Showing 66001 words to 69000 words out of 121250 words

Chapter 23 - ALKIBLA complete

Start ads

24 Aug 2025

458

Middle Ads

dama can duk wanda ya sa ta yasan tana da wannan zarrar,amma a yanzun takatsantsan da kamewan ya qaru,tunda ada issue din karatu yakan hadasu,amma a yanzun mawuyacine idan ba ya zama dolen dole ba.
23/10/2021, 08:45 - 👍🏻👍🏻: 24
*_Are you guys looking for where to buy ur skincare product @ mg's skincare is the best plug for you🤗_*
*_Do you wish to have that flawless skin that's free of all skin prblm_*
*_Do you wnt to achieve that milky skin that turn heads wherever you go😉_*
*_Try mg's product nd I assure you you'll never use any other product except mg's product✅_*
*_Mg's will gv you the best out of all_*

*_With mg's product ur skin is 💯 clear,fresh,smooth nd ur skin will absolutely glow all day💃_*
*_We have herbal whitening black soap now nd beauty set available_*
*_Nd both the soap nd the beauty set is for all skin type everyone can use it🤗_*
*_Just gv it a try now nd see wonders✅_*

Chat:08062991549
Call:08064532391
Soap price:3k
set:11k

Follow us on
Instagram@glow_with_mgs
Facebook:mg's skincare

*_Nd guess wht🦻_*

*Duk Wanda zesiya Kaya daga yau Alhamis 30-9-21 zuwa Nanda 5days that is ranar talata there will be 20% off discount a soap nd the set😍so what are you guys waiting for hurry nd grab urs💃 now is the time to glow🧖‍♀️*
*Pamper ur skin🦵*
*Shine like a bride 👰*
*be part of the glow* *team karkubari abaku lbr*

Just chat 08062991549 to plc ur orders😘



Do not forget to follow us👆
Like nd comment pls dearies😘
Patronize us🙏
mg's always serve you the best✅❤️
______________________________



*_BAYAN SATI BIYU_*



karfe biyu na rana suka fito daga aji,sauri take tana Allah Allah ta isa daki ta cire kayan jikinta ta samu ta watsa ruwa saboda zafi da rana,tuni ruwan sama ya fara samuwa a wasu garuruwan kamar legos abuja da sauransu,ya zuwa sannan kano da kaduna suma suna saka ran samun nasu ruwan saman na farko.


Tana tafe tana qiyastawa a ranta,a qalla wannan satin tanason taje gida weakend,don tunda ta dawo bataje din ba,saboda kuma raguwar karatu da fara shirye shiryen jarabawa tana tunanin zata dauki kwana goma kafin ta dawo,don yanzu sam ba kasafai take jin dadin zama tare dasu hindatu ba,takatsantsan take,batason wata matsalar ta sake kunno kai,saidai duk da haka bata fasa gaya musu gaskiya ba,kuma alhmdlh tana ganin hasken hakan,don da yawa daga dabi'un da basu daukesu a bakin komai ba a baya zuwa yanzu babu mafi yawa daga cikinsu.


Tana gab da shiga dakinsun wayarta da bata jima da kunnata ba ta dauki tsuwwa,saita dauko tana duba me kiran,ya shamsu ne,tadan ja tsaki tana murmushi,tana rayawa a ranta wala'alla ya kirata ne kawai ya tsokaneta ya kuma cakar da ita
"Sai matar yaya" ya fada yana dariya,shida musty kusan sun soma sauya mata suna,tun tana bala'i harta gane ma zugasu takeyi
"Cima zaune....ya akayi?"
"Hajja....ita tasa na kiraki,kuma sai an biyani kudin katin dana qona"
"Karka damu,an gaya maka mu fuqara'u ne irinka?"
"Ni nasan kun girmi wajen....matar aliyyu dabo ce fa.....muma aci gaba da yi mana addu'a....ya haidar ya mana alqawari,upper dinmu tana nan zuwa hannu"
"Kaga...ka gayan saqon hajja ya shamsu koka qona katinka a bati wallahi"
"Naga alama kin soma rainamu nida musty tunda aka daura miki igiyar auren ya zaki....to hajja tace ta kasa samunki,ki shirya nan da minti ashirin ina hanya,zan daukeki nakai mata ke airport"
"Airport kuma?....me hajja keyi a can?"
"Kinga idan kinje kyaji,nidai aikina zanyi"
"Shikenan....saika qaraso" ta fada tana kashe kiran,sannan ta tura qofar dakin nasu ta shiga.


Hindatu ta samu ta zaune gefan gado riqe da plate tana cin abinci,daga ita sai vest da zanin atampha,da alama itama bata jima sa shigowa ba,zafi ya haukatata,sai jannat dake zaune a qasa ita kuma tana shan lemo.


