Showing 6001 words to 9000 words out of 87059 words

Chapter 3 - AMRIYA HATSABIBIYAR ALJANA

Start ads

Ashar   

11 Aug 2025

402

Middle Ads

shigowar sa kenan. Haka ma Mr. CEO duk da nisan dake akwai tsakanin offishin sa da corridor yaji wannan karar. Saving aikin da ya fara a computer yayi tare da fitowa da sauri domin ganin meke faruwa. Yana fitowa yayi kicibus da yayan shi Mr. Kamal da shi ma karar ce ta fito dashi.

“Karar meye wannan?” Mr. CEO ke tambayar dan uwan sa. Shi kuwa daga masa kafada kawai yayi a matsayin amsa.

Nufar inda suke tunanin karar ta fito suka yi. Tun daga nesa suka tsinkayi kamar alamar mutum a kwance. Sai da suka karasa Amar ya gane Zahara ce. Tambayar kansa yake abinda ya faru da har ta tsinci kanta a nan. Tsoro ne ya kama shi ganin ya tabata bata motsa ba. Durkusowa dan uwan nasa yayi tare da taba jijiyar hannunta kafin yace :
“Suma ne tayi.”

Ajiyar zuciya Amar yayi, cak ya dauke ta ya nufi office din sa da ita. Shi kuwa dan uwan sa ya tsaya tattare takardun da suka zube a kasa.

Aje sakatariyar tasa Amar Yusuf yayi kan doguwar kujerar da ke a offishin nasa. Kokarin tayar da ita ya shiga yi a hankali amma bata tashi ba. Dan uwan sa ne Kamal Yusuf ya shigo, ya ajiye takardun bisa desk din Amar kafin ya samu kujera ya zauna. Amar kokarin kiran likitan su yake domin yayi gaggawan duba Zahara, amma ya dakata sakamakon ganin ta fara motsi. Kokari take ta tashi zaune da sauri yazo ya taimaka mata ta zauna.

A bangaren Zahara kuwa, har yanzu hankalin ta bai dawo jikin ta ba, bata iya tuna komai ba. Razanar da tayi yasa ta manta a wajen aiki take.

Sunan Mama ta kira tana murza idanun ta. Tana kallon wanda ke a gaban ta, da har yanzu dishi-dishi take ganin sa. Sai dai lokacin da ta fara dawowa hayyacin ta, ta fahimci hannuwan da ta taba yanzun ba na Mama ba ne. Daga kanta tayi anan tayi arba da fuskar Amar wato ogan ta. Da sauri tayi baya tana mai tashi daga kujerar. Kamal da ya mayar da hankalin sa ga wasu takardu ya dan juyo ya kalle su.

“Dan..dan..dan..Allah..ku..kuyi hakuri, ban..bansan me nake..yi..ba anan.” Zahara ta shiga i'i'na tana bada hakuri ba tare da tsayawa ba.

“Suma kika yi, shi ne na kawo ki nan. Lafiyar ki kuwa?” Cewar Amar.

“Dan..Allah..kayi hakuri, ba da gangan...”

Wai hakuri take badawa da suman da tayi? Kamal ya fada a zuciyar sa tare da sake kallon su karo na biyu.

“Me yasa kike bani hakuri? Ba fa da gangan kika yi ba. Toh saboda me ma zaki yi karyar suma? Zauna ki huta, bari na kirawo doctor.” Amar ya fada da sigar umarni amma Zahara ta cigaba da bashi hakuri.

“Kayi hakuri, ban so in takura ka ba.”

Kamal da ba shiga lamuran mutane yake ba, yaji halin Zahara ya takura shi yace :

“Bayar da hakurin ya isa haka, ki jira ya kira doctor idan kuma ba zaki iya aikin ba ki tafi gida.” Ya fada da kakkausar murya da alamun an takura shi.

Wannan ne karon farko da ya fara yi mata magana tun zuwan ta kamfanin nan. Ya fada mata hakan ne yana kallon ta cikin ido. Hakan kuwa ya tsorata Zahara ba kadan ba. Allah yayi mata dabi'ar bada hakuri ba tare da ta tsaya taji ita ke da laifi ko kuwa. Bata son tashin hankali ko kadan shi yasa da abu ya hada ta da mutum take kokarin su rabu lafiya.

