Showing 159001 words to 161239 words out of 161239 words

Chapter 54 - KWARATA

Start ads

28 Aug 2025

618

Middle Ads

dani nima banda ruwa da kowa babu mai so na sai Allah banda wanda zai nunamin kyakkyawa ko mummuna duk rayuwar dana ɗauko ita nakeyin abuna gani yau na zama marainiya.....

Kallona Dikko yayi yace ke ba marainiya bace Allah yana tare dake kuma Dikko yana tare da rayuwarki , duk wanda kika ga ya mutu kwananshi ne ya ƙare ki daina mishi kuka kiyi mishi addu'a , nace to , Dikko yana gidanmu shi ya tayani zama a ɗakina yana min nasiha sai 1:39am yabar gidanmu ,

Bayan tafiyarshi ma na tuna banyi magib ba bare isha'e , fita nayi nai alwallah nazo nayi sallah nayi karatun al'qur ani mai girma tare da roƙawa Babana rahma a wurin ubangiji , har gari ya waye banyi bacci ba kuma banje ɗakin da aka kwantar da gawar Babana ba ,

Tunda safe gidanmu ya fara ɗaukar mutane su Amisty da suka zo ɗakina suka sauka , suna shigowa ni kuma na tattara wayoyina da tawa data Mamy na fita , ɗakin da aka kwantar da gawar Baba na nufa , har anyi masa wanka an shiryashi yana kwance a mankara , ina tsuguniya abinda ya tunomin shine ,

Ranar da muna zaune dashi a ƙofar gida nace Babana ina sanka ina kuma tausayawa rayuwata ranar da za'a wayi gari babu ɗaya a cikinmu , murmushi yazo ya tsayamin a rai da maganarshi da yace min ai bazai tafi ya barni ba , a bayyane nayi magana cikin kuka nace shine ka tafi ka barni...

Naci gaba da kuka mai tada hankali , ina Allah ya jiƙanka ubangiji yasa ka huta , Allah yasa can yafiye maka nan Allah ya sadaka da mala'ekun rahma ubangiji ya kauda kai akan duk laifukan da kayi masa ya yafe ma ya gafarta maka ya baka aljanna dan arziƙin annabi muhammadur rasulillahi sallallahu alaihi wasallam....

Zainab ce ta riƙeni duk gidanmu Zainab tafi kowa tausayi na tana so na , tace Sultana kiyi shiru don Allah , cikin kuka na rungumeta nace don girman Allah ki tasheni daga baccin nan haka nan wallahi zuciyata ta kusa ɓarewa ,

Haƙuri kawai take bani , ina nan zaune a ƙasa kusa mankarar Baba sai kuka nakeyi , bayan wani lokaci kuma maganar Baba ta faɗomin a rai da yace idan har na mutu karki sake kimin kuka addu'a zakimin shine kaɗai zai tabbatarmin da soyayyar da kike min , shiru nayi naci gaba da gumji ina addu'a wa Babana ,

Misalin 08:50am gidanmu ya gama cika duk ta inda baka tunani , 09:00am aka ɗauki mankarar da Babana yake sama kwance za'a fita dashi domin salla tar gawarshi shi , shikenan Baba zai tafi inda bazan sake ganinshi ba bazan sake jin muryarshi ba har abadan abada duk soyayyar da yakemin ya tafi da gaske ya barni.... Sake ɗaukewa nayi na ƙara somewa !

Har akayi ma Baba sallah aka kaishi gidanshi na gaskiya Sultana bata san inda kanta yake ba , zata dawo² shiru har la'asar babu Sultana babu labarinta , duk wani taimako daya kamata ayi mata anyi amma har 5 na yamma bata dawo ba ,

Dan haka yasa Dikko yace a fito da ita a kaita asibiti , Zainab ce akan Sultana sai firfita take mata dama itace ta kula da ita a asibiti lokacin da Dikko ya farke mata mutuntakarta , da taimakon wasu matan aka fitar da Sultana aka sakata a mota da Zainab kaɗai aka tafi sai Ashiru dake tuƙi saishi Dikkon.

Asibiti mai kyau aka kai Sultana likitoci suka rufa akanta dan ceto rayuwata , amma duk yadda akayi saida Sultana ta kwana huɗu bata cikin hayyacinta , ga dai ido tana kallon kowa amma ƙiri² bata iya magana , bata ci bata sha sai kuka , hankalin Dikko idan yayi dubu ya tashi ya lallashi Sultana har ƙarfinshi ya ƙare amma Sultana taƙi tayi magana da kowa , da tsiya² Dikko ke bawa Sultana ruwan tea shima idan tasha saita amayar dashi ,

Zainab itace ta bawa Dikko shawara ko a riƙa ba Sultana fura duk tsiya dai ko tayi amai wata zata tsaya , Dikko yasa Ashiru ya samo fura ake ba Sultana amma ko tasha sai ta dawo da ita ,

Dikko yace haba An mata wai me yasa kikeyin haka ? Gaskiya banajin daɗin abinda kike yi ko nima so kikeyi in mutu shikenan sai ki huta ? Kiji tsoron Allah ki tausayawa rayuwata haka nan mana , ke shikenan abu baya wucewa wurinki ? Kina nufin ke Allah bazai jarabce ki ba ? Ko akanki ne aka fara rashin iyaye ? Ba'a fara a kanki ba , ba kuma za'a gama akanki ba , mutuwa tana nan tana zagayawa tsakanin rayuwar kowa kuma babu bararre a duniya duk wanda yazo sai ya koma , ina ilimin naki da kike alfahari kina dashi ? Wannan shine sakamakon da zaki sakawa rayuwa dashi ? Shi kukan mutuwa da kika ganshi ba'a gamashi kuma baya ƙarewa har sai ranar da rai ya ƙare kiyi haƙuri don Allah .

