Showing 78001 words to 81000 words out of 87059 words

Chapter 27 - AMRIYA HATSABIBIYAR ALJANA

Start ads

Ashar   

11 Aug 2025

425

Middle Ads

ba, duk da haka yace
“Ya kike Zahara?"

“Lafiya lau daƙiƙu kaɗan baya nake, excuse me now akwai inda zan je." Ta faɗa kafin ta rufe ƙofar gidansu. Ta gabansa ta bi da niyyar tafiya amma ya riƙo hannunta.

“Zahara, please ki saurare ni, ki bani mintuna biyar dan Allah. Idan ba gaggawa bane ba zan zo nan ba."

“Ba so kake ka tafi ba? Kayi tafiyarta kafin raina ya ɓaci kuma ka yarda ba zaka so gani na rai a ɓace ba."

“Ni da Khadija zamu..."
Katse shi tayi.

“Ni bana son jin komai, ba zan saurare ka ba dan haka kayi tafiyarka kuma kar ka sake dawowa nan ko kuma ka ji maganganun da ba zasu yi maka daɗi ba..."

“Shikenan ba zan yi maganata da Khadija ba, babban abinda ya kawo ni nan shine Amriya." Kamal ya faɗa.

“Meye Amriya?" Zahara ta tambaye shi da mamakin ta inda ya ɓullo.

Dawowa Kamal yayi suna fuskantar juna sannan yace :
“Ina tunanin tana nan...tana ƙoƙarin tarwatsa min rayuwa da kuma ta Khadija. Ba wai ina faɗar haka ba ne domin neman uziri a gare ki amma ina tunanin ita ce silar sa inyi nesa da ke. Ita ce silar rashin lafiyar da nayi ta yi. Ina tsoron ta cutar da ke, da ni da kuma bab...da kuma dangina."

“Bravo... Ka zo ne ka bani wannan labarin kawai dan na yafe maka? Ɓata lokacinka kake, ni ba sakarya ba ce Kamal."

Tafiya Zahara tayi kafin ta waiwayo.

“Da ka samo wani labarin ba wannan ba, tsoho ya riga yayi maganin Amriya kuma wannan layar tana nan koda zata dawo. Yanzu ka koma ka sake ƙirƙiro wani labarin da yafi wannan sannan ka dawo mu gani ko zan yarda da kai." Ta faɗa kafin tayi tafiyarta ta bar Kamal tsaye jiki a sanyaye.

Jiki a sanyaye, yanzu ya fahimci adadin yanda Zahara ke fushi da shi. Abinda yayi mata ba ƙaramin laifi ba ne, daidai idan tayi fushi. Shi ma zai iya shiga wannan yanayin idan Zahara tayi nesa da shi babu wata ƙwaƙwarar sheda.

Ya kamata ya nemo hanyar da zai yi mata bayanin komai cikin kwanciyar hankali kafin ya makara. Ba zai taɓa yafewa kanshi ba idan har Amriya ta cutar da ita.


ƁANGAREN AMMAR

Tun da sassafe ya tashi domin kai Hafsat gida. Ya yiwa ɗan uwansa alƙawarin kula da ita da kyau. Kuma ko babu wannan alƙawarin, ba zai yi komai ba wanda zai cutar da Hafsat. Ya ga halin da take ciki jiya, kuma koda basu jituwa, ya damu da halin da take ciki kuma yana son sanin abinda ya faru da ita.

Bayan ya iso ƙofar gidan Kamal, ya yi knocking ƙofa. Bayan wasu mintuna... yana ta jira amma babu wanda yazo ya buɗe masa. Ƙara nocking yayi, wannan karon sai ga Hafsat ta buɗe masa.

Bai yi mamakin ganin yanda fuskarta duk ta kumbura ba.

“Da sauki jikin naki?" Ya tambaye ta. Ji wata banzar tambaya kuma. Ya faɗa a ransa.

Saidai Hafsat bata bashi amsa ba. Juyawa tayi ta koma cikin ɗaki, kafin ta rufe ƙofa Ammar yace :

“Ni ne zan mayar da ke gida, idan kin shirya ina falo." Ya faɗa mata.

A matsayin amsa, Hafsat ta rufe ƙofar ɗakin da ƙarfi. Ammar yaji kamar sun yi musayar hali. Da fari shi ke yin duk abinda zai yi ganin yayi nesa da yarinyar nan amma yanzu ita ce ke gudunsa. Shi ma ba wani son su zama friend yake ba lokaci guda, saidai yana binta a sannu ne ganin abinda ya faru da ita. Daga ƙarshe sai da ya fara nadamar sakar mata fuska da yayi.

