Showing 66001 words to 69000 words out of 161239 words

Chapter 23 - KWARATA

Start ads

28 Aug 2025

615

Middle Ads

wani cire room kawai mu kirata da mother , shewa sukayi dukansu lokaci ɗaya suna cewa uwa...

"Yar gajeriyar dariya nayi cikin sigar barikanci na wuce ɗakina banyi musu magana ba , hotuna sukaci gaba dayi har na gama shiryawa nima na fito !

Ina fitowa suka ɗauki sowa domin sun san mother tasu ba daga baya ba wurin iya ɗaukar wanka , banje koya ba kuma babu wanda ya ɗorani nice na koya dakai na kuma ni na ɗaura kaina , banda uwar ɗaki nice uwar ɗakin kaina kuma nice uwar ɗakin wasu ,

Amisty ce ta bani kujerar roba na zauna, da "yan daba da duk wata kwartuwa mun hallara wurin, bayani na farayi musu kamar yadda muka saba a duk lokacin da muka zauna...

Hafsa kuwa ciro wayarta tayi ta faramin vidio kamar yadda naga ta koya kwanakin nan, saboda haka sai nayi shiru yayin da su Amisty suka ci gaba da goga bayani tare da ƙara ƙwarara wa kowa guiwar shi a cikin harkar bariki !

Komai ɓaro ɓaro sukeyi suna sakin maganganu yadda harshen kowa yake iya furtawa, Hafsa kuwa abinda yasa banyi mata magana ba na lura da halayyarta tana da saurin hasala sannan kuma tana da ɗauka da ajiyewa , na ukku kuma abinda na lura da ɗabi'ar ta zatayi tonan asiri haka kuma zatayi cin amana zata tona asirin wanda suke tare idan suka rabu ...

Ni kuma banda haƙuri idan abu ya ɓatamin rai saina bigi mutum nake samun natsuwa , tou zan ƙyale Hafsa amma nasan irin zaman da zanyi da ita , sannan nikam dai sirri na ƙarya takeyi taji shi kuma anƙi a rabun da ita dan idan har na rabu da Hafsa zata yankamin ƙunya biyu dani da "yan team inta zamu zama abokan hamayya , kuma babu abinda zai hana asirce asirice saboda su sun ta allaƙa da malam tsibbu amma maganinta ɗaya shine zan sace wayarta ta ɓace kwata kwata babu layi babu wayar bare kuma tabi tsohon tarihin jerin kira ta samu wasu lambobi, idan taƙamarta sabko tabbas ni a wurin na kwana ,

Har aka gama zaman ban sake cewa umm umm ba, bayan an gama duk suka zagayeni akayi ta hotuna , duk wanda yaga hotunanmu yasan ni iskanci na ya fita daban a cikin nasu, yadda suka bani shugabar iskanci tabbas iskanci ya fito a tattare dani...

Bayan an gama hotuna muka fito ƙofar gida , saman motar Hafsa nayi tsalle na haye , Hafsa tace bari in ƙara ɗaukarki hoto murmushi nayi tare da cewa ngode , ɗaukana tayi nanma kowa ya ƙara yayyaɓeni sai an mana maza da mata duka Hafsa taci gaba da bamu filasha !

Saida ta gaji da ɗauka sannan mukayi sallama da ita , ta wuce gidansu mu kuma muka koma namu gida , dukanmu a ɗakina muka sauka , har dare suna nan domin Amisty zata kwana wurina ne kuma ma dai ta dawo wurina da zama kwata kwata...

Bansan abinda yasa ba kuma ban tambayeta dalili ba , sai dare sosai su A ` i suka tafi gida , Nana da Karima kowa ya shige ɗakinshi muka rage daga ni sai Amisty, addu'a nayi na kwanta bacci ,

A ɓangaren Hafsa kuwa dan ta wulaƙanta ni ta tozarni a idon Dikko idan ina da sauran mutunci ko ƙima ta kakkaɓe a wurin shi , duk hotunan data ɗauka gaba ɗaya ta tura mishi su , da vidio maganar dana fara da kalaman batsar dasu Amisty sukayi , da kirana da uwar gidan kwarata da akeyi duk saida ta bawa Dikko labari bayan ta gama tura hotunan da vidio ',

Idan ran Dikko yayi dubu saida ya ɓaci amma bai nunawa Hafsa ba ranshi yayi mishi babu daɗi ba dan baiyi tunanin irin wannan hotunan zata riƙa kawo mishi ba , kawai dai ya ɗauka hotunan Sultana zata turo sai kuma idan tana zaginshi sune kaɗai zata faɗa , amma wannan vidio ya girmi ganin idanuwanshi maganganun sun girmi jin kunnuwanshi ,

