Showing 48001 words to 51000 words out of 121250 words
fada da dakakkiyar murya mai qarfin amo da sauti,irin ta sojan daya saba karba da bada umarni a fagen daga.
Yadda dai daikun mutane suka juyo suna kallonsu ya ankarar dashi,saiya sake mata hannun nata da sauri,fuskarsa na gauraye da wani irin bacin rai,ya zare muqullim motar daya maida aljihunsa ya cilla mata,ya kuwa sauka saman qafafunta,duk da taji zafin amma ba shine a gabanta ba,tashin hankalin dake a gaba take hararowa,tasan cewa abinda zai biyo baha din ba dan qarami bane,ta kuma fahimta me yake nufi,don haka ga duqa ta dauki key din ta fara takawa tana ficewa daga wajen kamar kazar da qwai ya fashewa a ciki.
Sai data fice sannan yabi bayanta ba tare daya tsaya amsar number dakin da yake nema din ba,tana gaba yana bayanta amma ba zaka zaci tare suke ba har ta isa bakin motar,daidai lokacin matashin da tun dazun yake dawafi cikin hotel din yana nemanta tare da burin sake ganinta ya hangeta,don haka da sauri sauri ya sauko a nufosu idanunshi a kansu,yana ganin sanda haidar ya fisge muqullin ya buda motar ta shiga baya ta zauna.
Sai daya tabbatar ta shiga sannan ya sanyawa motar lock,duk da ya dage dukkan gilasan motar bakan baisa yayi tunanin kunna mata ac koya rage wani glass din ba don iska ta shigo mata.
Yana zare key din yaji an dafe hannunsa,ya daga kai a nutse don ganin waye
"Me haka kake?,zaka kama yarinya ka rufe cikin mota saboda me?" Wani banzan kallo haidar din ya kafeshi dashi,cikin ransa yana tambayar kansa da kansa shi din waye?,sosai ransa ke tafasa baiso ya huce masa laifin da bashi ya aikata ba,amma kuma yanajin wani sabon bacin ran na taso masa dangane da rainin hankalin da yakeson zuwar masa dashi,shi waye nata da zai qalubalanceshi kan hakan?,ya santa ne?,shi ya kawota?,ko tare suka zo?.
Zare key din yayi ba tare daya sake bi ta kansa koya dubeshi ba,ya juya ya soma takawa zaibar wajen saurayin ya mara masa baya yana ci gaba da cewa
"Malam ka budeta nace tun kafin ka gano kuskurenka.....bakasan waye ni ba ko?" Ya fada cikin zafi dason nuna nashi qarfin qwanjin.
Wani irin juyowa haidar din yayi a zafafe har hana take masa rabin qafa da ingarman takalminsa
"Idan kaci gaba da bina kana min wannan ɓaɓatun sai na saka kayi nadama kai da banzan matsayinka,kuma zaka gane kuskuren aikatamin hakan kafin ni na gane nawa kuskuren,stay awa frm me tun ban rugurguza kwanyarka" tabbas ya hangi wani strong abu cikin idanunsa,ya kuma hangi yadda yake furta maganar bilhaqqi,ya kuma tabbatar ba'a banza yake magana kan yarinyar with confidence haka ba,amma a amtsayin da mahaifinsa keda shi a nigeria yafi qarfin wani da baisan ma ko waye ba ya gaya masa magana irin haka ya qyale ba,don haka zai jira yaga yadda za'ayi ya fita daga hotel din ya kulle 'yar mutane cikin mota
"Zan gani ta yadda zaka fita daga wannan ginin" ya furta sanda haidar ke komawa zuwa ciki,sai daya sake bi ta reception aka gaya masa dakin sannan ya wuce.
A nutse ya bude dakin da sallama a bakinsa,mutumin wanda a qalla ya kusa shekara hamsin da biyar ya amsa mishi,yana zaune saman kujera riqe da jarida yana dubawa,koda ba'a gaya maka ba shima kasan cewa soja ne,irin wanda ya jima cikin harkar bautawa qasa da bawa rayukan al'umma tsaro.
Fuskarsa dauke murmushi dake nuna kulawa da qauna yace
"Barka da zuwa aliyyu" qyam ya tsaya ya sara mishi kamar yadda sojoji keyi don nuna girmamawa ga manyansu,ya karba gaisuwar yana nuna mishi wajen zama.
