Showing 18001 words to 21000 words out of 116763 words

Chapter 7 - SHAHAAB COMPLT

Start ads

10 Aug 2025

791

Middle Ads

hannu yana daga kwancen.

(kaii jama'ah, shegiya yaudara =?D?)

Babu musu ta qarasa tana wani irin taku tana karkad'a jikinta, hakanne yad'auki hankalin sa, har me aukuwa ta auku, tayi tunanin zaiyi mata godia Bayan komai yagama wakana saboda dazu dazun Nan tagama shan wasu magunguna data siya wajan qawayenta, a jikin maganin ma saida akai kashedi idan kinsan kinada kishiya to karkiyi amfani dashi Dan Zaki gigita maigida.

Shikam Shahaab daqyar yasamu yayi released, zuwa yanzu Kam yariga ya saduda,ya daina qorafin komai, danhaka yauma bai nuna mata komai ba.


******

Zaune suke da Hajja, tunani take a ranta hartana cizon yatsa, Sai yanzu ne takejin haushin kanta kan rashin maidawa wannan mutumin martani.

daya ce mata ogonsa ne ya aiko shi, meyasa bata maida masa martani tace yaje ya fadawa ogan nasaba?
Takaici yazo wuyan ta ya tsaya, Sai yanzu haushin kanta duk yabi ya isheta, mutumin datake nema ruwa ajallo Kuma yanzu tasamu Damar da saqonta zaije gareshi Amma tayi watsi da damar ta.

Hajja dake Gefe tace "me sunan qawa yau me Zaki dafa mana a gidan?"

Taji shiru, ita kuwa Aisha tunani ne yayi Nisa batasan ma Hajja tana yimata magana ba.

Saida Hajja tata6ota tace "mesunan qawa!"

Sannan ne ta kalleta, Amma batayi Mata magana ba, cikin sauri Hajja tace "idan de akan naqi yimiki kitso ne kika fara gaba Dani har Ina miki magana kina qyaleni to dauko mataji nayi Miki, saikiyi gabar da mamuda ko Hadiza"(>?-?)

"Hajja menene Kuma ummah da Abba na suka miki Zaki sakosu aciki?"

Hajja tace "kidauko nace, ni banason mita wallahi, dama azumi ne yasa nace bazan miki ba, saboda ranar Bana Gani sosai yunwa tasa duhu duhu kawai nake Gani"

Tashi tayi ta dauko mata matajin tabata, sannan ta zauna suka fara, manyan kitso suka fara guda goma, kasancewar gashin baida cika saide tsawo, Sai yarfe hannu take saboda zafi.

Jummai ce tashigo gidan tasamu waje ta zauna, Bayan sun gaisa tace "Hajja babu Dan sauran abinci awajanku nabawa jikana"(=??)

Hajja tace "Ina zamu samu sauran abinci jummai, muda ba Yara ne damu ba, Hadiza ta daina haihuwa, danma mamudan nawa jarumi ne gashi harda yaransa biyu, Amma ni har nayi zamani na nagama aishi kadai na Haifa, tundaga Kansa ko 6atan wata ban qara ba, Amma shi kinga yayansa biyu "

Jummai tace"um aikuwa mamudan naki ya'iya haihuwa jummai, ga 'Ya'ya nan kyawawa kamar yayan larabawan labanu"

Aisha da takaici ya cikata tataba sauran gashin taji saura guda biyu agama,batason jin takaicin firar Hajja da jummai Wai labanu...

Can Kuma Sai jummai tace "oh nikam Hajja ya mukaji da labarin taliya, har yanzu tana nan muna Jan dafaduka da'ita, wannan yaro Allah de yabiya shi,masu kudi dazasu dinga haka dasun samu Lada awajan Allah"

Hajja tace "masu kudi sunada kudi infada miki, Amma Kuma suna qara son kudin su, kiduba kiga Yan siyasa sunada kudin, wani ma har jikokin sa bazasu taba talauci ba, Amma a hakan nema suke susake Hawa kan mulki, mukuma talakawa muna Nan Sai godiar Allah, ni yanzu ko dubu talatin aka Bani ai jikinane zai fara karkarwa, wallahi zazza6i zai sakani "

Jummai tace"aikuwa in hakane Hajja A'i kakarki ta yanke saqa, Ina Yaron Nan inusa me kanti na qofar gidana?"

