Showing 63001 words to 66000 words out of 121250 words

Chapter 22 - ALKIBLA complete

Start ads

24 Aug 2025

456

Middle Ads

uwarta ne zamu ci gaba da dawainiya da ita?,ko bakasan haqqoqin mata akan mijinta ba na kira malami su karanta maka?" Ta qarashe da tambaya gami da zuba mishi idanu,idanunsa kawai ya dauke daga kanta ba tare da yace komai ba,kamar bazai magana ba sai kuma ya amsata
"Nima cikin satin nan zan koma,saboda 'yan kwanaki ya rage na karba sabon matsayina" kafada hajjan ta daga
"Oho maka....kaika jiyo,ka fara sallamarta tukunna da dukkan abinda ya dace,idan yaso kafi ruwa ma gudu"
"Hajja hajja" ya kira sunan nata har sau biyu,tsohuwar tana son takai masa iya wuya,itama sai tace
"Ali...ina jinka,da magana ne?" Kai ya kada yana miqewa
"A bani abinci idan akwai"
"Zakaci iya na kwanakin dana diba maka ne kawai wlh,don bazanci gaba da aikin baban giwa ba" ta fada kamar me qunquni,yaji me ta fada amma sai yace
"Magana kike hajja?"harara ta dalla masa,saboda ta fuskancin yanzun so yake ya tsiro da wasan jika da kaka tsakaninsu
"ban sani ba,nace ka quce dakinka za'a kawo maka"
"Godiya nake" ya fada yana ciro wani turare daga aljihunsa ya aje gabanta,tabi turaren da kallo kana ta raka aliyyun da ido.


Turarenta ne da take amfani dashi,take kuma matuqar so,aliyyun yasan lagonta lokutta da dama,ba banza ba take sonshi duk cikin jikokinta,koda tayi fushi ta ruwan sanyi yake sauketa,sai tasa hannu ta dauka turaren,tana qwalawa inna gaje kira.


Cikin sakanni ta bayyana
"Gani hajiya"
"Shiryawa Aliyyu abinci maza gaje"
"Toh...toh,yanzu za'a kai masa?" Kai ta girgixa
"A'ah....ki hada kawai,matarsa ce zata kai masa"
"To toh,hakan yayi kyau" ta fada tana juyawa zuwa cikin kitchen din tana murmushi,ko ita abun yayi mata sosai,ta jima a ranta tana qiyasta auren aliyyu da xahra,ta dade tana sha'awar haka,amma bata taba furtawa ba,sai gashi Allah ya haskawa hajja,don haka cikin kuzari ta shirya komai cikin wani foldable basket mai kyau,sannan ta dawo ya shaidawa hajjan ta hada,ta amsa mata sannan ta turata ta shiga daki ta kira mata zahra,sai a sannan ma abunda ya faru dazu ya dawo mata kai,wato bisa dukkan alamu tajiyo maganarsa ne tun kafin ya shigo shi yasa tabar falon?,saita saki murmushi kawai cikin ranta tana addu'ar Allah ya shiryesu,ya kuma hada kansu.


Tare da inna gajen suka fito,tana dan rarraba idanu a falon ga zatonta yana nan saboda qamshinsa daya barwa falon,sai data tabbatar baya nan sannan ta qaraso tana sakin jikinta.


"Dauki abincin nan ki kaiwa yayanku" tace da ita tana murtuke fuska don kada ma ta kawo qabli da ba'adi,ido tadan fiddo
"Waiya musty ko ya abubakar?"
"Zaki" hajjan ta amsa mata a taqaice,ba shiri ta nemi wajen zama gefan kujera saboda yadda maganar taxo mata ba zata,wanne irin masifa hajja keson janyo mata tana zaman zamanta ne?,meye hadinta da kaiwa ya aliyyu abinci?,ita kaf rayuwarta ma zata iya tuna sau nawa ta shiga sashensa,shigarta ta qarshe ma kusa shekara goma,don duk abinda zai kaita dakinsa bata yarda ya hada da ita,iyakarta dakinsu ya musty,ko su dinma ba'a barinsu suje saida dalili,
"Amma hajja da kin baiwa su ilha..."
"Ban isa na aikeki ba kenan?" Ta jefa mata tambayar tana kallonta,xancan umminta ya dawo mata,saita saita fuskarta tana girgixa kai
"A'ah ba haka nake nufi ba,bari na dauko mayafina" ta fada tana miqewa,hajjan tabi bayanta da kallo cikin ranta tana dariya gami da cewa
"Kyayi kya gama".


