Showing 27001 words to 30000 words out of 116763 words

Chapter 10 - SHAHAAB COMPLT

Start ads

10 Aug 2025

790

Middle Ads

gama saisu sanar dashi.


Kasance war kwana daya baizo office ba Sai ayyuka suka taru suka masa yawa, Bai koma gida ba Sai Bayan sallar la'asar.

Da daddare Bayan yagama komai, yad'auko wasu takardun mama na wasu filaye daya siya mata da kudin ta daya saka hannun Jari awani company, takardun sunkai guda goma, yasan cewa idan yabata kudin ma cewa zatayi ya ajiye, shiyasa yayi dabara yasai mata manyan filaye dasu, daya Bayan daya yagama dubasu, zai dauke kenan Sai aka kira wayarsa, yayi mamaki ganin Kiran daga office dinsu ne, Bayan ya dauka suka tabbatar masa cewa wannan file din daya basu sungama bincike akansa, tabbas kudin Alhaji Audu ne, ba kudin sata bane, ya saida wasu kadarorin sane, sannan ya Gina gidan man, umarni ya basu cewa atura file din zuwa kano, Sai asakar masa gidan mansa.

Wani irin farinciki ne ya kamashi Bayan yagama wayar, shi Kansa baisan dalilin yin farincikin ba, maganar tace tafado masa Arai, "kanaji ko Yaron oga... Mahmud Wakili bashida mutunci"

Murmushi yayi, yamiqe tsam yashige toilet domin watsa ruwa, kwata kwata ya manta bai dauke takardun filayen mama ba.
Munirat data shigo Dakin domin kawo masa coffee,taci Karo da takardun azube atsakar d'aki, juyawa tayi ta kalli cikin Dakin kamar tana tsoron wani zai ganta, tsugunna wa tayi tadudduba takardun taga na filaye ne, mamaki ya kamata, ta ajiye coffee din hannun ta, ta sake duba takardun dakyau, take hudubar mahaifiyar ta tafado cikin ranta, cikin sauri ta dauke takardun manyan filaye guda biyu, sannan tayi gaggawar ficewa daga d'akin batare data ajiye masa coffee dinba.

Shahaab kuwa ya dade yana wanka sannan yafuto jikinsa daureda towel, hannu yasa yadauke takardun batareda yasake dubasu ba, Kai tsaye yabude wata yar qaramar akwatin sa ta adana sirri, yasaka takardun agefen inda ya ajiye ribbon din daya siyowa Aisha,kallon ribbon din yayi na Yan seconds sannan yasaka wasu numbers yarufe akwatin, ya shirya tsaf, sannan yafada kan gado tareda daukar wayarsa, number daya dauka a wayarta yakamo ya zubawa ido yana kallo, cikin zuciyar sa yace "ko tayi bacci yanzu?"

Har zai kirata saiya fasa, Tome zaice mata?
(nikam nace idan ka kira ma dandalewa zakayi da Hajja >?#?)

Ahankali yace "idan taji labarin Mahmud Wakili yasa ansaki gidan man Alhaji Audun nasu, nasan zatayi farinciki" fillo yaja yarungume a qirjinsa, da wannan tunanin bacci me dadi ya dauke shi, saida yatashi sahur mamaki ya kamashi yau meya hanashi neman munirat har yayi bacci shi kadai? (>??)


******

Zaune suke atsakar gida, Aisha da Jummai suna tsince shinkafa, jummai ta kalli Hajja tace "Amma Hajja A'i wannan 6arawo naku da rashin kunya yake, Dan tsabar rashin mutunci ga mamuda yana kwance atsakar gida Amma har ya'iya dirowa cikin gida irin wannan me tsaro?"(>?#?)