Murmushi Sultana tayi mai ciwo dan gani takeyi Dikko baima da hankali , ya za'ayi ta daina kukan rashin Babanta ? Ubanda ya ɗauki soyayya duniya ya ɗora mata , cikin "ya "ya sattin da wani abu itace kaɗai ya ɗauki duk soyayyarshi ya bata , taya ma zata manta Baba ? Taya zata daina kukan rashin shi ? Duk ma wanda yace tayi haƙuri ta daina kukan rashin shi wallahi mahaukaci ta ɗaukeshi ,

Banyi magana ba na sauko daga saman gadon na fice daga ɗakin , Dikko ya biyo bayana yana ina kuma zaki ? Banza nayi dashi ban juya ba kuma bansan abinda ya sameni ba bana iya magana sai hawaye , da sauri ya iskoni yasha gabana ina zaki nace ? Kaucewa nayi daga inda ya tsaya na tun kari hanyar fita asibitin ,

Zainab ma tambayata takeyi ina zanje duk banza nayi dasu nayi wurin mota na tsaya dan gida nake so inje , murmushi Dikko yayi mai nuni da baya san abinda nakeyi amma bai sake magana ba ya buɗemin mota na shiga na zauna ya rufe itama Zainab shiga tayi Ashiru ma haka amma yanzu Dikko yaja motar rashin a matuƙar ɓace ,

Har muka iso ƙofar gida babu wanda yayi magana , bayan yayi parking Zainab ta fita nima na fita Dikko kuma bai mana magana ba yaja motarshi yabar anguwarmu ranshi a ɓace , jiki a mace na shiga gida Zainab tana bina baya har ɗakina dan "yan gidanmu sai sharholiya sukeyi yadda kukasan ba mutuwa akayi ba , wayoyina Zainab ta kawomin tare damin bankwana tace Allah ya ƙaddara saduwarmu ,

Taci gaba da cewa yau kwanan Baba 5 da rasuwa ke kuma kina asibiti tunda aka ɗaga mankarar shi baki sake sanin abinda kikeyi ba , wannan gida naki ne babu maishi duk duniya saike tou a cikin kwanaki biyar da rasuwar Baba har sun siyar da gidan sun raba kuɗinsu an bani nidai gaskiya ban ansa ba , kuma wanda ya sayi gidan yaba kowa daga yau zuwa gobe ya tashi .

Murmushi nayi tare da jinjinawa Zainab kai , ansar wayoyi na nayi ta fice ɗakin , tashi nayi na dudduba , kayana masu kyau da tsada duk an sacemin su kaf har kuɗaɗene gaba ɗaya an dauke su , tsoki nayi na fita nayi wanka na wanko bakina nazo nayi sallah magrib na gamesu da isha'e , ƙarfe 10 na dare kuma Dikko baiyi zuciya ba yazo ,

A saman dakali muka zauna , ya ƙaramin gaisuwa tare damin nasiha yacemin kuma idan Allah ya kaimu zaije Abuja kwana biyu zaiyi ya dawo idan ya dawo zai tafi dani , cikin kuka nace to kuma kayi haƙuri ɗazu da nayi maka shiru , jawoni yayi jikinshi cikin sigar rarrashi yace ba komai An mata ai kinsan bana iya zuciya dake ,

Murmushin ƙarfin hali nayi cikin shashshekar kuka nace Allah yasa kaima kar a kashe ka , yace shima da suka kashe shi sai kuma ya kauda maganar da cewa tunda har An mata tayi rashin lafiya nima banajin daɗi ,

Bai dai wani daɗe ba mukayi sallama dashi har mota na rakashi ya bani kuɗi masu yawa yace in ajiye mishi nace ni sata akemin yanzu , yace idan an sace ba komai idan baki da kuɗi na arami ki , nace nidai bana ajiyewa haba yi haƙuri ki ajiyemin , nace kuɗin sunyi yawa bazan iya ajiyewa ba , kallona yayi yace tou ibi wanda zaki iya ajiyemin , nidai ko ɗaya bana iya ajiyewa ,

Tou ɗauka na baki duka , zaro ido nayi banma yi mishi magana ba na wuce da sauri gida , An mata zo , da Allah kizo kiji , ban dawo ba , murmushi Dikko yayi yaja motarshi ya tafi...

Jiya Dikko ya koma Abuja kuma munata waya dashi yana gayamin ya ƙagara gobe tayi ya dawo kuma yacemin yanzu idan zan koma makaranta Abuja zai tafi dani bazan sake makarantar kwana ba , yace shine zai riƙa kaini yana ɗaukoni wai sai muzo katsina juma'a da daddare mu riƙa komawa lahadi da daddare , bawan Allah shi kaɗai ke lissafin shi , haka dai ya ƙari surutunshi yamin saidai safe.

Muna gama waya da Dikko aka aiko kirana , dan haka na ajiye wayar na fita , Al ' Ameen na gani ƙofar gidanmu bayan mun gaisa yacemin mai gida yace nazo na ɗaukeki ki gano wani gida idan yayi miki yana so acan zaki koma da zama , murmushi nayi nace aiko yanzu muka gama waya dashi bai faɗamin zaka zo ba ,

Al ' Ameen yace nidai shine ya aiko ni , ni kuma nace tou bazanje ba na juya da niyar komawa gida , matan dake bayan mota suka fito kaca² muka fara kokowa har sukayi nasarar dannani a mota Al ' Ameen aja muka bar ƙofar gidanmu...





07/10/2019


*JAMILA MUSA....*💅🏻







An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login