Hajja tace "wai inusa wannan me shago?"

Jummai tace "shide, jiya jiyan Nan yazo ya sameni yace tunda ke aminiyata ce inyi masa hanya mana yazo wajan mesunan qawarki, Kuma Hajja A'i inde Aisha ta amince ba abunda bazai muku ba, yanada sakin hannu"

Aisha tanajin haka kunya ta kamata, tatashi da gudu tatafi daki
Jummai tace "laaa Hajja A'i kode harta amince ne, Naga tatafi daki cikin kunya"

Hajja tace "ai mungama amincewa jummai"

"to Alhamdulillah zan sameshi nafada masa, saiki fada mata idan zaizo ta dinga kwalliya, 'Dan janbakin Nan ta dinga shafawa, taci kwalliyarta da mayafi"

Hajja tace "Ina me sunan qawa zata saka miki mayafi? Dan qirgen dangin take 6oyewa, Kuma kinsan Yara inde suna wannan matakin Tofa ko yayan limamai Albarka, Amma inda tana kwalliya ai samari Sai mun kori wasu,tun yanzu ma gashi anfara aike, kinsan Kuma farinjinina ta Dauko da alama, Saboda Nima alokacina saida aka kawomin Goro d'aid'ai har guda sittin"(=?3?)

Jummai tace "to aikuwa zan fada masa dangin farinjini yake so, tun kafin wani yazo yatureshi Gara yadage, 'Dan man Nan ya dinga siyo mata tana shafawa duk Dama Naga jikar Taki fara ce sol ga hanci har baka inni mayya ce incinye kaina" (=??)

Hajja tace "fada masa Kam gaskiya"

Jummai tasake Kallan Hajja tace "Hajja Kuma Yaya kikayi da Goron da aka kawo miki?"(>??)
Hajja tace "ai inafada miki a makaranta ma malamai fada suke akaina, da sukaga Bana kulasu kawai saide kiga sun shirya sun Kai Goro gidanmu, Ahaka Ahaka har guda sittin kinji zancen gaskiya, Amma dayake aure rabo ne duk masu son Nan nawa babu wanda na za6a Sai uban mamuda Allah yaji qan rai "

Jummai tace" ikon Allah, banta6ajin irin wannan labari nakiba ko a hikaya"

Hajja takauda kanta Gefe tace"to yanzu kinji"


******

Yau Shahaab da munirat sun Lula qasar Saudia umara, munirat kamar ta zuba ruwa aqasa Tasha Dan murna, saboda tarabu da jarabar mama, yau itama de take6e itada mijinta.

A hotel suka sauka, kwanansu biyar da zuwa qasar Amma munirat har wata qiba tayi, jikinta yayi wani irin fresh, kasancewar bata tafi da kayan magungunan ta Wanda ta siya awajan qawayenta ba, Sai jikinta yake sauya wa, ita akaran kanta tasan ni'ima ta saukar mata, tunda kullum cikin hutu take babu tunanin mama, saide taita cin fruit masu kyau tana kwanciya, shiyasa a kwanansu na shida tarasa gane kan Shahaab, tunda ya ratsata yaji ta sauya Nan da Nan ya rikice mata, kamar mahaukaci haka ya dinga abu daya.
Yanda take samun hutu a qasar Sai take jin Dama su dauwama Ahaka,ga Kuma uwa uba Mahmud dinta yana tare da'ita, shiyasa gaba daya addu'ar ta taqare 6angare daya, wato Allah yabar mata Mahmud, ya mallaka mata zuciyar sa ya kasance ita kadai yake Gani acikin mata, duk wata mace dazata mata shamaki da mijinta to Allah yasa Shahaab ya dinga kallon ta a namiji

Sa6anin Shahaab daya duqufa wajan yin addu'ah Allah yabashi 'Ya'ya nagari idan yanada rabo,saikuma mama datace masa yadinga yimata adduah Allah yasa kafin ta mutu tahadu da qawarta Aysha Sulaiman Bompai, wuni yake a masallaci yana wannan addu'ar, idan tare suka tafi da munirat gajiya take da jiransa Takoma masauqin su, shikuma daga baya Bayan yagama addu'ar sa saiya dawo shi kadai.