Tabbas zai takawa Hafsa burki da irin wannan vidio kuma zai tsawatar da ita zai gwalashe abun idan ba haka ba irin wannan vidion na An mata zasuyi ta yawo a social media shi kuma idan har haka ya faru baiji daɗi ba,

Tunani dai barkatai a zuciyarshi , amma ranshi da zuciyarshi yafi bashi cewa kayi mata magana gaskiya shekaru biyu idan suka tafi a haka kaga zakayi takon saƙa da karuwa mutuncinka martabarka da ƙimarka zai zube a wurin al'umma ga siyasa bata raina abun magana, sai ka tsaya takara zaka gane abun ya zama shirme, shawarar da zuciyarshi ta yanke shine ya fita daga harkar taron yara don asali nasaba da mutunci gidansu ba iri ɗaya ne dana gidansu Sultana ba.

Burun duniya akan shi ɗaya tal mahaifinshi ya dogara yayi tsayuwar arfa wurin ganin ya zama mutumin kirki ya fito cikakkan mutum ya kashe kuɗaɗe da yawa wurin ganin ya tsaida ni a saman ƙafafuwana , mutane suna cewa duk "ya "yan da aka ɗauki soyayyar duniya aka ɗora musu gurɓatacci ne , mafiya yawansu basu da tarbiyya , ni kam ba lalatacce bane domin idan nayi duba da yadda nazo...

Tsoki yayi tare da kiran Hafsa yayi mata tatas yace daga ita harma Sultana duk zaici mutunci su bayasan maganar Sultana haka kuma itama bayasan ta sake shiga sabgarshi ko kiranshi ta sakeyi ko text wallahi sai yasa an kulle mishi ita , yafa ci uban Hafsa sosai ya ƙara da cewa itama Sultanar ta sake ambatar sunanshi wallahi zaici ubanta ne, saida ya tata iskanci mai isarshi ya kashe wayarshi,

Al ' Ameen yace mai gida lafiyarka kake ta faɗa , idanuwa jajir Dikko yace Al ' Ameen idan aka ce maka na taɓa zina tsakaninka da Allah zaka yadda ? Al ' Ameen yace mema yasa kake faɗar wannan maganar don Allah ka daina abinda ma bazai taɓa yuwuwa bane ba...

Idon Dikko cike da hawaye yace kasan yarinyar dana shaƙe a asibiti ? Al' Ameen yace Eh nasanta mai gida , Dikko yace kaga ai yarinya ce sosai ko ? Al ' Ameen yace Eh , Dikko yace wallahi da nayi auren wuri ina iya haifar yarinyar nan , amma tsautsayi da ƙaddara yasa na saki wani irin ƙatoton layin da inaji kamar in cakawa kaina wuƙa in mutu kawai in huta,

Murmushi Al ' Ameen yayi tare da cewa haba mai gida ina kai ina haifo mai shekarun yarinyar nan , da kayi aure kam da wuri baka tsaya karatu ba kuma gashi har yanzu duniyar nemanta akeyi duk wanda kuɗi yayi ma yawa so kawai yake a kirashi ranka ya daɗe , duk dai haka gaskiya baka haifi yarinyar nan ba , tsoki Dikko yayi tare da ɗaukar wayoyinshi ya shige ciki , gefen gado ya zauna tare da zagba tagumi ya fara tuno wa kanshi ko shiɗin waye.....


*_WAYE DIKKO...?_*

Dikko Umar Kurabau shine cikaken suna na...


Mu cikakkin asalin "yan cikin garin katsina ne , bamuyi rayuwa a ƙauyen kurabau ba haka mahaifina da kakana basu rayuwa a wannan ƙauye ba , amma kakan dadyna shine yayi rayuwa a cikin wannan ƙauye dake ƙarƙashin kauyen rimi local government...

Mutane ne masu cikakken arziƙi da wayewa kuma sarautar kauyen a gidansu kakana take wacce suka gada suma tun iyaye da kakanni , ko a wancan lokacin mutanen kurabawa tuni su wayayyu ne kuma tuni suka waye da ilimin zamani !

Kakan dady na duk da yake bakauye baya da kidadanci haka kuma bashi da jahilci , wayyen tsoho ne da yasan rayuwa , kuma tsohone mai cikakken ilimin addini,

Abinda ya kawo kakana cikin birni shine neman ilimin zamani , kuma shima mahaifinshi shine mutumin daya fiddoshi dan neman ilimi bayan ya tabbatar daya haddace al'kur ani mai girma a saman kanshi kuma yasan littafai na musulinci .

Karatun boko bai wani bashi wahala ba saboda yana da ilimin addini sosai , saida kakana ya gama karatun sikandire sukul { Secondry school } ya koma kauyen kurabau,

Mahaifinshi yace tunda ya ɗagawa ƙauyen na wasu shekaru ya haƙura kawai ya koma cikin garin da zama , dan a samu ci gaban rayuwa !

