Showing 102001 words to 105000 words out of 161239 words

Chapter 35 - KWARATA

Start ads

28 Aug 2025

614

Middle Ads

da sarƙa suka tafi dani ofishinsu...

Suna zuwa office sukaci gaba da dukana babu ji babu gani , sunma hanani nayi magana bare naji laifina ? Saida suka min lullusar fitar hayacci sannan aka wurgani cikin cell aka rufeni ,

Saida na dawo hayyacina naga Bello gefena yana kyalkyalamin dariya , ƙarami na gefe sai kuka yakeyi , goge hawaye nayi tare da cewa me mukayi haka abu babu mutunci ? Dariya Bello yaci gaba dayi yana shan lolypop inshi...

Ƙarami na kalla nace meye wai ? Cikin kuka yace wai rafe naji dai suna cewa , cikin ɓacin rai nace rafe me ? Miye rafe kuma ? Ƙarami yace nima ban sani ba kawai dai haka naji suna cewa , tsoki nayi zuwa can nace waye yayi rafe ɗin ? Cikin kuka yace mu duka naji suna cewa , har yanzu Bello dariya yakeyi yana shan lolypop , raina naji ya ɓaci na tashi nayi kan Bello naci gaba da dukanshi babu ji babu gani ina cewa me mukayi ne ...?

Dariya Bello yakeyi yana cewa wallahi hauka yasa suka kawoku , ni kaɗai nayi kuma yarinyar da kanta tacemin tana so in rantsar da ita , itama ta zama cikakkiyar mace kamar kowa , tou dan nayi abinda takeso sai azo a rufemu , ai godemin ma ya kamata suyi , shaƙe Bello nayi sosai tare da cewa itama ka zuƙe.......?

Bushewa yayi da dariya to me ake jira da abun kwaɗayi.... ? Yau taji abinda uwarta keji , da sauri na rumtse idanuwana dan naji kaushin maganar Bello a raina , murmushi yayi tare da cewa kaji babu daɗi ko ? Tou ai itama uwar ta tuni na bata alƙalamin daraja kuma yanzu nan zata zo ta fitar damu dan nace idan har ta bari muka kwana sirrinta a buɗe yake dan ina da babbar sheda ,

Kallon Bello nayi idona cike da hawaye nace hajiya ma .....? Murmushi Bello yayi yace harda tukwuici take bani ma , kuka naci gaba dayi dan banji daɗin abun ba , daga haka nayi shiru na samu wuri na natsu muna jiran tsammani...

Hajiya itace tayi cuku² dan Alhaji shine yasa aka kamo Bello kuma Bellon yace tare mukayi kowa saida ya zagaya sau biyu domin ya buɗe mutuntakar a yarinyar yadda ya kamata !

Saida Hajiya ta saki kuɗi sosai tare da ƙaryata zance mijinta cewa ba Bello ne yayi wannan aika ² ba wasu daban ne sukayi kuma suka gudu haka nan aka ɗaura alhakin tuhuma akansu yara marayu basuji suka gani ba sai Allah ya saka musu...

Saida aka kai ruwa rana sannan muka fito , Bello yace mena faɗa muku nace muku zamu fito babu ɓata lokaci , haushin sa kawai nakeji domin naji ciwon wulaƙantawar da yayiwa yarinyar da nake ma kallon ƙanwata , kuma naji ciwon keta mutunci mahaifiyata Hajiya da ta ɗaukeni matsayin ɗa , kuma nima daga wannan lokaci na ɗaura ɗamarar saina masa yaji idan da daɗi !

Alhaji kuwa korar kare yayi mana daga gidanshi bayan yayi maganganu masu zafi da ɓatanci akanmu , kayanmu muka kwashe daga gidan Bello ya bamu mazauni a gidansu...

Duk lokacin dana kalli Bello sai naji kamar in haɗiye zuciya in mutu saboda tsabar baƙin cikin abinda yayiwa mutane masu mutunci , koda zai fita da daddare binsa nayi domin na fara harin rayuwarsa ,

Gidan caca muka nufa dashi , shine zuwana na farko dan kallon wasan da Bello zai buga , bayan yayi "yan al'adunshi ya binne ya ɗaura , hankalina ya tashi ganin tulin kuɗi da aka zuba , cikin ƙanƙanin lokaci aka fara gabatar da wasa , an ɗauki lokaci mai tsayi ana gwabzawa bayan wasan yayi zafi Bello ya lashe wannan makudan kuɗaɗe ,

Bayan ya kwashe kuɗinshi aka fara shagali , kwalaben giya suka fara wali da dai duk wani mai ɓatar da hankali , ina cikin ɓacin rai dan haka bansha ba , amma Bello yace idan nasha zan rage damuwa , dan haka na ansa nasha cikin ƙanƙanin lokaci na nemi damuwa na rasa !

