Showing 54001 words to 57000 words out of 116763 words
shiyasa ya shirya mata wannan yaudarar,kaiii yaudarar tayi yawa, tasa hannu ta share Hawayen idonta, Sai yanzu ne takejin haushin kanta, taji ta tsani kanta sakamakon tunawa datayi har bijrewa iyayenta tayi, saboda shi, daga qarshe ga abunda yafaru, dama ance duk Wanda baiji maganar iyayensa ba,to yana tareda matsala, tun kafin taci gaba da ganin wannan matsalar Gara Takoma gida ta roqi iyayenta gafara sannan Kuma tashawo kan inusa, tana zaune tana tunani har qarfe shadaya da rabi na dare yayi batare data Sani ba
Shabiyu daidai yafuto daga d'akin sa, tun Bayan barinsa part din mama daya shiga daki baisake futowa ba Sai yanzu, Kai tsaye d'akin munirat yawuce, tana kwance akan gadonta, ta dora hannunta daya akan goshinta Wanda yake mata barazanar rabewa biyu, idonnan ya kumbura suntum saboda kuka, tanajin shigowar sa Amma tayi masa mursisi ta nuna kamar batason yashigo dakinba, zama yayi akan gadon tareda janyo ta jikinsa, ahankali yabude bakinsa yace "munirat...."
Cikin sauri ta qwace jikinta tareda matsawa can Gefe,
Bai saurare taba yajata jikinsa ya rungume ta, kuka tasaki Mai cin rai, baice mata komai ba Sai bayanta daya Dan bubbuga alamun tayi shiru, daga Nan yajata suka kwanta, tun yana jin kukan ta har yaji tayi shiru jikinta yasaki alamun tayi bacci.
Har qarfe daya saura Idonsa biyu bai runtsa ba, Ada idan yadawo daga tafiya qarfe goma yayi yawa ya kwanta, Amma yau shine har daya saura Idonsa ko alamun bacci babu, inda Dane yadade bai kasance da matarsa ba to kwana biyu ne zuwa uku, idan tashiga hannunsa kuwa saita koka, Amma yanzu shine yayi tafiyar wata daya da 'Yan kwanaki Amma ko kadan baiji yana sha'awar munirat ba, tunanin sa gaba daya yana wajan Aisha,ya dade rabonsa da matarsa, yadawo daga doguwar tafiya Kuma mama ta tarbeshi da wadannan abubuwan na Aisha masu wuyar mantawa.
Ya tabbatar da cewa bazata taba saurarensa ba koda yaje inda take yanzu, Amma Kuma tayaya zai tunkareta yabata haquri agaban mutane da rana? Idan mama ta ganshi ta'ina zai fara yimata bayani? Ahankali yazame munirat daga jikinsa, batareda tunanin komai ba yafice daga d'akin, Kai tsaye yanufi part din mama.
Yana zuwa yaga part din shiru alamun duk sunyi bacci, saida yasake kallon ko'ina ya tabbatar babu wani mahaluqi dayake falon sannan yawuce Dakin da yaga Aisha tafuto daga ciki dazu, kama handle din Dakin yayi yatura, yashiga cikin Dakin sannan ya maida Dakin yarufe, baiyi mamakin ganin ta a zaune akan sallaya ba, kanta yana cikin cinyoyinta, qamshin turaren dataji ne yasa taqi d'ago kanta bare ta kalli inda yake.
Jin gina yayi da jikin qofar Dakin yazuba mata ido yana kallon ta, gabansa faduwa yake yarasa ta'ina zai fara yimata magana? Ahankali yasaki ajiyar zuciya sannan ya qaraso wajan ta ya tsugunna gab da'ita har tanajin yanda hannunsa yake gogar Nata, cikin muryar rad'a yace "ki... kki... kiyi hakuri"
Tana jinsa, Amma taqi d'ago kanta ta kalleshi, wani irin haushin sa takeji, ko menene yakawo shi dakinta cikin dare? Wata zuciyar tace da'ita abinda bai gamaba yazo ya qarasa, wani irin tsaki tasaki cikin ranta, tasake cusa kanta cikin cinyoyinta, ganin hakan datayi yasa yasan cewa ba bacci take ba, ajiyar zuciya yasauke yasake cewa"nasan cewa nime laifi ne awajanki, banyi komai ba saida dalili Maaamah, Dan girman Allah kiyi hakuri ki yafemin..."
