Showing 3001 words to 6000 words out of 121250 words

Chapter 2 - ALKIBLA complete

Start ads

24 Aug 2025

442

Middle Ads

nan wallahi,kinxo akan gaba" salma daya daga cikin 'yammatan ta fada,harara yusra ta jefa mata daya daga cikin fararen 'yammatan
"Eheen,kedai kin shiga uku wallahi"
"Ke kuma fa,tara kika shiga?" Salma ta fada itama tana maidawa yusra hararta duk da cewa mai kama da dariya dariya ce
"Kinga manta da ita,bani nasha ya akayi?"
"Bari mu saka labule tukunna saboda 'yan saka eyes....."
"Kunga ku tashi ku bani waje tun ban kira yayanku ba" hajja ta fada saboda sanin hali,ta sani sarai labarin nasu baya wuce na samarinsu shi yasa tayi musu haka,sosai suke wasan jika da kaka da ita,tun tana fada da fushi harta haqura ta qyalesu ta zubawa sarautar Allah idanu,harya zamana ma yanzu bata damuwa ya zame mata jiki,mutum daya ne tak da idan yana nan take samun salama,saboda dukkaninsu shakkarsa suke,kuma tsoron hukuncinsa suke.


"Idan wajen mama zaki don Allah ya zahra kice mata yanzu zan shigo na mata bayanin aiken" yusra ta fada tana duban zahra wadda ta miqe da wayarta a hannu tana murmushi
"Bafa can zata ba" hafsat wadda ta shigo daga qarshe ta fada
"Kema ai tunda kika ga ta miqe tana doka murmushi ai kinsan kwanan zancan" hafsat ta sake fada tana yin fuska,cikin dan jin kunya da nauyi zahra tace
"Kamar a kunnenshi kika fada" saita soma yin gaba cikin sauri sauri yayin da hafsat ta bita da magiyar ta tuba tayi haquri ta fice abinta tana dariya.


"Ni ina mamakin yadda soyayya ke gudana tsakanin yaya da yaa zahra"
"Ahto ai haka Allah ke lamarinsa,ku kuke masa wani kallo da bahagon hukunci,saboda ALƘIBLARKU ta bambanta ta wajen ra'ayi,kowanne bawa komai irin halinsa akwai yadda Allah ya sallada wanda zai iya zama dashi ya kuma rayu dashi".


Tsam zahra ta miqe tana maida hijabin unifoarm din jikinta,wanda har yanzu bata kai ga cirewa ba tana cewa
"Bari na shiga ciki kan ku gama lacture din" don sam bata son irin wannan dogon sharhin na hajja,gani take koda yaushe aikinta shine bashi kariya dason wankeshi a idanunsu,bagan sun riga dasun gama sanin halayyarsa ciki da waje,kuma kowacce cikinsu ta kwana da sanin wannan,so tana ganin babu buqatar dagiya wajen bashi kariya da yima halayyarsa kwaskwarima a tsakaninsu.


Kamar hajjan zatayi magana sai kuma tayi shuru kawai ta bi zahran da kallo sanda take ficewa daga falon abinta ko a jikinta,har takai bakin qofa saita dakata
"Don Allah hajja wayata,tunda na dawo nake jina ba dai dai ba,na tabbata nuruddeen nacan yana nemana wallahi,tunda yasan yau zamu dawo" daquwa wannan karon ta watsa mata
"Qaniyarki,yanzu nake muku nasiha kika tashi kika barni zaune wajen,shine yanzu kikeso naje na dauko miki waya,idan kin damu ai kinsan mazaunarta kije ki dauko da kanki" dariya tayi cike da nishadi,ita da hajjan sun saba hakan,suyi tsiya suyi dadi,duk yadda suka kai ga shaquwa da juna amma indai akan irin wannan batunne sun saba haurawa,ita sam dole saita sanyata sun jitu da juna,ita kuma tana jin wannan shine abu na qarshe a rayuwarta da bazai taba yiwuwa ba,komai nasu yasha banbam,tun kan ta mallaki hankalin kanta yadda ya kamata ta fahimci alqiblarsu tasha banbam,hakan ya haifar da duk wani abu dake gudana a yanzu.


Kanta tsaye ta nufi dakin gadon ya hajjan,harta kusa sai kuma ta sauya akalarta zuwa kitchen dinta,inda take jin qamshin abinci na fitowa.


