Showing 18001 words to 21000 words out of 87059 words

Chapter 7 - AMRIYA HATSABIBIYAR ALJANA

Start ads

Ashar   

11 Aug 2025

409

Middle Ads

kenan. Nida nake son yau na shiryawa Alhaji Al'amin, amma abinda kika fada min yanzu, zan tunkari Mr. Amar na fada mishi nima ina sonshi.”

“Toh kiyi yaya da budurwar sa?” Zahara ta tambaye ta domin tabbatar da hakan ba zai dakatar da ita ba.

“Ina ruwana da ita. Ina ce ba aure suka yi ba? Dan haka zan kwace gurbin da dama nawa ne. Mu shiga ciki domin wajen nan akwai sanyi.”

AMRIYA
(Hatsabibiyar Aljana)

Love 💞 and Horror ☠️ story 📖

By Malik al-Ashtar 🖋

On wattpad : https://www.wattpad.com/story/270492485

CHAPTER 6


*HOME OF QUALITIE'S WRITER'S ASSO📚*
_(The Home Of Qualitative Writers That Are Educate Humanities)._
https://www.facebook.com/100495222137315/posts/100496042137233/?substory_index=1&sfnsn=mo

*[📝I.W.A📝]*

Koda ta shigo cikin falon duka kallo ya koma kanta. Har wani shuru ya karade falon na wasu yan mintuna tsabar ta dauke hankalin kowa dake wurin. Duk da haushin ta da Salmah take amma tasan da tayi kyau. Juyawa tayi wajen Khadija da itama ke ta faman kallonta. Zungurar ta tayi domin maidota a duniyar zahiri. Salmah a ranta tace tanada kyau amma ba wani abun ayi ta kallon ta bane, kuma ita ba zata iya saka wannan rigar ba, domin ba wata mai tsada bace.

“Ki daina kallonta dan Allah Khadija. Kina kunyatar dani.”

Cigaba da kallon Zahara tayi na wasu yan dakiku, kafin tace
“Wai dan Allah wacece wannan yarinyar?”

“Ita ce sakatariyar Amar, na tsaneta ko cen dama, karki kara bani wata hujjar da zata sa na kara tsanar ta. Ki daina kallonta.”

“Ita ce tazo tace miki kiyi hankali da guy din ki? Hum.. inda nice ke, da zan yi hankalin. Kinga yanda take kuwa?”

“Oh mayar mana da hira baya zaki yi kenan, cen dama a dame nake. Kuma ke kika ce na manta da ita. Kenan kina nufin na yarda da abinda ta fada mini? Ni nasan Amar kuma nasan ba zai taba cin amanata ba.”

“Eh da wannan yarinyar kam, ko limamin limamai zai iya fadawa tarkonta. Amma dai...” Khadija tacewa Salmah tana kallonta.

“Mtsw, ni bansan me yasa nake ta biye miki muna maganar ta ba.”

Juyawa Salmah tayi dan ta zauna kusa da Khadija, amma taga har yanzu Khadija Zahara take kallo.

“Khadi ki daina kallonta!” Salmah ta fada da dan daga murya, amma Khadija ta riko kanta tana kokarin tirsasata sai ta kalli inda Zahara take. Kokarin kwacewa take amma koda ta tsinkayo saurayin ta ya nufi wajen Zahara, zuciyarta ta bada dam.

“Maza tashi ki je..” Khadija ke fada mata, ba tare da ta janye kallonta akan su Zahara ba.

“Kwarai kuwa zan je.” Salmah ta fada tana mikewa tsaye da sauri dan kwalinta na faduwa. Ita ma ta nufi wajen su.

Suna tsaka da magana, Salmah bata san me suke tattaunawa ba amma suna ganinta suka yi shuru.

Zuwa tayi kusa da Amar tana wani shigewa jikin sa, kafin ta juyo ta kalli Zahara tace
“Sannu Zahara'u ko?”

“Yauwa sannu Salmah. Kin yi kyau fah. Kuma Zahara sunana.”

“Humm nagode. Kema bakida laifi.” Salmah ta bata amsa da murmushin ta na munafunci.

Sarat ce ta karaso inda suke.

“Sannun ku duka.” Ta gaishe su.