Wani i r i n k u k a m e s a u t i t a s a k i , b a t a c e m a s a k o m a i b a S a i h a n n u d a t a d a g a m a s a . ( =ؐ??)
K a l l a n t a y a y i , b a b u m u s u y a j i j j i g a K a n s a t a r e d a m i q e w a y a f i c e d a g a d ' a k i n , d a m a y a s a n c e w a b a z a t a s a u r a r e s h i b a , h a k a y a k o m a p a r t d i n s a j i k i n s a a s a n y a y e , k a n g a d o n y a k o m a ya kwanta, munirat tanajin kwanciyar sa tace "daga Ina kake? Ko yanzun ma wajan ta kakoma zaka sake taba mata nonon?"
Runtse idon sa yayi, ahankali yace "me kike nufi Danine munirat? Kina nufin zan iya neman mata awaje?"
Cikin fishi tace "idan ba neman matan kafara ba, kwanan ka nawa rabona dakai?Dakazo ka nemi wani abu awajena ne? An tura Maka tsayaiyan nono kana ta6awa yaushe zaka nemi nawa?kun cuceni wallahi, Kuma dole kasa yarinya qarama tadena ganina da qima da mutunci"
Murmushi yasaki kamar wanda baya cikin damuwa, ahankali ya fusgota jikinsa tareda tura hannunsa cikin yaluluwar rigar baccinta, yayiwa breast dinta wani irin kamu, sannan yafara kissing dinta.
Sosai yayi Nisa wajan nuna mata yanda yayi kewar ta, soyake ya mantar da'ita abunda tagani dazu, saide shi Kansa kawai yanayin Hakanne Amma kokadan bayajin sha'awar, saboda tashin hankalin dayake ciki,daga Nata bangaren itama Qin bashi hadin Kai tayi, Dan dole yarabu da'ita tareda juya mata baya yayi kwanciyar rub da ciki, itama kwanciyar ta ta gyara tarabu dashi, saide ko minti goma batayi ba taji Hankalinta yaqi kwanciya, yariga yata6o mata inda yake mata qaiqayi, ahankali ta juya ta rungume shi tabaya, yanajinta yarabu da'ita, sake Matsowa jikinsa tayi tana goga masa qirjinta a bayansa, saide hakan datake masa ma ba komai tatuna masa ba Sai Wanda yata6a dazu, ahankali yasaka hannunsa ya janye ta daga jikinsa, sannan yaja fillo ya rungume a qirjinsa.
Mamaki ne yakamata, yau itace take neman Mahmud Amma yana janye ta da hannunsa? Babu yanda ta'ita duk yanda take jin sha'awar sa haka ta qyaleshi.
Washe gari da safe tsaf ya shirya cikin suit dinsa, baisaka jacket dinba Sai zuba uban qamshi yake,soyake yafita domin shirye shiryen sabon company dazai bude, Wanda yayi alqawari zai Bawa matar datake da muhimmanci awajansa wato munirat ,tun qarfe takwas na safe suke masa waya, already har sun gama tsara komai, kawai jiransa ake yazo yasaka ranar daza'a bude companyn, baisan daliliba, haka kawai yake jin wani irin farinciki acikin ransa, Kuma yasan cewa hakan baya Rasa nasaba da kasancewar Aisha acikin gidansa,yarasa menene yakawo ta gidan a matsayin maiyiwa mama hidima, tayaya tazo? Dole itace zata bashi labari Kuma tana fishi, inda Dane ba lalle ya tsaya yin break fast ba saboda jiransa da ake, Amma yau Kam dole zai tsaya yaci abinci kodan yaganta ma.
Munirat tana wanka danhaka yafice shi kadai, Kai tsaye part din maman yanufa, yana zuwa kuwa yaga ma'aikatan sun gama shirya komai akan dinning, mama tana zaune, yayinda Aisha take tsaye tana qoqarin hada mata tea, yau taji jikin Nata dadan qarfi, babu zazza6in ya sauka tun Bayan datasha magani cikin dare, wani irin dadi yaji, cikin takunsa me aji ya qarasa dinning din tareda sallama, mama ta kalleshi tace "nayi tunanin zaka huta ne bazaka fita ba?"