Da kansa ya tashi ya nufi fridge na dakin ya daukowa zaki abun sha,yana mitar
"Bansan ina haisam ya shiga ba....almost one hour daga zaiyi waya" ya qarashe maganar yana miqa haidar drinks din,wanda ya miqe yasa hannnu ya amsa yana cewa
"Thank you sir"
"U r welcome" ya amsa mishi yana murmushi,suka zauna a tare.
Saida Aliyyun ya soma shan lemon sannan suka soma maganar daya sanya ya kirashin,general hamza adamu gusau kenan,mutum mai kirki qwarai da tausayin na qasa dashi,kusan shi ya zama kamar role model na aliyyu,saboda yadda yake da hazaqa da gaskiya riqon amana da aiki tuquru,yana son aliyyu sosai,hakanan yana mu'amalantarsa kamar dan cikinsa,saboda yadda Aliyyun keda jajircewa sadaukantaka gaskiya riqon amana da rashin tsoro,duk wani abu na ci gaba yakanyi qoqarin kawo aliyyun ya sakashi agaba,tun matsayinsa baikai wajen bama,hakan ya sanya cikin qaramin lokaci ya dinga samun qarin girma har zuwa matsayin da aliyyun yake kai a yanzun,yana samun kulawa da horaswa ta musamman daga wajen general hamza din,hakan yasa Aliyyun ya zama gagara badau,kuma qwararren soja daya iya aikinsa ya kuma san me yakeyi,dalili kenan da yasa su kansu sukeji dashi,domin kamar sun horeshi ne yazo ya kuma fisu qwarewa da sanin dabarun aiki kala daban daban,don haka ko ame akace akwai haidar din a ciki basa haufi.
Sunyi nisa da tattaunawar da sukeyi akayi kncoking,general ya bada umarni sannan aka turo aka shigo.
Daga kai aliyyu yayi daga duba wani map da daddy ya bashi kamar yadda yake kiransa yana amsa sallamar,idanunsa ya sauka kan saurayin,sun gane juna fes,sai kowanne ya daure fuskarsa,aliyyun yaci gaba da duba map din saurayin kuma ya qaraso ciki lokacin da daddy hamza ke cewa
"Daga ina haka?,kusan awanni biyu?" Shafo kansa yayi yana cewa
"Am sorry dad....wani abune ya tsaidani,but am back ai" kai ya jinjina yana nuna masa haidar
"Da daya yarona nan,Aliyyu mas'ood dabo" da sauri ya cira kai yana duban aliyyun,saboda koda fuskarshi boyayya ce to sunansa sananne ne a kunnuwa mutane ciki harda shi,bare ya jima yana jin sunan a bakin baban nasa,da kuma yadda yake ji da haidar din
"Ku gaisa mana haisam" yayi maganar yana maida kallonsa ga aliyyun,wanda ya aje takardar hannunsa saboda girmamawa ga daddyn ya miqe tsaye,yayin da haisam din shima ya tako inda aliyyun yake ya miqa masa hannu,shima miqa masa yayi sukayi musabaha,murya can qasa haisam din yace
"Nice to meet you!" Kai kawai haidar din ya kada masa yana zame hannunsa daga na haisam din ya koma ya zauna.
"Ka ganshi nan,yaqi aikin soja,yafison kasuwanci" inji daddy yana nuna haisam da baki,fuskar aliyyu ce kawai tadan motsa alamun murmushi yayi,sam hankalinsa shi bai wajen,Ya qagauta ma su gama maganar da zasuyin yabar wajen.
Sai daya qara kusan wata awa dayan sannan general ya sallameshi,ya miqe ya sara mishi ya qame sannan yamiqa masa hannu sukayi musabaha,ya dubi haisam
"Ka raka dan uwanka haisam zuwa mota,kwayi musayar lambobin waya ko?"general ya fada bayan sun gama sallama da aliyyu
"Ok daddy"ya fada yana miqewa,ya gyara zaman shirt din jikinsa yana bin bayan aliyyu.
