Showing 111001 words to 114000 words out of 116763 words

Chapter 38 - SHAHAAB COMPLT

Start ads

10 Aug 2025

819

Middle Ads

Allah karki barni kinji...."

Wani irin dadi ne yakama Aisha, bata ta6a tunanin haka ta kwarewa Shahaab dinba Sai yau, ita Kam Ina ita Ina rabuwa dashi?ahankali ta sauka daga Kansa, sannan tasaka hannayenta ta rungume shi, ta kalleshi cikin ido tace"tayaya kake tunanin zan iya rabuwa dakai?jin dadi na dakuma walwalata bazasu ta6a samuwa ba muddin Bana tare dakai, idan rayuwa bazata iyu batareda iska ba, to tabbas Aisha bazata iya rayuwa batareda Shahaab ba, Ina sonka Baby"

Ta qarasa maganar cikin sigar rad'a, murmushi yayi yasaka hannunsa ya rungume ta, cikin shagwa6a yace"maamah..."

Tanajin salon yanda Yakira sunan Nata, tasan cewa qari yake nema, cikin shagwa6a itama tace"Anjima kayi"

Yace"sosai kamar na yanzu?"

Tace" idan kanaso fin hakama"

Cikin jin dadi yace"thank u maamah"

Yasaka hannu ya daukata suka shige toilet, sabon wanka sukayi, sannan Aisha tasake gyara Dakin suka shirya suka dawo falo Daddy yana hannun Shahaab, ita Kuma ta wuce fridge tadauko chocolate tana Sha, kallo suke cikeda farinciki gaba dayansu, harda Daddy Wanda kawai hasken TV ya zubawa ido yana kallo.

Ranar basu koma part din mama ba, itama batayi jajensu ba, tana can tareda Hajja,har dare Shahaab yana naniqe tareda Aisha, Bai daga mata qafa ko dayaba ranar.
Washe gari takama weekend yana gida, Bayan sunyi wanka sun shirya part din mama suka nufa,Bayan sunci abinci Aisha ta nufi kitchen tad'auko ice-cream roba guda ta zauna tanasha, shikuma ya amsa waya yafita, Bai dawo gida ba Sai Bayan azahar, yana zuwa yaga mama tana cewa Aisha"sakashi a jikin ki yaji dumi sosai"

Zama yayi yace"lafiya? Meyasame shi?"

Kafin su bashi amsa Yaron yasaki atishawa, mama Tace"wallahi yanzu yanzu fa kawai Naga yanata atishawa kode kun kwana da esi a kunne ne?"

Cikin sauri Aisha tace"mun kunna kam"

Ran Shahaab ne yayi baqiqqirin yace"babu ruwan esi,yanzu haka sanyin da aka dinga dura masa ne"
Yaqare maganar yana daukan Daddy yatashi yana jijjiga shi.

Mama tace"sanyin me Kuma?"

Cikin damuwa yace" mama dazu Ina shirin fita Ina kallonta da uwar robar ice-cream Sai Sha take ko tausayin Yaron Nan bataji, may be sanyin ya zuqo daga nononta"(>?-?)

Mama ta jijjiga Kai tareda sakin ajiyar zuciya, taga alama al'amarin Shahaab gaba yake yi akan Yaron Nan, inajin Nan gaba saiya Hana Aisha kyakykyawan motsi saboda Daddy.

Aisha ta kalleshi tace"yanzu Uncle wannan Dan ice-cream din da Nasha shine zai saka shi mura? Bafa duka na shanye ba, Dan kadan Nasha ko mama?"

Tajuya tana tambayar mama.
Bai saurari abinda mama zatace ba yace"ungo taso ki goyashi, ai d'umin runguma yayi masa kadan, zoki goyashi idan yaji d'umin ki sosai may be yadena atishawar"

Mama ta zuba masa ido tana kallon ikon Allah Kuma tanaso taga me uwar Dan zatayi (>??=??)