Aisha takwashe da dariya tace "infada miki iya jummai nice nafara jinsa lokacin daya shigo, Ina tsugunne aqofar bandaki naji kamar andiro ta cikin bandakin, aikuwa nayi tsilak natashi nadawo kusa da Abba"

Jummai tace "ahaf, to inaga Dama yasaba shigowa yana muku dauke dauke, Amma naso kun kamashi, da Sai mun Tara masa jama'ah"

Kafin su bata amsa daya daga cikin jikokin ta yazo Yakirata, daga Nan tayi wa su Hajja sallama tatafi gida.
Hajja tacewa Aisha"nikam da 6arawon Nan yashigo ya kwashe min kudin qanqara Aida bazanyi azumi ba gobe, wuni za'ayi Ana yaiyafa min ruwa"

Ummah data futo daga daki tace "Gobe jajiberan mutane Sai shiri suke yi, azumi yatafi kamar yau muka d'auka"

Aisha tace "au Wai Ummah da gaske gobe jajiberan kasuwa zataci kenan?"

Hajja tace "insha Allah jibi zamuyi sallah, mun kusa muhuta, gobe Kuma kasuwa zataci, inada cinikin qanqara gobe"

Aisha tace "dole ki riqe lokacin kasuwa ai, saboda kina samun kudi, larabawa suna kuka azumi zai tafi, kekuma murna kike jibi zakiyi sallah"

Hajja tace "ke suma kukan munafurci suke, wannan wahalar azumin idan dan'adam yakaishi lafiya ai abun azo har gida ayi masa barka ne, insha Allah jibi sallah"

Aisha tace "Wai Hajja waye yacemiki jibi sallah? Idan kuma ba'aga wata bafa?"

Hajja tace "ke Bari kiji, duk masifarki daga gobe de mungama azumin Nan, ke koba'a gamaba nikam na sauke, Kuma babu uban daya Isa yasa nayi, ai kowa kabarinsa daban"

Aisha tace "yanzu ma babu Wanda yahanaki saukewa, walakiri ne zai kamaki yadinga jibgarki kekadai babu me cetonki Sai Allah...."

Lokaci daya Hajja A'i tafashe da Kuka, ihun datasa ne yaja hankalin wasu samari daga waje suka shigo gidan sunyi tunanin mutuwa akayi, Ummah kuwa cikin ranta cewa take innalillahi wa inna ilaihirraji'un, yau Kuma abun na Hajja yatashi, tambayarta samarin suka farayi waye yamutu? cikin kuka Hajja tace "yanzu munzali, nime sunan qawa zatayi wa fatan walakiri yakamani da jibga kamar wata kafura"

Kafin su munzali subata amsa ta juya ta kalli Aisha tace "insha Allah babu abinda walakiri zaimin, fatan ki yaqare akan Hadiza da Mamuda..."

hawaye ne ya taru a'idon Ummah, ahankali ta juya ta shige cikin dakinta, sumasu munzali suka Bawa Hajja haquri sannan suka juya

Aisha kuwa harara ta zubawa Hajja, sannan ta wuce Dakin Hajjan kaitsaye, duk wani kayanta dayake Dakin Hajja yau saida tafitar dashi tas..., ko dankwali bata Bari ba, ta wuce ta maida shi Dakin Ummah, Ummah tana kallanta batace mata komai ba, ahankali ta zauna abakin gadon ta kalli mahaifiyar Tata tace "Ummah Dan Allah Kidena kuka saboda wannan tsohuwar, kiyi hakuri insha Allah ni nariga na yanke alaqata da Hajja, hakan bazata sake faruwa ba"

Ummah batace da Aisha komai ba, abinda tasani shine idan tabiye mata suks taru suka zagi Hajja, to Ana jimawa zasu shirya da Hajjan, menene amfanin ka daurewa yaro gindi? Ita kanta tasan cewa haifar Aisha kawai tayi, Amma duk wata wahalar ta da rainon ta Hajja ce tayi, shiyasa suka shaqu, koka shiga tsakanin suma kaine zakaji kunya.