Ta jima a dakin tana jan innalillahi,gaba daya hajjan ta sakota gaba,meye na aikenta wajensa bayan tasan yadda suke dashi?,sai data gama dibi dibinta sannan ta zari zumbulelen hijabinta da baka ganin komai sai hannayenta da saman qafarta ta zura ta dawo falon ta dauki kwandon ta fice.


A hanya ta hangi aslam dan abban tsakiya,ta miqa masa kwandon
"Yauwa mutumina,don Allah kaiwa ya haidar yana dakinsa kazo na baka lada" baya yadanja yana dubanta
"Wa?,ni?,ba ruwana inna wuro,kinga,mommy ce ma ta aikeni zan karbo mata gugar kayanta zasu fita yanzu da abba".


Yaran gidan kusan hudu ta hadu dasu kafin takai,saidai kowa ta nemi yakai abincin sai taga yaja baya,abun saita lura kamar hadin baki,ko suna tsoron wani abu,tunda dai tasan yaran gidan kaf da tsananin bin na gaba dasu,koda kuwa ba wasu shekaru masu yawa ka basu ba,hakanan basu da qiwa sam koda ga jama'ar waje bare na cikin gidan,da haka da haka tana haduwa dasu kowa na bata uzurinshi har ta isa kofar dakin nashi.
23/10/2021, 08:44 - 👍🏻👍🏻: 23

*Assalamualaikum warahamatullah taala wabarakatuhu*
08121491609
*Aisha s bayero traditional medicine and herbal reaserch center*
08121491609

*_MUN TANADAR MUKU INGANTATTUN MAGUNGUNA WADANDA BABU NA BIYUNSU KAMAR HAKA_*

*Step 1*

1_maganin sanyi
2_maganin niima set
3_maganin nankarwa
4_maganin kiba babba 8kkkarami
5_maganin hips
6_maganin gyaran nono
7_maganin rage kiba
8_maganin saka feeling
9_maganin cida kwai
10_zuma yar asali
11_maganin basir kowanne iri
12_hodar niiama
13_maganin mallaka
14_gumbar nonon rakumi 10k boket😨
15_gumbar madara 10k boket😨
16_turaren farin jini
17_kaza Mara kwai
18-turaren mallaka 3step
19_hadin matar minister
20_ kaza me kwai

*Step 2*

1.Turaren mallaka me kwalba
2. Me kunama Dan matsi 3k
3.tuaren goshi
4.turaren girji
5.tauwadar Mata
6.memory
7.kahon mallaka 8.yajin maza tea din maza
9. Dambun matsi
10. Man ayu 11.man damo pure daga zuwa sama
12. Kwallin idonka idona
13 garin Sha daka me kyau
14. Kubewar Mata gasunan dai da yawa bazan iya lisaafawaba harda na kyakkayin cinyoyin da matse matsi kina shafawa zakiji wasai

08121491609
dadai sauransu serious buyer yabiyoni private
me shawara ta bari saita gama karki batamun lokaci please

*_ku tuntubeni ta wannan number wayar_*👇🏽👇🏽👇🏽

08121491609

Tana tura qofar dakin wani bala'e'en sanyin Ac da qamshin freshner ya mata sallama tun kafin takai ga shiga,ashe da gaske ne ranannan data ji su hafsat na gulmarsa kan yadda yake babbakawa kansa ac,saita maida hannayenta cikin hijabi saboda sanyi,sannan ta sake tura qofar ta shiga sosai bakinta dauke da sallama qasan maqoshinta.


Tsaf dakin yake,hakanan babu wani tarkacen kaya duk da girmansa,babban gadone lafiyayye guda daya,sai kujera one sitter da two sitter da tv plasma daga gabansu kadan zaune saman wata tv stand ta zamani me tsari da yawan lockers,wanda ta tabbatar anan ya boye tarin takardunsa masu muhimmanci,bayan dan qaramin study room dinsa dake manne da dakin.


Haidar dake zaune saman daya daga cikin kujerun ya daga kanshi ya amsa sallamar,suka hada idanu saiya maida kan nasa qasa yana ci gaba da duba takardun daya barbaje a gabansa.


