Showing 36001 words to 39000 words out of 121250 words

Chapter 13 - ALKIBLA complete

Start ads

24 Aug 2025

468

Middle Ads

Sai a sannan zahra dake labe ta fito da hanzari muryarta na rawa kamar zata sake kuka tace
"Kinji ko hajja....kinji sharrin da yakeson yimin,ni ba'ace komai a kanshi ba saboda zaman bariki ba saini don ina makaranta"
"Kinga dagani....na gaji da wannan iskancin naku keda zaki,yara kamar mayu?,kamar masu ganin hanjin juna?,to wallahi idan bakuyi wasa ba aure zan saka iyayenku su daura muku naga qaryar iskanci" wani irin tsalle zahra dake zaune a jikin hajja ga buga kamar wadda aka dorawa kunama a jiki,ita kanta hajjan saida tayi sak cikin tsoron tana duban zahra dake fadin
"A'uzu billahi minash shaidanir rajim,hajja....wacce irin masifa kike ambata da yammacin juma'ar nan?" Ta fada idanunta duka a waje,tafin hannu kawai hajja ta saka tana rufe bakinta dashi tana fadin
"La'ilaha ilallahu,muhammadurrasulullahi,sallallahu alaihi wa sallam inna wuro?,kamar wadda tace miki tsohuwarki ta mutu?,wannan zancen ne masifa?,anya zahra?" Ganin yadda bacin ranta ya bayyana yasa ta sassauta nata,ta qarasa wajen hajjan ta zauna tana narke murya
"Kiyi haquri hajja,ba haka nake nufi ba,don Allah ki haquri,amma.in sha Allah na daina shiga huruminsa,dama ni ba shiga nake ba,shine haka nan ba gaira ba dalili ya matsantamin"
"Kema ai bajin magana kike ba,ko don kinga ina baki kariya?"kamar zatayi kuka tace
"kiyi haquri dai don Allah abar zancan,na daina in sha Allahu" shuru tayi kamar ba zatayi magana ba,sai kuma ta sake ajiyar zuciya
"Ai shikenan....Allah ya kyauta" jin haka don kada ta sake jan wata maganar saita miqe kawai tayi dakinta,a ranta tana juya zancan
"Itama.hajjan nan wani lokacin wlh tuburarriya ce,haka kawai da yammacin ranar juma'a,dai dai sanda ake amsa addu'a ki fadi wannan mummunan kalamin kisa 'yan amin su amsa?" Ita daya ta qaraci mitarta cikin daki harta haqura.


Da magariba zata gurin me gadi amsowa hajja goro da me gadi yace tazo ta amsa taga qofar gidan nasu cike da jama'a,kusan hakan ba sabon abu bane wajensu,duk randa aliyyu ya sauka a garin gidansun baya rabo da mutane,duk da cewa ko baya nan din ba'a rasa mabuqata jifa jifa masu neman taimako,amma kuma cikarsu bata kaiwa yadda take a yanzun.


A yanzun ma rabon kayan abincin azumi da alama yasa akeyi,don ga kwalayen kayan abinci nan kala kala da qananun buhun shinkafa,tabe baki tayi sanda taji wani yana zabga addu'a da koda layin duk da baya wajen,don baya zama a inda ake rabon,saidai ya wakilta ma'aikatan gidan
"Uban tausayi uban talakawan unguwar nan dama gundumar nan gaba daya,zuciyarka fara tas take hakama ayyukanka,ubangiji yasa kafi haka,ya qara arziqi da daukaka"
"Green snake....under green grass kenan" ta fada qasa qasa tana sake tabe baki,tana tsaye tana kallon yadda suke layi suna karba cikin farinciki,don mai gadin shima yana can,sai daya hangota sannan ya iso yana cewa
"Kiyi haquri uwar masu gida,banga zuwanki ba,saqon hajiya hajja ko?,ina can muna rabon aikin alkhairin haidar.....wannan yaro ya dace,ubangiji ya kareshi yasa yafi haka,yana faranta ran talakawa" ya fada yana cusa kanshi dan dakinsa,ya dauko saqon ya miqa.mata ta karba ta juya,tana sake jiyo kalaman yabo daga bakin mutane.