Sai da yayi jiran kusan awa uku kafin Hafsat ta fito daga cikin ɗaki. Sosai ya kai wuya, shi da har aiki ya baro office dan yazo ya taimaka mata, amma duk da hakan ba zai ce komai ba dan kar ransa ya ƙara ɓaci.

“Muje ne?" Ya tambaye ta.

Hafsat bata bashi amsa ba ta nufi ƙofar fita. Rufe gidan Ammar yayi da keys. Ɓude mata ƙofar motar yayi ta shiga ta zauna ba tare da tayi ko tari ba. Ammar bai yi tunanin kasancewa da Hafsat guri ɗaya ban haushi gare shi ba sai yau.

A hankali Ammar ya fara jin sa a takure. Bai san me yasa wannan situation ɗin take sa yake jin sa a takure ba. Kuma abinda Hafsat take yi ba gyara komai yake ba.

Ko kaita wani wurin yake yi ta ci wani abun kafin ya kaita gida? Yanke shawarar kaita restaurant da babu nisa da inda suke ya yi. Wata ƙila bayan taci wani abun ta ɗan saki jiki da shi. Saidai koda ta lura da Ammar ya sauya hanya kuma tashin hankalin yana dab da zuwa restaurant ɗin da ta yiwa farin sani tace

“Me kuma yake ƙoƙarin yi ne?" Hafsat ta faɗa ranta.

Yayi alƙawarin ba zai yi wani scene ba amma wannan guy ɗin ya fara kai mata wuya. Koda yaushe cikin faɗa suke toh me yasa yanzu yake son dole sai yayi kamar su wasu shaƙiƙan abokai ne? Ita ba zata iya munafuncin yin kamar komai bai faru ba tsakaninsu.

Kamar yanda tayi tunani, Ammar ya faka daidai restaurant ɗin.

“Meye haka kake ƙoƙarin yi? Ka yiwa girman Allah ka kaini gidanmu." Ta ƙwalla ƙara tare da jefo masa jaridun da ke gefenta cikin motar.

“Ra'ayi fa kawai nake son canza miki.” Ya faɗa shima da ɗaga murya tare da dukan steering mota.

“Babu abinda nake so daga gare ka, gida kawai nake son zuwa!"

Tunawa yayi da maganar da ɗan uwansa ya faɗa yace
“Kamal.. yayi gaskiya.. ina ɓata komai koda nayi niyyar yin abun ƙwarai. Gwara nayi saurin kaita gidansu kafin ta min hauka anan."

Tayar da motar yayi, fuska a murtuke. Yana nadamar amincewa da kaita gida da yayi. Babu abinda yake tafiya daidai idan suna tare.

“Kana son ka nuna min kai yau mutumin kirki ne, alhali ni da kai mun san ka tsane ni da iya zuciyarka." Hafsat ta faɗa.

Ammar ƙoƙarin share ta yayi, domin yasan idan har ya mayar mata da martani, zai haddasa yaƙin duniya ne na uku. Hafsat ta cigaba
“Ka adana tausayinka, bana buƙata. Zan kasance mafi farin ciki a duniyar da babu kai ! Ni ma na tsane ka amma ni bana pretending. Ka mayar da ni gidanmu babu hayaniya hakan zai sa komai ya je daidai."

Ammar bai kula ta ba ya cigaba da tuki. Bayan kamar mintuna goma kuma sai Hafsat ta cigaba da cewa
“Daga nan kuma sai me? Zaka kai ni gidanmu ne, sannan ka haɗa min abinda zan ci sannan ka cigaba da kula da ni?”

Wani wawan birki Ammar ya taka, da yasa kaɗan ya rage Hafsat ta buga kanta gaban mota ba.

“Are you crazy? So kake ka kashe ni ne ko me?" Cewar Hafsat ta faɗa cikin tsawa.

“Ba abinda kike so ba kenan? Mu kashe junanmu? Bah, gashi kin yi nasara kin tayar da sheɗanin da ke jikina. Sauka !"

.........

“Nace ki sauka !" Ya daka mata tsawa.

Ƙin motsawa Hafsat tayi sai ma kuka da ta fashe da shi.

Dogon numfashi yayi yace “Me kuma na ƙara janyowa kaina?"

“Yanzu faɗa min me yasa kike kuka? Ba so kike na cigaba da nuna ƙetata a kanki kamar yanda nayi yanzu ba.. yanzu kuma da nayi kina kuka? Me yake damunki ne wai ! Kina ta ihun kina son ki sauka yanzu nace ki sauka... Kin ƙi ki sauka. Meye matsalarki?”