Yadan masa rata amma ya dage ya cimmasa,ya tsaya daga gefan kadarsa,saidai duk da tsahonsa ashe aliyyun ya zartashi a tsaho,duk da yayi masa kallon nashi tsahon yafi nasa,ashe cika da murjewar jiki da haidar din ya fishi yasa yayi tunanin ya zarta tsahonsa
"Yaronmu kake ashe?,sai kabi a hankali ko?" Haisam ya fada yana duban haidar ta gefan ido.
Cak haidar din ya tsaya,ya zube hannayensa cikin aljihun wandonsa yana dan fidda wani murmushi na gefan baki,tsahon sakan biyar sannan ya waiwayo sosai yana duban haisam din,sai daya nuna hanyar da suka baro da hannu sannan yace
"Wancan da muka baro....girmansa nada yawa a dunun haidar....banda haka daka fahimci cewa ko jimina ta saka kanta a tabo...ba za'a kira kaza ba,amma duk da hakan zan gaya maka wani abu guda daya wataqila yayi maka amfani.....yaro tashi ka nemi suna....karka raba kanka da kowa,zaifi maka kyau da cikakken alfahari ka shaidawa duniya kai tsaye cewa kaine wane wane kamar yadda kullum nake alfahari da cewa nine Aliyyu mas'ud dabo....bawai ka cewa duniya kaine ɗan general hamza tahir ba" saiya murza yatsunsa saman fuskar haisam sannan ya qara da cewa
"Ka kiyayi shiga gonar haidar ta irin wannan sigar.....i repeat my self....ka kiyayi shiga gonar haidar" daga haka ya juya yaci gaba da tafiya ya barshi nan a tsaye.
Maganganun haidar din sun masa ciwo sosai,yana son ya nuna masa nasu qarfin ikon amma abu daya ke masa shamaki,yarinyar daya sanya cikin mota ya kulle,wanda tunda ya ganta yaji nan duniya ya samu matar aure,baisan alaqar dake tsakaninsu da ita ba,yana tsoron kada yaje ya bata rawarshi da tsalle,don dai yasan tabbas ba shakka baya ga macen bariki,babu wanda zaiwa macen da bai isa da ita haka ba ta bishi ta kuma yi biyayya,amma koma meye zaibi a sannu ya bincika,saboda haka ya nufi tashi.motar da sassarfa ya bude ya shiga,yayi ready yana jiran yaga tashin motar aliyyun don ya mara masa baya.
Duk da rashin mashiga da mafitar iska cikin motar amma a cure take waje daya,duk da gumin daya gama jiqeta saboda tsabar tunanin data fada yasa sam batajin jiqewar,tunanin mafita da makomarta take,harta hango kanta a gabansu abba tsakiyarsu suna tuhumarta meya kaita hotel,da wanne baki zata kare kanta?,wanne irin wawanci da dolanci haka ta aikata?,me yasa?,me yasa?,haka take tuhumar kanta,hankalinta a wani matuqar tashe.
Sanda taji yana bude qofar sai da hantar cikinta ta kada,wani matsanancin tsoronsa da bata taba jin irinsa ba ya rufar mata,tana nan a yadda take har zuwa sanda ya bude motar ya shiga,ya maidata ya rufe sannan ya tada ita ba tare da yace mata kanzil ba,abinda bata taba tsammata ba,tana jiran taji hukunci ko wata magana daga bakinsa amma saidai tunda suka fara tafiya har suka isa gidan babu abinda yace da ita.
"Fita!" Ya fada cikin daka tsawa data sanyata kama murfin motar ta fito da hanzari,cikin gudu gudu sauri sauri tayi sassan hajja,saidai tana gab da shiga sukayi karo da anty uwani,taja da baya da sauri,haka itama anty uwanin,mace guda daya tilo da halayyarta kan zahran ta bayyana,tana matuqar adawa da yadda hajjan kewa zahran,kulawa qauna da soyayya da take nuna mata,ko dama can macace mai fada,masifaffiya ce ita din,ita 'yace ga qanwar hajjan,tayi aure tana da yara hudu,uku maza sai mace guda daya autarta suwaiba,wanda itama ta dauki son duniya ta dorawa suwaiban,ji take sosai da ita,mijin nata ya rasu,koda kuma bayan rasuwar tasa bata sake wani auren ba.