Ta sani cewa wani lokaci akan zo ma su hajja godiya kan wani abu da aliyyun yayi cikin unguwar,saidai su amsa don babu wanda yasan ma yayi din,kusan haka dabi'arsa take idan zaiyi wani abun alkhairin,itakam tana dauka kawai shashanci ne irin na mutane,don bataga alamu a yadda aliyyun yake da baqar zuciya,zai iya wani abun arziqin da zai farantawa wani rai ba.


*************

Kamar da wasa kuwa wata washegarin ta gama wankewa hajja qananun kayanta ta fito ta falo,tana tsaye gaban tv taji kamar muryar hindatu tana magana,da alama yaran gidansu ne da yau gaba dayan 'yan mazan da matasan abba babba ya raba musu gyaran flowers da farfajiyar gidan,tunda an yiwa wanda yake musu wannan hidimar rasuwa,ya tafi qauye.


Aje remote din tayi tana tafa hannu cikin mamaki da jin dadi
"Na zaci zancanki ne kawai fa da kika ce zaki zo" itama tana murmushin tace
"Kin taba ganin na saba alaqawari" kai ta girgiza tace
"Ina sara miki ta wannan sashen ai".


Sai data gabatar mata da ruwa da lemo sannan ta yiwa hajja magana ta fito suka gaisa,ba wannan bane zuwanta gidan na farko ba,ta taba zuwa sau daya,wannan ne na biyu,hindatun ta jima sosai suna hira,don a nan taci abincin rana ma,sannan ta kira jannah batula nadiya da farida suka hada kira na bai daya suka sha hira har zuwa sanda akayi sallar la'asar,ta shiga nan bandakin zahra din ta daura alwala.


Tana saman abun sallar zata tayar kenan ta waiwayo ta dubi zahra
"Yauma fa na sake ganin yayankunnan,ya hakimce saman kujera qafa daya saman daya yana karatun jarida,duka yaran kowa cikin hankalinsa yake aikinsa ba hayaniya da alama shike gadinsu,bakiga yadda tsare gidan da yayi yayi masa kyau ba"hindatu ta fada,kallonta zahra tayi
"Wanne fa?,ya musty ko ya shamsu?"
"A'ah fa....sojan nan....wallahi nikam idanuna basu taba ganin namijin da yamin kwarjini,ya kuma burgeni,na kuma ji na shirya aurensa ba irinsa....don Allah qawata ki shigemin gaba mana" ta fada cikin karyar da murya.


Tsaki zahra taja
"Don girman Allah ki tada sallarki ya fiye miki arziqi,wannan maganar taki ki nema abokin yinta amma ba zahra'u ba" saita sanya filo saman katifarta ta kwanta rub da ciki,hindatun dai bata haqura ba tace
"Saboda me kika ce haka?"
"Ki barni don Allah hindatu" da taga ta matsa da maganar,da zancan saita gaya mata dalili sai tace
"Ba ya haidar ba?,ai nan ne gidansu,kuma yana cikin gidan,kina iya gwada sa'arki,kije ki gabatar masa da kanki mana qawata"
"Au haka kika ce?,zakiga aiki kuwa da cikawa"ta fada tana kabbara sallarta
"Da dai yafi" itama ta amsa mata tana gyara kwanciyarta.


Tare suka fito don mata rakiya,zuwa sannan sun gama gyaran sai ganyayyakin da suke hadawa,ya mustapha na nuna musu inda zasu zuba za'azo a kwashe daga wajen kwashe shara.