“Please ka mayar da ni gidanmu... Ba zan sake magana ba."

“Eh amma ni kuma ina son sanin dalilin wannan sabon sauyin naki?” Ya tambaye ta cikin sanyi wannan karon.

“Bana son yin maganar yanzu.” Ta faɗa bayan ta ɗan nutsu.

“Shikenan kamar yanda kike so." Ya bata amsa kafin ya tayar da motar.

Kamar yanda yace ya kaita har gidansu. Fitowa tayi daga motar ta nufi ƙofar gidansu.

“Hafsat." Ya kira sunanta.

Tsayawa tayi ba tare da ta juyo ba, Ammar yace
“Nasan bai taɓa jituwa ba tsakaninmu amma idan kina buƙatar wani taimako ko kuma kin shirya maganar abinda ya faru da ke zaki iya zuwa ki gan ni. A'a.. kuma ba wai tausayi ba ne... Kawai na gane babu wata fa'ida ne faɗan da babu wani dalili.”

Cigaba da tafiya Hafsat tayi ba tare da ta juyo ba ko tace masa ƙala amma abinda ya faɗa sosai ya shiga kunnenta.


BANGAREN KHADIJA

Bayan kwanaki da ta yi tana tunani, ta yanke shawarar aikata abinda Amriya take so. Tana son tseratar da kanta, soyayyarta da kuma cikin da ke gare ta. Kuma yin abinda Amriya take so shine kaɗai mafita. Ta nemi da ta cire layar da ke hannun Zahara.

Khadija bata yi tambaya ba kuma bata san me hakan zai amfanar da Amriya ba amma duk da haka zata aikata abinda take so. Babu wanda zata cutar idan ta aikata hakan. Khadija ta faɗa a zuciyarta, kawai tana son tseratar da familynta ne. Wa zai ji haushinta idan yaji dalilin da yasa ta aikata hakan?

Dan haka ta shirya zuwa gurin Zahara da wani ƙulli a ranta.

To be continued...

AMRIYA ☠️
(Hatsabibiyar Aljana)

Love 💞 and Horror ☠️ story📖

By Malik al-Ashtar 🖋


CHAPTER 32

I just published Amriyar Hatsabibiyar Aljana Chapter 32 of my story “AMRIYA Hatsabibiyar Aljana”

http://www.ashblogg.com.ng/2022/03/amriya-hatsabibiyar-aljana-chapter-32.html

Zahara bata daina yin kuskure ga files ɗin da zata kai ba. Yanayin oganta ba top ba ga kuma kurakuran Zahara da ke ƙara ɓata masa rai. Haɗuwarta da Kamal ta takura ta yanda ta dena baccin dare.

Tunanin jin Amriya ta dawo ya tsorata ta. Bata sani ba ko ta yarda da maganar Kamal ko a'a. Ko ma dai meye yana iya ɓacewa na tsawon kwanaki daga baya ya dawo ya yi mata ƙarya. Me yasa ma ba zai yi mata ƙarya ba dan ta dawo gare shi? Tambayoyi da dama ke mata kai-kawo cikin kai.

Saidai ba su kaɗai ba ne wanda hankalinsu baya jikinsu. Sarat, ita ma ba daidai take ba kwana biyu. Tana jin kamar ta rasa komai. Tana jinta a ƙazanta, wacce aka yi amfani da ita aka jefar. Bata san me zata yi ba dan dawo da mutumin da take so. Komai zulle mata yake.

“Ya isa haka Zahara... Idan kin yi kuskure na farko zan iya karɓa amma nan baki aje hankalinki ba. Idan bakida ra'ayin aiki yau sai ki faɗa min.” Cewar Ammar cikin tsawa gaban ofishin Zahara rai a ɓace.

Batada wani zaɓi da ya wuce ta bashi haƙuri, miƙewa tayi tare da ba ogan nata haƙuri.

“Ka yi haƙuri, zan mayar da hankali daga yanzu.”

“Abinda ya kamata ki yi kenan, matsalolin da ke gare ni sun isa haka.” Ya faɗa kafin ya koma cikin ofishinsa ba tare da ya manta da rufo ƙofar da ƙarfi ba domin nuna rashin jin daɗinsa.

Sarat da gaban idonta aka yi komai, ta yanke shawarar ajiye girman kanta ta nufi ofishin nasa ganin meke faruwa. Ta gaji da zama cikin duhu.