Uwar masu gida labarin dai bazai buɗu duka ba , dan wasu labaran bai kamata na faɗa miki ba , mu tsaya haka nan , domin nima na zama atsabibin matsafi dan ko magana nayi bata faɗuwa ƙasa na koma kamar wani mai kambun baka saboda tsabar neman asiri irin nawa !

Daga nan na shiga wasan caca nima , naci gaba da harkar mata , shaye² da duk wani abunda ya zama zunubi , nayi nisa banajin kira , sheɗan yaci gaba da busamin sarewar halaka na shi , ga Bello bashi da ƙanne ,

Bayan ƙarami ya gama secondry sch yacemin bazai ci gaba da karatu ba , nayi juyin duniya yacemin daga haka ya tsaya , to ni na bashi gidan zama wanda a caca na ciwoshi , kuma ni na bashi kuɗi yaci gaba da kasuwanci , kuma duk matan daya aura nine na kashe kuɗi nayi masa hidima ,

Ƙarami bai daɗe da aure ba Malam ya saki wasan , wato ya mutu , bayan yasha doguwar jinya an girbi abinda aka shuka domin aikin tsubbu ɓata ce , ya lalata maka zuri'arka ga dakon zunubi , wasu an ɓatar an raba an haɗa dan dole an talauta wasu an raba aure an raba uba da ɗa anyi an gama dai duk an tafi an iske Allah....

Bayan ƙarami yayi aure aka barni daga ni sai Bello mukaci gaba da gurza rayuwa , har Allah yasa ya samu yarinyar da yake mugun so , kyakkyawar yarinya mai hankali da biyayya Bello ya mutu akan yarinyar nan , sukaci gaba da soyayya , na tambayeshi ko itama dai kamar sauran ? Yacemin a , a wannan ta aurece gaskiya , naji daɗi sukaci gaba da zuba soyayya sun shaƙu sosai tarayyarsu abun burgewa ,

Basu wani daɗe suna soyayya ba sukayi aure , lumshe ido Babana yayi sannan yaci gaba da cewa ango na shirin shiga ya angonce Binna ya anshi budurcin matar Bello , Bello yayi kuka saida yayi jinya gashi kuma yana mata san da baya iya rabuwa da ita , uhum tafasha azaba yarinyar nan , bayan Bello ya samu sauƙi akaci gaba da abota ,

Nima yana nan zai rama ashe , to yanda kasar suri bata cuwuwa ga bakin duk wani bil'adama haka Uwar masu gida tafi ƙarfin Bello dan yasan idan yace akanki zai ɗauki fansa tabbas nima zan rama akan "yar sa , shi yasa ya matsamin na sakaki a caca , hawaye ya cikawa Babana ido ,

Yaci gaba da cewa yasan duk duniya ya cire soyayyar Allah da manzan sa babu wanda nake so a faɗin duniyar nan bayan ke , tabbas yasan zanci caca shine suka juyarmin da hankali ta hanyar bani asiri cikin abunsha , bayan sunyi galaba a kaina suka rasa abunyi , shawarar abokinmu ya nema shine yace yasan wani da yasan Dikko , yace idan aka kaiki a wurin bazan iya ja da hukuma ba , hankalina ya kwanta da naji wurinshi kike nasan babu abinda zai faru ,

Ashe shima sun shirya mishi gadar zare , ɗan masu aikin gidansu shine yayi jagoranci , cikin kuka Babana yace aka ciwa "ya ta mutunci , haka na gudu na ɓuya kamar ƙolo na boye saboda kunyarki , duk da nayi haƙuri ban ɗauki fansa akan abinda Bello yayi ba duk da haka bai faru ba ,

Amma dana biyewa sharrin zuciya gani takaini ta baro ni , murmushi nayi nace ba komai Babana na yafe maka , kuma wannan abun ka ƙaddara babu abinda ya faru , !