******

Yau gaba d'ayansu atsakar gida sukai sahur, Abba yana Gefe yana karatun alqur'ani, Ummah da jabir da Hajja suna zaune atsakar gida, Aisha kuwa adaki taci Nata abincin, saida tagama tafuto,ta bude fridge din Hajja dayake cike da qanqarar sayarwa, tad'auki ruwan Sanyi ta tsugunna tanasha, Hajja ta bita da kallo tace "kaga shafaffiya damai, inajin bata mayi sahur dinba"

Jabir yace "aikuwa kamar kinsani Hajja batayiba"
Hajja tace "Ahaf! Aini tabiyo, Nima fa wannan sahur din bawani damuna yayi ba, Amma jiya duk da nayi sahur azumin Nan yabani wahala, ko yaya na sunkuya kawai duhu nake Gani, duk jijiyoyin jikina saki sukayi, sallar la'asar ma a zaune nayi ta"
Gaba dayansu dariya suka sa, harda Abba, Hajja kenan me abun mamaki, tace sahur bai dameta ba Amma Kuma mutumin da sahur bai dameshi ba shine yake sallah a zaune tsabar wahalar azumi, Kuma sude asaninsu da Hajja kullum Saitayi sahur, wannan ladan baya wuce ta.

Ta kalli Aisha data gama shan ruwa tace "debomin ruwa a kafara na qulla nasaka a fridge, babu pure water yaqare, harna fara kewar azumi wallahi, tunda muka shiga goman qarshan Nan"

Aisha tatashi zata bata ruwan tace "ai dole kiyi kewar azumi, tunda kina cafkar kudin qanqara"

Sarai taji abunda Aishan tace Amma Saitayi shiru, saboda tasan tabbas tana samun kudin qanqarar, Kuma tsaf me sunan qawa zata fadawa mamuda abinda take samu kullum, danhaka Saitayi shiru taqi ta tanka mata, saima cewa da tayi "Bani ruwan sanyi a fridge Nasha jabir, wadannan masu gaggawar yanzu zakaji sun fara Kiran sallah, idan shan ruwa ne Sai sun gama Jan ajinsu sannan su kiramana sallah, Amma idan lokacin sahur ne abincin ma baya tsirga musu suke tafiya masallaci sukira sallah "

Jabir yayi murmushi yad'auki ruwan yabata


******

Ana azumi na Ashirin da d'aya, sannan su Shahaab sukai shirin tafiya, munirat tasashi agaba tana so tayi wa yan'uwan ta da qawayenta tsaraba, dole yad'auki maqudan kudade yabata, tasashi ya shirya domin suje super market da boutique tayi siyaiyar acan, haka badon yasoba ya shirya suka tafi.

Kai tsaye BIN DAWOOD HYPERMARKET sukaje, shide babu abunda zai siya, kawai Kallan ta yake tana za6ar duk abinda taga yayi mata.

Ajiyar zuciya yasauke, yarasa meyasa yake tunanin ta, tun Bayan tahowar su daga Garin yake nema ya yakice tunanin ta a ransa Amma yakasa, gaba daya taqi barinsa ya huta, yarasa Yaya zaiyi da ransa.(>?&? B&?)

Kayan yaci gaba da kalla, anan yaga wani ribbon dark green Mai masifar kyau, babu Wanda yasake fad'o masa Arai face ita, ya tuna yanda dogon gashinta yake ko ribbon babu, cikin ransa yafara magana "marar kunya 'yar qarama...."

hannu yasa yad'auki ribbon din yaga ansaka shi cikin wani gida, kana Gani kasan yanada tsada, price dinsa yagani,kudin ribbon din kadai yafi kudin daya Bawa munirat tayi siyaiya dashi.(=?F? @&?)