Tana aje jakarta tana musu sannu gami da zare mayafinta,sannan ta soma qoqarin canza kayan jikinta zuwa na wanka,hindatu ta dubeta
"Ga abincinki fa..."
"Ai hindu inajin saina dawo zanci,yanzu ya shamsu yakirani hajja ke nemana wai kuma a airport...ko lafiya" hindun nakai lomar abinci bakinta ta amsa masa
"Lafiya mana,dadai asibiti akace shine zaki tsammaci ba qalau ba"
"Hakane" ta fadi tana sanya hijabinta gami da daukar shower gel dinta ta nufi bandaki.


A gurguje ta shirya cikin atamfa riga da skert da sukayi matuqar yi mata kyau da amsar jikinta,tana fesa turare kiran shamsu ya shigo
"Ki sauri don Allah,hajja nata azalzalata fa"
"Am coming" ta fada tana jefa wayar a jakarta gami da qarasa daura agogon hannunta,ta zura takalminta tana rataya jakarta hindatu tace
"Wannan kwalliyar kyanta zakin maza aka yiwa ita,bakiga yadda kwalliyar ta amsheki ba,sai yaushe kenan?"harara ta jefa mata tana gyara eye glasses dinta wanda ta soma amfani dashi kwanan nan
"To bashi aka yiwa ba sai yaya?,Idan na dade awa uku,shi daya kaini shi zai dawo dani,saboda jibi zan wuce gida,ban kuma gama shirya kayana ba,zanje dasu gida na canza wasu"dariya tayi
"Ai shikenan,Allah ya hadaku a hanya ya dauke abarsa inga ta tsiya,any way.......saikin dawo" inji jannat
"Ki gaida hajja" hindatu ta fada ita kuma tana dariyar maganar jannat wadda zahra keta aikawa saqon harara
"To zataji" ta fada tana fita da dan hanzari,don tasan halin ya shamsun da shegen qorafi.


Suna tafe a mota suna taba hira,duk da yawanci duk tsokana ce yake mata kamar yadda ya saba,kusan haka halinsa yake saidai idan ba'a hadu ba,ba yadda batayi dashi ya gaya mata meke faruwa ba yace shima bai sani ba,yana gida aka bashi wannan umarni,idan taje ta gani,sai tayi shuru kawai tana dan nazari a zuciyarta.


Babu jimawa suka iso filin sauka da tashin jiragen sama dake garin namu na kanon dabo,kai tsaye ya mata jagora tana biye dashi har zuwa inda yace mata hajjan nacan a zaune.


Tun daga nesa ta hangi hajjan,gefanta mama ce da umma matar abba yusuf,daga daya side din kuma abba babba ne da abban tsakiya,gabanta ne yadan fadi kadan,ta ambaci sunan Allah a ranta,sannan ta qarfafawa kanta gwiwa ta isa inda suke.


A ladabce ta gaida kowa idanunta na karantar fuskarsu,babu alamun tashin hankali tattare dasu,saima farinciki data karanto kan fuskar kowannensu,da alamu kuwa tafiya ce ta kamasu,don akwai travelling bag tare dasu,ta kasa tambayar kowa har sai data zauna kusa da hajjan tata
"Hajja....sai ina kuma haka?,ko bana anyi kira?,Allah yayi za'a koma umra?" Ta fada cikin sigar tsokana,baki tadan tabe
"A'ah fa....duk da itama umarar muna saka rai nan ba da dadewa in sha Allahu....amma yanzu dai yayanku ne bikin qarin girmansu ya tashi.....shine ya aiko mana da tikiti zamu sameshi can abujan" ta gane sarai kan wa take magana,saita dan dauke kai cikin sigar bagarar da zancan tace
"Shine takanas kikasa aka dauko miki ni,yanzu hajja ba zamu iya yin sallama ta waya ba?"
"Sallama dawa?,ai dake za'a tafi,kema na siya miki naki tikitin,tafiya kawai ta rage miki" da sauri ta dawo da dubanta ga hajjan
"Tafiya kuma ina?"
"Au....bakiji duka bayanan dana miki ba dazu....to can abuja inda za'ayi bikin".