Amma me yasa ka bar iyalinka cikin wahala ? Tsoki yayi sannan yace nima haka aka barni a saman titi bansan mai kyau ba bansan mara kyau ba , banda mai nunamin kyakkyawa ko mummuna , babu wanda ya kula dani shi yasa nima na saki kowa yayi rayuwarshi ,

Baba Allah fa yana kallonka , ka karanta kuma kaji ka gani kuma kasan abinda Allah yace akan iyali , girgiza kai yayi tare da cewa kar muyi haka dake Mamana , banasan maganar su , tou Babana amma me yasa baka aiki ne ? Wannan ra'ayina ne , caca na zaɓa kuma zanci gaba bazan daina caca ba sai numfashina ya ƙare , cike da damuwa nace ko kana da dalili ne ? Uwar masu gida mubar maganar nan ,

Tou Babana ina Sahura ? Kuma me yasa kayi kangara kana ƙarami ? Murmushi Baba yayi tare da cewa wannan kangara wani aiki ne malam yayi akan wani yaro dan ya lalace , matar Babanshi tazo ayi mata aiki ne , sai abun ya dawo kaina ,

Matar ta dawo ta faɗawa malam buƙata bata biya ba , can wurin binci kenshi ya gano inda aiki ya sauka kuma ya warware komai , idan dai kayi mugunta tou ka daina saurin rufe ƙofa domin dawowa takeyi , Sahura kuma tana can gidanta bana dai zuwa gaskiya...

Tou ita Inna baza ta dawo ba ? Manta da ita gani nan na isheki taje can tayi ta zuciyarta , kallon agogon hannunshi yayi ya miƙe yana cewa bani makullin motarki , miƙa mishi nayi ya fita yana mita ba'a kawo mishi kuɗin wayoyinshi ba , gaskiya Babana bansan irin halinshi ba , dandai yaƙi yadda ya faɗamin komai duk haka ya bani labari nidai a duƙunƙune....

A ƙofar gida ya anshi kuɗin wayoyinshi yayi gaba , "yan gida kuma cewa sukeyi da wani yake da motar nan sai Baba ya siyar da ita amma da yake ta Sultana ce komai daren daɗewa zai dawo mata da abinta , saboda kar yamin faɗa raina ya baci shi yasa baiji a ina na samu mota ko yamin faɗa ina hawa mota ba ,

Haka dai rayuwa taci gaba da tafiya , Babana yake amfani da mota ta , Bello ya fita harkata nima na fita harkashi , d c o babu ruwana dashi , Hafsa da Amisty banda labarinsu , su A ` i ma bana shiga sabgarsu , mijin Zalifa da Zalifar duk na daina jinsu , Alaji kaɗai yake zuwa fira danshi ya matsa aurena zaiyi...

Haka nan na tsira yin bedday babu gaira babu dalili , nayi i v nasa akaci gaba da rabawa , har a gidan radio nasa Alaji yakai sanarwa , manyan baƙi a wurin Baban Amisty mai yanka cake kuma Baban Hafsa , wurin taron kuma wani zuƙeƙen gidan Baban Hafsa , nayi gayya duk wani lungu da saƙo na zaƙulo manya ² karuwai nakai musu gayyata wanda duk ba ƙawaye na bane nasu Amisty ne ,

Al'amarin wannan taro ya karkato da hankalin jama'ar gari a kaina dan ban ibo abun da wasa ba , kowa da abinda yake faɗa akai na yayin da wasu mutane suka cewa taron iskanci ne ba wani taron birthday ba ,

Hafsa kuwa Amisty tayi mata waya ta faɗa mata cewa zanyi birthday amma taga venue gidan shaƙatawar Dady inta ne , yaushe ne ake taron Hafsa ta tambaya ? Amisty tace mata ranar laraba , Hafsa tace tou Allah ya kaimu zata ga yanda zan wulaƙanta ta ....

Nima da Nana ta bani labari dariya nayi tare da cewa Nana nima zan wulaƙanta ta yayin da taga Dad inta ya yanko cake ya rungumeni yana bani a baki na , itama Nanar dariya tayi tare da cewa Allah ya kaimu zanje idan har Audu ya barni ,

Lokacin da Dikko ya samu labarin wannan taro da zanyi zuciyarshi tayi mishi ɗaci domin yasa ana biyayyar mishi rayuwata duk wani motsina da komai nawa babu wanda Dikko bai sani ba ,

Tsoki yayi tare da kallon agogon hannunshi jinjina kanshi yayi ya cusa "yan yatsun sa ko wane yana gogar ɗan uwansa , laraba , ya faɗa a bayyane tare da sake jinjina kanshi , litinin kuma ya faɗa a bayayyane Allah ya bamu aron rayuwar muje larabar dani dake........




19/09/2019



Jamila Musa 💅🏻
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_



*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_



*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_


_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻

*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_

&

*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*



🅿 ------ 35


Har yaci gaba da cin abinci kuma yaji gaba ɗaya moƙoshin nashi abincin baya wucewa , tsananin ɓacin rai da damuwa suke ta kartar masa zuciya , dakel ya haɗiye yawu mai ɗacin gaske , kallon Al ' ameen yayi yace kiramin Umar....