Yau daya sai taji ya mata wani irin kwarjini daya ratsa har cikin qasusuwanta,duk da cewa ba yaune karon farko data saba ganinsa ya hade girarsa haka ba,a'ah....dama dabi'arsa ce hakan.


A nutse ta qaraso gabansa ta aje kwandon,so tayi ta tafi amma suna hada ido sanda take shirin tashi saita koma ta zauna,kaf gidan sunsan tsarinsa baya sarving abinci da kansa,tuntuni sun saba al'adarsa haka,yana da wata izza da jin sarauta a jininsa.


Tana kammale kwanukan taji ya magantu cikin qasaitar nan tasa,takarda da biro ne ya aje gabanta
"Ki rubuta duk wani da kike buqata na komawa school",daga haka ya dauki bowl din dake daukw da farfesun danyan kifi ya saka spoon ya fara shan romon a nutse bayan ya harde qafarsa cikij ta juna,yayin daya maida kallonsa ga tv dake aiki kan qaramin sauti da bazai damu mutum ba.


Ta gefan idanu ta kalli takardar sannan taja tsaki cikin ranta
"An gaya masa na damu ne da wani kayan hannunsa,koda can shi yakemin" tana kaiwa nan ta miqe abunta ta soma takawa zata bar dakin.


Taku biyu rak tayi ta tsinci dakakkiyar muryarsa yana cewa
"In kika sake kika fita saina biyoki har gaban hajjan na kakkarya wadan nan sili silin qafafun" yadda yayi maganar ya tabbatar mata bada wasa yake ba,duk da taji haushin ba'ar da yayi mata haka ta shanye,ta juyo tana zumbure zumbure,ta dawo ta samu can gefe ta zauna bayan ta dauko takardar.


Abu uku kawai ta rubuta taje gabansa ta ajjiye,da idanu ya kalli rubutun,kamar zaiyi magana sai kuma ya janye idanun nasa ba tare da yace komai ba,hakan ya bata damar ficewa tana gunguni cikin zuciyarta.


Koda ta koma da kallo hajja ta bita,saboda bata tsammaci dawowarta da wurwuri haka ba,amma saita shanye,bata ce da ita komai ba.


Washegari tana kwance hajjan ta shigo
"Tashi kije ki gyara dakin mijinki" batasan sanda ta dawo rigingine daga kwanciyar rub da cikin da take ba fuskarta a hade tana duban hajja
"Waye kuma mijina?" Daquwa ta watsa mata
"Ungo nan....nace ungo nan,zaki tashi ko sai na radeki?" Ta fada tana kai mata dundu,tuni ta hantsilo daga gadon tana sosa bayan kamar ma ta sameta tana kuma duban hajjan
"Abun har yakai haka hajja?" Ta tambayeta kamar zata saki kuka
"Yama fi haka,indai zaki dinga min musu da shegen taurin kai....kuma indai kika ci gaba da yimin haka naga wanda ya isa ya karba miki takardar taki duk duniya" da haka ta juya ta fice daga dakin.


Tsoron furucin da tayi ne ya sanyata zarar mayafin doguwar rigar jikinta ta yafa tana ta mita a haka ta fice.


Har zata wuce hajjan ta kirata ta miqa mata key din,wanda dama can hajjan nada shi,daya a wajensa daya a wajenta,daya kuma a wajen mamarshi,ta amsa ta wuce tana fadi qasa qasa
"Kya ci gaba da share masa idan na komawata makaranta"
"Idan na barkin kin koma ba" hajjan ta bata amsa,sai tayi turus ta dakata da tafiyar da take tana dubanta kamar zata saki kuka
"Haba hajja,bafa haka mukayi dake ba"
"Zaki wuce ko saina iskeki?" Kamar zata dora hannu aka haka ta juya ta fice.


Kamar waccar ranar dakin ba wani dauda yayi ba,sai squeezing da beadsheet din yayi alamun an kwanta akai ne,mayafin ta daura saman kanta sannan ta fara kauda kayayyakin da suke ba'a muhallinsu ba.


Ta isa gefan gadon bayan ta gama gyara qasan,tasa hannu tana janye zanin gadon wasu frames masu kyau suka fado,cikin fargaba ta zagaya inda suka fadin,tana addu ar Allah yasa basu fashe ba,ta tsugunna ta soma daukesu.