Har yanzun haidar din na zaune inda yake,saidai wannan karon maimakon jarida wani littafine a hannunsa yana dubawa,mai kalar kakin soja,tabo zahra hindatu tayi,saita matsar da hannunta ba tare data dubi zahran ko inda haidar din yake ba,don ta fuskanci abinda take nufi,sai tayi gaba hindatun na biye da ita.


Bata ankara ba taji hindatun na gaida haidar cikin wani salo,saidai bai amsa ba sai data sake magana karo na biyu sannan ya amsa ciki ciki da qyar kamar wanda aka tilasta.


Suna qarasa ficewa qofar gidan zahra ta kwashe da dariya
"Wai me hakan?" Hindatu ta tambaye ta tana dubanta
"Ai gwara da kika ga halinshi da idanunki,idan da gaya miki nayi ba lallai ki yarda ba" tsaki hindatu taja
"To sai me?,ni wallahi burgeni ma ya sakeyi"
"Au Allah?"
"Qwarai kuwa"
"To Allah ya taimaka" zahra ta fada tana dariya harta raka hindatun bakin 'yar qaramar motar da aka siya mata ta tasheta tabar layin,ita kuma ta koma ciki.
23/10/2021, 08:40 - πŸ‘πŸ»πŸ‘πŸ»: 14
*OUM DUFAIL!!*
_GIDAN ADO ƘAWA DA KECE RAINI_πŸ’„πŸ’…πŸ½

_OUM DUFAIL ta tanadar muku dukkan nau'in kayayyakin gyaran fata gashi dama jiki gaba daya ZAHIRINKI DA BAƊININKI samfurin MAIDA TSOHUWA YARINYA_

*kayayyakinmu sune kamar haka*


FACE AND BODY SCRUB=2500(300ml)
Face and body mango butter=3k (250ml)
Face cream= 1800
Corretor oil/vitamin C oil=2k
Fairness skin lotion= 2500
Hot chocolate skin lotion 2500
Serum (for Nuckles )2k
Nuckles cream (stubborn)3500
Mix fruits Arabian black =soap 1800
Mix fruit glycerine soap =1900
Beetroot=1900
Coconut, milk,egg..face soap=1200
Lavender mix fruit soap =1800
Body wash =1500
cleanser=1600
Hair spray =700
Hair oil =1500
Hair relaxer =700
Hair butter 1700
Shampoo =1500
Breast=oil 2k powder 2k
Strech marks cream= 2k
Beetroot pink lips =700
Baby care soap glycerine=1k
Baby care butter =1500
Shea butter baby soap =700
Tsumin tula =2200
Tsumin zinariya =1200
Sliming tea =1500
Amarya set =25k
Liquid Arabian black soap =1900
Cleansing water =1500


*Ku dubamu a handle namu na Facebook da Instagram*
Ummu Dufail

*ko ta number wayarmu kamar haka*

07067943479

*_muna turawa kowacce jaha dake fadin nigeria da yardar Allah_*

*_INGANCI DA RAHUSA SHINE TAKENMU_*🀞🏾🀞🏾🀞🏾
_____________________________


Za'a iya cewa abdulyasar ya samu shiga wajen zahra saboda halayen daya nuna,wadanda suka sanya tun tana dari dari dashi harta saki jikinta,saidai shi kansa yadan dauki lokaci kafin ya samu ta sake dashi,saboda tana ganin kamar za'a koma 'yar gidan jiya ne,saidai yadda yake kaffa kaffa da ita,da yadda yake nuna tsananin kishinsa a kanta,da kuma yanda yake yawan jan hankalinta kan rayuwa kamewa da kula da mutuncin kai yasa ya sake samun fada a wajenta.


Sau tari idan yaga wata halayya ta wasu yammatan yakan qalubalancesu,don hatta su hindatu sai daya so ya rabata dasu,saidai data zauna tayi masa bayani da kuma alfanun zamansu tare ta yadda zata ci gaba da nusashshesu yasa ya fahimta ya kuma haqura.