Ta gaban Zahara ta bi da ke ta faman zubar da hawaye amma Sarat bata bi ta kanta ba. Ta kunna kai cikin ofishin Ammar ba tare da tayi knocking ko ta rufe ƙofar a hankali bayan ta shiga ba.

“Na gaji da ajiye ni gefe da kake yi, ba zaka dinga amfani da ni kana yar wa ba duk lokacin da ta raya maka !"

“Saurare ni Sarat, yanzu ba lokacin irin wannan...”

“Ba ruwana ko lokacin ne ko ba lokacin ba ne. Tsawon makonni kenan ban ce komai ba toh ya isa haka. Idan baka son aurena ne ka faɗa min ba wai ka bar ni cikin duhu ba. Na gaji da zaunawa jiran gawon shanu kamar wata sakarya.”

“Domin Allah Sarat, bana son yin aure da ke. Bana son ɓata miki ne shi yasa ban...”

“Ya isa haka, bana son wani tausayi ko wani abu daga gare ka. Amma ka sa wannan a ranka kowa ya ci zomo, ya ci gudu. Ka yi wasa da ni, kuma ina fata zaka cutu kamar yanda nake cutuwa a yanzu.” Sarat ta faɗa tana iya ƙoƙarinta ganin ta rike hawayen da ke son zubo mata.

Miƙewa tsaye Ammar ya yi yana ƙoƙarin zuwa kusa da ita amma ta ja baya. Jiki na mata rawa, ta fice daga ofishin. Koda ta saka ƙafa waje hawaye suka fara zubo mata, da gudu ta shige toilet.

Ammar bai kai ga samun lokaci na tunanin abinda ya faru yanzun ba, wayarshi ta yi ringing na kiran da tun ɗazu yake jira. Ɗaga kiran ya yi ba ɓata lokaci. Wanda ya kira shi yana ƙoƙarin gaishe shi Ammar yace
“Please Farouk mu ajiye gaishe-gaishen nan. Faɗa min komai ko hankalina zai kwanta.”

“Ok." Cewar wanda ya kira da Farouk. “Na samu bayanai da yawa cikin ƙanƙanin lokacin nan. Sai da ma nayi hacking duka wayoyinta. Na ɓata duka daren jiya ina karanta chatting ɗinta. Fatan dai ba zata ji haushina ba?”

“Ina jinka Faruk, ka faɗa min abinda nake son ji kawai.” Ammar ya faɗa tare da zaunawa dan kar ya faɗi.

“Ina tunanin abu ne da zamu iya saurin shawo kansa. Ta haɗu da wani saurayi ne a cikin gari... Suna magana amma kuma suna exchanging nude pics sosai. Saidai saurayin ya fara yi mata barazana lokacin da ya gano ƴar gidan mai Shakur Company ce. Da fari tana yin abinda suka ce, saidai a hankali ta fara yi musu tawaye, hakan kuwa ya sa abun ya juya kanta. Saurayin ya fara bibiyarta har zuwa ranar da ta zo gidan yayanka mutanen sun doke ta kuma sun mata barazanar zasu dawo idan ta faɗawa wani. Yanzu haka suna son ta same su a hotel ran asabar.”


“What? Innalillahi wa inna ilaihi raji'un." Ammar ya faɗa cikin tashin hankali.

“Bana tunanin babu abinda mutanen nan zasu yi mata. Amma inada sunan saurayin da kuma adress ɗinsa. Zamu iya cafke shi da mutanensa.”

“Nagode sosai da wannan aikin naka Farouk. Ka turo min duk wani abu da ka samu, zan turo maka ladan aikinka zuwa gobe. Ni zan ji da sauran.”

“Game da mahaifinka kuwa, zan yi maka bayani zuwa gaba idan mun haɗu. Har yanzu ina kan abinda muka tattauna a baya.”

“Ok, nagode Farouk. Na yarda da kai. Sai mun haɗun."

Ya kasa yarda har yanzu ana yin irin wannan abun. Bai taɓa tunanin Hafsat zata aikata hakan ba. Ta iya turawa wani hotunan tsiraicinta har ya yi mata barazana da su. Dole shine zai gyara komai tun da har ya saka kansa tsundum a ciki.

Hafsat zata ƙara tsanar sa idan ta san ya shiga rayuwarta amma idan hakan shi zai yi ya ceto ta, a shirye yake ya sake maimaitawa.


ƁANGAREN KHADIJA

Gaban madubi take tana shiryawa rai a jagule. Da ƙyar take iya jiyo me aminiyarta take cewa. Tana tunanin yanda zata yi ta cire layar hannun Zahara. Bata san meye amfanin wannan layar ko abinda yasa Amriya take son ta cire ta ba. Abinda kawai ta sani, shi ne ba zata so ta shiga tsama da wannan aljanar ba.