Hotunan yaa zahra ne dukka guda ukun,kowanne sanye da hijabi take,fuskarta dauke da murmushi,kamar idan ka kirata zata amsa maka
"Margayiya" ta fada cikin zuciyarta,dan tsurawa hoton idanu tayi,sai kuma ta miqe tana jan tsaki data tuna daga inda hoton ya fado
"Aikin banza....har wani kwana da hoto yake waishi baban soyayya,aisai ka bita can shine ka burge,inda wani ne da yaji magana a wajenka" ta fada tana tuna yadda ya dinga treating din issue dinta dasu nuraddeen,locker din gefan gadon ta jawo ta watsa frames din,duk da tana iya hangen wasu pics din wanda da alama na yaa zahran ne,saita koma gadon taci gaba da gyarawa,kafin ta gama ta shiga toilet dinsa don wankewa.


Sai data kalli bandakin ta tabbatar komai ya fita fes sannan ta murda qofar ta fito.


Bata tsammaci ganinsa ko dawowarsa ba a sannan,bayanshi kawai ta hanga yana tsaye gaban gadonsa ya baje wasu takardu yana zaba,da alama daukarsu ne ya dawo dashi.


Jin taku ya sanyashi juyawa a hankali,sai suka hada ido na sakanni kafin ya dauke idanunsa ya maida ga abinda yakeyi ba tare daya ce komai ba,sai tabi ta bayansa itama ta fice daga dakin.


Batafi minti biyu da fita ba ya shiga wajen hajjan yana hadiye zuciya riqe da envalope a hannunsa
"Hajja....me yarinyar can kemin cikin daki bayan bana nan?"
"Sata ubana" ta amsa masa itama tana tsareshi da idanu,saiya lumshe idanunsa,tsohuwar tana bashi ciwon kai yadda ya kamata,ita kadai duk duniya ta isa tayi masa karen tsayen da take masa,saiya juya kawai ba tare daya sake cewa komai ba ya fice daga sashen
"Zanyi maganinku" ta fada a ranta,tana dauke idanunta saiga zahra
"Wai hajja ma tuhumata yake da shigar masa daki?,nidai wallahi hajja kina jamin ina zaman zamana" ta fada kamar zata saki kuka
"Yanzu ma na fara jaza miki" tuni ta tara qwalla a idanunta
"Bazan sake masa shara ba Allah,ayiwa mutum aiki sannan ya rasa me zai sakamin dashi?,to dakin nasa dakin wa yafi cikin gidan nan?"
"Idan bakije kinyi ba nida kaina kuwa zan dauki tsintsiya naje na share masa,idan kuma banje ba zansa daya daga cikin iyayenki yayi"saroro zahra tayi kafin ta juya zuwa cikin dakinta da sauri.


Mita take ita daya kamar zataci kanta,tana qissima sauran kwanakin daya rage tayi tafiyarta makaranta,ita gobe ma gidan salma ko hafsat zata,sai kuma ta tuna idan tace zata din sai hajjan nan tace saita tambaya,ita kuwa data tambaya gwara haqura da zuwan.


*BAYAN KWANA BIYU*


Ana ya gobe zata koma makarantarta,tana falo tana sake goge wasu kayan da zata tafi dasu atamfofinta,musaddiq jikan gidan yayi sallama shi da nurain,hannunsu dauke da leda suka zubw gaban hajja
"Gashi inji yaa zaki,na yaya zahra ne"
"Shi yana ina?" Hajja ta tambaya
"Yana waje yana sallamar wasu baqi ne" inji nurain yana hayewa saman kujera
"Jeka kace min idan ya gama yazo ina son magana dashi".


Jin haka ya sanya zahra a gurguje ta gama goge kayan nata ta miqe zata shige daki
"Ke....dawo ki kwashe wadan nan kayan daga gabana" tana zumbura baki tana fushinta haka ta dawo ta kwashe ledojin ta jasu har cikin daki,ta musu waje ta jibge ta shiga sabgarta.


