Showing 99001 words to 102000 words out of 121250 words

Chapter 34 - ALKIBLA complete

Start ads

24 Aug 2025

478

Middle Ads

data fito dasu,sanadin daukowa zahran abinda ta batan,ta san sarai indai baisan da tafiyarta ba bazai qyale ba,don baya daukan irin wadan nan abubuwan.


Sai data shiga ta yiwa duk mutanen gidan sallama,bata tarda mama ba ta fita tun sassafe dubiya,umminta dubu biyu ta bata,sai taqi karba,duk da ta yiwa account dinta tas saboda siyayyar data yiwa kanta da kanta,don kada ta tambayi haidar din,wanda tunda take bata taba yiwa kan nata siyayya ba sai wannan karon.


Gaban motar ta shige sanda mustapha ke kunna motar,ya tasheta suka fice daga gidan.


Tun basuyi nisa ba suka soma hirarsu yadda suka saba,cikin raha da zolaya,gab da zasu shiga farawa wayar mustaphan tayi tsuwwa,sai zahran ta xolayeshi
"Tun daxu ake faman kiranka,hala wata mai rabon wahalarce" ta fada tana sheqe masa da dariya
"Allah kinga makwancina da yawa.....ki zuba ido,sai nafi mijinki kudi,kibar ganin aikinmu har yanzu baizo hannu ba,hausawa suka ce gayawa wanda ya tara ya kiyayi me nema.....kai shine ma ke kira" ya fada yana zaro ido,sai zahran ta qyalqyale da dariya
"Qaryar kawai,ashema cika bakin naka bai kai ba,tunda gashi daga ganin sunansa kawai ya saka fargaba" hannunsa daya ya daga
"Na yarda wallahi....ke....kinsan soja kuwa....hmmmm" daga haka ya daga wayar,ya sanyata a handsfree.


Husky voice dinsa ce ta cika wayar,kamar bai jima da tashi a barci ba
"Kai kana ina?" Ya tambayeshi a dake,cikin girmamawa yace
"Gamu a hanya zan maida inna wuro makaranta"
"Waye ya baka izini?" Ya jefa masa tambayar data saka mustapha ware idanu yana duban zahra,wadda itama shi take kallo,dukkansu gabansu na faduwa,bai iya amsa mishi ba ya tsintoshi yana cewa
"Duk inda kuke ku dawo yanzu yanzun nan" daga haka ɗif ya katse wayar,saiya soma neman wajen tsayawa,ya gangara gefan titi zaiyi reverse.


Kallonsa zahran tayi
"Wai komawa zakayi?" Girarsa ya dage duka yana kallonta sannan yace
"Eh mana....au so kike nace masa a'ah,tab....wallahi bazan iya ba,ke da kike matarsa ma bakice komai ba saini"
"To gaskiya malam tsaya na fita,na tari wata ta kaini,saboda indai banyi attending class ba daganan zuwa lokacin da lecturer din yace ba da wuya bai zame min matsala ba" lock yayi sauri ya sanyawa qofofin sannan ya fara reverse yana cewa
"Kinsan Allah ba xaki jawomin ba,ai kiyi haquri kawai na miqa masa ke da motar sa".


Kafin su isa gida kuwa mita da qorafi mustapha ya shata,kamar ma shine haidar din,shidai dariya yake sheqa mata
"Sai dana tambayeki ya san zan kaiki kika ce eh,to ashe ma ko sallama bakiyi masa ba,bayan kinsan halin guy din nan,ba'a canza masa ko take masa doka,nidai na kaiki lafiya shine kawai mafitata a wajensa" .


Suna shiga harabar gidan ya sake kiransa
"Ok" kawai taji yace,ya kashe wayar sanda xahra ke tambayarsa
"Me yace?"
"Yace nakai masa key din" haushi takaici da baqinciki ya cika,wato ita bata ga tsuntsu bata ga tarko,saita balle murfin motar ta shige sassan hajja.


A falo ta sameta zaune tana karyawa,ta dinga kumbure kumburenta da qunquni amma hajjan bata ce mata ci kanki ba,a haka har kusan awa daya,wanda tuni ta fara qwalla,sai ga husna ta shigo,tace wai ta fito inji ya haidar,jakarta ta figa tafita kamar jakarce tayi mata laifi,ko magana bata yiwa hajjan ba,ita kuwa hajja sam bata damu ba,murmushi kawai ta saka,saboda hango tarin nasarori daga wajen haidar,wanda ta tabbatar nasarar da zata samu akan haidar,ita zata kai har kan zahran.