******

Kayane masu mutuqar kyau da tsada azube agaban mama, dubasu tayi sosai sannan ta ware wasu, wayarta dake gefenta ta d'auka takira Shahaab Wanda ya dawo daga wajan aiki yake shirin shiga wanka, yanaso yatafi masallaci wajan tafsir, cikin ladabi ya dauka kamar yana gabanta, munirat data gama debe kayan daya cire Sai jinsa tayi yana fadin "to mama, gatanan zuwa"

Cikin zuciyar ta tace "kome take buqata Kuma? Jarababbiyar tsohuwa kawai"

Kallanta yayi yace "kije inji mama"
Daga Nan yawuce toilet.

Bata dauki dogon lokaci ba ta wuce wajan mama, tana zuwa mama tabata kayan data ware tace "ga kayan sallarki Nan, wannan Kuma ki aikawa tsohuwa, inji Dan Albarka Mahmud Wakili"

Maganar tamata ciwo, domin kuwa wani qullutun baqin ciki ne yatokare mata maqoshi, ahankali ta daga mata Kai, cikin ladabi tace "to mama mungode, Allah yaqara Arziqi"

"tun kafin kizo Arziqi Kam Dama can yana qaruwa, ke kanki Arziqin ne ya janyo ki, tashi kibani waje"

Wannan Karon munirat batace komai ba, tatashi tatafi.
Tana zuwa Kai tsaye d'akin sa ta wuce ta zubar da kayaiyakin akan gado, sannan ta zauna aqasan gadon tafashe da Kuka, yana futowa daga wanka yaganta tana kuka, ya kalli kayan dake kan gado, sannan ya dawo da kallon sa gareta yace "menene yake faruwa?"

Cikin kuka tace "yanzu abunda akemin a gidan Nan hakan adalci ne? Ni banida ikon siyo abinda nakeso kullum saide asiyo abani? Mama tayi Kane Kane akan komai nikuma anmaida ni saniyar ware"

Ajiyar zuciya yasaki, baice da'ita komai ba,Dan qaramin towel din hannunsa yad'ora a lallausar fatarsa datake shinning,saida yagama goge jikinsa sannan ya zauna abakin gadon dab da munirat

Ahankali yace "munirat... Mama mahaifiyata ce, nayi tunanin yanda na dauki momynki a matsayin uwa, kema hakane,wani lokacin rikicin mama harda na tsufa, ni abinda nasani arayuwata shine inason mama, Kuma inason duk abinda takeso, karki manta dede da second daya banta6a ganin fuskar mahaifi naba saide a photo, mama itace komai nawa, itace uwata, itace ubana, tamin gatanda ko mahaifina yana Raye abinda zaimin kenan, duk lokacin da mama ta 6ata miki rai kidauka momy ce ta6ata miki, babu yanda zakiyi da'ita, a koda yaushe inaso ne kitayani yimata biyaiya nasamu narabu da'ita lafiya.... Ta hanyar biyaiyar danake mata ne zaisa inshiga aljanna munirat, nikaina nasan wani lokacin Rikici ne kawai irinna mama Amma a hakan nake goyon bayanta Dan in rabu da'ita lafiya, Amma ke kin kasa gane hakan, idan momy ce ta zazzageki wazaki kaiwa qara? Babu Wanda Zaki fadawa saide ma kibata haquri, to inaso kidauki mama kamar momy, idan kikamin hakan kingama min komai munirat.... "

Jikinta ne yayi Sanyi Bayan tagama Sauraron kalamansa, lokaci daya ta sauya kukan Nata ya dawo na kissa, cikin wani irin Salo tace"ainima Bahaka nake nufi ba, Ina kuka ne akan irin wariyar da mama take nunamin, yanzu wannan kayan waye zai dinka min insaka su jibi? Ai Yanzu ni a ganina mama ta wuce ace itace zata dinga siyo mana Kaya, a matsayi na namatarka ainice yakamata ace nasiyo mana, ita Kuma mama ta huta, ni bansan meyasa mama bata sona ba"

Runtse Idonsa yayi, bayason jin kalmar Nan datake fada akan mama, cikin sigar lallashi yace "yanzu me kike so?"

Ahankali tace "ni wannan kayan basumin ba, Kuma momy ma ta dade da dinka irinsu, saide nabawa ma'aikata su, inyaso nida momy muhaqura"

Ahankali yace "a a, ki dauki kudi acikin briefcase dina, saiki siyo muku Wanda kike so, shikkenan?"

