Showing 24001 words to 27000 words out of 116763 words
de Sai mutane sun shiga tsakani sun raba mu, Amma kabamu awa uku, saide kaga mun shirya, ko ban kulata ba, to ita Kam saita kulani, tundaga Nan da mutane suka gane halin mu, ko sunga suna fadan saisu qyalemu saboda sunsan zamu shirya"
Aisha tace"to Hajja bakida photon tane kinuna mana? "
Tace"inada shi mana, yana cikin adaka ta aqasan gado na, zan nuna miki takwararki, har saurayinta na makaranta ma duk inada photon sa, Shima zan nuna miki "
Cikin sauri Aisha tace"au Hajja har soyaiya kuke a makaranta? "
Hajja tace" emana, kafin muyi candy kowacce tanada saurayi, mudinga rubuta wasiqa muna aika musu, suma suna aiko mana, Bayan munyi candy ne Kuma muka rabu da samarin kowa tafara tunanin aure, ni muka dawo jigawa, ita Kuma suna kano "
Jin ankira sallar asuba yasa firar tasu ta tsaya, Abba yatafi masallaci, sukuma kowa yafara kokarin daura Alwala.
******
Yau saura kwana uku sallah, tunda sassafe yatashi yayi wanka, yadauko suit takai Kala biyar, duk wadda yad'aga saiya ga batayi ba, daga qarshe yasaka wata ruwan toka wadda ta qarfi fatar jikinsa
Yayi mutuqar kyau shi Kansa daya kalli Kansa a mirror yasan yayi kyau, murmushi yayi yad'auki turarensa yafara feshi dashi ajikinsa
Munirat data shigo Dakin saita zubawa sarautar Allah ido tana kallo
Cikin mamaki tace "my Dear yanaga ka zubar da kayaiyaki akan gado, lafiya?"
Batare daya kalleta ba yace "naza6i Wanda zan saka ne"
"to yanzu duk wannan daka zubar akan gadon basu Maka ba? Dubafa kagani harda suit din Dana siyoma a Cairo"
Yatsina fuska yayi sannan ya kalleta yace "wannan naza6a"
Hannu tasa a qirjinta ta hardesu, sannan ta fuskance shi sosai tace "zakaje wajan Mr President ne?"
Gabansa ne yafadi, Sai alokacin yadago Kansa ya kalleta "no, zamuje jigawa nida Ramadan,ganin aikin gidan marayun Nan"
Wata wawuyar ajiyar zuciya tasaki sannan tace "Alhamdulillah....na yi tunanin wajan wata zakaje wallahi, yanda kake zuba kwalliyar Nan ai sai kasa jinina yahau, nasan inde kafita saiwata ta kallemin Kai, Amma tunda qauye zakaje, nasan banda damuwa,nasan Babu wadda tayi daidai da kalar mijina a wannan baqauyen Garin, babu ita, ba Kuma za'a yitaba"
Kansa ya girgiza yace"hakane"
Bakinsa yad'ora akan goshinta yasakar mata kiss, sannan yafice daga d'akin cikin sauri
Kai tsaye wajan mama yatafi, ganin ta yayi tana matsa qafafunta da kanta, cikin sauri ya qaraso ya tsugunna yaci gaba da matsa mata qafa fun, Kallan sa tayi tace "masha Allah,Dan mama yau Kuma Sai Ina? Ko qasar zaka Bari Amma baka sanar Dani ba?"
Murmushi yayi, dimples dinsa suka futo, yace "Wai nayi kyau ne mama?"