Yana zaune gaban motar ya kamo sashen labari na bbc hausa yana sauraron labaransu na ranar,yayi masifar kyau cika da kwarjini cikin qananun kaya,idanunsa saye cikin wani sunglasses mai azabar kyau qirar wannan shekarar,wanda glass din ya qara masa kwarjini qwarai,jikinsa ba abinda yake fitarwa sai qamshi mai sanyi,wanda yacakuda da qamshin freshner na motar da sanyin ac dai wadda baya rabo da ita.


Tana shiga motar sanyin daya cikawa motar ya sanyata yin gulmarsa a ranta,taja murfin motar ta rufe,sannan ta waiwaya kadan tana gaisheshi,ko kallonta baiyi ba ya tada motar,ya jata da gudu suka fice daga gidan,saita lafe jikin murfin motar kawai,tana jin bugun zuciyarta yana sauyawa.


Shuru ne ya ratsa motar sanda yake tsala gudu dasu saman hanya,duk da suna cikin gari basu fita wajen gari ba,ta karanci shima gwanin gudu ne sosai a mota.


"Kin rainani ko?" Ta tsinci muryarsa yana fada a taqaice,dan waiwaya tayi ta dubeshi kafin ta dauke kai,kansa da idanunsa suka suna kallon titi ne,kasa amsawa tayi,sai tayi shuru tana murxa yatsunta kamar yadda shima yayi shurun,kamar bazaice komai ba kuma saiya bude bakinsa gently yace mata
"Ko auren uwaka ubaka mukayi dake auren tasha nidin mijinki ne,kinda da haqqi wuyana kamar yadda nima nake da haqqi wuyanki,bare ma aurenmu yafi gaban nan,koda bakiso bani so,koda babu shaquwa a tsakaninmu,tunda iyayenmu mutane mafi daraja a rayuwarmu su suka daurashi,fita babu izinin miji haramunne kuma ba dai dai bane....sannan komai niya kamata na zama a sahun gaba wajen sani kafin kowa.....so please.....please kada ki sake,idan ba haka ba saina daure qafafunki a inda ake daure qafafun marasa ji irinki" maganganunsa sunsa jikinta yayi sanyi,saita tsinci kanta da furta
"Kayi haquri" softly,wanda hakan ya bashi mamaki,sai kuma yaji dadi har cikin ransa,kamar yadda itama mamaki ya kamata,tayi tunanin zai balbaleta da fada ne har yayi ma kamar zaya daketa,kamar yadda yake musu acan baya idan sukayi laifi,ko kuma zai gaggaya mata magana,ko yace ta tafi a motar haya,a haya suke hangen halinsa,mutum mai kushin hali fushi da fada,kafiya da taurin kai,amma sai taga duka baiyi ko daya ba,ya gaya mata magana ce ta hankali,wanda duk me hankali ta isheshi ya fahimta cikin ruwan sanyi,basai an qara masa da wani abun daban ba.


Bata yanke daga wannan tunanin ba taga ya tsaya qofar wani babban kanti,wanda ya hada komai da komai,kusan komai.na buqatar yau da kullum da amfanin rayuwa suna saidashi
"Wait" kawai yace yana cre set belt din jikinsa ya bude motar ya fita ya nufi shagon,saita bi bayansa da kallo,yana yin yadda yake taku cike da nutsuwa qasaita da ginshira,sai daya shige sannan ta dauke idanunta a hankali tana sauke ajiyar zuciya,yaushe ya haidar ya sauya?,yaushe yayi laushi,to amma ita game da yadda yake mu'amalarsa da yaran gidansu bataga sauyi ba,donko ranar suna sai daya yiwa su salma fata fata kan sunkai dare,kuma mazansu sunzo daukarsu kowacce ta shanya mijinta,har kusan kuka sukayi.


Babu jimawa taji an bude set din baya,shine riqe da babbar leda ya sakata a bayan motar ya rufe,sannan ya dawo set dinsa ya shiga ya sake tada motar.


Basuyi nisa sosai saman titi ba taji ya sanya casset na karatun dr malam umar sani fage,kamar yasan xabinta kenan cikin dukka malamai,babu malamin da take bin karatunsa qafa da qafa kamarsa,take kuma nutsuwa da dukka fatawoyinsa kamar shi,zallar hikima da dora bawa bisa hanya,da doron shari'a hanyar da zaka samu lahira irin malamin,batajin a wannan qarnin akwai malami kamarsa,zaiyi wuya,duk da ba'a rasa bayin Allah,wadanda suke lunguna da saqon qasa da garinmu,kuma Allah baiyi ambatonsu ya bayyana ba a bakunan bayinsa,amma shi yasan da zaman kayansa.