Wayar ya ɗauka da sauri ya fara kiran wayar Umar , saida Umar ya ɗauki wayar ya miƙawa Dikko cikin ladabi , ansa Dikko yayi cike da ɓacin rai yace har yanzu kana anguwar ko ka fita ne ... ?

Magana Umar ɗin yayi , Dikko yace tou kaje ka kaima An mata waya zanyi magana da ita yanzu ² yi sauri karka ɓatamin lokaci , saida ya jira abinda Umar zai faɗa sannan Dikko ya kashe waya ,

Ina zaune ƙofar gida dani da Alajina muna fira Umar ya faka da machine inshi , kallo ɗaya nayi masa na kauda kaina yayin da na ciro wayana na fara ƙoƙarin kiran Wane Yaro ,

Sallama yayi suka gaisa da Alaji nima ya gaisheni , ansawa nayi babu yabo ba fallasa , ɗan gyara tsayuwarshi yayi tare da cewa dan girman Allah saƙo aka bani wurinki , daina kiran wayar Wane Yaro nayi na tattara hankalina kaf wurin Umar nace waye ya baka saƙon ne ...?

Cike da ladabi ya miƙomin waya bayan ya kira number ya miƙomin yana cewa kiyi magana an ɗauka , cike da wasi² na kara wayar a kunne na tare da cewa Assalamu Alaikum....

Ansa sallamar yayi yana mai ci gaba da cewa An mata kinaso in saka ƙafar wando ɗaya dake ne ? Shiru nayi banyi magana ba , Dikko yaci gaba da cewa na rantse da Allah ki kama kanki wannan iskanci birthday in da kika taro ki warwareshi tun kafin inzo wurinki ina fushi , banda kyau idan na ɓata rai ki roƙi Allah ya rabaki da ganin fushi na amma na rantse da Allah.... Saida yayi rantsuwa mai sa faɗuwar gaba sannan yace idan kunne yaji ....

Sai kuma yayi shiru bai ida faɗar maganar ba , ni kuma na ɗaura da cewa idan ka barni na huta baka ƙaunar Allah , tsoki nayi tare da miƙawa Umar wayarshi naci gaba da magana na da Alaji ,

Cike da masifa Dikko yace Umar ya maidomin wayar , bani yayi nima kuma na ansa , cikin sigar lallashi yace An mata nine bana ƙaunar Allah ? Wai mi yasa kike min magana haka babu ɗa'a , ai kasan gidanmu ba'a koyamin ɗa'a ba shi yasa ma har nayi rashin ɗa'ar a cikin gidan ubana ,

Dikko yace idan kinajin rashin kunya ki fita daga cikin mutane ki zageni idan kin isa , ni nasan baki isa kimin rashin kunya inda babu kowa ba , dama kin tsaya a gaban waɗanda ko naso nayi miki hukunci zanyi haƙuri a haka kike tunanin bakyajin tsoro na ne ? Idan dai bakijin tsoron Dikko maza ki tashi daga inda kike kice Dikko ƙarya kakeyi nafi ƙarfin ka takuramin ki faɗi haka kiga yadda zanyi wasan kura dake wallahi ....

Kamar wata sakara na miƙe na matsa daga inda su Umar suke , ashe shi kuma yayi wayau ne dan kar in riƙa wulaƙantashi ne a gaban yaronshi , saida na matsa sannan nace ƙarya kake ni nafi ƙarfinka kuma nafi ƙarfin ka takurani dan banajin tsoronka kayi duk abinda kakejin zaka iya yi na matsa daga cikin mutanen....

Dikko yace tou babu komai dani dake aga fasashshe , ni zanzo katsina insha Allah gobe talata , ke kuma zakiyi birthday ranar laraba sai nazo , kuma karki sake kiyi mafarkin gemuna na faɗa miki....

Gemun banzar ka gemun wofi , Allah ya sawaƙe min in ganka a barci na , cikin murya mai saukar da kasala yace nifa bana san cika baki bayan nasan komai , kawai yarinyar kirki taga ustaz ta maƙale mishi aidai kina so na ko.... ?

Tsoki nayi ban bashi ansa ba na kashe wayar naje na bawa Umar ko sallama banma Alaji ba na shige gida raina a ɓace ,

Murmushi Dikko yayi bayan na kashe waya tare da cewa An mata rigima , zaki zo kusa dani kuma inaji a jikina wata rana zaki rumgumeni ki kalli cikin idanuwana kice Dikko ina sanka , yana maganar yana nuna yanda Sultana zatayi , cikin farin ciki yaci gaba da cin abinshi bai sake kiran Umar ba , kuma koda Umar ya kira dan ya faɗa masa cewa Sultana ta tafi bai ɗauka ba ,

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login