A gurguje ya leqo saboda kiran da hajjan tace tana masa,bayan sun gama gaisawa tace dashi
"Qarfe nawa zaka miqata makarantar a gobe?,don inason na qarasa hada mata abinda yayi shaura" kansa ya daga ya kalli hajjan
"Oh....ai dama bani ke kaita ba ko?"
"A sanda take babu igiyar kowa a kanta kuma ba matar wani bace ba ba...banason dogon magana,ka shirya gobe da wuri ka maidata makaranta" yasani cewa koda ya fada wani abun ma babu abinda zai janyo masa sai bala'en hajjan,wanda ya lura da cewa yanzun wani bala'i ta koya,motsi kadan zata ce anemo mata tsoho da tsohuwarshi.


******* *WASHEGARI********



K'arfe takwas da wasu mintuna ta gama shirinta tsaf,ta shiga tayi sallama da umminta sannan ta shiga sashen abba babba shima tayi masa sallama,sannan ta wuce dakin mama,maman haidar ta mata sallama
"Allah ya kiyaye hanya,ya bada ilimi me amfani" ta miqa mata wata baqar leda da batasan meye a ciki ba,hannu biyu tasa ta karba tayi mata godiya sannan ta fito.


Tana takowa zuwa bakin motar tana kallon yadda ake sanya mata kayanta bayan motar tashi,shi yana zaune daga ciki ba tare da ya ko motsa ba,tana tsaye har aka gama sanyawa sannan ta matsa ta bude gaban motar ta shiga a hankali.


"Ina kwana" ta furta domin bin umarnin umminta,bata ji ya amsa ba duk da taji alamun motsin fitar sauti,dama kuma ba damuwarta bace ya amsa din ko kada ya amsa,illa iyaka tasan cewa ta fita haqqi,ta kuma cikasa nasiha.


A hankali ya tada motar kana ya saitata ya fice daga gidan,kafin subar layin ya sanya hannunshi gaban motar ya dauko wayarsa yayi kira ya sata handsfree ya aje,bugu biyu aka daga
"Ka sameni a nasarawa sardauna cresent" daga haka ya katse kiran ba tare daya jira amsar da za'a bashi ba.


Tafiyar kurame da takura daga wajen zahra ta mintuna ba dasu gaza ashirin ba ya tsaya qofar wani gini wanda ake gab da kammalashi,kashe motar yayi ya zare key din ya fita daga cikinta y kulle sannan ya jingina da murfin,ita dai batace komai ba tana kalloshi ta cikin glass din har zuwa sanda ta hangi shigowar ya musty a napep na haya,bataji me suka tattauna ba,saidai taga ya miqa masa.key din,kana ya matsa daga jikin motar zuwa ginin gidan dake gabansu,shi kuma mustapha ya bude motar ya shigo.


Sai daya rufe sannan yace da ita cikin tsokana
"Sai matar babban yaya....Allah dai ya biya,matar soja marmari daga nesa" harara ta watsa masa
"Kaga ya musty bama haka dakai,dadai ya shamsu ne nasan zaiyi abinda yafi haka,don Allah ja muje,ni hakan ma yafimin dai dai" ta fada tana yatsina,yayin da mustapha ya qyalqyale da dariya.


Ko kadan hakan bai bata haushi ba,saboda tasan cewa inda shine zai kaita babu komai cikin tafiyar face zallar takura har su isa,wala'alla ma sai yayi ko ya gaya mata abinda ranta zai baci a banza.


Sanda ta shiga dakinsu kamar hadin baki duka roommate din nata suna nan,har da sauran ma,ihu suka saka suna kiran ga amarya ga amarya,bata tanka su ba saima harara data watsa musu
"Duk ku iya bakinku wallahi" don har ga Allah har cikin zuciyarta tana jin sune sila,su suka jaza mata komai,saidai ko kadan basuji gargadin nata ba,saima ci gaba da zolayarta da suke,hindu tace
"Erhmmm....erhmmm...ashe ashe dai....yayan dai da aketa nunamin sam baida kirki.....ashe dai kece zaki wufffff da abinki akemin hannunka me sanda" kicin kicin zahra tayi da ranta sanda take aje jakankunanta saman katifarta
"Kinga hindatu....idan baso kike aji kanmu ba ki aje wannan maganar....am seriouse bana sonta" saida suka gama kidansu da rawarsu sannan suka qyaleta.


Zuwa washegari ta gama gyara komai nata,batayi qasa a gwiwa ba ta koma lactures cike da hazaqa karsashi da qwarin gwiwa,saidai haka nan ta samu kanta da takatsantsan da mu'amalarta da mazan ajinsu,duk da cewa

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login