Batare da tunanin komai ba yadauka matashi.







(=?2?>??tabdi sorry Munirat=?%?)





SHAHAAB littafin kudi ne,naira 300 ne kacal =?L?

Zaki tura 300 ta wannan account din


0164549488
Amina muhammad
GTbank

Zaki tura shedar biya ta wannan number 08033300034









Amnah El Yaqoub
'
[10/09, 22:14] +234 803 697 8511: (Romance)


Writing By Amnah El Yaqoub

Dedicated to Aisha's Name
https://www.facebook.com/amnahel



13&14


'Boyeshi yayi a Bayan hannunsa, Karo na farko kenan daya fara 6oyewa matarsa wani abu, Kallan ta yayi yace "munirat idan kin gama kisameni awaje,I'm tired"

Juyowa tayi tace "okay my dear five minutes"

daga Nan taci gaba da tafiya tana za6ar abinda takeso tana sakawa acikin kwando.

Juyawa yayi cikin sauri, yaje ya basu atm dinsa suka dauki kudin ta dollar account d'insa, sannan ya 6oye abun acikin aljihunsa, yakoma cikin mota yana jiranta.

Bayan tagama siyaiyar tafuto,hotel suka koma, saida yaga tashiga wanka sannan yasaka ribbon din cikin jakar kayansa data had'a masa tun Daren jiya.


Cikin dare jirginsu yatashi zuwa qasar Nigeria,Bayan sun sauka munirat Kam bacci ta kwanta, shikuma yatafi wajan mama, saida ya ganta tana bacci sannan ya dawo part dinsa.

Ganin baccin munirat din yayi Nisa yasa ahankali yatashi, yabude cikin jakarsa ya dauke abun kama gashin daya siyo, yasaka shi cikin wata akwati, sannan ya danna wasu numbobi security din jikin akwatin yakoma yarufe, sannan ya ra6a gefen munirat din shima ya kwanta tareda sakin wata irin ajiyar zuciya ya Lumshe Idonsa Sai bacci.

Dasafe baije wajan aiki ba, tun safe da suka tafi wajan mama bai dawo ba, munirat ce tadawo ita kadai saboda tana shirin kar6ar baqin qawayenta Wanda zasu zo mata sannu da zuwa.

Sai yamma yakoma part dinsu, anan yaci Karo da baqin munirat da basu dade da zuwa ba,har hada baki suke suna gaida shi, ya amsa musu fuskarsa adan daure, sannan yawuce daki

'Daya daga cikin su mesuna meji (maijidda) tayi qasa-qasa da muryarta cikin sigar rad'a tace "tabdi, lalle munirat kina qoqari, irin wannan ingarman mijin naki yaushe wasu matan zasu iya dashi, kema fa Dan kina dagewa ne da shan magungunan damuke baki, Amma wallahi da idan ya riqeki, Sai kinyi kuka da idonki"

Murmushi tayi tace"Meji kenan, to waya fada miki baya sakani kukan? Ai ranar dakuka aikomin da magungunan kasa gane Kansa nayi, Nasha wahala ranar harda kuka, har mukaje Saudia a haukace yake "

Dariya suka saki harda shewa, ikee (iklima) data cika bakinta da naman kaza kasancewar tana period bata azumi, tace" ahh waya fada miki mudin na wasa ne? Ai inde kinbi wannan magungunan kina shansu akai akai, wallahi keda kishiya saide kiji anayi a maqota"

Munirat tace "hmm kude kubari kawai, Bari inje insame shi, kunsan shi da shagwa6a yanzu saiya fara min rigima nabarshi shi kad'ai"

Hauwi (Hauwa) tace "A a jeki Kam, adeyi ahankali kar akaryawa megida azumi, Amma fara sallamar mu dadan abun ta6awa saboda shan ruwa, saimu tafi"

Tace "karki damu Hauwi, harda tsarabar ku ta Saudia zan kawo muku yanzu yanzu"
tana fadar haka tajuya zuwa dakinta, sukuma suka hada ido tareda ta6e baki, kowaccensu haushi takeji Dama itace a matsayin da munirat din take.