Tana karasowa Amar ya dauke wuta, wani irin kallo yake binta dashi. Kallo daga sama zuwa kasa kafin ya koma ya kalli Zahara da itama shi take kallo. Kan Salmah ya daure, bata fahimci komai ba. Tana ganin raini ne a gareta. Sun sha zuwa wuri mai dauke da yan mata masu kyau amma Amar bai kallon su sai dai ya maida hankalin sa gareta. Kodai ya boye mata asalin halinsa ne tsawon wannan shekarun da suka yi? Kenan Zahara tayi gaskiya da tace mijin da zata aura ba wanda take tunani bane?

Ganin irin kallon da Khadija take masa, yasa a rikice yace
“Yauwa..sannun..ki Sarat.'”

Rikicewar da yayi ta kara sakawa Salmah shakku. Ta kasa fahimtar me yasa zuwan wannan yarinyar ya saka shi cikin wannan yanayin. Ko yana cin amanarta da ita ne? Ko kuma ya taba gwada cin amanarta da ita?

“Zan iya magana da kai na minti biyu?” Salmah ta tambaye shi.

“Eh me zai hana? Afuwan ladies.”

A hankali Salmah taja hannun sa zuwa wani bangare da babu kowa.

“Amar... ko zaka fada min meke faruwa?”

“Ke dai zaki fada min abinda ke faruwa da ke. Kina yin wani abu wanda na kasa fahimta.”

“Haka ma zaka ce? Ke dai ne ke wani abu kamar wani karamin yaro sabon shigan zuwa night club. Sai wani tadi kake da matan nan a gaba na ba tareda ka damu ba, faduwa kawai yayi saura kayi yanda kake kallon su. Na kasa fahimtar meke faruwa da kai, da ba haka kake ba.”

“Ki daina min irin wannan kallon, ni ban taba yiwa waddanan yan matan wani kallo na daban da ba na dan uwa mai kallon kannen sa ba. Salmah kece ke wani abu a yanzun nan, wannan walimar na hadata ne saboda kamfani kuma saboda na bayyanawa kowa ke a matsayin wacce zan aura, dan haka please kar ki bata komai ki samarwa kanki nutsuwa domin Mommy na na wurin nan, ya kamata ki kama jikin ki kin gane?”

“Ina son mu kare wannan maganar anan Amar, ni ba wawiya bace naga yanda kake kallon wannan yarinyar... Saratu take ko wa”

Dogon numfashi ya sauke tareda dafe kansa da hannu biyu.

“Baki ji abinda na fada miki bane ko me? Zamu iya yin maganar idan kina so amma ba anan ba. Bansan me yasa kika fara zama haka ba, na fara gajiya da wannan halin naki Saly.”

“Ba haka nake ba, idan kaga ina yi saboda ka bani hujjar yin hakan ne. Bari wani wayencewa, ni da kai mun san akwai abinda ke faruwa tsakanin ka da yarinyar cen. Toh ba'a haka dani. Na gama.”

“Kinsan wani abu. Kiyi duk abinda kike ganin ya dace.” Ya fada kafin yayi tafiyar sa.

Tayi kokarin tsayar da shi kuma taga kamar zubar da aji ne. Tasan wadannan munafukan wato Zahara da Sarat abinda suke so kenan. Tana cikin wannan tunanin nata sai ta hango Zahara na nufowa inda take. Taku take daya-daya yanda take tafiya ya kara janyo hankalin mazan wurin da dama, hakan kuwa ya kara bata ran Salmah. Ba'a taba hauda Salmah irin yau ba, domin ta lura har wata baiwa ke ga Zahara ta saka mata takaici. Tun ranar da ta fara ganinta komai ya dagule mata.

“Toh yaya..?” Zahara ta fada lokacin da ta karaso kusa da Salmah. “Da alama kin fara fahimtar abinda na fada miki. Kin kira ni da ballagaza alhali ni ankarar dake ne kawai nake son yi.”

“Ya ishe ki haka!” Salmah ta fada a hankali tana dantse hakoranta dan ta daidaita nutsuwar ta.

“Kin gani idan ana son mutum makancewa ake, ba'a ganin kuskuren shi. Kin wani dauki yardar ki kin bashi kuma na bude miki ido, amma kin kasa ganin gaskiya. Na dauka ke wayayyiya ce.”

“Zahara ya ishe ki haka....!”

“Bai ishe ni ba, kinga wannan rigar da Sarat take sanye da ita?”

Iya kokarin ta tayi dan kar ta kalli rigar amma abun yafi karfin ta. Kishi ne ya turnuke ta sosai, a hankali ta daga kai ta kalli Sarat. Tana cikin magana da wata mata.