A nutse ta tura qofar tana wara idanu don ganin wace a kitchen,kamar kullum gaji ce,'yar aikin hajjan qwaya daya tilo data jima da ita,takun shigowarta ya sanyata waiwaya tana duban qofa,cikin fara'a da washe baki ta qarasa waiwayowa gaba daya
"A'ah,ashe kina hanya inna wuro.....marhaba da uwar dakina" murmushi zahra ta saki,saboda gaje ta wajenta ce sosai,yadda ya hajja ke ji da ita haka itama gaje ke ji da ita
"Yauwa inna gaje,na sameku lafiya"
"Lafiya qalau alhmdlh inna wuro,ya makaranta?"
"Mun gode Allah" zahra ta fada tana neman wajen zama saman kanta,kusa da wasu kwanuka data gani a rufe,hannu ta miqe tana shirin budewa gami da cewa
"Me aka tanadar mana haka yaketa zabga qamshi"
"Gasunan bude ki gani,duka naki ne hajja tace a yi miki" a nutse ta dinga budewa tana dubawa,sosai taji dadi har ranta,hakan kuma ya bayyana zuwa saman fuskarta,batun yau ba ta shaida da soyayyar da kakar tata ke mata,bata san me yasa ta fita daban cikin jikokinta ba,ko don sunanta taci?,ko kuma don ita din ita daya ce ta zama marainiya a cikin tarin jikokin hajjan?,saita ture wannan tunanin ta sanya hannu ta soma daukan abinda ke cikin kwanon tana sawa a bakinta.


Duk sai data gama dandanawa sannan ta fara lashe yatsunta tana cewa
"Ashe dai 'yar tsohuwar nan na sona haka,bari naje cikin gida na gaida mutane inna gaje na dawo" ta fada tana ficewa da dan sauri saurinta ba tare data saurari abinda inna gajen ke cewa ba.


Sai data fara biyawa ta dakin ya hajjan ta dauko wayartata hade da charger,ta shiga dakinta dake sassan ya hajjan ta jona chargy sannan ta fito.



*MAMUHGHEE* _UBAIDMALEEK_

*BILLYN ABDUL*
_MAKAUNIYAR QADDARA_

*HAFSAT RANO*_MABUDIN ZUCIYA_

*MISS XOXO*_DALAAL_

*HUGUMA*_ALƘIBLA_


*ZAKU IYA BIYAN NAKU KUDIN TA WANNAN HANYAR*

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

*_08085405215_*

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

  0903 234 5899
23/10/2021, 08:35 - 👍🏻👍🏻: *KIJI TSORON ALLAH,KARKI TABA KAYAN DABA NAKI BANE,BA MALLAKARKI BANE*

02




Falon yanzu babu kowa duka sun yoye sai ya hajjan kawai,tana zaune tana gyara falle fallen littafin dala'ilu,da alama ta karantasu ne suka kuma hargitse mata take gyarawa,don ita din har tsufanta bai hanata bibiyar litattafan addini ba.


Ta baya ta rungumeta tana cewa
"Ashe dai har yanzu ana yi dani 'yar tsohuwa mai ran qarfe,bari naje na dawo na kwashi gara,Allah dai ya jiqan tsohon mijinki" daga haka ta juya cikin sassarfa tana barin falon.


Wannan karonma da kallo ya hajjan ta bita,cikin ranta ta amsa addu'ar data yiwa mijinta kuma masoyinta,tana jin yarinyar cikin ranta sosai fiyr da sauran jikokinta,su biyu kacal suka samu irin wannan babban matsayin,duk da qoqarin boyewa da take da kuma nuna duka dai dai suke.


Tana yawan godiya ga Allah daya sanya qauna da zumunci mai qarfi tsakanin ahalinta,tun daga kan yaranta zuwa jikokinta,tsabar son su zamaTsintsiya madaurinki daya ya sanya tun mijinta na raye suka yanke zaman dukka yaransu maza tattare a waje daya,matanne basu da wannan ikon ko qarfin a kansu,hakan kuma yayi tasiri wajen sake maida zuri'ar tata tsintsiya madaurinki daya,duk da ance zaman tare zo mu zauna zo mu saba,hakanan baka rasa banbancin halaye da ra'ayi wanda kan kawo sabani lokaci zuwa lokaci,saidai a nata ahalin akwai qarancin hakan sosai,don bazai yiwu ace babu ba,kusan halayya ce tadan adam,kuma sunna ce ta zaman tare.