Tunda yashigo yaga munirat bata biyo shi ba, saiya kwanta agadonsa tareda d'ora Kansa akan hannayensa ya zubawa Saman Dakin ido ya fad'a duniyar tunani, tunanin sa yayi zurfi ko shewar da qawayen munirat suke yi ba yajin su.


Mamakin Kansa yake, yana jinsa kamar bashi ba, haka Nan yakeji kamar ansauya shi, Bai ta6a tunanin akwai wata yarinya dazata tsaya masa a ransa Bayan munirat ba,saboda yasan Kansa, yasan bazai ta6a son wata yarinya bayantaba.

To Amma meyasa tunanin yarinyar yakasa barin qwaqwalwar sa? Wata zuciyar tace dashi "may be Dan kanason Yara ne, Kuma ka ganta yar qarama kamar Baby shiyasa kake tunanin ta"

Wata zuciyar Kuma tace dashi "kokuma saboda maganganun data fada Maka ba"
to kuwa in hakane dole ya nemeta domin yaji dalilin dazaisa tace masa matsiyaci, Shima abun atuhume shine, shi me yayi?

But ta wacce hanya zai sake ganin ta?

Cikin jin haushin Kansa yace "Wai meyasa zan damu kainane, saboda wata qanqanuwar yarinya?

Munirat ce tashigo Dakin Bayan ta sallami qawayenta.

Jin shigowar Tata ne yasa Shima ya watsar da tunanin yarinyar, saboda shide yasan cewa ba sonta yake ba, to menene zaisa yadamu Kansa akanta?
Kwanciya tayi agefen sa ta dora kanta akan dantsan hannun sa, cikin kulawa tace "tunanin mekake my Dear?"

Kai tsaye yace "Haihuwa"

Gabanta ne yafadi, tatashi zaune tana Kallan sa tace "My Dear haihuwa ta Allah ce, nide nasan lafiya ta kalau, Kuma kaima haka, sannan sisters dina dasukai aure kowa tana haihuwa a gidanta, Kuma my dear ni banga abunda zai saka tunani ba, kanada komai na rayuwa, meyasa zaka damu saboda haihuwa, ni Bana tunani akan haihuwa, saboda nasan lafiya ta kalau, Kuma haihuwa gadon Miji takebi ba gadon mata ba, inda gadon mata takebi to da tuni na haihu,tunda Bani kadai momy na ta Haifa ba, so nasan matsalar daga kaine, tunda mama ma Kai kadai ta Haifa......"
( '
Babu musu tatashi tafice daga d'akin Sai mita take cikin ranta, Dame ta rageshi a rayuwa? Kullum cikin neman magunguna take saboda ta gyara kanta yasamu yaji dadi, Amma duk da haka baya Gani, yaje wajan masifaffiyar tsohuwar sa ta hure masa kunne akan haihuwa, Nima zaizo ya dameni.

Shikam tana fita runtse Idonsa yayi, me munirat take nufi? Kenan shine baya haihuwa ba'ita ba? Duk haqurin Dayayi akanta yake zaune da'ita shekara da shekaru bai ta6a yunqurin qarin aure ba shine take fada masa shi kadai mama ta Haifa? Tsaki yasaki yatashi yafita daga gidan gaba daya, ko ruwa baisha tareda su ba, a masallaci yasha, Bayan an idar da sallah ma bai dawo gidan ba Sai wajan shadayan dare,munirat tun tana jiran dawowar sa taji shirun yayi yawa saboda Bahaka yasa baba, saita zargi kanta, kanta tayi wa fada karfa taje yakoyi Zaman waje duk da tasan ayyukan sa bazasu barshi ba, Amma idan ya Koya lokaci daya zasu zigashi yafara neman aure, ita Kuma abinda bazata juraba kenan, shiyasa yana shigowa ta rungume shi tareda fashewa da kukan kissa, tun yana shareta har tayi nasarar shawo Kansa yahuce