Mahaifinshi da kanshi yazo ya nema mishi wurin zama sannan ya bashi kuɗaɗe ya kama kasuwanci ya nemi abinda zai dogara da kanshi, dan a wancan lokacin idan mutum yayi secondry sch anan yake tsaya dan duk wanda yazo wannan matakin gani ake an ƙure.

Allah kuwa ya saka ma nemanshi albarka dan kano yake zuwa sarin atamfofi da shaddoji da yadika ,kafin shekar ya zagayo abubuwa sun fara canzawa domin Allah yasa ma neman albarka kuma Allahn ya yaddar mishi ! Dan ubangiji dayace maka zama zaka zama....

Haka rayuwa taci gaba da tafiya cikin ƙanƙanin lokaci sunan Dikko Muhammad wato kakana ya fara zagawa a cikim garin katsina dan zuwa wannan lokaci ya baza yara suna neman mishi kuɗi dan kasuwar tafi ƙarfin mutum yanzu, kuma mutum ne shi mai kauta ,

Shi kuwa Muhammad baban Dikko wato kakan babana ganin dukiya ta fara yawa hankalinshi ya fara tashi gashi har yanzu Dikko baiyi auren farko ba , kuma zuwa wannan lokaci ya rage zuwa gida dan sai yayi wata shidda ko fiye da haka baije gida ba , idan yaje malam yayi mishi magana yana daɗewa baizo ganin gida ba sai yace abubuwa sunyi yawa yanzu ma dakel ya samu yazo,

Ganin haka yasa malam ya yanke shawara aura wa Dikko mata kuma "yar nan cikin ƙauyensu dan malam yace idan "yar gida ce yake aure dole za'a riƙa ganinshi ko baizo dansu ba zaizo dan matarshi,

Haka kuwa akayi malam ya aurowa Dikko mata bada saninsa ba yasa aka kawo mishi amarya har katsina, saida aka kawo amarya akayi masa bayani malam ya auro masa ita , bai wani ji komai ba yace Allah ya basu zaman lafiya,

Zaman lafiya sukeyi da matarshi Binta saboda matace mai haƙuri da kuma kauda kai da duk wani abu na rayuwa , saboda itama sai tayi wata nawa bata ga Dikko ba dan shi ba auren yake saurare ba duniyar kawai yake nema ita kuma Binta bata wani damu ba tunda ci da sha har sutura bata rasa ba , idan Dikko yazo mata as miji zasuyi rayuwar aure idan baizo ba babu abinda ya dameta...

Haka dai rayuwarsu taci gaba da tafiya , kuɗin Dikko kuma har an fara zarginsu a cikin gari cewa tsafi yake yi , dan shima kanshi zuwa yanzu baisan iyakar abinda ya mallaka ba , koda Binta ta samu ciki gida Dikko ya maida ita ta aihu , tunda ya kaita bai sake komawa ba har ta aihu ta gama wanka baije ba, abinda ta aifa ma bai gani ba babanshi yayi duk abinda akeyi ma duk macen data aihu komai anma Binta da ɗanta da yaci suna Ummar wato mahaifina...

Har Umar ya iya tafiya Dikko bai dawo ba kuma bai aiko ba yana can yana neman duniyarshi danshi matan ma basu ne gabanshi ba kuɗi kawai, baisan komai ba kuma baya gane komai sai naira , abun ƙauye aka fara tira iyayen Binta su kashe auren su mayar da Baban Dikko ɗansu tunda dai ɗanshi ya zama ɗan iska, Binta kuwa ta kifa kanta ƙasa tace ita duk duniya babu wanda ya isa ya kashe mata aure,

Ganin za'a kashe mata aure dole yasa ta saɓe abunta ta dawo wurin mijinta , koda Dikko ya dawo gida ya sameta yaji daɗin dawowanta yace tayi haƙuri abubuwa ne sunka sha mishi kai da yawa da yawa shi yasa baizo ba , tace ba komai da yake itama bata da matsala.

Can ƙauye kuwa da aka tabbatar da Binta ta koma wurin Dikko iyayenta sunsha zagi da tirr da Allah wadai da halin ɗiyarsu, basu da yadda zasuyi tunda suma basu san Binta zata koma wurin Dikko ba dan batayi shawara dasu ba ta tafi.

Tun lokacin da Binta ta dawo wani abu bai shiga tsakaninta da Dikko ba , ita kanta wahalar gani yake mata dan yanzu kasuwancin nashi ya fara ketarawa , kuma babu damar taje ta faɗa gida dan tun abun baya damunta yanzu harya fara damunta.