Cikin murna da farinciki tace "eh, nagode my Dear"
Tafadi hakan tareda rungume shi ta manna masa kiss akan lallausan lips dinsa.
Cikin wata irin murya yace "Bari mana munirat azumi fa"

Murmushi tayi, tazuba masa wata irin hararar masoya, sannan tafice daga d'akin.



Mutara zuwa anjima, insha Allah zaku samu update =?O?
To Aisha de tace ta yanke alaqa tsakanin ta da Hajja=??

Ko Yaya za'a qare akan takardun filayen mama? >??


Bazan tsaya Ina Allah ya'isa akan novel ba, Amma duk wacce ta karanta min littafi batareda ta biya ba nabarta da mahaliccinta, saboda nide ban yafe mataba


Mrs Usman ce
'
Page 19&20



Atamfa ce turmi uku da wani yadi irinna maza Mai kyau agaban Ummah da Abba, Bayan Ummah tagama Gani tace "mukam kasan ba zamu samu dinki yanzu ba, saide Bayan sallah mesunan qawar Hajja sai takai mana, Amma Naka Dana Jabir bansani ba ko zaku iya samu"

Aisha datake kwance akan gadon Ummah tana Kallan su batace musu komai ba, har yanzu idan tatuna fad'an da sukai da Hajja jiya ranta sake 6aci yake, kullum sukai fada da'ita saita sako iyayenta aciki.
Kafin Abba yayi magana Hajja ta doko sallama cikin d'akin, kallanta yayi yace "Hajja sannu da zuwa"

Tace "sannu mamuda, a zaune kuke?" bata jira amsar dazai bata ba tad'auki jakar kayan Aisha, Aisha tana ganin haka ta juyar dakanta Gefe ko kallon Hajja batayi ba, Hajja ta kamo hannunta tace "tashi mutafi mana mesunan qawa, duk fadan da mukai dake ai Bama raba makwanci, Amma jiya har kayanki saida kika kwashe, meyayi zafi haka? Tashi mutafi madubinki yana Nan nasake goge miki shi kiji dadin Kallan Kallan da kike" (>?-?=?F? @&?)

Cikin sauri Aisha tatashi, ganin irin kato6arar da Hajja takeson yimata agaban Abba, Wai mutum da abunsa danya kalla shikkenan Hajja ta dinga magana daya, saukowa tayi daga gadon tana tura baki gaba, suka futo daga d'akin Kai tsaye suka koma cikin Dakin Hajja.

Suna zama Hajja tace "yanzu mesunan qawa abinda kikai ya kamata kenan? Ki hadani da walakiri, aiko maqiyi na bazai min irin wannan fatan ba"

Aisha tayi shiru batace mata komai ba, Hajja tasaki ajiyar zuciya tace "shirya muje kasuwa musiyo kaji da d'an kayan miya muzo mu gyara gobe Sai ai miyar sallah dasu"

Tashi tayi tad'auki hijabin ta tasaka sannan cikin qasa-qasa da murya tace "muje"


******

Yana zaune a office dinsa Bayan yagama ganin mutanan office din nasu Wanda suka masa sallama saboda tafiya garuruwan su hutun sallah, Shima tunani yake Ina yakamata ace yaje ya huta?
Itace tafad'o masa, to kode ziyara zaiKai matane? Mamakin Kansa yake, duk lokacin dasuke samun hutu irin wannan babu abinda yake tunawa illa munirat, yanda zai dauketa sutafi wata qasar suje Sud'an huta sannan su dawo, Amma yau kwata kwata yakasa tunawa da'ita, cikin zuciyar sa yace "tunda ba sonta nake ba menene zai dameni dannakai mata ziyara?, to Amma idan naje mezance mata? Wancen Karon akwai dalilin daya kaini, Amma yanzu fa?"