“Rigar ta an kerata a daya daga cikin manyan fashion house. Kuma kinsan wanda ya siya mata? Ko kina son mu tambaye ta? Ok”

“Sarat dan Allah minti biyu!”

Sarat kallon su take da mamaki amma duk da haka ta nufo inda suke.

“Nasan karya kike yi, zaki iya fadar duk abinda kika ga dama amma ba zan kama ba.”

“Ni ban magana sai na tabbatar inada hujjah.”

Sarat ta karaso daidai lokacin. Komai yana tafiya daidai kamar suna bitar wasan kwaikwayon da ita Zahara ta rubuta da kanta. Salmah ji take tamkar tana a cikin film din Nollywood.

“Kawata rigarki tayi kyau, tuna mini ma waye ya siya miki?” Zahara ta tambaye ta.

Irin kallon tausayi Sarat ta yiwa Zahara, kafin tace cikin kasa da murya
“Please ki daina ba'a haka nan Zahara.”

“In daina me? Ina son nasan waye ya baki wannan rigar. Zaki fada ko a'a?”

“Saurayin ki ne ya siya mata.” Zahara ta sake fada. “Wannan rigar daga Seoul babban birnin kasar Korea take. Ba sai na tsaya yi miki wani dogon bayani ba. Nasan kwanyar ki tana aiki kuma kin fahimci daga inda ta fito.”

“Na fada miki ya ishe ki haka!” Salmah ta daka mata tsawa tare da tura ta jikin bango da iya karfin ta.

Tangal-tangal Zahara tayi bisa takalminta masu tsini kafin ta fadi kasa. Karar buguwar da kanta yayi KUMM! da bango shi yayi silar janyo hankalin duka mutanen dake wurin.

Ja baya Salmah tayi cike da mamaki da tsoron irin karfin da ta sa wajen ture Zahara. Ita kuwa Sarat da mamaki ta ture Salmah ita ma.

“Baki da hankali ne ko me?” Ta fada kafin ta duka dan taimakawa kawarta.

Mutanen wurin ne suka yo kan Zahara ganin har yanzu bata iya tashi ba. Kallon Khadija Salmah tayi dan ganin ita yanda take kallon abun, itama kuwa kallon Salmah take da mamakin me ya kaita aikata wannan abun. Matsowa tayi tare da kama hannun Salmah ta janye ta gefe.

“Me yake damun ki?” Khadija ta tambaye ta. “Kin rasa hankalin ki ne ko me? Me yasa kika ture ta irin haka?”

Salmah kokarin magana take amma hawaye sun cika mata idanu. Bata so ta ture ta ba, kawai taso ta rabu da ita ne.

“Na rantse miki Khadija ba da gangan nayi ba. Ta kai ni makura ne...”

Katseta Khadija tayi
“Hakan bai baki damar kiyi mata irin wannan turar ba. Kin manta ne? Abu na farko kar ki taba nuna iya adadin fushin ki, domin hakan zai baiwa mutane damar yi dake.”

Fashewa da kuka Salmah tayi domin tasan Khadija gaskiya ta fada mata. Kokarin rarrashin ta Khadija take amma ta kasa daina kukan. Sautin tafiya suka ji a bayan su, Salmah tasan ko waye amma kunya ba zata bari ta hada ido dashi ba.

“Khadija... Dan bamu wuri dan Allah.” Ya fada.

Khadija rada ta yi mata a kunne da ta daina kukan tare da shafa bayanta kafin ta bar wajen. Goge hawayen Salmah tayi tare da juyowa tana fuskantar shi.

“Kinga abinda kika janyo koh?”

“Ita ce ta...”
Katse ta yayi.

“Bana son jin komai. Saboda abinda kika yi ya zama doli na daga bayyanawa kowa ke a matsayin wacce zan aura zuwa wani lokacin.”

“Please ka saurare ni... Ce min tayi...”

Sake katse ta yayi
“Mommy na har ta samu labari kuma tasan ke kika yi. Kina tunanin wannan abun da kika yi yanzu zata yarda da soyayyar mu? Wannan shine burin ki? Duk abinda nayi domin mahaifiyata ta yarda da auren mu.”

A hankali yake magana kamar yanda ya saba idan yana cikin bacin rai. Salmah ta fahimci irin tabargazar da ta aikata. Duk watannin nan da suka bata wajen shawo kan mahaifiyar Amar sun tashi kan banza. Yanzu take danasanin biyewa Zahara.

“Please ka bari na yi maka bayani Amar.”