Duk da wannan babban abinda ke bata mamaki da daure mata kai shine rashin jituwar dake tsakanin zahran da yayanta,kusan abune daya dauko dogon tarihi ya kuma samo asali da tushe tun da dadewa,tun abun bai zama wani abun damuwa kallo ko dubayya ba har takai a yanzun yana damunta lokaci zuwa lokaci,saidai tana saka ran watarana komai zai zama tarihi,kamar akwai sauran quruciya ne jikin xahran.


Sashen yayan mahaifinta da suke kira da abba babba ta fara shiga,sashe ne mai kyau kamar yadda ainihin ginin gidan ya nuna,babban falo wanda ya cinye set din kujeru har guda biyu,dakuna a qasa kitchen da bandaki,sai dakunan matan gidan dake sama,duk da kowacce tana da guda daya a qasa.


Mommy ta tadda a falon ,wanda ke mazaunin amaryar abba babba tana cirewa yara da dawowarsu gidan kenan unifoarm,wanda dukkansu yaran gidan suna makaranta guda ne,akan daukosu tare a kuma kaisu tare,bisa jagorancin drivern gidan a wadatacciyar motar da aka ware musu don wannan hidimar.


Kanta ta daga tana amsa sallamarta sanda take cirewa yaronta safarshi,fuskarta fadade da fara'a tace
"Maraba da 'yan boarding" qarasowa tayi tana murmushi,ta zauna hannun kujerar tana amsawa gami da yiwa mus'ab da ake cirewa safa tsiya
"Wai kai bakasan ka girma bane,saura kadan kayi shekara goma fa,amma har yanzu safa ake cire ma"
"Murmushi mommy ta saki
"Kema kya fada inna wuro,kullum sai an cire masa kamar yaron goye..." Dariya ta sakeyi tana kuma dan tsokanarsa kafin daga bisani ta juya tana gaida mommyn,fuska a sake take amsata,ta tambayi abba babba
"Abbanku ai kinsan ba zama,tun sassafe ya fita kasuwa"
"Mama fa?" (Uwar gidan mommy)
"Yau suna hidima ne,ita dinma tun dazu ta fice" jin haka yasa ta miqe tana zura hannu a aljihun rigarta,ta soma zaro alawa masu dan girma tana rabawa wadanda ta taras a falon,duk data girmesu amma ba wani girma ne me yawa can ba,shekarun data basun bazai gaza biyu zuwa uku ba,idan yayi yawa hudu
"Baki gajiya,keda kika dawo daga makaranta harda wata tsaraba" murmushi kawai ta yiwa mummyn tana ficewa.


Sashe na biyu ta shiga,sassan abba yusuf,wanda keda matan aure biyu shima da yara tara,amarya nada uku,uwargidan nada shida,shima dai kamar shigen ginin waccan sashen,komai cikin tsari,da alama kusan dabi'ar jama'ar gidan ce wato tsafta,su dinma faran faran suka gaisa ta wuce sashen abba abu wanda cikakken sunanshi shine abubakar,matarshi daya da yara bakwai,sai abban tsakiya shima matarshi daya,daga nan sai sashen mahaifinta.


Sashe ne dake da girma da qima a idanunta,yake kuma da dimbin tarihi cikin rayuwarta,sashen da a shekarun naya suka rayu kamar sauran sassa dake gidan,cikin walwala farinciki da qaunar juna,qarqashin inuwar adalin uba kuma mahaifi a wajenta,saidai ta farat daya mai rabawa ta raba mai raba soyayyar iyaye da 'ya yansu wato mutuwa,a lokacin da suke tsaka da gudanar da rayuwarsu.


Mahaifinta uba ne da ya zama daya tamkar da dubu,wanda bashi yiwuwa ta manta soyayyarshi garesu,musamman ita din da take 'yar fari a wajensa,ta kuma ci sunan mahaifiyarsa,saiya zamana soyayya da kulawar da yake bata ta dabance,har kullum mutuwarshi sabuwa ce a ranta,rana da lokacin basu taba bace mata ba daga idanunta.


A hankali tayi sallama cikin falon,qannenta dake xaune suna cin abincin rana suka amsa,cikin farinciki qauna irin ta 'yan uwantaka suka miqe suna mata oyoyo,fuskarta washe da fara'a take amsa musu,wanda hayaniyarsu ta fito da mahaifiyarta dake kitchen.