“Kina son na kira likita ne ya duba ki? Ko zaki tafi gida ki huta. Zan samu wani sai ya karasa aikin naki.” Cewar Ogan nata.

Juya Zahara tayi tana fuskantar shi tare da cewa zata iya cigaba da aikin nata.

“Bana son na kara tarar dake a kasa. Na yarje miki, zaki iya tafiya idan baki jin dadi.”

A cikin ranta, babu abinda take so kamar zuwa gida, amma bata son taje bayan takurawar da tayi masu. Gashi kuma tana da aiki da yawa, kuma tana son kammala documents din da ya bata dazun. Tunawa tayi da har takardu zata kai a dakin meeting. Amma bata sani ba ko tana da kuzarin da zata kara tunkarar wannan corridor ba. Har yanzu tana tuna abinda taji lokacin da hannun nan ya taba ta. Lokacin da ta juyo bata ga kowa ba. Alhali ita tasan hannu ya dafa ta.

Amar gani yayi sakatariyar sa tayi nisa cikin tunani kuma da ka ganta zaka san akwai abinda ke damun ta. Koda basu wani dade ba a kamfanin nan, yayi wa sakatariyar tasa farin sanin koda yayi mata tambayoyi ba amsa masa zata yi ba. Irin kullum cikin tunani take, ga wahalar fitar magana a bakin ta.. Kamar dan uwan shi. Ya fada a zuciya. Niyyar ya barta taje yake da, amma kafin nan yana son yaji me ya kaita cikin corridor nan.

“Fada mini Zahara, me ya kai ki wannan wurin? Idan ban manta ba cewa nayi ki hado min coffee.”

“Naje na kai wasu takardu ne a dakin meeting.” Zahara ta fada kanta kasa.

Kunya ce ta kamata da ta gayi hakan, domin taje aiken Sarat akan na oganta.

“Na dauka wannan aikin Sarat ce ya kamata ta yi shi?”

“Eh, amma tana wani aikin ne..”

Amar yasan sakatariyar sa karya take masa domin ba sau daya yana kama Sarat ta saka ta aiki ba. Yayi shuru ne da tunanin ko badin ba jima Zahara zata daina yarda Sarat na sata aiki sai dai ba haka abun yake ba. Canza maganar yayi domin baya son yayi ta gaban dan uwan sa da yasan halin sa. In yaso sun yi maganar daga baya.

“Zaki iya tafiya.” Ya fada.

Zahara ji tayi kamar tayi tsalle da jin abinda oganta yace. Zuwa tayi da niyyar daukan takardun amma ya hana, yace ta barsu nan. Fita daga offishin tayi bayan tayi masa godiya. Koda ta rufe kofar office din Amar yaji alamun shi yayan sa ke kallo.

“Wai da gaske wannan ce sakatariyar ka?” Cewar kamal.

Gyada masa kai Amar yayi yana kokarin kunna computer.

“Ban ga alamar iya aikin nan gare ta ba. Anya kuwa tana yin aikinta yanda ya kamata?”

“Tana da kwarewa sosai. Kawai tana da dan sanyin hali ne. Amma tana aikin ta da kyau.” Cewar Amar.

“Gwara ka sallameta idan ba zata iya ba. Domin kana dab da ci baya idan ka barta a matsayin sakatariyar ka.”

Kamal ya kasa gane me yasa dan uwan shi yake iya zama da ma'aikata masu sanyin hali kuma suke iya kallon sa cikin ido. Yasan dan uwan shi da tausayi, yana iya daukan mutum aiki dan ya dinga samun albashi mai kyau ba wai dan kwarewa ba. Bai san iya adadin lokacin da ya kori ma'aikata ba a madadin dan uwan shi saboda rashin kwarewa. Saboda halin dan uwan shi, yake zuwa duk bayan wata uku kamfanin dan bincikawa idan komai na tafiya daidai.