Wannan karatun shiya jagorancesu,ya kuma rakasu har cikin makarantar.


Suna shiga ya rage gudu,ya dinga gangarawa a hankali har yakai iyakar inda motoci ke tsaiwa daga nan babu qari,ya kashe motar sannan yana qoqarin bude murfin motar yace mata
"Dawo set din baya" saiya fita,bude murfin tayi kamar yadda ya umarcetan.


Yana tsaye a wajen motar hannunsa a qirji yace mata
"Ki duba kayan idan sun miki,an siyo su late.....but remember,nidin bamai kudi bane" ya fada carelessly kamar ma bashi yayi maganar ba.


Ledar kawai ta buda ta rufe tace
"An gode,Allah ya saka da alkhairi" saita fito.


Yana tsaye jikin set din data zauna dazun,kuma tabar jakarta a wajen tana da buqatar dauka,murya qasa qasa sanda take tsaye a gabanshi nesa kadan dashi tana facing dinsa tace
"Jakata" saiya dauke idonsa daya tsareta dasu,ya bude motar ya dauko jakar,kudi ya ciro dubu ashirin daga aljihunsa ya bude jakar ya sanya mata yana cewa
"Ki riqe wannan saboda koda wata buqatar zata taso....zanyi tafiya ne,koda zasu yanke miki kafin na dawo,karki tambayi kowa,kiyi gayawa mustapha,zaiyi handling komai" saiya miqa mata jakar,ta sanya hannu zata ansa,sai daya tabbatar ta riqe saiya janye jakar,ta bada amannarta gaba daya,hakanan bata zata ba,don haka ta biyo jakar talau,sai gata taja birki a gabansa,dab dashi,don taqi kadanne tazarar dake tsakaninsu.


Qas tayi da kanta saboda kallon da taga yana mata,ta kuma kasa janyewa,saboda ko yaya ta motsa jikkunansu zasu hadu.


Jakar ya sake miqa mata,ta miqa hannu a sanyaye karo na biyu zata karba,sai yasa daya hannun masa caraf ya damqe tsintsiyar hannunta,a tausashe ya jata ya jinginata da jikin motar,a maimakon dazun da shine ke tsaye jikin motar,sannan a tausashe ya sanya qafarsa tsakanin nata qafafun,ya kuma dafe gwiwar hannunsa saman motar dab da kafadarta,idan daga nesa ka hangesu zakayi tunanin tana rungume cikin jikinsa saboda kusanci,kusancin da jikinta da zuciyarta suka kasa dauka,saboda duk wani fitar numfashinsa tana jin saukarsa saman fuskarta,hakanan qamshin turarensa daya danne nata,uwa uba idanunsa masu kaifi da suka sake yi mata nauyi,sai tayi hanzarin yin gefe da kanta,wanda kafin sakan daya yasa yatsun hannunsa ya kamo habarta,ya maido da fuskartata saitin tashi.


Bai barta ba sai daya lalubo qwayar idanunta ya saka tashi a ciki,cikin wani irin sauti dake fita da qyar,can qasa kamar wanda bacci yaci qarfi ya soma magana
"Zanyi tafiya me nisa.....waje mai hadari,zan iya dawowa,zan iya salwanta a can,duk da bai cikin aikina.....amma zan shiga da kaina saboda na sake sadaukarwa da qasata ruhina,inason in samawa wadanda suke cikin qunci salama da nutsuwar ruhi.....pls forgive me if i hurt you a tarayyarmu"wani irin rauni taji ya mamayeta irin wanda bata taba ji ba,saita daga idanunta da cikin qaramin lokaci suka hada qwalla taf ta dubeshi,bata wani abu mai nauyi na sauka saman zuciyarta cakude da wani yanayi da batasan wanne iri bane,idan kuma ya mutu fa a can kamar yadda yace zai iya salwanta?,wani sashe na zuciyarta ya raya mata,rayawar daya sanya qwallar data tara ta subuce mata,ta gangaro saman kuncinta zuwa habarta
"Oh....no,bafa kuka nace ba,banason kuka ko kadan" yatsunsa ya sanya guda biyu ya dinga dauke mata qwallar,sai daya gogesu tas,maimakon ya daukesu saiya zarto dasu saman qirjinta,tun daga wuyanta zuwa qasa ya fara mata tafiyar tsutsa dasu,ya kuma sanya idanunsa cikin nata,take jikinta ya dauki rawa
"Am gonna miss my......" Shuru yayi bai qarasa ba yana ci gaba da kallonta,cikin qarfin hali ta sanya lallausan hannunta tayi caraf ta riqe hannun nasa tana girgiza masa kai,murmushi ya saka yana sauke hannuwan nasa,sannan yace
"Matsoraciya......" Saiya saka tattausan labbansa a hankali,yayi kissing nata softly da wani irin sanyi saman labban nasa da suka ratsa har kwanyarta ya sakata lumshe ido,tana jin wani feeling na cika zuciyarta,wani yanayi na farinciki yana cikata kamar ana yawo da ita a duniyar gajimare.