Tace "sosai ma kuwa, kamar Ango"
Murmushi yayi tare dayin qasa da Kansa, yad'ora hannunsa akan sumar Kansa ya Dan Sosa qeyarsa, sannan yace "haka munirat ma tace Wai nayi kyau, babu inda zanje mama, jigawa kawai nakeson zuwa saboda ganin aikin gidan marayun dakika sakani"
Cikin farinciki mama tace "Allahu akbar, Allah yayi Maka Albarka Mahmud, yanda kakemin biyaiya kaima Allah yabaka Wanda zasuma fiyeda haka, Allah yasa kafin nabar doron duniyar Nan Inga jikokina Kuma Inga Qawata Aysha Sulaiman Bompai"
Cikin sanyin jiki yace "Amin mama, Bari intafi, Ramadan yana jirana a Airport"
Tace "to Allah ya dawo daku lafiya, ABINDA KAJE YI ALLAH YABAKA NASARA AKANSA"
Ahankali yace "Amin mama" sannan yakama hannunta yayi kissing Bayan hannun, yafice daga falon cikin sauri, binsa tayi da kallo tana jin dadi a ranta, cikin zuciyar ta tace "Allah ka qara aramin lokacin dazanga yayan Mahmud dina...."
Motoci biyu ne suka rakashi Airport, daya yana ciki, dayar Kuma sojoji ne, suna zuwa Ramadan yazo da sauri yatareshi, sannan suka qarasa cikin Airport din.
Bayan sun sauka a dutse, wani direban ne yasake daukar su, Kai tsaye wajan aikin gidan marayu suka wuce, komai yayi, suna aikinsu yanda ya kamata, saida sukai sallar la'asar awajan, Shahaab ya dubi Ramadan yace "muje ko?"
Ramadan yace "Ina?"
Kai tsaye yace "Abinda yakawo mu"
Wayarsa ce tafara ringing Kiran munirat, Bayan sun gaisa tana masa qorafi bai ta6a tafiya yaqi kiranta ba, Sai wannan tafiyar, goshinsa yadan shafa yayi shiru, shi Kansa yasan gaskiya ta fad'a masa, baisan menene yake damunsa ba yau din, haquri kawai yabata, sannan yafada mata aiki ne yamasa yawa, zasuyi waya anjima, daga Nan yakashe wayar
Kallan sa Ramadan yake lokacin dayake waya da Munirat, gaskiya Shahaab ya sauya sosai, Kuma yasan cewa duk a dalilin wannan yarinyar ne, kowacce irin yarinya ce haka data sauya masa tunani lokaci daya? Shikam zai so yaga wannan yar baiwa, to matsalar Kuma shine shi yaqi yarda son yarinyar yake, Amma babu damuwa ai lokaci zai nuna komai.
Shahaab yace "Ramadan bakajini bane?"
Ramadan yace "najika Sarai, kaine de kunnanka yadena aiki, idonka yarufe, kwata kwata ka manta waye Kai, ka manta cewa kaine MAHMUD WAKILI...."
cikin rashin fahimta yace "mekake nufi?"
"Abokina kaine kace min yarinyar Nan batasan waye kaiba, asalima ce mata kayi kaidin Yaron Mahmud Wakili ne, Kuma Sarai ta ganka, Kuma yanzu Sai muje garinsu da yamma, mu parker mota aqofar gidansu, muyi magana da'ita, karka manta ita kadai ce batasan waye kaiba, bawai mutanan Garin ba, itama nayi mamaki dakacemin bata sanka ba, to yanzu kuwa muna zuwa, idan wani yaganka ya ganeka, zai fadawa na kusa dashi, Shima ya fadawa wani, dahaka mutanan qauye su taru azo wajan Mahmud Wakili ayi masa godia saboda kwanaki ya aiko musu kayan abinci, Shahaab kana buqatar privacy, karka manta a Abuja ba Kai kadai kake yawo ba, Nan dinma kwanciyar hankalin jihar ne yasa kake yawo ko'ina haka "
Ajiyar zuciya ya sauke yace "to aini banga abun damuwa ba, saboda bawai zama zanyi da yarinyar har mutane suzo su taru akaina ba, kawai de Naga suna cikin yanayi na rashi, shiyasa zan taimaka mata, sannan Kuma ta fada min abinda yasa take min rashin kunya, idan batada hujja saina mata hukunci daidai da rashin kunyarta inkama gabana, shikkenan fa "
Ramadan yace"idan kuwa ka temaka mata ai zataso kudinga zumunci, ko yar wayar nan idan tana cikin halin buqata zata Iya kiranka ai, kayi hakuri muje da daddare yafi sirri gaskiya, babu wanda yasan munje, babu Wanda yasan mundawo"
Badon ransa yasoba haka yayi shiru, Bai qara magana ba saboda 6acin rai Wanda shi Kansa baisan dalilin hakan ba, Ramadan yadan juyo ya Kalle shi qasa-qasa dariya ta kamashi ganin yanda abokin nasa yahad'e girar sama data qasa
Karfe biyar na yamma suka koma masauqin su, saida aka Sha ruwa, suka huta, wajan qarfe bakwai da rabi suka futo, Ramadan ne yake driving, shikam Shahaab a sonsa, driver yakawo su, Amma Ramadan Sai yaqi yarda yace babu damuwa shi zai kawo su Garin.