Saida yadan kalli Aisha yaga tahade girar sama data qasa, yasaki murmushi sannan yace "akwai mutanan dasuke jirana ne dangane da bude wannan sabon companyn, shiyasa zan fita, Amma bazan dade ba zan dawo"
Kafin mama tabashi amsa, qasa-qasa Aisha tace "Ina kwana"
Murmushi yasaki, yasan cewa Dan kada mama taji taqi gaida shi ne, shiyasa tayi masa wannan gaisuwar, Amma Badon hakaba Shima yasan bazai samu gaisuwa agareta ba
Maimakon ya amsa Sai yayi shiru tareda zuba mata ido yana Binta da wani irin mayen kallo,har zuwa wannan lokacin bai zauna ba, yanda Aisha take a tsaye tana qoqarin hada tea din, haka shima yakama daya daga cikin kujerar dinning din yariqe, wani irin nishadi yake ji a ransa harma ya manta cewa mama tana wajan.
Mama ta d'ago zata masa magana taji Aisha ta gaishe shi Amma yaqi amsawa saita kamashi yana kallon ta, cikin mamaki tace "menene kake kallon ta,kokuma yanda kake tuhumar 6arayin Gwamnati itama tuhumar ta kake?,to wannan de Batada abun dazaka tuhumeta akansa"
Murmushi yasaki, dimples dinsa suka futo, yaja kujerar yana qoqarin zama, Hips dinta ya kalla yanda suka sake bajewa fiyeda ranar daya fara ganin ta, ya tuna tsayaiyun breast dinta yanda yake matsa su cikin nishadi kamar karya daina, cikin qasa-qasa da murya yace "tana dashi mana"
Mama t a c e " a u t a n a d a a b u n t u h u m a r k a c e ? "
C i k i n s a u r i A i s h a t a b a r w a j a n , d o m i n k u w a D a m a m a m a t a c e i n d e d a n t a y a n a w a j e t o k a B a r t a t a g a n a d a d a n t a , q a s a - q a s a y a b i b a y a n t a d a k a l l o , c i k i n z u c i y a r s a y a c e " w a n n a n a i i t a c e y a k a m a t a a t u h u m e t a , t u n d a h a r t a m a l l a k i w a d ' a n n a n a b u b u w a n K u m a t a s a c e M i n z u c i y a a i d o l e n a t u h u m e t a , k a m a t a y a y i m a n a s a k a t a a d a k i n a k u l l e k o f a r n a f a r a t u h u m a r t a t a y a y a a k a i t a m a l l a k i w a n n a n k a y a n a l a t u n ? ( =?
?)
M a m a d a t a j i y a y i s h i r u i t a m a s a i t a s h a r e s h i t a f a r a c i n a b i n c i n t a , s u n k u s a g a mawa kenan sannan munirat tafuto itama taja kujera ta zauna tafara cin abinci Bayan ta gaida mama.
******
Da yamma Bayan yadawo yana zaune a part dinsa yanashan Lemo, ya kalli munirat yayi mata magana, ciki ciki ta amsa masa, ahankali yasake ce mata "ki shirya jibi zamuyi taron bude sabon company, kece nafara fadawa, idan da wadanda Zaki gayyata saiki sanar dasu"
Wani irin farinciki ne yakama munirat, batasan lokacin data rungume Shiba, nuna masa tayi batasan cewa ita zai mallaka wa kamfanin ba, cikin kissa tace "Congratulation my Dear, Ina tayaka murnar bude sabon company, Allah yasa mu mora"
Mamaki ya kamashi,tabbas yasan yamata laifi saboda abinda tagani jiya yana yiwa Aisha, Amma Kuma yanda tad'auki zafi da fishi akan hakan kawai lokaci daya yanzu daga jin maganar company harta manta abinda yafaru? Cikin mamakin sauyinta na lokaci daya yace "Amin ya Allah"
Tashi yayi yatafi wajan mama domin itama ya sanar da'ita, yana fita munirat tad'auki wayarta tafara Kiran Yan gidansu tana sanar dasu jibi akwai taro, Shahaab zai mallaka mata sabon company, Bayan takira yan'uwanta, saita koma kan qawayenta, babu Wanda bata kiraba, acikin danginta ma wanda ta dade bata kirashi ba yau ta kirashi, saboda tana so ta kankarowa kanta daraja a'idon duniya.