Kamal yana da tsanani idan akan aiki ne. Shi yasa Amar ke tsoron kar ya kori Zahara, domin shi yana tausayin ta sosai. Gashi yanzu saura yan watanni dan uwan nashi yazo duba aikin kamfanin, dan haka zai yi kokari yaga Zahara ta sake da mutane dan ganin dan uwan shi bai koreta ba. Abinda yasa yake son zama da Zahara saboda tana tuna mishi da dan uwan shi, kusan dabi'un su daya, na koda yaushe shuru-shuru da kadaice kansu daga mutane. Abin mamaki ne wata kila amma Kamal yanada karancin yarda da kanshi, amma da yake shi mutum ne very intelligent sai ya zamana yana iya controlling rashin yardar shi.

“Ka barni na tafiyar da ma'aikatana yanda nake so dan Allah, kai ma kaji da naka damuwowin.”

“Ni kai ne damuwa ta, nasan idan na kyale ka, shekara daya tayi yawa ka durkusar da kamfanin nan.”

“Daddy kai ya fara yiwa tayin zama CEO a kamfanin nan amma kace baka da bukata. So please kaji da naka matsolilin, ni nasan yanda nake tafiyar da kamfani na.”

“Zan kyale ka ne duk ranar da ka iya handle emotions din ka.” Cewar Kamal da ransa ya fara baci.

“Ba'a ce dole sai mutum ya zama robot kafin ya iya tafiyar da kamfani ba. Ni ba kamar ka bane Kamal. Ba mai fatan ya zama kamar ka. Ina son naji ni a raye, in yi kuka idan abun kuka ya sameni haka ma dariya idan ina cikin farin ciki. Bana da ra'ayin cire duka wannan kawai saboda aiki.”

Cewar Amar shi ma cikin bacin duk da yasan ya dan wuce gona da iri wajen fadawa yayan sa wannan kalaman. Kuma ya yiwa yayan nasa farin sanin da yasan irin wannan kalaman suna taba shi amma ba zai taba nunawa ba. Sai dai ya kamata ya fada masa gaskiyar abinda yake tunani game da halin yayan nashi.

“Ni ba munafuki bane. Ba zan yi karyar dariya ko kuka ba domin nunawa mutane akwai ni. Ina yin abinda nake ganin ya dace ne, bana bukatar sai mutane sun soni. Amma idan kana tunanin gaba kake da ni saboda kana kewaye da mutane masu sonka, toh congratulations.”

Kamal kayan shi ya shiga tattara yana kokarin barin office din. Shi kuwa Amar yaji bai kyauta ba, kuma ba zai juri fushin dan uwan sa ba.

“Bro, tsaya please... Kayi hakuri akan abinda na fada maka... Ba wai nayi bane dan...”

“Kana bani hakuri ne saboda da gaske kayi nadama ko kuwa dan ka nuna min kai mutum ne mai kawa zuci? Toh ka sani emotions ba zasu amfanin komai ba idan dai ba abinda kake ji bane da gaske.” Kamal ya fada kafin yayi tafiyar sa ya bar dan uwan nasa yana tunani.

A bangaren Zahara kuwa, tsoron da take ji ya sake nunkuwa. Domin motsi kadan sai ta tuna da hannun da ya dafa ta dazun. Ta kasa gano me yake damun ta. Amma yanzun ta fara tunanin ko aljanu ne ke bibiyar ta. Idan kuwa haka ne me aljanun nan suke nema da ita? Me tayi masu? Wata kila idan ta samu tattaunawa dasu zasu fada mata abinda tayi masu, daga nan ma ta nemi yafiyar su, su shafa mata lafiya.

Har wajen karfe sha biyun rana, Zahara na bisa internet tana neman yadda ake korar aljani, ko yanda mutum zai yi magana da aljani mai bibiyar sa. Gaba daya tabi ta karanta duk wani posting dake bayani game da shafar aljanu. A wasu shafukan shawara ta samu akan ta yawaita saka suratul Bakara duk safe da yamma domin korar aljanin. Wasu kuma wuridi suka bata da zata yi da dare domin yin magana da aljanin. Amma ita tafi ganewa saka Al-kurani mai girma.

Tana cikin binciken nata, sai ga Sarat ta shigo a kidime...

“Mr. CEO yana ciki? Yanzu ya kira ni, yace yana nema na.” Sarat ta tambayi Zahara.

“Eh yana ciki.” Zahara ta bata amsa.