Kyakkyawar mace mai kyan zubi da haiba,ma'abociyar tsafta nutsuwa da kyakkyawar dabi'a,wanda kyawun dabi'arta ya sanya koda bayan rasuwar mai gidanta dangin mijinta suka kasa rabuwa da ita,suka roqi alfarma taci gaba da xama dasu har zuwa sanda xata buqaci aure,su kuma zasu tsaya mata tamkar nata dangin.


Duk da cewa bata rasa wani gata ko kulawa daga nata dangin ba,amma hakan bai hanata amsar tayinsu ba,saboda tsantsar dattako irin na uwar mijinta,da yadda ta nuna mata qauna da kulawa tun haduwarsu har xuwa yau din,bugu da qari kuma,bata jin xata iya sake aure a sauran rayuwarta data rage,tunda ta rasa miji daya tamkar da dubu irin sa'id uban 'ya'yanta.


A nutse ta qarasa daura da inda mahaifiyar tata ke zaune
"Ina wuni ummi"
"Lafiya qalau,ya makaranta ya kuka barosu"
"Lafiya lau ummi,wannan karon duka babu dadi,ni kadai aka bari a makaranta,yasira ta rigani dawowa" tana zare carbin hannunta ta amsa
"Eh ai jikin nata alhmdlh da sauqi,jiya na shiga na dubata" ajiyar zuciya tadan saki
"Tana raina ummi,gobe in sha Allahu nima zanje na dubata"
"Ya kamata kuwa,don dazu yaayan ma ya kirani yace an daukoki ko?"
"Eh su ya musty ne ma suka je a motar wancan mutumin" sosai ummin nata ta tsareta da idanu tana kallonta,sai a sannan ga gane tabargazar data tafka,saita dauke nata idanun tana son wayancewa
"Inna wuro?,waye wancan mutumin?,yayan naku?,ashe qara lalacewa kike?,duk fadan da nake miki bakiji kenan?" Marairaice mata tayi,don idan da sabo ta saba da fada daga wajen ummin indai a kanshi ne,abu na qarshe kuma data fi tsana kenan a rayuwarta
"Kiyi haquri ummi,mantawa nayi,bazan sake ba" kanta ta dauke kawai daga gareta,tasan ta fada ne kawai,amma wannan halayyar ta jima dason rabata da ita amma ta kasa,ta zame mata jiki,rabuwa da ita sai a hankali,bata tashi daga wajen ba sai data ji tace
"Allah ya kyauta,Allah ya rabaki da wannan halin".


Dakinta dake sashen wanda ba kasafai ta fiya kwana a ciki ba ta wuce,tsaf yake kamar ko yaushe,duk da bata kwana ciki amma kullum saita gyarashi,'yar madaidaiciyat cupboard dinta ta bude,ta zabi kayan sawa adadin wanda takeso,ta debi kayan kwalliya mayafanta da sauran muhimman abubuwa don maidasu sassan hajja,saboda muddin ta dawo hutu tafi xama a can,bama ita kadai ba duka 'yammatan gidan dakin dake sashen hajjan suke tarewa har sai ta koma.


Ita dinma tafison zaman can din,saboda tafi sakewa sosai fiye da sassansu,hajjan na barinta tayi yadda takeso koma bayan ummin nata dake da tsauri da kuma dokoki iri iri.


Kai tsaye ta koma sassan hajjan,duka sun fice da alama kowacce akwai abinda zatayi,hakan ya mata itama saboda wanka takesonyi ta kuma rama bashin baccin da batayi ba daren jiya a makaranta,don su kwana waqe waqe na murnar tafiya gida hutu,gabanin asuba koma kowa ya shiga sabgarsa taci gaba da hada kayansa da kuma bin layin wanka.


Sai data fara zuwa gun wayarta dake chargy,hopefully ta taba screen din ya kawo haske cikin zumudi,don ta tabbatar zata iske texs ko miscal na nuraddeen kamar yadda ya saba mata a kullum idan ta dawo hutu.


Saidai kuma ga tarin mamakinta babu kiran hakanan babu saqon nashi,sosai abun ya daure mata kai,amma saita bashi uzuri,ta shiga ta duba balance dinta.


Naira hamsin ce tayi ragowa a layin nata,ta tuna zahra takwararta ce ta mata transfer kyauta ana ya gobe xasu koma hutu,tunda tace ga wanda ya tura mata kudin ta raba musu 50/50 a ciki sai taji credit din bai burgeta ba,amma yanzun zai mata amfani,don haka kai tsaye ta shiga rubuto lambobin nuraddeen daka wanda ta jima da haddacesu ta danna kira,take sunan my happiness ya bayyana saman screen dinta,ta kalli sunan ta saki murmushi tana kuma sauraron yadda wayar ke ringing.