Murmushi take ta saki ita kadai tana lissafa irin mutanan dazata dauka aiki a qarqashin companynta.
Tun daga ranar dasuka hadu a dinning bai sake ganin Aisha ba, yasan kuma Sarai fishi take dashi, shi Kansa idan ya tuna da yawan qaryaiyakin Dayayi mata saiya ji tabbas duk hukuncin data masa din hakan yayi, koda yazo wajan mama baya ganin ta, gaba daya a kwana dayan dabai ganta ba, duk Sai Idonsa suka fada.
anar bude company Shahaab tun sassafe yafita, Aisha kuwa tana d'akin mama, yau tasaki ranta ganin yanda maman take janta ajiki, itace ta fesa mata turare sannan ta kalleta tace "mama kinyi kyau sosai, nasan idan kikaje wajan Nan Sai kowa yace mama nah tafi ta kowa kyau"
Murmushi tayi tace "ki shirya muje"
Cikin sauri tace"a a mama, zan zauna agida inyi miki girki me dadi kafin ki dawo"
Bakomai ne yasa tafadi hakan ba Sai Shahaab da batason Gani, sosai ranta yabaci saboda abunda yamata, Sanadin sa tafara ja'inja da mahaifinta, duk yanda take da kunya saboda Shahaab tafuto fili ta fadawa Abban ta cewa itade Shahaab take so.
Cikin farinciki mama tace "to shikkenan"
Hannunta Aisha ta kama suma futo har compound din gidan, driver yad'auki mama, sannan ita Kuma tajuyo cikin gida.
Wajan taro yayi tsari da kyau yanda yakamata, manyan mutane Yan kasuwa da sauran abokan huldarsa sun halarci taron, Bayan anbude taro da addu'ah anyi Yan jawabai, daya daga cikin masu ruwa da tsaki akan aikin companyn yatashi yafara bayanin yanda sukayi aikin companyn cikeda inganci dakuma ingantattun kayan aiki daga qasar waje.
Munirat tana hakimce agefe guda ita da bataliyar mutanan ta, taci Gayu harta gaji, ta matsu a kirata a matsayin mamallakiyar company, momynta Sai zungurinta take alamun itama ta matsu Akira munirat din.
Ramadan yana kusa da mama, acan Gefe Kuma Shahaab ne yayi masifar kyau cikin manyan Kaya, Ramadan yasake kallon girman wannan company Amma cikin ransa yana mamakin irin son da Shahaab yakewa munirat, tun ranar dayace zai mallakawa wani mutum Mai mutuqar muhimmanci yasan cewa ba kowa zai Bawa ba face munirat.
Bayan gama bayanin company da abundaya qunsa aka Bawa Shahaab damar magana domin nunawa mutanan dasuka halarci taron jin dadinsa dakuma godia agaresu.
Tashi yayi cikin nutsuwa yafara da gaida mutanan wajan sannan yad'ora da cewa "a rayuwa inajin dadin yanda mamana take Bani kulawa, da yanda ta tsaya tsayin daka wajan ganin ta inganta min rayuwa ta, banida abinda zance da mama face godia, sune jin dadina itada matata munirat"
Munirat tayi wani fari da idonta tana sake hura hanci,wajan yayi tsit kowa yana jin yanda Mahmud din yake magana kamar bayaso, saida yasake kallon kowa sannan yaci gaba da cewa "saide wannan company, ban ginashi da sunana ba, tun farko akwai wadda nayi niyyar mallakawa, ita din mace ce mai mutuqar muhimmanci a gareni, zan'iya sadaukar da rayuwata domin ta.... Dalilin hakane yasa na mallaka mata wannan company, ba kowa bace face AISHA"
Daukacin mutanan wajan Nan da Nan suka dauki tafi.