A hankali take tafiya,duk da ta bashi baya amma tana jin tsaiwarsa a wajen cikin jikinta,saidai batasan meye ya tsaidashin ba,kafin wani lokaci kafin takai ga bacewa a wajen taji tashin motar tasa a hankali,saita dinga jin wani abu me kama da kewa yanason kamata,inda tayi qarfin hali ta tattara duk wani jarumtata tayi tayi fatali da wannan batun,ta kuma qaryata kanta da kanta.
23/10/2021, 08:48 - 👍🏻👍🏻: 38


Wani mugun shewa taji sanda ta shiga dakin kwanansu,dama tun cikin aji ta fuskanci suna gulmarta da ido,don dai da malami a ajin,babu damar suyi mata magana ne.


Da ido ta bisu ganin yadda suketa mata dariya
"Dalla malamai,banason iskanci,meye abun dariya a jikina?,koni mahaukaciya ce?" Sai sannan hindatu tace
"Mahaukaciya tuburan kuwa......ah,ya haidar din da bashi da mutunci,ya zakin da babu ruwanki dashi,aka hanani neman soyayyar dan bawan Allahn nan,ash kinsan cewa qarshe ne shi a soyayya,ya gama haduwa tako ina,sai gashi ya kasheki da soyayya agun ajiyar motoci,har jama'a suka wuceku ma baki sani ba...nidai gaskiya qawa kinmin yankan baya ba kadan ba" ta fada tana hade fuska,janna tace
"Nifa banga laifinta ba,tsakani da Allah fa,waje zaiga guy irin wannan yana da dama ya bari ya wuceshi,wallahi ko nice sai inda maina ya qaremin,idan kuwa ina zaune yazo ya taya,ai babu wani kwane kwane zanyi wuff da abina".


Babi babi na tsiya suka bude suka dinga yi mata,ita dai ci kanku bata ce musu ba,hakanan ta samu kanta da kasa tanka musu,sai data tafi bandaki sannan suka saurara mata,data dawo kuma aka shiga hirar yaushe gamo,nan ma sai da suka tsokaneta
"Daga yanzu zanje na dawo qawa kuma sai mukaji dif" tsaki taja tana nade abun sallarta
"Wallahi hajja ce,ashe ta timer min" dariya duka suka saka,janna tace
"Allah dai ya biya hajja,wallahi ta kyauta min" harara ta jefa mata,hindatu ta cafke
"Ta taimakeki kuwa,don bakiga kyan da kika qara ba,Allah yasa anyi me gaba daya" ta fada suna tafawa,dadai ta fuskanci iskanci da tsiya suka tanadar mata buhu buhu,saita miqe tabar musu dakin,saidai zancan hindatu ya tuna mata da abinda ya faru a wancan ranar,ranar da yaso yayi mai gaba daya din,sai wani qaramin murmushi ya sube mata,ita kadai taja hijabinta zuwa qasan hancinta tana jin kunyar kanta da kanta.


Dawowarta ba jimawa aka soma jarrabawa,wanda daga ita din watanni kadan suka rage musu suyi jarabawar kammala makarantar,kamar kowanne lokaci dai bata daga qafa ba,ta bada himma wajen karatunta sosai,duk da cewa lokaci zuwa lokaci tunaninsa yakan fado mata a rai,har yakan tsaidata na wasu mintuna kafin ta dora,tun tana yaqin ture zuwan tunanin kwanyarta harta haqura ta bashi dama,saiya zame mata jiki,don kusan duk sanda tazo kwanciya bacci shine abu na qarshe da zatayi kafin baccin ya dauketa,kaf xamansu na abuja sai tayi bitarsa,ranar da zasuyi sallama na qarshe da sauran moments nasu.