Afili ya furta "babu dalilin zuwan" duk yanda zuciyarsa taso hanashi, haka yaqi yarda, ahankali yad'auki wayarsa yadubo number ta daya d'auka ranar dayaje, batareda tunanin komai ba ya danna mata kira.


******
Suna futowa daga gida sukaga wani me adedeta, cikin sauri Hajja tace "Tsaya! tsaya!! d'an sahu"

Tsayawa yayi, Aisha tace masa "kasuwa zaka qarasa damu"

Yace "ba haya nake yi ba"

Cikin sauri Hajja tace "haba kaikuwa yaro, Nima nasan ba hayar kakeyi ba tunda mukam agarin Nan Ina mukaga wani adedeta sahu, saboda Allah zaka kaimu saina baka 'yar nera hamsin kasayi gasara Kasha ruwa da magariba"

Murmushi yayi yace "tokushigo"

Shiga sukayi, sun fara tafiya kenan wayar Hajja tad'auki qara, cikin mita tace "Kai wannan jaraba da yawa take, da ranar ma baza'a bar mutum ya huta ba?"

Aisha tace "to idan ba'a kiraki da rana ba cikin dare kike so a kiraki?"

Cikin mita tace "aikuwa koma waye bazan dauka ba,da azumin zanji koda Kiran waya?" tafadi haka tareda kashe wayar

Daga nasan bangaren mamaki ne ya kamashi, kamar fa rejecting din Kiran akayi? Metake da wayar zata katse masa kira? Wata zuciyar tace "kasani ko game takeyi?"
Ahankali yace "may be" sannan yasake Dialing number, wannan Karon Kiran yana shigowa Hajja tasa hannu zata kashe Aisha tace "Bani In dauka"

Babu musu Hajja ta bata wayar, ahankali cikin zazzaqar muryarta tace "Hello Salamu Alaikum"

Atsaye yake, Amma yanda yaji muryar Tata tana neman kashe masa jiki, saiya nemi kujera ya zauna tareda Lumshe Idonsa

A 6angaren Aisha kuwa dataji shiru saita sake cewa "Ba'a jinane? Wake magana ne?"

Hajja tace "maganinki kenan, kina ganin number special kece mecewa Zaki dauka, baki Sani Bama ko masu shan jini ne"

Dariyace ta kamashi, Kuma bayason taji shi, Sai yayi sauri yakashe wayar, yana cikin murmushi Ramadan yashigo office dinsa, cikin mamaki yace "Abokina lafiya?"

Saboda Rabon daya ganshi yana irin wannan farincikin harya manta, ahankali ya girgiza masa Kai, sannan yace "nothing"

Aisha kuwa dataji an kashe wayar, saita Bawa Hajja wayarta, me adedeta yace "Hajiya Kidena futowa da waya fa, kinganni Nan, to yau -yau dinnan nafuto daga gidan yari, Kuma satar waya ce takaini, gobe sallah idan kinsan ma zakije wajan idi toki tafi da paper da biro duk Wanda yace kibashi number ki saiki bashi paper ya rubuta miki, kema ki rubuta masa, saboda zamuyi patroll goben"

Cikin sauri Hajja tasake qanqame Jakarta, tace" innalillahi.... Aikuwa Gara daka fada mana Kai 6arawo ne, tsaya ka saukemu anan "

Cikin dariya yace"mama ni bazan muku komai ba, inda zan muku da tuni na zubar daku, kawai de fada muku nake ku kiyaye "

Cikin tsoro tace"to mungode, Kuma zata kiyaye, kasan jikar tawa farinjini ne da'ita kamar kudi, Yanzu haka me Kiran ma inka bibiya mashinshi nintane".


Suna zuwa kasuwa ya saukesu, Bai kar6i kudin su ba, godia suka masa sannan suka shige suka sayi abinda yakawo su, sannan suka juyo gida,ummah ce ta gyara kayan miyan jabir yakai wajan niqa, Aisha Kuma ta gyara kajin ta soya su, Hajja Kuma tadafa musu jallop din macaroni da sauran man da Aisha tayi suyar kajin dashi, sannan sukai wanka suka zauna kowa yana jira Asha ruwa.