Cikin sauri Aisha tace"d'azu d'azu nagama goyashi, wallahi nagaji,ka kira me aiki ta goyashi"

Cikin sauri ya kalleta, fuska daure yace"ki goyashi mana"

Dan qaramin bakinta ta turo gaba sannan tatashi ta juya masa baya, yad'ora mata Yaron tagoyashi, sannan tafara jijjiga shi, Sai a lokacin yasaki wata irin ajiyar zuciya yanemi waje ya zauna, har zuwa lokacin mama bata ce musu komai ba, tana zaune tana ganin ikon Allah, Aisha kuwa daga gaji da tsaiwa saita nemi waje ta zauna, tana dora duwawunta akan kujera Daddy yasaki kuka, Sai atishawa, gaban Shahaab yafadi, cikin sauri ya kallesu, ganin yanda yake kallonta yasa tasake tashi tsaye, tana tashi Daddy yayi shiru, falon tafara zagayawa tana Dan jijjiga shi, cikin akasi inda ta cusa towel din goyon yafuto, aikuwa Daddy yayi baya zai fad'i (=?2?=?F? @&?)

Ita de mama tana zaune, Amma batasan Yaya akai ba Sai ganin Shahaab tayi yayi wata irin super, Sai gashi agaban Aisha, Aisha tayi wata irin zabura ta tsorata, cikin tashin hankali yace"ki riqeshi dakyau mana,kinga kawo Shima, dama can ba qaunar goyon kikeba, kawo shi, Dan idan nabar miki Shima Zaki iya yarda shi, Kuma ko bemiki mita a ransa ba Nima sainayi"

Mamaki yakama Aisha,Kallonsa tayi cikin 6acin rai tace"tayaya zan yarda d'ana aqasa uncle?Dan Allah kadinga saukaqewa kanka damuwa akan Daddy"

Maimakon yabata amsa saiyace"waya sanima ko mintsininsa ake, yaro tun dazu daga kuka Sai atishawa"
Kallonsa tayi da sauri ta Girgiza kanta ta nemi waje ta zauna ta dora qafarta daya Kan daya tareda d'aukan remote, Shima Yaron yafara jijjiga wa,da yaga jijjigawar ba zatayi ba saiya dorashi a bayansa yafara zagaye falon da Yaron, Hajja data idar da sallah tafuto daga d'aki taga Shahaab da goyon Daddy tace"yau kaine da rainon?"

Cikin sauri yace"Hajja ruwan Sanyi ta dinga d'urawa Yaron Nan, gashinan Sanyi nema yake ya kamashi"

Hajja tasa hannu ta kar6eshi tace"kawo shi mugani"

Babu musu yabata shi, sannan yanemi waje ya zauna kusa da Aisha, mama tasaki ajiyar zuciya tayi murmushi ganin yanda suit din dake jikinsa harta fara tattarewa daga baya saboda wannan Dan goyon Dayayi, Sai wata zufa yake hadawa kamar wanda yayi tseren gudu(=??)
Ganin ya zauna kusa da'ita ko kallo bai isheta ba yasa yasake jin wani irin haushi, yasaki qaramin tsaki nanma Aisha ko juyo wa batayi ba, yasaka hannu ya fizge remote din hannunta, Sai Alokacin ta kalleshi ta kawar da kanta itama tana Girgiza qafa alamun akusa take, Hajja kuwa da batasan wainar da mutanan falon suke Toya waba saita shige daki domin shafawa Daddy man kad'e ajikinsa.

Haka rayuwar take tafiya yau dadi gobe babu dadi, Hankalinsu kwance suke rainon Daddy, idan kaga Shahaab da Aisha sun samu Sa6ani to akan Daddy ne, kokadan bayason abinda zai ta6a Yaron, mama kam idan yana wani abun saide ta zuba masa ido tana Kallonsa kawai, wani lokacin ko wankan Daddy ake haka zai zauna yadinga mita shide Adinga yimasa wankan Ahankali, haka suka dinga Haquri dashi har Daddy Yacika wata hudu, kwata kwata ba zakice Yaron watansa hudu ba saboda yana samun kulawa ga nono ga madara, uwa uba ga abincin Yara da'ake bashi, shiyasa suka fara zaunar dashi Kuma daram yake zama, Amma duk wani abu dayake gefensa inde hannunsa zaikai wajan, to yanzu zaiyi ajalinsa, kokadan hannunsa baya zama waje daya, idan Shahaab yadawo daga wajan aiki haka zai zauna akusa dashi yadinga yimasa hira kamar wani me Hankali, wasa kuwa idan yacire kayan jikinsa yadauke shi suka dinga wasa afalon saide Aisha ta jiyo sautin dariyar su, wani lokacin tayi musu vedio wataran Kuma ta dinga kallon su tanajin farinciki acikin ranta.