Koda ta shiga Zahara ta tuna bata kai takardun da ta bata ba. Oga yace kar ta yi. Ta ma manta da takardun na meeting ne. Addu'a take har cikin ranta Allah yasa dai kar Sarat ta tsane ta. Cikin rashin sa'a kuwa Sarat na fitowa ta wurgo mata wani mugun kallo wanda yasa Zahara shan jinin jikin ta.

“Idan kin san ba zaki je ba, me yasa baki fada min ba da ki je ki kaiwa Mr. CEO su. Ba'a taba wulakanta ni ba irin na yau.” Sarat ta fada kafin tayi gaba.

Idan da ta tsaya da Zahara tayi mata bayani zata fahimci cewa ba laifin ta bane taso da gaske taje ta kai takardun... Amma, koda yake yanzun bata da lokacin wannan, domin matsalar Sarat auta ce a cikin matsalolin da take fuskanta yanzu. In yaso daga baya ta ma Sarat bayani.

Komawa tayi ta zauna ta cigaba da abinda take. Da ta gaji ta aje ta shiga tunanin da ta saba, kafin Mr. Amar ya katse ta, ta dan tsorata domin bata san lokacin da yazo ba.

“Oh sorry na tsorata ki?” Ya fada.

A lokacin ita ko ya kankanin motsi yake ma tsoro yake bata.

“Ah ba komai.” Ta fada tana gyara zaman ta.

“Kin karasa aikin ne?”

“A'a saura kadan dai na karasa.”

“Kadan ya rage? Ok, zaki iya zuwa dashi gida ki karasa. Muje na aje ki, yau kusan unguwar ku zan je..”

Tunani take daman yasan gidan su. Nan take kuma ta tuna wata rana da suka taba haduwa daidai kusan gidan su. Tana tunanin akwai wani da ya sani nan unguwar su.

“A'a kar ka damu sir. Zaka iya tafiya ni ba yanzu zan je gida ba.”

“Umarni ne Zahara. Kashe wannan computer ki same ni a mota ina jiran ki. Na baki minti goma.” Yace mata kafin ya tafi.

A ranta tace me yasa yake son dole sai ya kaita gida. Tafi gane ma ta shiga dan sahu yayi ta gararanba da ita akan ta shiga motarshi ta takure kanta. Ba dan taso ba ta mike ta tattare kayan tabi bayan shi. Ta tabbata yana son yi mata maganar Sarat ne da aikin da take sa ta. Maganar zuci ta fara kafin ta karasa bakin motar “Wayyo Allah, kuma wacce matsalar na sake jawa kaina? Nasan cewa zai yi ba son aikin kamfanin nake ba... Daga karshe ma ya kore ni. Toh kuma idan kora ta zai yi ai ba zai ce min naje da files din gida na karasa aikin.”

Ba zata so ace ta rasa wannan aikin ba, domin a halin yanzu shi kadai take iya yi. Idan har ya kore ta ba zata iya jurewa ba, domin aikin ya fara sawa ta fara yarda da kanta. Ba wai aikin da take mafarkin samu bane, amma tasan idan har tana yinshi zata fara sakewa har nan gaba taje ta nemi wasu kamfanonin na jarida.

Suna zuwa wajen parking, yace ta jira ya fiddo motar. Hakan kuwa tayi, ta labe bakin wata bishiya dan kar wani ya ganta. Domin yanzu mutum ake kiwo ba dabba ba. Sai dai cikin rashin sa'a, lokacin da baka son haduwa da kowa, lokacin ne zaka ga kowa a waje. Sarat dan sahu ko bus ta saba shiga idan zata je gida, amma yau sai gata tare da Hajiya Hasana sun nufo wajen parking. Da ganin su Zahara tayi kokarin guduwa amma aka yi daidai da Mr. Amar ya fito da motar shi kuma ya faka daidai gaban Zahara. Tuni cikin Zahara ya duri ruwa, tsoro da kunya duk sun dabaibaye ta. Ba tare da ta kalli su Sarat ba tayi saurin shigewa mota.

Kin tayar da motar Amar yayi sai da ya gaisa da Hajiya Hasana da kuma Sarat.

“Zahara sannu.” Cewar Sarat tana wani yamutsa fuska.

“Yauwa.” Abinda Zahara ta iya ce mata kenan.

Bayan Mr. Amar yayi musu sai gobe ya tayar da motar.

