan sanda kuma zan yi amfani da duk wani karfi na ganin na shawo kan Afnan ta bada shaida. Fatan zaka dauki mataki mai kyau da kanka.”
“Kace mahaifi na? Kar ka raina min hankali Doctor ! Kamar yaya fyade aka mata?”
“Ba zan yi gangancin bayyana abinda ba gaskiya ba, kanwar ka ta fada min komai kuma sai da na tabbatar ba karya take yi ba."
“Kace mahaifina shi ya yiwa kanwa ta fyade? Yar uwata Afnan? A'a ! Ba zai yiwu ba, wannan ba gaskiya bane domin mahaifina ko kuda ba zai iya cutarwa ba."
“Ka kwantar da hankalin ka sannan kayi tunani."
“Ta yaya zan kwantar da hankali na bayan abinda kazo ka fada min? Wannan ba karamar magana bace Doctor ina son yin magana da yar uwata."
“Zaka iya magana da yar uwarka, amma kar ka takura ta domin har yanzu rauni gareta. Ya kamata taji zata iya dogaro da kai, kar ka sa wannan kwarin gwiwar nata ya rushe."
“Ba zan maka alkawarin komai ba, ina son sanin idan da gaske ne ko a'a.."
Ya tabbatar kuskuren fahimta ne, ba zai taba zama gaskiya ba.. a'a.. ba dai mahaifin su ba.. Mommy ta fada masa wani saurayi ne ya yiwa Afnan ciki. Wata kila shi ne wanda yayi mata fyaden. Toh me yasa zata zargi mahaifin su...?
To be continued....
[03/03 à 05:18] ASHTAR: AMRIYA
(Hatsabibiyar Aljana)
Love 💞 and Horror ☠️ story 📖
By Malik al-Ashtar 🖋
For more novels http://www.ashblogg.com.ng/search/label/Hausa%20Novels
On wattpad : https://www.wattpad.com/story/270492485
CHAPTER 25
⚖ HOME OF QUALITIE'S WRITERS ASSOCIATION 📚
Watanni sun shude kuma abubuwa da dama sun faru.
Kamal har yanzu cikin bakin ciki yake tun lokacin da ɗan uwansa ya faɗa masa abinda mahaifinsu ya aikata. Kamal bai iya haɗa idanu da Afnan; babu wanda yake iya yin hakan duk da ƙoƙarin da suke yi wajen nuna kamar komai bai faru ba. Yayyun Afnan din sun yi mata alƙawarin cigaba da kallonta kamar a baya amma bata san kawai dauriya ce suke yi ba. Ba mai yiyuwa bane nuna kamar komai bai faru ba.
A ranar nan lokacin da Ammar ya kira family meeting kuma kowa yazo, har da Kamal da yake asibiti sai da ya nemi da a kawo shi gida. Ya gaji da zaman asibitin kuma wannan meeting din sai ya zamar masa wata dama, duk da ƙaguwar baro asibitin nasa ta ɓace lokacin da yaji gaskiyar dalilin kiran meeting din.
Ammar yazo da Afnan. Daddy kuwa sai muzurai yake, yana kallon Afnan cike da tsana. Yaso yayi wani wasan kwaikwayo a wurin kuma ya tari Afnan hannu biyu saidai hakan bai yiyu ba sakamakon tsanar da yake ji game da yarinyar. Abinda bai sani ba, Afnan ba zata bari yayi magana ba ko yin dramar da ya shiryo ba. Tana jin wani ƙwarin gwiwa a tattare da ita sakamakon kasancewar Ammar a gefenta. Ba zata ce bata jin tsoro ba, amma tana jinta cikin tsaro kuma a shirye take domin tunkarar wannan dodon.
Lokacin da Hajiya Karima ta dawo gida tareda ɗanta Kamal da kuma daya daga cikin nurses na asibitin, Mijinta da Afnan na zaune a falo babu yanayin alkhairi a yanda ta gane su, dandanan ta fahimci meke faruwa. Kuma ta fahimci lallai familynta bai gama rushewa ba.
Cikin yanayin ɓacin rai ta taimakawa Kamal ya zauna. Ta gaishe da mijinta bayan ta ba banza ajiyar Ammar da Afnan. Wuri ta samu ta zauna sannan ta fara magana
“Me ya kawo ku gidana?” Tace da Ammar da Afnan.
“Ki yarda