Ramadan yajuya ya kalli munirat da gumi ya wanke wa fuska, ya kalli Shahaab yasaki wani irin murmushi, yasan mutane dayawa zasuyi tunanin mama yabawa company duba da yanda yafara da yabon ta, sannan Kuma da kasancewar ta itama sunanta AISHA, wata irin dariya ce ta kama Ramadan yayi qasa da Kansa ya tuntsire da dariya domin Gano inda maganar abokin nasa tanufa.
Dam dam, gaban munirat yafadi, lokaci daya gumi ya wanke mata fuska, mutanan data gayyata kuwa gaba dayansu juyowa sukai suna kallonta jin labari yasha bambam
Shahaab kuwa yana gama wannan jawabi yad'auki takardun company, wajan da mamallakin company zaiyi sign yakalla, shiru yayi yarasa wanne irin sign zaiyi mata? Baisan Yaya take signature dinta ba, danhaka yabi shawarar zuciyar sa yayi mata sign da ASH~HAB
( y a u S h a h a a b y a t a r o D e c e m b e r a w a j a n m u n i r a t =??????
@&?D a n y a w u c e m a r c h )
L i t t a f i n S H A H A A B n a k u d i n e , d u k w a d d a t a q i b i y a n k u d i t a k a r a n t a b a z a n t a 6 a y a f e m a t a b a , h a r a b a d a , k i b i y a n a i r a 3 0 0 k a c a l t a a c c o u n t d i n a
0 1 6 4 5 4 9 4 8 8
A m i n a m u h a m m a d
G T b a n k
K o k u m a k a t i n M T N t a
K a t s u r a s h e d a r b i y a t a w a n n a n n u m b e r 0 8 0 3 3 3 0 0 0 3 4
M r s U s m a n c e
'??
P a g e
2 7
M a m a t a g i r g i z a k a n t a , t a s a n d e b a d a i t a S h a h a a b y a k e b a , d o m i n k u w a i d a n i t a c e b a z a i c e A i s h a K a i t s a y e b a .
t a j u y a t a k a l l i R a m a d a n , t a g a y a n a ta dariya,ahankali ta rage muryarta tace "wacece Aisha?"
Cikin sauri Ramadan ya kalleta, dahar zaice Aisha ai tana tare dake mama, Sai yayi tunani Gara taji daga bakin Shahaab din, tunda yasan dole zaiyi mata magana cikin fahimta, Girgiza Kansa yayi yace "jinake ke yake nufi mama"
Mama ta kalleshi tayi murmushi, tasan Dama bazai fada mata gaskiya ba, Amma babu abinda bai saniba akan Shahaab tunda tare suke komai.
Cikin iya kissa munirat tatashi tana dariya wadda tafi kama da yaqe, Sai firfita take da hannunta ta silale tabar wajan,
Qawayanta suka Mara mata baya.
Mama kuwa bata tafi ba, saida aka gama taro da'ita, har zuwa lokacin Ramadan yana tare da'ita, mutane Sai zuwa suke suna gaishe ta, saida mutane suka Dan ragu, sannan Ramadan ya rakata mota tatafi gida.
Mama tana zuwa gida tasamu Aisha afalo tana kallo, tana ganin Zuwan mama tatashi tsaye, cikin ladabi tace "mama sannu da zuwa"
Mama ta zauna a kujera tana cire agogon dake daure a hannunta tace "sannu Aisha, yagida? Kina zaune ke kadai bakya gajiya da wannan kallon ne?"
Murmushi tayi tace"mama agida Bama kallo, shiyasa yanzu yake birgeni, Amma idan bakya so insha Allah zan Dena"
Cikin sauri tace"a a, yi abinki, idan nahanaki kallo menene ribata? "
Cikin ladabi tace"to mama nagode, nakawo miki abincin danayi miki?"
Murmushi mama tayi tace"saida kika yi girkin de, tojeki kawomin "
Cikin murna ta wuce kitchen tazubowa mama dambun shinkafar datayi Wanda yaji kayan hadi harda su hanta yanata turiri, mama tace "masha Allah, Aisha kece kikai wannan?"