"Me haka ke kuma kamar wadda aka biyo?" Ta fada cikin masifa tana qare mata kallo
"Ina kwana yakumbo" ta fada kamar yadda suka saba gaya mata,ko amsarta bata tsaya ji ba ta qara wuta zuwa ciki,sai anty uwanin ta bita da kallo ta kuma fara masifa
"Eyeee....ni zaki gaisar a haka?,lallai yarinyar nan iskancinki kullum qara gaba yake,koda yake kina da daurn gindi ne shibyasa,amma zamu hadu dake bari naje na dawo" ta fada tana buga cinya gami da yin gaba.
Sam bata kula da umminta dake falon hajjan ba sai data isa gaban hajja,saboda abune baqo a wajenta,ba kasafai ta saba ganinta din ba
"Lafiya?" Hajjan ta jefa mata tambayar tana duban qwayar idanunta,saboda yadda ta ganta kamar a birkice,yayin da ummin tata itama hankalinta gaba daya yake kan zahran a fakaice,don a zahiri ba zaka ce hankalin nata yana kanta ba.
Ko kafin tace komai haidar yayi sallama,a nutse yake takowa zuwa cikin falon,yana qoqarin rage zafi da radadi da yake ji daga cikin qirjinsa zuwa maqoshinsa,kallo daya ummin ta yiwa fuskarsa tasan ba lafiya ba,don idanunsa nakan hajjan da zahran,hakan ya sanya ta miqe don basu waje,duk da can qasan zuciyarta hakanan ya cika da zulumi da fargaba,sai taji batason tafiya,amma saita tanqwara zuciyarta ta duqa ta dauki carbinta ta fice ba tare da sun ankara bama.
Tana barin cikin falon taji ta kasa sake daga qafarta,abinda bata taba yiba kaf tsahon rayuwarta ta tsaya sauraren zancan wasu koda kuwa ya shafeta,amma a yau din sai taji tabbas tana son jin me ya faru?,wanda jikinta ya bata kan zahra ne,don ba haka ta saba zuwa gida weekend ba.
"Kai zaki.....lafiya?" Hajja ta jefa masa tambayar ganin yadda idanunsa suka sauya launi,ya kafeta da ido ya kuma kasa cewa komai
"Gata nan hajja,a hotel na daukota" idanu hajjan ta zaro sosai,hannunta dafe a qirjinta
"Kai haidar,banason shirmen banza da wofi,kasan kuwa me kake fada?,otel fa kace!" Kai kawai ya jinjina mata alamun tabbatarwa
"Kai!,haidar.....na gaya maka banason sakarci ko?,ka gayan gaskiya" wannan karon sai yaqi tanka mata,illa lumshe idanunsa da yayi kawai bai sake furta komai ba,sai hajjan ta waiwaya inda zahra ke tsaye,tana jin kamar zata saki fitsari
"Innawuro....abinda ya fadi gaskiya ne?"kamar ta dora mata dala da gauron dutse haka taji
"Eh hajja....amma...." Salatin hajjan shi ya katse sauran magana da bayanin da tayi niyyar yi mata,yayin da umminta dake tsaye daga can bakin qofa ta soma maimaita
"Hasbunallahu wa ni'imal wakil,Allahumma ajirni fi musibaty,wa'akhlifni khairan min ha" daga haka ta ja qafafunta da take jin sun mata nauyi ta soma barin wajen cikin matsanancin tashin hankali,wani hazo hazo take gani a idanunta,a haka takai kanta bangarenta cikin mawuyacin hali.
"Zahra'u....hotel fa zahra'u,hotel aka ce fa?" Ta fada tana duban zahra wadda takejin inama ana iya maida hannun agogo baya ta maida ta goge dukkan wani kuskure data aikata nabin su hindatun da tayi
"Hajja....ki tsaya na miki bayani,wallahi ba abinda kuke zato bane,ba abinda kuke tunani bane....na rantse d...."
"Rufemin baki....zahra'u ai yau ni kika kunyata,ni kika baiwa kunya wallahi,oh ni fadimatu" hajjan ta fada cikin matsancin firgici tsoro da kuma tashin hankali
"Matsa daga kusa dani,tashi ki ban waje nace" karon farko da hajjan ta taba korarta daga inda take tunda suke a rayuwarsu,hakan yasa taji wani sabon tashun hankalin ya rufto mata,saita kasa jurewa ta kwasa da gudu tayi daki.