Ta nata fannin sosai take qoqari wajen ganin ta kyautata masa shima,saboda yadda ya damu da dukkan lamuranta,ta lura mutum ne maison cima mai dadi,saidai ba kowacce iri ba,hakan ya sanya duk sanda zaizo wajenta girki na musamman take masa,koda bazaizo bama,sau tari idan akwai kudi hannunta zata kirashi ranar taji abinda yafi sha'awar ci,shi zata dafa masa ya aiko a karba masa,ko yazo da kansa,yawanci yafison cimar gargajiya,kamar dambu,danwake,alala,wainar fulawa da sauransu wani lokaci harda dan malele,to koda su din zata masa,zata kashe kudi sosai ta qawata masa su,misali alala,na 'gwangwani baifi uku ba,zata zuba masa qwai wadatacce,hakanan wainar fulawa zata cika mata qwai,harka dinga jin kamar wainar qwai qwai,fulawa fulawa,kirkinsa da yadda ya samu fada wajen hajja saboda dabi'unsa yasa koda batayi niyyar yi ba hajja da kanta zatace tayi masa,da kudinta kuma,takance
"Abudulyassar akwai kirki akwai hankali,ai babu abinda ba za'a yiwa yaron nan ba,yana da nutsuwa da sanin ya kamata,ni ba abinda yake burgeni irin yadda yake tsaronki,kamar yadda yayanku haidar yakeyi".


Hatta fita siyan katin waya idan yaji tayi ranar babu zaman lafiya,ya dinga fushi kenan da ita,bare kuma ya kira sama da sau biyu yaji busy,alamun tana waya kenan,ya dinga mita da qorafi da binbini,tun bata saba ba har halayyarsa ta zama ba baquwa bace wajenta,abokai da na kusa da ita kance
"ki gode Allah,mai yiwuwa sauyi alkhairi ubangiji zai miki,shi yasa dama ya kore dukka wadancan ya kawo miki wannan".


Na biyu tana jin dadin aduk sanda tayi girkin ya tafi dashi gida yake cewa mama(mahaifiyarsa)taji dadinsa,harma wani lokaci yakan kirata ya bata maman su gaisa ta kuma yi mata godiya
(A baya nasa abdulyasar dan kaduna ne,afwan zamu canza mu barshi a dan kano ne saboda wasu dalilai da anan gaba zan fadesu).


Bata mantawa akwai wani lokaci da wasu 'yammata suka zo suka wucesu,sosai sunyiwa fuskarsu bleeching wanda koda yaro qarami yana kallonsu zai gane,tasan halinsa,don haka tayi sha'awar tsokanarsa
"Nima man nan xan fara shafawa fa.....dama duk cikinmu da muka tashi na fisu duhun fata,kaga nima saina fito washar abuna" fuska ya tamke sosai yana dubanta
"Zahra'u,kice min kawai lokacin rabuwarmu ne yayi" idanu ta fiddo tana boye dariyarta
"Kamar yaya?"
"Eh mana....,ai daga randa naga kalar fatarki ta canza,ko naga qibarki tafi yadda kike a yanzu,hakan na tabbatar min kina amfani da wasu magunguna kenan,todaga ranar bana jin alaqarmu zata ci gaba da wanzuwa" dariyarta ta sake,tana sake jinjinawa tsantseni irin na abdul yassar din,da kuma yadda yake kiyaye doka da qa'ida,da qoqarinsa na azata bisa turba kowanne lokaci
"Ka kwantar da hankalinka,nima duka irin wadan nan ababen basa birgeni sam,saboda dukka alqawari ne da shaidan yayi kan saiya batar da 'yan adam,ya sanyasu sun aikata hakan,Allah ya bamu labarin hakan cikin suratun nisa'i wato surar mata kenan,saboda ubangiji yasani cewa mu mukafi kowa saurin dulmiya daga kaidin shaidan,suratun nisa'i,aya ta dari da sha tara.