Har zuwa lokacin Hajja tana gidan,idan sungaji da Zaman gidan itada mama haka zasuyiwa Shahaab magana yasa a fitar dasu wani wajan Sudan Sha iska su dawo, ahankali ahankali rayuwa take tafiya har Daddy yafara rarrafe, tunda yafara rarrafe mama ta Dena ajiye wayarta aqasa, idan tea aka kawo musu saide su riqe a hannun su, baya ta6a zama shi kadai, idan kuwa aka jishi shiru babu 6arna to yasamu wani abun ne yana lalata shi, shine zakaji shi shiru, gaba daya falon mama yazama kamar falon renon Yara uku saboda yanda aka baje masa kayan wasa, haka zai zauna daga shi Sai pampers yana wasansa afalon, suma masu aikin gidan inde sunzo falo Tofa Sai sunyi masa wasa zasu wuce, ganinsu dayake yau da gobe yasa baya musu qiwa, saide in baiga wani yashigo falon ba, yanzu zai fara daga hannu yana kuka alamun yanaso a dauke shi.

Tunda Shahaab yatafi lagos Kwanansa biyu bai dawo ba, yau yana hanyar dawowa yakira Aisha yace tahada masa cake idan yazo zaici, gashi su mama basa Nan, Kuma tunda taji Yakirata yafada mata hakan tasan cewa to bayason na ma'aikatan gidan ne, ta kalli Daddy dayake wasa cikin motar wasan Yara, ta dauke shi ta goyashi suka shige kitchen tafara aikinta tana masa magana kamar wanda yake jinta, Shikuwa gwarancinsa yake ma yana saka hannunsa abaki, Bayan tagama hada komai tasaka butter da suger tana mixing tace"Daddy na d'an Albarka yau ai zaka barni in yiwa Abbanka cake ko?"

Tadauko qwai tafasa taci gaba da mixing, Hankalinta yayi kan abinda take batayi aune ba taga Daddy yaja fulawar data ajiye ya kwaro musu ita kansu, lokaci daya ta tsorata tasaki qara saboda zubar fulawar kawai taji, shikuma qaran data saki ne yasa ya tsorata yasaki kuka Kuma ya qanqame bowl din yaqi saki, baqin ciki yakama Aisha(=??).


Tunda yashigo kitchen din ya tsaya abakin qofar kitchen din yana kallonsu, sosai tayi masa kyau da goyon Daddy musanman da yaji tana masa magana kamar Dame Hankali take magana, ganin aikin da Daddy yayi mata yasa ya tuntsire da dariya yafara yimusu vedio, juyowa tayi ta kalleshi da fuskarta data cika da fulawa tafashe da Kuka, qaraso wa yayi kitchen din ya qwace bowl din hannun Daddy sannan ya kunce mata shi, kuka take sosai cikin kukan tace"kana ganin abinda yamin fa, ya 6are baki yanamin kuka kamar bashine yamin laifin ba"

Cikin jin dadi ya janyo ta jikinsa ya rungumesu gaba daya, sannan yafara kad'e mata fulawar yana lallashin ta, daqyar yasamu tayi shiru sannan yace"ai nine nace amin cake din, to abarshi tunda Daddy yahana"

Cikin shagwa6a ta kalleshi takai masa Dukan wasa a qirjinsa.


Da daddare suna zaune a part dinsu suna kallo, Sanye take cikin rigar bacci tana kallon film din da ake haskawa, agefe daya Kuma waya take da faty tana sanar da'ita ansaka ranar bikin ta, shikuma Shahaab yana zauna aqasan kafet yana aiki a computer, yayinda Daddy yake Gefe yana wasa, saida tagama wayar sannan ta kalli Shahaab tace"Uncle ansaka ranar bikin faty fa, nanda wata shida"

Hankalinsa yana kan aikin dayake yace"Allah yakaimu, Amma Ina tunanin zuwa lokacin Bama Nan ai, inaso muje umara gaba dayanmu, dasu Ummah dasu Hajja, daga Nan Kuma zamu je muga jabir"

Cikin farinciki tace"Uncle Saudia zamu tafi gaba dayanmu?"