Haka suka taho su biyu, da tambaya da komai Allah yakawo su Garin CHAMO, mutane dayawa Sai kallon motar suke saboda yanda take daukan ido tana wani irin qyalli na sabunta, Ramadan ya juyo ya Kalle shi yace "inane gidan?"
Kalle-Kalle yafara, can yace "danyi gaba kadan"
Ramadan yayi gaba, yasamu wani waje can Gefe ya Parker mota, Shahaab ya kalli Ramadan yace "Anya ba zamu koma ba kuwa Ramadan? Gabana faduwa yake, karnaje aljana ce"
Ramadan ya riqe hannunsa yace "mutum ce, duk da banganta ba nasan mutum ce, Ana daure duk wani shedanin aljani lokacin azumi, saboda haka kayi addu'ah kawai ka qarasa gidan"
"tokai bazakaje ba?"
Ramadan yace "Ina jiranka amota, ka dauki Bluetooth dinka saimu dinga magana ta waya"
Girgiza masa Kai yayi, sannan yasaka hannu yabude gidan Bluetooth din yad'auki guda daya,yacire jacket din suit din jikinsa, yacire Agogonsa Mai tsada, niktie din wuyansa ma yacire shi, Jiyayi botir din gaban rigar tasa ya kamashi, yasaka hannu ya6alle guda uku, Nan da Nan kuwa lallausar sumar qirjinsa tafara bayyana kadan, saida yagama gyarawa tsaf sannan yafita daga motar yana tunani a ransa yaushe zai iya bata kyautar dubu biyar saboda ya gwadata kamar yanda Ramadan yabashi shawara? Yanzu Yaya za'ayi ya ganta?.
Tafiya yake ahankali hannunsa daya zube cikin aljihun wandonsa, Sai Kalle Kalle yake kamar yana tsoron wani Wanda yasan shi ya ganshi
Har yaqara so qofar gidansu Aisha, yaja ya tsaya agefen wata bishiya dake kofar gidan, yadade a tsaye awajan yana tunanin wazai tura gidan Akira masa ita?to wazaice Akira masa shida baisan sunan taba?
Ramadan yakirashi yace "kakirata?"
"no, Ina jiran yaro de"
Yace "okay"
sannan yakashe wayar
Shiru shiru babu wani yaro dayazo wucewa ta qofar gidan, bishiyar yasake kalla yanemi waje ya zauna ko Allah zaisa wani Yaron yazo wuce wa, har qarfe takwas da rabi babu alamun mutum Kuma unguwar tafara yin shiru saboda sallar tarawih da aka fara mutane duk suna can suna Sallah
Wani sauro ne yarafka masa cizo abayansa cikin sauri yamiqe tsaye yakai hannun sa wajan yana sosawa, tunani yafara a ransa yaushe Rabonsa ma da cizon sauro?