Shikam haidar na tsaye,sai a sannan ya bude idanun nasa,ya juya ya soma takawa zaya bar falon
"Haidar....zo nan" hajjan tayi kiran sunansa tana qoqarin binne tashin hankalinta,baice komai ba ya dawo ya tsaya daura da ita,ta masa kallo na tsaf,ta karanci yadda ranshi yake masifar bace
"Bana son naji maganar nan a bakin kowa haidar....banaso" idanunsa ya bude sosai yana kallon hajjan,kamar ba zaya tanka sai kuma ya bude bakinsa
"Me yasa zakice haka hajja?,sai yaushe xaki daina bata kariya kan dukkan laifin data aikata koda kuwa muninsa yakai wannan?,wannan kariyar ita ta zame mata rigar da take iya shiga ta buya a ciki,taci gaba da aikata abinda ranta yaso a sanda taso ba tare data samu wata tirjiye ko kuma shamaki da zai hanata kaiwa ga ci gaba da aikata mara kyau ba....don Allah hajja wannan karon....ki cire soyayya ko qauna,ki kuma kauda kai,ki bari ayi hukuncin dashi yafi dacewa"
"Haidara" hajjan ta sake kiransa karo na biyu
"Nasan zahra'u ciki da bai,na santa sanin dako mahaifiyarta bata sani ba,ni ina ji a jikina,ina jin cewa zuwanta ko ganinta a wajen baya nufin ta aikata ko tana aikata wani mummunan abu ne,kuma nasan bayanin da taketa qoqarin yimin kenan,saidai naqi bata dama da wuri tayi bayanin,har sai rashin bata damar ya zama wani hukunci mai zaman kansa a gareta,nayi imanin jinina bazai taba aikata wata mummunan alfasha har kamar haka ba,addu'a ba qarya bace" shuru yayi ransa yana baci,yana ganin hajjan tana bata kariya ne kawai saboda kada ta fuskanci hukunci,wanda hakan ya jima yana bata masa rai,shin ita hajja bata ganin sauyi qarara tattare da yarinyar ne?,har sai yaushe sannan zata ankara su yiwa tufkar hanci?,duk wasu doka da qa'idoji na gidan hajjan da karan kanta tasha karyasu indai akan yarinyar ne,wannan shine dalilin da yasa sam yarinyar bai hada idanuwa da ita,saboda yana da yaqinin duk sanda ta masa wani abu mai kama da sangarta ko rashin kunya zai iya ɓaɓɓalata ya zubar.
Saiya juya kawai yaci gaba da takawar,hajjan nada wani irin girma da qima a idanunsa,amma yana jin sam hukuncin bai kwanta masa a rai ba,saidai kodon saboda girmanta da matsayinta bazai iya tsayawa yayi ja'inja da ita ba,a haka ya fice ba tare daya sake cewa komai ba.
************
Kwana uku da dawowartata amma sam hajja taqi tsaiwa ta saurareta ko taji bayaninta,wanda hakan yayi mugun daga mata hankali,don hajjan itace last chance dinta,tana da yaqinin koda kowa yaqi saurarenta,koda kowa yaqi yarda da ita zata samu dukkan wadan nan abubuwa daga wajen hajjan tata.
Cikin kwana ukun ta rame ta fada saboda fargaba,sai a rana ta ukun hajjan ta tsaya da qyar ta saurari bayaninta,ta yarda da ita ta kuma gamsu,saidai tasha fada da masifa daga wajen hajjan irin wadda bata taba yi mata irinsa ba,duka bai damu zahra ba,tunda ta samu abinda takeso,sai data gama fadanta tsaf ta miqe sannan tace cikin dari dari da tsoron amsar da zata bata
"To hajja makaranta,anata CA bana nan" wani kallo mai kama da harara tayi mata
"Saiki jira kiji abinda yayanku zaice,don shurun da yayi kan zancan bazan sake tilastashi kan makomar makarantarki ba"
"Sai kace shine uban kowa cikin gidan nan?,koshi ya haifi kowa?" Abinda zahra keson fada kenan,amma tasan fadin hakan shi zai sake dagula komai,bata ma isa tace din ba,haka taja bakinta tasa masa zip ta zuge ta zubawa sarautar Allah ido,cike da fargaba kada ta rasa abubuwa masu muhimmanci acan makaranta.
Har hajjan