Yau kam ta hana idonta bacci ko Dikko zai kai safiya bai dawo ba zata jirashi kuma yau za'ayita ta ƙare , koda Dikko ya dawo gida daɗin bakin yayi ma Binta kuma ta haƙura amma kam a daren nan sunɗan caskaɗe dan tunda ta dawo wannan shine haɗuwarsu na farko,

Tou haka kwanciyar auren ta koma duk lokacin da Dikko ya kwanta da binta wani rantsetstsen rabo zai fita , adadin yawan "ya "yansu adadin yanda Dikko ya kwanta da ita , yanzu tayi yara bakwai ,

Kuma rabonshi da gida tunda ya maida Binta aihuwar Babana bai sake zuwa ba har Binta tayi "ya "ya bakwai , saida itace kaɗai take zuwa, mahaifin Dikko kuwa yayi danasanin kai Dikko birni ,

Haka rayuwar taci gaba da tafiya saida malam ya rasu Dikko yaje ƙaunye ta'aziyya, mahaifiyarshi kuma tayi kuka da tir da rayuwar birni, da yake shegen wayau ne dashi lallashinta yayi saida ya kwantar mata da hankalinta sannan yace tunda bata da komai a ƙauye zai tafi da ita birni !

Haka kuwa akayi bayan addu'an bakwai suka tattaro suka dawo tare da kakar babana, zaman kakarsu dady ta gano Dikko bata mace yake ba , ta jinjina wa Binta da wannan haƙuri, ita dai batace komai ba tana dai kallon ikon Allah..

Ummar wato Dadyna, yana gama secondry sch Dikko ya korashi ƙasar waje karatu dan bayasan ganin yara kusa dashi, tafiyar Ummar babu daɗewa kaka Dikko ya tsirawa kanshi aure rana guda aka kawo mishi mata biyu shi mai kuɗi, idan an haɗa da binta sun zama 3 kenan.

Nan fa haihuwar gasa ta tashi mata sunga kuɗi duk shekara sai an direwa Dikko "ya "ya amma banda Binta dan ita tana mamakin ma yaushe Dikko yake kwanciya dasu sakamakon ita ? Ko kuwa dandai su shine ya auro su da kanshi Oho,

Tunda Dady ya tafi karatu Kaka Dikko ya hanashi dawowa , da yaga mai zai matsa mishi saiya dawo ya tusheshi da kasuwa can yace ya nemi kuɗi ya manta da rayuwar nigeria shima haka babanshi yayi mishi.

Duk da Ummar yana ɗan farko saida Binta tayi magana a maido mata ɗanta karya halaka cikin duniya , Dikko yace bazai maido ba, shi ya akayi bai ɓace ba da babanshi ya kawoshi birni, dole Binta ta haƙura ta dainawa Dikko maganar Ummar , itama kakar Dady tayi harta gaji Dikko bai dawo da Ummar ba,

Kwanci tashi asarar mai rai , abubuwa da dama sun faru a ciki kuwa hada rasuwar Kakar Dady , Dady kuma yayi shekaru kusan 15 yana ƙasashen yahudawa, tun yana marmarin gida shima harya goge ya janye zance gida a rayuwarshi.

Shi kuwa Dikko yanzu hankalinshi ya tashi saboda mata sun tara tulin ɗiya sai meeting ɗin kasheshi sukeyi su kwashi dukiya , wannan dalili yasa ya cire Binta a gidan ya sake mata mazauni ita kaɗai daga ita sai "ya "yanta dan ya lura itace kaɗai take masa san tsakani da Allah.

Tou wannan dalili ne yasashi ya ɓanɓako dady daga ƙasar waje shi kuma zuwa wannan lokaci baya san dawowa nigeria dan shima ya riga ya kafa kanshi a can yayi kuɗi wanda saida suka tadawa Dikko hankali duk neman duniyarshi, yace Ummar da nasan zakayi kuɗi duniya da na zauna na mori rayuwata ban ba kaina wahala wurin tara abun duniya ba,

Dikko dai bai ɓoyewa Ummar komai ba ya sanar dashi cewa mata zaku kasheshi su gaji duk dukiyar daya sha wahala wurin tarawa , dan haka abinda Dikko yayi shine , duk abinda ya mallaka tsakanin gidaje filaye motoci filazozoji Dikko ya kasasu 10 ya bawa Ummar kashi 9 sannan yayi rabon gado da kashi ɗayan daya rage,

Duk wacce ta samu kuɗin nan ruɗewa tayi dan wannan kuɗi da Dikko ya bada gado wa duk "ya "yanshi iyakar almubazzarancin mace rayuwar duniya dai ba ƙiyama ba ya isheka, ganin kuɗaɗe a hannunsu kuma sun tabbata babu saura yasa kowa ta tsige aurenta ta kama gabanta...

Aure Dikko ya nemowa Dady ɗiyar wani aminishi suma attajirai ne na gaske , babu wani ɓata lokaci suka anshi tayin Dikko bikin bai wani ibi lokuta ba aka daura

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login