Yace"insha Allah"

Cikin jin dadi taje ta rungume shi tasakar masa kiss tace"wayyo Allah, Amma naji dadi uncle, mungode Allah yasaka da alkhairi yaqara budi"

Cak ya dauketa yadorata akan cinyarsa yace"Amin, idan kinyi waya da qawar ki ta jigawa kifada mata Faisal yamin magana yanaso inje gidansu in nema masa aurenta"

Fari tayi da idonta tace"wai Walida?"

Kansa yadaga mata yana sake gyara mata gashin kanta, cikin jin dadi tace"zan fada mata, Bari inkirata ma yanzu"

Tafadi haka tana qoqarin tashi daga kan cinyarsa, cikin sauri ya riqeta yace"Haba madam"

Murmushi tasaki kafin tayi magana yafara waigawa falon yace"ina Yaron Nan yake ne?"

Tashi tayi daga cinyarsa tace"inaga wasa yake"

Shima tashi yayi yana nemansa, acan suka hangoshi yana rarrafe yana bin ball dinsa yanaso ya dauko ta, cikin sauri Shahaab yadauko shi suka dawo kan kujera suka zauna ya kalli Aisha yace"yazaki barshi yana rarrafe a tile maamah?"

Tace"to Uncle akan cinyata zaiyi?na'isa in Hana Daddy rarrafe?tayaya ma zan San yatafi?"

Goge wa Yaron qafa yakeyi, sannan yadora mata shi akan cinyarta yace"ki kula dashi karki sake barinsa yana rarrafe a tile please,Bari in Dauko takardu adaki"

Aisha ta Girgiza kanta, Shima Daddy qoqarin zamewa yake zai sauka, babu musu kuwa ta sauke shi, wajan kallo yanufa ya zubawa TV ido yana kallo, itama Hankalinta yana kan kallon saijin ihun kukan Yaron tayi, cikin sauri ta nufeshi, Shahaab ma da yaji kukan yayi yawa cikin sauri yafuto daga d'akin hannunsa d'aukeda takardu yanufeta sannan ya karbi Daddy yace"me aka masa yake wannan uban kukan?"

Cikin damuwa tace"ni wallahi ban lura ba, Sai kukan sa naji, speaker yaja tafado masa ahannunsa shine yake wannan kukan"

Cikin sauri yaduba hannun yaga har yatsun sun danyi ja kasancewar sa fari, iska yadan hura masa a hannun sannan ya kalleta yace"maamah, kifadamin tsakaninki da Allah Anya ba cizon yaron Nan kikai ba?"(>??=??)

Cikin sauri ta d'ago ta Kalle shi tace"nashiga uku Uncle??"

Cikin damuwa shima yace"maamah idan cizon nasa kikai ma Yaya zanyi dake?"yana fadar haka yajuya da Yaron suka shige daki, ita Kam murmushi ma tayi tabi bayansu Dakin, gaba dayansu su biyun suka hadu suka lallashi Yaron har bacci ya dauke shi sannan ne Kuma suka shirya=??

Rayuwa tana juyawa Izuwa yini, yini yana juyawa Izuwa kwana, kwana yakoma sati, sati yakoma wata har Daddy Yacika wata goma, Adede lokacin Kuma suka shirya gaba dayansu suka tafi Umara, Mama,Hajja,Ummah,Abba, Shahaab, Aisha, dakuma Daddy, satin su biyu a Saudia, Adede lokacin Kuma akai bikin faty,Walida Kuma ansaka rana wata uku masu zuwa itada Faisal Yaron Hajiya zaliha,kana ganinsu kasan family ne daya amsa sunan sa Family Kuma suke cikin kwanciyar Hankali da walwala, daga Saudia Australia suka wuce wajan Jabir, yayi murna sosai da ganinsu ya girma yasake zama saurayi, yana ganin Daddy ya dauke shi bacci ne kawai yake raba shi da Yaron, satinsu biyu a qasar, suka dawo Nigeria.