Ta fada tana mai dora hannun ta daya kan hannun sa, dayan kuma a kafadar shi. Ba tare da yaji me zata fada ba ya janye jikin sa.

“Kar ki taba ni. Ba abinda zaki fada min, inada baki masu jirana. Zaki iya zuwa bangare na ko kuma ki samu wuri ki zauna har a kare.”

Kokarin tafiya yayi amma ta rike shi da iya karfinta tare da rungume shi. Bai wani kula ta ba.

“Na rantse maka ba laifina bane. Zan iya yi maka bayanin duk abinda ya faru daga farko har karshe. Wannan yarinyar ba wacce kake tunani bace, munafuka ce da take son...”

“Ya isa haka Salmah! Ba zan yarda ki zagi yarinyar da neman yanda zata gina rayuwarta ne ya kawota nan. Bansan me yasa kika yi mata haka ba, amma ina mai baki shawarar ki je ki nemi yafiyarta bayan an kare. Ko kuma ni kaina bansan me zan yi ba.”

Ture ta yayi tare da barin wurin. Sulalewa tayi jikin bango tana kuka kamar an mata mutuwa. Ta wargaza komai yanzu, ba zai taba yafe mata ba. Dole sai ta nuna masa asalin fuskar Zahara ya gane ba wacce yake tunani bace. Idan ta kyaleta haka, zata iya rusa mata aure kuma ita ce da faduwa cikin labarin...

A bangaren Zahara kuwa, taga tsantsar hauka gun Salmah, domin bata shiryawa irin haka ba. Matsanancin ciwon kai take ji sakamakon buguwa da tayi a bango.

Sarat ce ta kama mata ta tashi, kusan duka mutanen wurin kuwa sun kewaye su dan ganin ko tana lafiya. Kasa tsayuwa tayi, domin zafin da kanta yake mata. Amar ne ya roki Kamal da ya rakata dakin kanwar su, kafin ta warware. Matsowa Kamal yayi kusa da ita da fuskar sa dinnan marar annuri, ya dauke ta cak ba tareda yaji nauyin ta ba. Kamal yanada girma sosai, dan haka sai Zahara ta zama tamkar gashin kaza a hannun sa. Labewa tayi cikin jikin sa, shi kuwa ya nufi stairs da ita. Zahara ta kasa fahimtar hali irin na wannan mutumin, hatta numfashin sa yana yinsa ne kamar an takura masa. A ranta tana tunanin wata kila yana yin hakan ne dan ya nesanta kanshi da mata. Dagaske kyakyawa ne shi kuma cikaken namiji... Burin kowacce mace...

Yar tafiya yayi kafin yazo kofar wani daki wanda daga corridor sai shi. Ajiyeta yayi kan gado tareda taimaka mata ta cire takalminta ba tareda wanin su yace kala ba. Kamar ma baya son kallonta.

Ajiye takalman yayi karkashin gado kafin ya juya da niyyar tafiya..

“Tsaya...” Zahara ta fada tana mai mikewa daga kan gadon da duka iya karfinta.

Tsayawa tayi gabansa tana kallon shi, shi ma kallonta yake yana jiran yaji me zata ce.

“Me yasa baka son kallona?” Ta tambaye shi tana mai kara matsowa kusanshi.

Ja baya yayi kafin yace
“Ki kwanta ki huta.”

Kokarin tafiya yayi amma ta riko hannun sa na hagu. Kallon hannayen nasu yayi tareda yi mata wani irin kallon da ya sata jan jinin jikinta.

“Ban yi...”

Tayi kokarin magana amma ta kasa, daidai lokacin wani ya konkwasa kofar dakin. Ba tareda an jira amsa ba, aka budo kofa. Wata mata ce mai tsananin kama da Amar da wata matashiyar budurwa a bayanta. Dukan su sun ga lokacin da hannun Zahara yake rike da na Kamal. Da sauri Kamal ya ja baya tareda kwace hannun sa ya fice daga dakin ba tareda ya kalli matar nan ba. Zahara taji haushin katse musu magana da matar nan tayi, amma duk haka ba komai tinda dama haduwa da matar yana cikin plan dinta.

Matsowa matar tayi tareda murmushinta ta tambayi lafiyar Zahara.

“Da sauki Mama... Kawai kafata ce ke dan yimin zafi.”

Ba wani zafi da kafarta ke yi mata, amma da yake ta shirya kicihin son ganin wannan matar ta nesanta danta da Salmah toh komai ma tace.