A saman hanya ba wanda yace kala cikin su. Daman haka Zahara take so, dan bata ma san me zata ce ba. Shi kuwa ta kasa gane dalilin da yasa yayi shuru, domin bata taba ganin sa haka ba.

“Ya jikin naki?” Ya tambaye ta.

A ranta tace ashe nayi azarbabin ganin rashin maganar sa. Ya tambaye ta ya jikin ta ita da ba rashin lafiya tayi ba.

Cigaba yayi dacewa
“Daman kin saba suma ne irin haka? Ko kina fama da wata rashin lafiya ne?”

“Eeh a'a..”

“A'a me?”

“Lafiya ta kalau kuma babu wata rashin lafiya da nake.”

“Oh, tambayoyin nawa ne kika hade kika bani amsa da a'a? I see. Ke ba mai yawan surutu bace. A office naga kullum kamar a takure kike, amma nan kina iya sakin jikin ki. Mu biyu ne kawai anan.”

Abinda bai sani ba, a office din tafi sakewa akan cikin motar shi, domin a cen ba'a cika magana a kanta ba, amma anan ya zamar mata dole tayi magana kuma idan zata yi sai ya kalle ta.

“Kayi hakuri.” Ta fada.

Ji tayi alamun yana kallon ta.

“To shi hakurin na meye Zahara? Kina bani hakuri ne saboda baki da surutu ko kuwa? Wannan ai ba laifi bane. Daga yanzu bana son na kara jin kin bayar da hakuri ba da dalili ba. Da wannan halin naki, sauran ma'aikata sai su raina ki.”

“Kayi hakuri.” Ta sake fada kafin ta tuna abinda baya son ji ne.

Ya jima yana kallon ta kafin ya girgiza kai.

“Ba da gangan nayi ba..”

“Kin san wani abu, ni ban ganin aibun abinda kike yi, amma wasu suna ganin kamar sakarcin ki yayi yawa. Sorry da kalamin.”

“Na sani..”

“A'a baki san irin girman wautar da kike yi ba. A tunanin ki tauye kanki wuri daya, ba zai sa ki samu matsala da mutane ba, amma bari na fada miki mutane sun fi samun dama ga irin ku wajen cimma wata manufa tasu. Ki duba kamar Sarat, na lura kullum cikin saka ki aiki take yi. Kuma ita ba girme miki tayi ba. Na lura da komai amma nayi tunanin wata rana zaki yi wani abun amma naga baki da alama, in banda ni yau da na mata magana da ba zaki taba yi mata ba... Ni ban ce abinda kike yi yana da aibu ba. Ke ma'aikaciya ta ce, kuma hakki na ne na taimaka miki akan abinda ya shafi zamantakewa da mutane. Amma kafin nan kema sai kin yi yaki da tunanin ki. Shi yasa na nemi da na kawo ki gida, dan mu tattauna akan hakan. Dan haka idan kina bukatar wani abun kar kiyi sanya wajen fada min.”

“Nagode sir.”

“Bari yimin godiya. Ina yin hakan ne domin cigaban kamfani. Yayana Kamal zai dawo domin binciken ma'aikata kuma idan har bai tarar da aiki mai kyau ba zai yi sanya ba wajen kora. Duk da ina kokarin na hana shi yin hakan, amma mu biyu muke da hakki akan kamfanin kuma yafi ni kwarewa akan aikin.”

Shuru kowannen su yayi, sai da suka shigo unguwar su Zahara, Amar yace
“Toh ina tunanin idan kika bi nan zaki isa gida da wuri. Ni zan je ganin matar da zan aura ne a cen kwanar take. Nasan ma ba zaki rasa sanin ta ba.”

Zahara bata cika fita ba, dan haka ba lallai bane ta santa.

“Meye sunan ta?” Tayi karfin halin tambayar sa.

“Salmah Idris sunan ta.”

Kamar yanda tayi zato, bata taba jin sunan nan ba a cikin unguwar su. Kowa na burge Zahara amma banda masoya. Bata taba soyayya ba, kum bata tunanin zata yita nan gaba. A nata yin soyayya ba sauki gare shi ba. Bata san ta yaya mutane zasu sota idan bata ao kanta ba. Idan ace tana soyayya, zata dinga

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login