Bayan sati daya Aisha da Shahaab suna zaune afalon su suna kallon Ball, gaba daya hankalin sa yana kan ball din da'ake bugawa, Aisha ma daba sanin Yan ball tayi ba tazuba ido tana Kallonsu har aka gama wasan, taga an nuno wani matashin saurayi da yaro ahannunsa dagashi har Yaron Sanye suke cikin kayan ball Sai mutane yakewa sign a takardar dasuke bashi, sosai yake Fara'ah dimples dinsa Sai lotsawa suke, Yaron hannunsa yadaga masa yana gudu da Yaron sosai alamun ball din dasuka buga tamasa dadi, Shahaab yayi murmushi yace"wannan Yaron bayaji"

Aisha ta juya ta kalleshi tace"musulmi ne?"

Murmushi yayi tace"sosai kuwa,d'an asalin Niger ne,Amma a Nigeria suke, family dinsa da kowa da kowa da matarsa duk suna kano,sunansa BIG BROTHER, but wasu suna kiransa BABBAN YAYA,ya'iya ball sosai"

Aisha tayi ajiyar zuciya tace"um, ku kuka San Yan Ball Uncle"
Juyawar dazatai taga Daddy yabude fos dinta yafuto da kudin ciki Yan Dari biyar biyar da dubu dubu gaba daya ya yaiyaga su, cikin 6acin rai ta daki Yaron tace"Daddy kudi kake yagawa haka?"

Cikin sauri Shahaab ya kalleta, Jiyayi kamar shi ta daka,lokaci daya yafara huci yana Kai zuciyar sa nesa, jiyake kamar ya Fashe, daqyar ya'iya controlling kansa yace"maamah duka? Yanzu Harkin fara Dukan yaron Nan agabana maamah?"

Cikin 6acin rai ta kalleshi tace"Uncle kudi fa yake yagawa, idan Bana dukansa bazai ta6a gane yayi laifi ko baiyi ba"

Yace"to kudi Kuma saiki masa irin wannan Dukan? Ina laifin ma kisamu tsinken tsintsiyar laushi? Kidena masa irin wannan Dukan kinji nafada miki, idan kika sake Kuma zakiga abinda zai biyo baya"

Haushi yakama Aisha,baqin ciki ne yasa batasan lokacin data sake kaiwa Yaron duka ba, Shahaab yana ganin haka yatashi tsaye, tana ganin yatashi tsaye takwasa a guje tayi dakinta, tana kokarin rufewa yayi nasarar shiga Dakin, akan gado suka zube, yajata jikinsa ya matse ta, dariya tafara tana kokarin qwatar kanta, tasan zata Iya shan wahala awajansa, inde akan Daddy ne, shiyasa tun kafin yayi mata wani abu takai hannunta tata6o masa inda tasan cewa dole yayi saranda, Shima anasa 6angaren hannunsa bibbiyu yad'ora akan nashanunta yana murza mata nipples d'in da qarfi, cikin muryarsa Mai cikeda buqata yace"meyasa bakya jine maaa-mahhhh"

Yafadi sunan Nata a rarrabe, cikin kissa tafara zuba masa kukan shagwa6a, hakan ne yasake tunzurashi yaci gaba da aikata mata saqo, cikin tsananin azaba taji cikinta yayi wata irin murdawa, Nan da Nan tasaki kukan na gaske, cikin kuka tace"Uncle cikina, zan mutu Uncle"

Idonsa a Lumshe suke, Amma yanda yaji tayi masa magana cikin serious, yasa yabude Idonsa yakai Kallonsa gareta, ganin halin datake ciki yasa cikin tashin hankali ya dauketa, yadawo falo yad'auki Daddy suka futo, Adede lokacin mama da Hajja suna compound din gidan suna zancen su, ganin yanda ya Dauko Aisha a hannu yasa suka iyo wajan sa cikin damuwa, mama tace"muje Asbiti kawai, ciwon ciki abun tsoro ne"