******


Yau Aisha gajiya tayi da girkin, gashi Ummah batada lafiya, itama Kuma tagaji, ita Kuma Hajja tana kulada sana'ar qanqarar ta, Dan haka itama yau tayi fuska ta wuce Dakin Hajja tayi kwanciyar ta
Saida Hajja tagama siyar da qanqara lokacin har hud'u na yamma ta gota sannan ta nemi waje ta zauna, taleqa daki tace "me sunan qawa, futo kije ki siyo mana Dan tattasai kidafa macaroni ko jallop ce"

Cikin shagwa6a tace "wallahi Hajja nagaji sosai, jinake kamar na fadi"

Hajja ta Jinjina kanta tace "ai shikkenan Naga alama yau iskanci kikeji tonima nazama yar'iska, kowa ya zauna da yunwar sa" (>?-?)

Aisha tace "A a Hajja, abun bekai nanba,ni Bana fada da Azumi, saide in qarshe aka kaini" daga Nan tafuto daga d'akin tasaka hannu acikin cinikin Hajja tad'auki kudin tattasan,sannan tafita taje tasiyo tadawo ta dora musu abincin


******

Kwana daya Shahaab yayi yana yaqi akan tunanin Aisha, daqyar ya'iya yin wuni daya, da yaji zuciyar sa tana so ta kawo masa tunanin yarinyar, Sai yayi sauri yad'auki wani abun dazai dauke masa Hankali,acikin kwana dayan Nan wuni yayi da jarida a hannunsa,har munirat tana mamakin sa, to Amma Kuma karatun jaridar ma daya fara zata Fado masa, baisan lokacin Dayayi wulli da jaridar ba aikuwa tayi d'aid'ai a falon nasu (=??)

Yau tunda sassafe ya shirya yafita office, yanaso ya tsiri aiyuka dayawa ko hakan zaisa ya yakiceta a ransa, saide yana zuwa ma aikata suka shaida masa cewa yaune ranar dayasa zasuyi meeting akan sabbabin masu bada horo daya gayyato daga qasar Germany domin su sake wayar wa da sabbabin ma'aikatan su dasuka dauka wannan watan Kai.

Hamdala yayi a ransa, yaji dadin hakan sosai saboda shaf Yama manta da wannan batun, shadaya daidai na safe suka fara meeting din.

Qwararrun masu bada horon ne suke bayani cikin salon birgewa dakuma sanin makamar aiki dangane da yaqi dacin hanci da rashawa, Dafarko Kam a nutse yake, yana kallon komai daki-daki yanda yakamata, Amma basufi minti talatin ba da fara meeting din ya Lula duniyar tunanin ta....,wata zuciyar tace dashi "kotayi dinkin sallah?"

Magana masu bada horon suke masa Amma inaaaa... Hankalinsa yariga yatafi, Ramadan dake gefensa yata6ashi, firgigit yayi ya dawo cikin hayyacinsa, Kansa yadafe ya kallesu yace "am.. Idan babu damuwa Dan Allah kuyi hakuri kuci gaba da metting d'in, inada wani Babban uzuri agabana"

Daya daga cikin ma'aikatan efcc din yace "Amma Boss maganar dasuke fa tanada muhimmanci, yakamata ka tsaya..."

Agogon hannunsa ya kalla yace "kuyi hakuri please, Babban uzuri gareni" yajuya ya kalli baqin nasu yace "mr Jone next time ok?"

Kafin wani yasake magana yad'auki jacket dinsa, tareda zira hannunsa guda daya cikin aljihun wandonsa, cikin sauri yafice.

Gaba d'ayansu da Kallan mamaki suka bishi, Bai ta6a yin hakan ba, kowa yasan inde akan aiki ne yana tsayawa ayi komai a gabansa,

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login