“Idan na matsa miki, faɗa min ya kamata ki yi Khadija.”

Juyowa ta yi ta kalli Salmah.

“A'a wallahi..ina sauraron ki.. kawai na ɗan yi nisa cikin tunani ne.”

“Ina faɗa miki, Mansoor ya nemi da na yi tunani akan tayin da ya yi min. Yace min yana son mu tsayar da magana kafin ya koma USA. Ni yana burge ni, kuma na san idan muka yi aure zan kamu da son shi, guy ɗin ne ya haɗu sosai. Amma ina tunanin anya zan iya jiran sa har na shekara ɗaya... Yace min zai yi iya ƙoƙarinsa ganin na je cen nima. Amma bana tunanin son ƙara barin garin nan.”

Miƙewa Khadija ta yi wannan karon !

“I'm sorry Salmah.. amma inada abubuwa da dama cikin kaina... Ban san me zan yi ba. Yanzun ma fita nake son yi amma zan dawo ba da jimawa ba, na yi miki alƙawari."

“Ina zaki je? Me yasa baki faɗamin komai ba? Lafiya babyn yake? Kina saka ni cikin damuwa Khadija." Cewar Salmah tana saukowa daga bisa gado.

“Kar ki damu, zan ji da komai. Na yi alƙawarin da komai ya tafi daidai zan baki labarin komai.” Khadija ta faɗawa ƙawar tata ba tare da ta yi mata wani ƙarin bayani ba.

Fita ta yi ta bar Salmah zaune cikin damuwa da ruɗu.


ƁANGAREN ZAHARA

Zahara ce ta fito daga office. Yinin yau sam bai mata daɗi ba, sai ma da ta ga Khadija tsaye bakin motarta tana jiranta. Ta yanke yin kamar bata ganta ba saidai tuni ta makaro domin Khadija ce ta ƙaraso inda take da sauri.

“Cen saurayinki... yanzu kuma ke...gaba kuma waye zai zo?”

Khadija jin saurayinta yazo gurin yarinyar nan, ta ji kalaman tamkar sukar wuƙa. Sai da ta jajurce kafin ta iya controling fushinta gaban Zahara. Ta zo ne aiwatar da wani aiki, dan haka ba zata so yin abinda zai kawo mata cikas ba.

“Ban zo nan dan faɗa ba, na zo ne mu yi magana."

“Babu maganar da zamu yi, yanzu na fito daga aiki kamar yanda kike gani, a gajiye nake dan haka ki min afuwa, bana da lokacin yin magana yanzu.” Zahara ta faɗa kafin ta gifta ta gaban Khadija da niyyar wucewa. Saidai Khadija ta fizgo hannunta da sauri.

“Please ki bani mintuna goma, ba daɗi ba ragi.”

Numfashi Zahara ta ja na wasu ƴan daƙiƙu kafin duk da haka ta yanke tafiya. Ba zai yiwu ta tsaya saurarar wannan matar ta faɗa abinda ita kaɗai ta sani ba.

“Wata ƙila ki yi nadamar tafiya ba tare da kin ji me zan faɗamiki ba."

Tsayawa Zahara ta yi, ta juyo a fusace.

“Barazana kike min yanzu? Ki saurare ni da kyau, ba zan bari a taka ni ba, ko ki tafi kowa ya je gida lafiya, ko ki tsaya ki ga ɓacin rai iya ɓacin rai.” Zahara ta faɗa da yanayin da ita ma bata san shi da ita ba.

“Me kike yi nan Khadija?”

Suka ji wata murya ta faɗa a bayansu. Dukansu sun san me wannan muryar ba kowa ba ne face Ammar.

Ja baya Khadija ta yi tare da kallonsa ta yi murmushi wanda da ka gani ka san ƙirƙirar sa ta yi.

“Na zo ne na ga Zahara..”

“Ko na kira Kamal ne?” Ammar ya tambaye ta.

“A'a... Tafiya ma zan yi yanzu. Zamu haɗu an jima.” Khadija ta faɗa tare da juyawa.

Komai ya tafi da sauri da ya sa Zahara bata san Khadija ta fizge layar hannunta ba.

Ammar tambayar Zahara ya yi da kallo. Ya san duka me yake faruwa amma baya son saka baki ne.


“Ko na zo na ajiye ki gida ne?” Ammar ya ce wa Zahara.

“A'a.” Ta

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login