Cikin sauri yace"ku zauna mama, Bari muje nakaita"

Hajja Tace"A a, Zaman me zamuyi? Muje kawai"

Babu musu suka dunguma zuwa Asbiti gaba dayansu, suna zuwa likita tabata taimakon gaggawa aka daura mata ruwa tareda allurai, Sai Alokacin tasamu bacci, gaba dayansu sunyi shiru suna mamakin wannan ciwon ciki na Aisha, cikin ikon Allah tafarka cikin qanqanin lokaci, Adede lokacin Kuma Likitan tadawo fuskarta d'aukeda murmushi ta kalli Shahaab tace"yalla6ai Yaron baba fa bayason guje-guje da tsalle-tsalle, congratulation madam tana d'aukeda juna biyu"

Cikin sauri Aisha ta tatashi zaune, Shahaab kuwa wani irin farinciki ne ya kamashi yace"Dr da gaske?"

Cikin farinciki tace"sosai yalla6ai"


Hajja da mama ma cikin farinciki suka daga hannu suna yiwa Allah godia, bata dauki tsawon lokaci ba suka sallamesu suka dawo gida, suna zuwa gida ta wuce part dinsu, acan dinma dakinta ta wuce ta zauna abakin gado tafashe dawani irin kuka, tunda suka taho a hanya ya lura kawai sune suke budurinsu, Aisha bata cewa komai, kwata kwata ya lura batayi farinciki da samun cikin ba, lokaci daya jikinsa yayi Sanyi, shiyasa yanayin parking da yaga tafita daga motar yasan cewa akwai damuwa, su mama kuwa basu lura da sauyin yanayin taba, suma part dinsu suka wuce, ahankali ya kalli part dinsu yasaki ajiyar zuciya sannan yabi Bayan Aisha.


Yana shiga kuwa, yaga bata falon, Kai tsaye dakinta yawuce, tun kafin yashiga Dakin ya tsinka yi muryar ta tana kuka, jikinsa ne yayi Sanyi kalau, yaja ya tsaya abakin kofar d'akin tareda harde hannunsa a qirjinsa yana kallonta, Sarai taji shigowar sa, Amma bata daga Kai ta kalleshi ba, asalima kukan ta taci gaba dayi, ajiyar zuciya yasauke yatako yaqaraso cikin Dakin ya zauna akusa da'ita yace"maamah"

Tayi shiru bata amsa masaba, Kallan ta yayi yace"atunani na zakiyi murna ne da kyautar da Allah yayi mana maamah, bansaniba ko kin daina sonane shiyasa bakya son ki hada jini dani"

Cikin kuka ta daga kanta tace"Daddy fa ko yayeshi banyi ba....kuma yanzu harna sake yin wani cikin"

Idonsa ya Lumshe sannan yabude, yace" bazanga laifin ki ba idan kinyi watsi da kyautar da Allah yayi miki, saboda Sai wannan shekarar ne Zaki cika shekara goma Sha Tara, Amma ni shekaru na arba'in dawani abu, banda Ina cikin jin dadi dakuma yanayin jikina ke kanki kinsan cewa niba qaramin mutum bane maamah,kiduba kigani fa Sai yanzu ne nafara haihuwa, kafin ace yarana sun girma sun fara taimaka min nariga na tsufa, shekara ta goma Sha da aure ban haihu ba Sai yanzu ne Allah ya dubeni yabani Daddy, Kuma yanzu saboda butulci irin nawa Sai inqi wata kyautar Dayayi min?maamah ko Daddy bekai wata goma ba kika samu ciki zanyi murna da hakan,Amma idan zubarwa kike so kiyi Nima saina miki allurar, idan hakan zaisa kiyi farinciki, saide Kuma agaba idan Allah yahanamu haihuwar har abada, karkiyi kuka Dani, kiyi kuka da kanki"

Hawayen idonta tashare tace"ni bazan zubar da ciki naba,Nasha wahala a haihuwar Daddy, Kuma ko shekara biyu beyi ba, gashi yanzu wata wahalar zan sake fuskanta"

Janyota yayi jikinsa ya rungumeta sosai sannan yace"maamah haihuwa

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login