Taimaka mata Mommy tayi ta koma kan gado, sannan ta cewa yarta ta dauko mata man sabara da tace mata ta kawo.

“I'm so sorry kan abinda ya faru. Ban ji dadin abinda ya faru dake ba, domin Dana ya nemi da in kula da bakinsa da zasu zo, kuma ayi a gama lafiya. Cikin rashin sa'a wannan mahaukaciyar da yake kira budurwar shi ta bata komai.”

“Kar ki damu Mama, na samu sauki yanzu. Ni kawai ina so...”

Kuka Zahara ta fara dan ta karawa lamarin suga.

“Kawai ina son nace mata ta daina abinda take yi ne.”

Kara rushewa da kuka tayi, Mommy ta rungumeta tana rarrashin ta.

“Fada mini komai 'yata. Ina son sanin komai. Karki ji tsoro, ina tare da ke.”

“A'a Mama... Bana son haifar da wata matsalar. Na tabbatar zata daina idan har dagaske tana son Amar.”

“Meye zata daina? Yana da kyau in sani, farin cikin dana ne ke cikin hadari. Idan kina tsoron wani zai miki wani abun, karki damu ni zan kare ki.”

“Amar ba zai ji dadi ba..” Zahara ta fada tana goge hawaye.

“Ba abinda zai sameshi. Ni na dade ina tunanin wannan yarinyar ba mutuniyar kirki bace. Nasan tana sonshi ne kawai saboda kudin sa. Nasha mafarkin zata cutar dashi.”

“Mama nasan zaki daidaita komai, ba sai na fadi wani abun ba.”

Mommy yarinyar dake tare da ita tace ta fita dan ta samu yin magana da Zahara ba tare da wani ya katse su ba. Bayan yarinyar ta fita, Mommy tacewa Zahara ta bata labarin komai.

“Salmah unguwar mu daya da ita. Tana da samari da dama... Ban sani ba ko ya dace na fada maki, amma ina tunanin... tana biyar.. tana biyar maza...”

Waro idanu Mama tayi tare da toshe bakinta kamar wacce zata saki kara. Jin maganar Zahara ta girgizata, domin tayi tsammanin jin komai amma banda wannan.

“Lokacin da Mr. Amar yace min ita ce wacce zai aura hankali na ya tashi. Na dauka ta daina komai saboda soyayyar da takewa Mr. Amar, ashe ta cigaba da aikata wannan danyen aikin nata ba tare da Mr. Amar ya sani ba. Ban so nayi mata maganar yanzu ba, domin nayi tunanin zan iya yi mata nasihar da zata daina abinda take amma koda nayi mata, shine ta rufe ni da duka...”

Mikewa tsaye Mommy tayi amma Zahara ta riko hannun ta.

“Dan Allah Mama kar ki fadawa kowa ni miki wannan maganar, domin zan iya rasa aikina.”

“Karki damu nasan me ya rage min nayi yanzu.”

AMRIYA
(Hatsabibiyar Aljana)

Love 💞 and Horror ☠️ story 📖

By Malik al-Ashtar 🖋

On wattpad : https://www.wattpad.com/story/270492485

CHAPTER 7

⚖HOME OF QUALITIE'S WRITER'S ASSOCIATION📚

Hajiya Karima matar Yusuf cike da samun nutsuwa. Daman ko ba dade ko ba jima tanada kudirin raba alakar tsakanin danta da wacce yake ikirarin yana so amma abinda yarinyar nan ta fada mata yanzu, bata bukatar hade sama da kasa ganin ta kawo karshen wannan soyayyar. A ranta tace wata kila dan nata bai san da wannan ba, da bai nemi ya aure ta ba. Wani namiji ne zai so auren "Yar gantali"? Kuma koda ma ya amince da wannan alakar, Hajiya Karima ba zata taba yarda ba, haka ma mahaifin sa Alhaji Yusuf.
Kowacce uwa zata so abun kwarai ga danta kuma tasan yar aminiyar ta ita ce wacce ta dace da Ammar. Duk da dan rawan kanta amma yarinya ce da ta samu tarbiya mai kyau daga mahaifiyar ta kuma tasan ba zata taba bada kanta ga namiji ba kafin aure.

“Zan samu baccin kirki ne kadai idan Ammar ya aure ta.” Ta fada a zuciyar ta.
Saukowa tayi daga kan stairs ta shiga neman Salmah. Bata ko bi ta kan bakin da ke kokarin gaishe ta ba. A cewar ta

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login