Dab da zata katse aka daga,sallama ya fara yi mata,saita sauke a jiyat zuciya cikin shagwaba tace
"Nayi fushi"
"Afuwa,kaina bisa wuyana,kina raina inata son na karki,damac ce ban samu ba". Duk da uzuri ya nema amma sai taji banbarakwai,don wannan shine karon farko daya soma neman uzuri irin haka a wajenta,amma saita saki murmushi
"Nayi maka,amma fa lasam nayi kewarka da yawa"
"Nima haka princess,an dawo lafiya?"
"Lafiya qalau alhmdlh"
"Ya makarantar,ya mutan gidan?"
"Kowa lafiya lau" zai soma magana taji ana mata warning cewa kudinta sun kusa qarewa,daga bisani ta tambayeshi me yace
"Nace ne ina hajja da ummi"
"Duk lafiya na samesu....." Ta kasa kunne taji yace xai shigo a yau din,saidai tuni kamfanin waya suka katse kiran saboda qarewar kudin wayar tata,saita aje wayar gefanta tana dan dubanta,tasan cewa babu jimawa xai biyo sawun kiran nata,don haka ta zauna daura da wayar tana dan gyaran kayanta tana dakon kiran.


Harta gama gyaran bataji shigowar kira ba,sai data miqe tana shirin shiga bandaki ta watsa ruwa taji sautin shigowar saqo,ta miqa hannu da hanzari tana dubawa,saqon daga nuradden dinne
"Zan kiraki" abinda ya qunsa kenan,saita maida wayar ta ajjiye ranta tana cewa
"Lallai yau wanne irin busy happiness ya shiga haka" ta wuce bandakin bayan ta daura towel din wanka.


Aqalla minti goma sha biyar ta shafe a bandakin sannan ta fito tana mita
"Haba,babu inda yakai gida dadi,me za'ayi da makarantar kwana,babu abinda yakai gida dadi wallahi,inda a school ne ina ka isa ka dade haka,da tuni an matsanta miki daki fito,mtseww...wallahi badan yaaya da kuma ummi da bazan koma ba" da wannan qananun mitocin mata ta qarasa gefan qatuwar kafitar dake dakin ta zauna,wanda daura da ita 'yar drower ce dake jere da kayan shafe shafenta,zahra ba daga baya bace wajen son ado da kwalliya,hakanan idan ta fannin yawan sutura da kayan qyale qyalen rayuwa ne tana sahun gaba cikin 'yammatan gidan,saboda ta kowanne fanni yi mata ake dalilin maraicinta,qannen mahaifiyarta mata da yayan mahaifiyar nata dake matuqar qaunarta,wanda dukkan abinda xaiwa yaransa to lallai fa saiya yiwa zahran,hakanan 'yan uwan mahaifinta dake gidan,duk sanda wani xaima iyalinsa saiya hada da ita,ga hajja a gefe itama da ba'a barta a baya ba.


Sa'annan uwa uba wani irin farinjini da Allah ya yiwa zahran tun tana mitsitsiyarta,don mahaifanta ma sam basa yarda a karbi abun hannun kowa akan yarinyar,haka halittarta take,tun abun na baiwa mamanta mamaki harya koma bata tsoro,hakan ya sanya tun kan ta mallaki hankalinta ta tsaya kai da fata wajen mata addu'ar samun kariya da samun miji na gari,don ita kanta tasan Allah ya yiwa diyartata baiwar wani asirtaccen boyayyen kyau,tana tsoro n kada hakan ya zama wata sila da za'a shiga rayuwar diyartata a cutata mata babu dalili,ta sani cewa sautari baiwar kyau jarrabawa ce,qalilan ne kuma cikin mutane ke iya cinyeta,musamman mata.

A nutse ta kammala shiryawa cikin doguwar rigar atamfa cotton mai budadden dinki,ta gyara kanta da ribbom wanda da wahala kaga kitso a kanta,duk wanda ya santa yasan bata qaunar kitso tun yarinta har zuwa yanzu data girma,duk sanda xa'a mata kitso saita tarawa mai kitson jama'a saboda tsabagen kuka,daya daga cikin abinda ya sake sawa basa jituwa da yayanta kenan,yana ganin kamar an bata ta ne an sangarta ta.


Tana tsaka da fesa turarenta mai sanyin qamshi wanda ta saba ta soma jiyo sautinsa.


End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login