Batasan me yasa a kwanakin take yawan duba wayarta ba,koda yaushe tana kan cheaking sms da watsapp massages fiye da yadda ta saba,batasan dalili ba,sai randa zuciyarta tayi mata wata tambaya,wanda a take ta girgiza kai alamar a'ah
"Kina tsammanin samun kira da gareshi ne?" Wannan itace tambayar data yiwa kanta,wanda ko sau daya bata taba yarda da hakan ba.


Jarabawar wannan karon suna samun intervals sosai,don haka duk sanda taga akwai interval mai yawa saita tafi gida,tafiya gidan yakan sa mata nutsuwa,kuma yakan sanya taji kamar tadan rage nisan dake tsakaninta da wani abu wanda ada yake nesa da ita.


Sannu a hankali ta tabbatarwa da kanta damuwa ce,damuwa ce ta rashin ganinsa ko rashin jin muryarsa na tsahon tagwayen sati,har ana neman shiga sati na uku,hatta a gida hajja ta fara qorafin shuru haidar,bai kira ba,koda an kira ba'a samunsa,to Allah yasa dai lafiya,addu'ar data sanya gaban zahran mugun faduwa,saboda tuna maganar daya gaya mata
_"zanyi tafiya me nisa.....waje me hadari,zan iya dawowa....zan iya salwanta a can.....ki yafemin idan na saba miki a tarayyarmu"_,kawai sai taji kuka ya subuce mata,ta danneshi har sai data kai daki sannan ta sakeshi.


Kuka tayi sosai wanda ta kasa yarda da dalilin kukan nata da zuciyarta keta bata,saidai ko ba komai ta danji nauyin dake qirjinta ya ragu,ranar sama sama tayi karatun jarrabawar da zata zana a jibi,washegari ta hada kayanta ta koma makaranta,wanda jarabawar kawaidai tasan saidai Allah ya tsallakar da ita,amma ita kanta bata gama tantance abinda take rubutawar haka yake ba,ko akwai kusakurai da gyararraki ba.


Hajja kuwa bin zahra tayi da kallo tun sanda taga tayi daki da sauri sanda take jajjabin kwanakin da haidar din ya shafe babu shi babu labarinsa,murmushi ta saki,duk da tana cikin fargaba,saita daga hannunta sama tana cewa
"Allah na gode maka,Allah na gode maka,ko yau na mutu ubangiji ka cikamin dukka burina,Allah ka qara hada kan zuria'ata da iyalina,Allah ka qarawa annabi muhammad S A W wasila da fadila" daga haka ta sauke hannun nata,zuciyarta na mata dadi,ba shakka komai yayi dai dai yadda takeso,tasan cewa da zarar ya dawo komai zai kammala dai daita.


Ranar da suka kammala jarrabawarsu suka samu hutu na wasu kwanaki ba masu yawa ba,saboda zasu dawo ne suyi maza su dora sabuwar semester ta qarshe,tana kwance a dakinsu kamar ba wadda ke shirin tahowa gida ba,tana kallon su hindatu sunata shiri.


Tun sanda ta dawo daga abuja ta lura da wani abu,dabi'un su hindatun su canza gaba daya,abubuwa da yawa sun daina yinsu yanayin shigarsu ya canza sosai,wanda hakan ya bata mamaki,saidai bata taba tambayarsu ba.


Hindatun ce ta qaraso ta taba zahran dake kwance rub da ciki,saita daga kai tana duban hindatu,hijabi ne dan madaidaici a jikinta wanda ta dorashi saman abayarta,wadda ta rufe jikinta ruf
"Tunanin me kike mrs haidar?" Murmushi ta saki,ta tashi ta zauna tana duban hindatun,fuskarta qunshe da murmushi
"Ina mamakin me ya canza qawayena haka tashi guda" murmushin itama hindatun tayi,ta zauna gefan zahra
"Tasirantuwa mukayi da qawar qwarai,hakan shiya canza mu,sannan kuma mukayi aiki da hankali da tunanin da Allah ya bamu,muka ga cewa
23/10/2021, 08:49 - 👍🏻👍🏻: 39


Da yammacine liqis,tana zaune a falon hajjanta,gidan yau kusan shuru yake saboda dukka yaran gidan suna islamiyya,saura kuma kowa yana wajen sabgarsa ta yau da kullum,kamar sassan nasu yau

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login