Kafin yagama tunanin yaga wata tafuto daga gidan, hannunta d'aukeda sallaya,da alama wajan sallah zataje.
Hankalinsa ne yakoma kanta, Hasken wayar Hajja dake hannun ta tana dannawa shine yasake bayyana kyakykyawar fuskarta, hijabin Nata dogo ne har qasa, yanada hula hijabin Sai hular tayiwa doguwar fuskarta kyau sosai, gabansa ne yafadi, kafin zuciyar sa tayi masa tunanin wani abu yayi sauri ya qarasa wajan tareda fuzgota can Gefe, sakamakon fuzgotan Dayayi har jikinsu yana haduwa Dana juna, wayar Hajja tayi Gefe tafadi aqasa, gabanta ne yafadi, abinda takawo ranta kawai masu satar mutane ne zasu saceta, ganin kafafun mutane sun dauke babu wani Wanda zai ceceta yasa tafara kokarin qwace hannunta daya riqe Wanda tuni yafara yimata zafi, Bayan ta qwace hannunta ta kwasa da sauri zata koma gida, cikin sauri shima yakai mata wani irin ruqo bai samu nasarar kama hannunta ba, hakan yasa hannunsa ya sauka akan Bajajjan Qugunta, baisan lokacin daya sake yimasa wani irin ruqoba,tsoro ne yasake kamata, har zuwa lokacin batasan waye ba, cikin sauri ta bud'e dan qaramin bakinta zata masa ihu,tun kafin tasaki ihun cikin sauri Shima yasaka tattausan tafin hannunsa na Dama yato s h e m a t a b a k i , h a n n u n s a n a h a g u K u m a y a n a r i q e d a Q u g u n t a , k a l l a n t a t a k a i g a r e s h i , l o k a c i d ' a y a t a g a n e s h i , z u b a m a t a i d o y a y i y a n a q a r e m a t a k a l l o a c i k i n d u h u n , h a k a i t a m a s h i d ' i n t a k e k a l l o .
A l h a m d u l i l l a h f r e e f a g e y a q a r e =???=???=???=???=???
Y a y a m a k o m a r s o y a i y a r I n u s a M a i K a n t i a w a j a n A i s h a ?
Y a y a a l a q a r t a d a M a h m u d W a k i l i z a t a k a s a n c e ?
Y a y a h a d u w a r A y s h a S u l a i m a n B o m p a i w a t o H a j j a A ' i , d a k u m a q a w a r t a A y s h a Y a k u b u S a g a g i w a t o H a j i y a M a m a ?
Y a y a a l w a s h i n m u n i r a t z a i k a s a n c e ? >??
B a ' i y a w a n n a n c e g w a g w a r m a y a r d a l i t t a f i n y a q u n s a b a , a k w a i d r a m a i r i i r i , K a s h i d a b a n d a b a n , d o m i n k u w a l i t t a f i n S h a h a a b y a z o d a w a n i S a l o n a d a b a n , k e d e k a w a i k a r k i B a r i a b a k i l a b a r i , b a h a u s h e y a c e d a a b a k a l a b a r i , G a r a k a b a y a r =?
?
D u k m e b u q a t a r c i g a b a n l i t t a f i n S H A H A A B , z a i t u r a n e r a 3 0 0 k a c a l =?L???k i k a r a n t a a b i n k i H a n k a l i k w a n c e >?p?
Z a k i t u r a 3 0 0 t a w a n n a n a c c o u n t d i n
0 1 6 4 5 4 9 4 8 8
A m i n a m u h a m m a d
G T b a n k
K o k u m a k i t u r a k a t i n M T N n a n e r a 3 0 0 k a c a l , t a r e d a s h e d a r b i y a t a w a n n a n n u m b e r 0 8 0 3 3 3 0 0 0 3 4 =??
A m n a h E l Y a q o u b
'??
1 7 &