Wani gumi ne ya yanko mata ta tsakiyar bayanta,wai me yasa hajja keson ta dinga yarfata ne,banda yarfawa tsakani da Allah kawai sai ta jata gayyar sodi haka akeyi?,yanzu tana magana kuma sai cibi ya zama qari,gashi basu kadai bane a wajen,akwai mama,wanda tsakani da Allah tana jin nauyinta,don tsaf hajjan zata iya mata tarere ta barta da kunya,amma saita yanke bari ta gwada tata dabarar
"Banda abun hajja....haka ake tafiya gaba gadi babu shiri babu sanarwa?" Sheqeqe hajjan ta kalleta,da alamu babu nasara a zancan zahran
"Wanne shiri kuma?,duk wani shiri kwa yishi tare da mijinki....idan kuma ta kayan sawa ne gasu nan,takanas na kira ilhama ta hada miki duk abinda tasan ya kamata,sai kuma me?" Shuru zahra tayi tana duban 'yar trolly dinta qaramar wadda takan dauka lokaci zuwa lokaci,cikin ranta tana furta innalillahi wa'inna ilaihi raji'un,daga sannan bata sake magana ba,sai kawai taja bakinta ta tsuke,illa wayarta data ciro ta turawa hindu text na cewa ba zata dawo a yau ba,ta kula mata da lamarinta koda wani abun zai taso daga gobe zuwa jibi ta shaida mata,daga haka ma saita kashe wayar gaba daya ta zubawa sarautar Allah idanu,gami da hasashen yadda komai zai wakana,itadai tasan basa hada inuwa daya da haidar,amma ta qarfi da yaji alo tsiya alo danja hajja ta kafe sai sun jiqa kanwa guda dashi,ita sam bata qaunar wannan girman kan nashi da ji da kan nasa kamar wani mace,macen ma saraki.


'Yar kallo kawai zahra ta koma tun daga shigarsu jirgi zuwa saukarsu,tsoron ma da akace akanji a hawa jirgi karon farko ita bai wani dameta ba,saboda inda zatan yafi komai damunta a ranta,ji take kamar ta rufe ido ta bude ta ganta a makaranta.



Suna sauka tun cikin airport din abujan aka taresu,wani matashi sanye da kakin soja ya musu jagora zuwa wata galleliyar sabuwar mota,wanda kallo daya zaka mata kasan cewa sabuwa ce da gaske,shi ya bude musu dukka suka shiga ya shigar da kayansu booth sannan shima ya shiga.


Gaishesu ya soma yi da tattaciyar hausarsa pure bisa dukka alamu dan arewa ne bahaushe,yanayin girmamawarsa garesu ke nuna yasan kosu din su waye a wajen aliyyun,saida suka gama gaisawa sannan ta yada motar suka fice,yayin da kunnuwan zahra ke biye dasu,tana jin yadda suke hirarsu,abba babba na nuna musu wasu guraren da ya sani cikin abujar idan sunzo wucewa ta wajen.



Tafiyar wajen minti talatin da uku ta sadasu da unguwar da suka nufa,unguwa ce dake cike da tsari da gine gine masu ban sha'awa,a hankali driver din yace
"Oga ya bada umarnin a saukeku a sabon gidansa,akwai duk abunda kuke da buqata,wani uzuri ya riqeshi amma nan bada jimawa ba zai iso ya riskeku a gidan"
"To ba matsala,ya kirani bayan mun sauka ai,munyi magana dashi" cewar abban tsakiya,kai matashin ke gyadawa sanda yake yunqurin tura motar tasu cikin wani madaidaicin gida dake dauke da matsakaicin qawataccen gate bayan mai tsaron gate din shima dake sanye da kaki ya bude musu gate din.


Wata madaidaiciyar rumfar adana motoci ya shiga ya faka motar kusa da wata mota dake a rufe ruf,da alama ita dinma sabuwace,zaka gane hakan kota iya tayoyinta.


"Ma sha Allah....ma sha Allah" kawai kowa ke fada,saboda yadda gidan ya tsaru ya kuma qawatu,duk da cewa ba wani qaton gida bane,saidai yana da yalwa dai dai misali,akwai haraba madaidaiciya wadda ke dauke da wata rumfa ta bunu da wasu irin kujeru qasanta da teburi saboda dora kofuna da lemuka,akwai balcony mai kyau da wasunirin kujeru guda hudu da wani irin qarfe da aka zube a cikinsa bayabga furanni wanda ta cikinsa balcony din zaka isa falon gidan,wanda ya dauki set din kujeru biyu sai dining area,daga daya bangaren akwai gajeran corridor wanda ke dauke da dakunan bacci guda biyu da bandaki a tsakiyarsu,duk da kowanne daki yana da bandaki,uwa uba kuma akwai wani spare dakin cikin falon.


Akwai ma'aikata maza guda biyu da suka tadda cikin gidan,daya shine kukun sa,daya kuma me gyara falon gidan da bandakuna,banda bedrooms dinsa.


Dakin dake cikin balcony din nan aka budewa su hajja,yayin dasu abba babba kuma aka bude musu na ainihin falon.