Washe gari sallah, karfe bakwai da rabi Aisha da jabir da Hajja A'i suka shirya suka tafi masallaci wajan sallar idi, aqafa suke tafiya ahankali suna tafe kowa bakinsa d'aukeda zikiri, jabir yana Sanye da yadi ajikinsa medan sauqin kudi, Hajja ma taci atamfar ta sabuwa wadda ta dinka da kanta, Aisha kuwa atamfar da inusa ya dinka mata, itace ajikinta, sun sanya sabon hijabi iri daya itada Hajja, Wanda Hajjan ce ta dinka musu.

Suna zuwa masallacin Hajja ta dubesu tace "ikon Allah, dama wannan ne sabon masallacin da'aka Gina?"

Jabir yace "shine Hajja, ga wajan mata can, saiku qarasa, idan an idar kujirani zanzo mutafi"

Hajja tace "to ni yanzu wannan danqareren masallaci da Bismillah zan fara shiga kokuwa?"

Aisha da taqaici ya kamata ta juya fararen idonta tace "Da zagi Zaki shiga, haba Hajja, wani lokacin kidinga abu kamar wata tsohuwa"

Murmushi tayi tace "Allah sarki, mesunan qawa menene Kuma yarage? Tsufa kan ai mun tsufa, saide fatan Inga takwararki, Kuma incika da Imani"

Hannunta Aisha taja batare datace komai ba, suka shige cikin masallacin, sallaya ta shimfida musu suka zauna, basu sake magana ba kowa zikiri yake cikin ransa,basu dade da zama ba wani mutum yazo yana kar6ar sadaka, Hajja ta bude gefen zaninta tabashi nera Dari, Aisha tayi murmushi tareda jijjiga Kai, cikin ranta tace "lalle Hajja yau take sallah"

Bayan sun idar sun koma gida, anan sukaga har Ummah takusa kammala abinci, Aisha ce tacire hijabinta ta kama mata aikin, Nan da Nan suka gama, mutane Sai shigowa suke anata gaisawa, masu shagunan caji Sai kunna waqa suke a mp, Bayan sunci abincin Aisha tayi wa Ummah magana tana so taje gidansu Walida, abinci Hajja tabata tace "kafin ki wuce kishiga ki kaiwa jummai abincin Nan"

Kar6a tayi sannan ta wuce.


******

Acan gidansu mama kuwa hidima tayi yawa, kamar Wanda ake dan qaramin biki, mama tana zaune tana ganawa da mutane masu zuwa yimata barka da sallah, kudi ne masu yawa agefen Dan qaramin fillon kujerar datake Kai, duk Wanda ya tsugunna ya kwashi gaisuwa idan yatashi tafiya haka zata dauki kudin tabashi, Shahaab kuwa bata ganshi ba, tasan yana can waje yana Fama da nasa mutanan, abinci ma bai samu damar zuwa yaci ba, Kuma tasan munirat bata nemeshi akan hakan ba, to itama dasuke zaune gida daya batazo ta gaishe taba bare tayi mata barka da sallah, batasan wacce irin mata Allah yabawa Mahmud ba, kafin tagama tunanin Nata yashigo cikin falon Nata yana Sanye cikin manyan Kaya farare tas,shadda ce dataji dinki Mai kyau da tsari, yasaka babbar Riga, hatta takalmin qafarsa fari ne, yayi mutuqar kyau kamar ka sace shi ka gudu, kasancewar baya saka manyan Kaya kullum Sai suit, Sai hakan yaqara qawata kyan halittarsa, Sai tashin qamshi yake Mai dadi, yana qaraso wa kusa da'ita duk mutanan falon suka tashi suka fice, Kallan sa tayi cikin farinciki tace "masha Allah, Mahmud kayi kyau sosai, yanda kake da kyan Nan Allah yabaka kyakykyawar amarya ku haifomin kyawawan jikoki"

Inda Dane tafada masa hakan bazai ji dadi ba, Amma yanzu wani irin murmushi yayi, tana

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login