"Allahu akhbar"ya fada yana lumshe ido
"Shi yasa kowanne lokaci nake godewa Allah da ya bani ke,na dade daji a jikina tun sanda na soma ganinki nayi matar aure,kuma irin macen da kowanne namiji zaiyi burin mallaka" kafin ya sake cewa wani abu wayarsa ta dauki tsuwwa,ya ciro ya duba
"Eh ina wajenta....ok to" ya fada yana murmushi,ya maida wayar aljihunsa
"Auwal ne"
"Ayyah....dama kwana biyu baiyo rakiya ba"
"Wallahi....wasu 'yan sabgogi ne suka sanyashi gaba,kinsan mu talakawa saida nema" murmushi kawai tayi sukaci gaba da hira,auwal abokinsa ne sosai,wanda yawancin lokutta yana daukoshi suna zuwa tare.


Ba'a rufa minti ashirin ba auwal ya iso saman babur dinsa lifan
"Na fatima zahra,bada kanka a sare kaje gida kace ya fadi" ya fada yana dariya kana ya bashi hannu suka cafke,kana ya maida dubansa ga zahra
"Dama ai nasani,bazai wuce nan din ba....gaskiya fatima kin dace da masoyi na gaske,kowa yasan abdulyasar yasan ki,ba wanda baida labarinki,ya dagawa kowacce mace red card saboda ke,wai don Allah meye sirrin?" Murmushi tayi tana cewa
"Um um auwal banda ziga,irin wannan koda abokinka haka?,kada fa naga ba haka ba" dukka hannayensa ya daga sama
"A'ah....aini bana shakka....bana shakka kan maganata,ke kike shakka saboda bakiga yadda ya damu dake ba ya kuma damu da zancanki ba....amma lokaci yana nan zuwa da zaki yarda"
"To Allah ya nuna mana". Baifi minti goma suka qara ba auwal din ya daukeshi suka wuce.


Cikin haka watan azumi ya sake kamawa,shima yazo musu a sanda ASUU suke halin nasu,don haka wannan karon ma a gida sukeyin azumin.


Rana ta farko misalin qarfe biyu na rana,bayan zahran ta idar da sallar azahar,kusan tana idar da sallar azahar take fara girke girken shan ruwa ita da baba gaje,wanda ita baba gaje da haidar suke shan ruwa a nan,sai kuma su abba babba da duk ranar satin qarshe suma suke shan ruwa tare da mahaifiyarsu,ma'ana duk bayan kwana bakwai,to tare dasu ranar za'ayi girki,to yanzun ma da haidar din bai dawo gida ba iya su ukune girkin,amma hajjan takam fidda sadakar abincin mutum uku haka zuwa maqota ko biyr wadatacce da zai isheshi mutu yaci harma ya rage,bayan wanda akanyi a raba sadaka,ta nade abun sallarta ta fito falo,dai dai sanda taji hajjan na cewa gaje
"Tunda haidar bai dawo ba,lokaci lokaci a dinga saka sanwa da yaron nan abdulyasar" murmushi baba gaje tayi
"Hajja kina ji dai da yaron nan"
"To gaje....ai duk wanda zaiso naka ya gama maka komai"
"Gaskiya ne....wannan haka yake" ta amsa tana komawa zuwa kitchen,zahra kuma ta qaraso wajen hajjan
"Hajja,da kawai an qyaleshi,tunda kusa da gida yake,inda ace nesa ne shine"
"Kijimin 'ya da rashin son alkhairi,to banda ma lalacewa ta zamani,mu a yadda muka tashi mukaga iyayenmu da kakanninmu nayi,koda wucewa mutum yazo yi ya dan zauna ya huta a qofar gidansu yana da kwano ranar a cikin gidan,ko kwana nawa zaiyi a wajen,bare kuma surukin gida guda" jin zata mata tarere saita barta,tabi bayan baba gaje zuwa kitchen.