Murmushi tayi tace"nice nayi mama, ko nazauna nabaki?"
Tace"A a karki damu, zanci dakaina,Amma ki ajiyemin shi da daddare zan sake ci, yanzu de jeki kiramin Munirat"
Cikin sauri ta kalli mama, itafa batason shiga sabgar wannan matar tasa,ko kadan batasan abinda zai hada su, cikin sanyin jiki tace"mama ai bansan part dinba"
Mama tayi murmushi tace"a a, baki ta6a zuwa bane?"
Daga mata Kai tayi,mama tace" a a baki kyautaba Aisha, masu suna Aisha fa sunada kirki, ko baki San Nima sunana Aisha ba?"
Kallon tayi tace"bansani ba mama, ashe haka sunan ki"
"haka sunana, Kuma nasan duk me suna irin nawa tanada kirki, saboda haka kede baki kyautaba da baki ta6a zuwa kun gaisa da munirat ba,karki damu da halin ta,haka take, Nima haquri nake da'ita,idan kika fita zakiga wani part daga hannun damanki, kije kice mata tazo in jini"
Tace "to mama"
sannan ta juya tafita.
Ta danyi tafiya medan Nisa sannan ta qaraso part din, wasu ma'aikata tagani a tsaye daga Gefe, gulma ta rufe musu ido ko lura da Aisha basuyi ba, daya daga cikin su yace"ai yau yalla6ai yayi maganin wannan matar tasa, muda mukaje muka tsatstsara wajan muka share, mu akai komai akan idonmu, kamfanin fa ta fadawa mutane ita zai Bawa, habaaa! yalla6ai yana tashi saiya Bawa Hajiya Mama kamfani, bakuga yanda take gumi ba"
Wani zai sake magana Aisha tace"dan Allah inane qofar shiga part dinnan?"
Juyowa sukai suka kalleta, saikuma suka fara kuskurin kunya, suna tunanin taji abinda suke fada Kuma suna tsoron taje ta fadawa mama, ita kuwa suna nuna mata ta wuce, tana shiga part din taga yasha bambam da'irin na mama, tsaruwar Kam harta yi yawa, idan anan part din take 6ata lokaci zatayi wajan kallon part din kawai.
Munirat tagani a zaune da wasu mutane su su hudu, Dan kwalin kanta yana riqe ahannunta, ta hargitsa gashin dokin kanta, masifa ta rufe musu ido basu maji shigowar Aisha da sallamar taba, ikee tace "waima wacce shegiya ce wannan Aishan?"
Kai tsaye munirat tace"uwarsa ce mana, da'ita yake"
Ajiyar zuciya ikee tayi sannan tace"ni narasa abun damuwa anan munirat....tun farko fa kece kikai wasa da damar ki da har Zaki Bari yadinga fifita wannan tsohuwar sama dake"
Hauwi tace "Allah natuba mezatai dawani company yanzu? Taci zamaninta tana neman shiga naki zamanin keda mijinki, Shima da niyya yabata ai, yasan tana mutuwa kudin de nasane"
Qanwarta Maryam tace"amma Anty ya Yaya Mahmud zai mana haka? Mommy tana can gida fa tayi gayya, tun jiya muke hada abincin baqi saboda mutanan data gayya ta"
Munirat ta goge Hawayen idonta tace"Dama mamarsa ta tsaneni, narasa Mena tsare mata, da kunne na naji yana cewa zai Bani, Amma nasan inde yafada mata Dama zata hanashi yabani,tunda gashinan anrubuta sunanta akan takardun ai shikkenan,Kuma wallahi Saita gane...."
Maganar ta ce ta maqale ganin Aisha a tsaye abakin qofar Dakin, cikin masifa tace"kekuma ubanme kike akanmu? Munafuka muna magana kinzo kin tsaya mana aka wato Zaki kwasa kije kifada mata ko?"
Cikin sauri tace"mama ce tace kizo tana kiranki "
Cikin tsawa munirat tace"fice kibarmin Nan kona tashi na kakkarya ki,annamimiya"
Cikin fishi Aisha ta juya tabar mata part dinta, qasa qasa tace"wallahi Bani ba saide ke"
Ikee