Sosai abdulyassar kuwa yake nuna yabawa da dawainiyar abincin,a haka har aka sallace azumin gaba daya,saidai ita abinda yake bata mamaki,duk da ba damuwa tayi da komai nasa ba,abdulyasar din ba gwanin kyauta bane,amma da sukayi maganar da salma sai tace
"Kada ki damu,wani haka yake,saikin shiga gidansa sannan zaki gane ba rowa bace,gwaji ne" da wannan ta share zancan.


Biyu ga salla gidansu ya cika da baqi,jikoki da yaran da aka aurar,cikinsu harda su salma yasira yusra hafsat,sai manyan yayyensu da suka dan jima da aure,anty alawiyya anty fiddausi da anty nusaiba,wadanda kowaccensu daga me yara hudu saimai biyar,dukkansu qannen ya haidar ne,anty nusaiba ce kawai ta bashi shekara daya da wata uku,mama tayi kwainika a tsakaninsu(gwarne inji wasu hausawan ko?πŸ˜‚),hakan ya sanya koda ka gansu ma ba zaka zaci ta girmeshi ba,duka saiya zama yayan kowa.


Itakam zahra ranta a bace yake,don gaba daya dinkunanta babu wanda telor dinta yayi mata,saboda rainin wayo ma data matsa sai yaran shagon sukace ya tafi ittikafi lagos,badon takai zuciyarta nesa ba a ranar su kansu yaran da sun sha ruwan zagi,Allah yasa tana da wasu kala hudu da maman hindatu ta dinka musu iri daya da hindatu ,dasu ta dinga amfani,amma ana ya gobe 'yan gidan nasu suzo,saboda wani dan qaramin taro suke ranar kowa zaizo,ta daga hankalinta,saboda akwai kayan da takeso sakawa a ciki,don haka ta shirya da safe da wuri ta iske hajja a falo.


Ita da haidar ne zaune,sai umaima 'yar abban tsakiya da nuratu dake gefe gaban tv suna goge kayansu,da alama suma su zasu saka yau ko goben da kowa zai hallara
"Ummm.....kaga 'yammatan gidan nan,wadan nan kayan na yaushe ne?" Da ido umaima ta mata nuni da sashen da haidar din ke zaune,don ita bata lura dashi ba,daga kai tayi ta dubi wajen,magana suke da hajja,hannunsa riqe da kudade,yayin da hajjan ke riqe da wata takarda wadda kamar list din sunayen mutane ne a jiki,ta kuma tabbatar da hakan sanda hajjan ke fadin sunayen yana irgo kudin yana miqa mata tana ninkesu,da alama su za'a baiwa kenan,saita yatsina fuska ta dawo da dubanta kan yaran,wato kowa indai da haidar a wajen baida sukuni?,for god sake zai dami kowa ne ahaan....


"Waye zai rakani amso dinki?" Duk sai sukayi matsa gefe
"Anya ko yaya zahra zaki samu dan rakiya yau,wallahi ya musty ne yace kowa ya shirya zai kaimu shoprite mu zabi abinda mukeso,daga nan mu wuce minjibir park" ta fada qasa qasa don kada haidar din yaji saita kama baki
"Yau ni ake qin rakawa?....to ai gobe ma rana ce" suna 'yar dariya suke cewa
"Ki haquri yaa zahra...Allah yace duk wanda yaje wani gun bazai jirashi ba" batace komai ba ta qarasa wajen hajja,a sannan har haidar din ya miqe,hannunsa empty,da alama ya rabar da kudinne gaba daya.


Fuskarta ba walwala ta gaidashi harda dan rusunawa kadan saboda idanun hajja,don ta fuskanci tun dag wancan lokacin ta sanya musu idanu,shi yasa take iya bakin

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login