"Ma sha Allah....gaskiya ne,wannan gida saidai fatan alheri,Allah yasa an shiga a sa'a" umma ta fada tana kallon kowanne bango na dakin da aka qawata da wasu fitilu da fenti mai kyau,ga kuma qyallin sabunta na haska dakin ya qara masa wani haske me kyau.


Tunda ta samu gefan qatuwar katifar dake yashe a dakin bata ce uffan ba,duk hirar da suke tayi a tsakaninsu nata idanu,abu daya tayi shine ta shiga tayi alwala bayan sunyi tasu,hajja kuma ta hada da watsa ruwa,don ita jin zafi gareta.


Duban zahra tayi sanda take fitowa daga bandakin,tana ware mayafinta zata lullube jikinta don yin sallah
"Banga alamun wanka a tare dake ba,ko kina nufin yadda muka taho a haka zauna" sosai hajjan ta bata kunya,ta saci kallon umma dake sallah kana ta maida dubanta ga hajjan tana kyabe fuska qasa qasa tana mata qorafi
"Au....yoni Allah na tuba hadiza baquwata ce?,ki koma kiyi wanka kinjiko?"sauri tayi kawai ta tada sallah,don tasan idan ba hakan tayi ba hajjan ba zata qyaleta ba.


Kafin ta gama sallar umma tuni ta gama,saita tattara abun sallar ta fita daga dakin,da alama itama nauyi takeji,hakan ya baiwa hajjan damar tsigale zahra tasss,saidai tayi kunnen uwar shegu da hajjan,charting dinta ma take abunta,harta gaji ta haqura.


Kafin sauran suyi wanka su huta tuni an cika teburin gidan da nau'in abinci kala kala,cikin girmamawa da gurbatattar hausarsa yake shaida musu an gama komai,su abincin ke jira
"To....to sannu da qoqari yaro kaji" abba babba ya fada,sai yayi murmushi cikin girmamawa yace babu komai.


Ganin an kusa sallar la'asar sai suka yanke suyi sallah dukkansu a jam'i sannan su zauna cin abincin,don basuga masallaci nan kusa ba,haka kuwa akayi,abban tsakiya ya jasu sallar,suka idar sannan suka hallara kan dining din,ita dai hajja mita ta soma kan ba zataci abinci kan teburi ba,don haka zahra ta diba mata nata ta shimfida mata ledar cin abinci a qasa sannan ta aje mata
"Yauwa,yanzu naji batu....ke ya kika samu waje kika zauna?" Tace da zahra wadda ta koma saman kujera ta zauna maimakon ta koma wajen cin abincin
"Na qoshi" ta amsa mata ciki ciki
"Ungo nan" ta fada tana watsa mata daquwa
"Sauko kici tun banci mutuncinki ba" soma saukowa tayi dai dai sanda qarar bude gate din gidan ta riskesu,ba jimawa saiga biyu cikin yaran gidan suna shigowa da kayayyakin amfani na gida suna jibgewa,suna kammalawa muryar sallamarshi ta cika falon,hakan ya sanya zahra janye yatsunta daga abincin da take ci din,saboda ji take kamar zai mata kallon makwadaiciya,saboda zuwa gayyar sodin da hajja ta jawo mata,bugu da qari ta tilasta mata cin abincin gidansa,wanda ita sam bataso hakan ba.


Saidai yadda suka gaisa a tsaitsaye ma ya nuna akan uzuri yake,don ko nuna ya ganta cikin falon bata ga alamunsa ba akan fuskarsa,ya tambayesu zai koma sai wajen dare zai sake shigowa,yanzu ma ya tsaida wasu abubuwanne yazo yaga isowarsu lafiya,idan da abunda suke buqata suyi magana,addu'a sukayi masa da fatan alkhairi ya miqe yana musu sallama cikin kuzari da hanzari irin na namijin soja,taku bibbiyu ya juya ya fice daga falon.


Zahra ita ta gyara komai da suka bata,su abba babba suka buqaci fita gari wajen wasu daga cikin mutanensu da suke harka dasu,saiga driver ya taso da hanzari,motar da aka kawosu cikin gidan ya bude musu yace su shiga,oga yace duk inda zasu ya kaisu,hakan ya musu dadi da kuma sauqi.


Cikin gida suma hirarsu suke abunsu,zahra ce kawai ta shiga daki ta kwanta saboda gajiyar da takeji a jikinta,bata farka ba sai ana gab da sallar magariba,koda ta leqa falo duka suna can sun daura alwalar salla,da alama su abban ma sun dawo,ga mamakinta sai taga ya musty,idanu ta fiddo
"Kai,yaushe kazo?"
"Sanda kikayi nisa a duniyar bacci,yarinya taji hadadden gida" ya amsa yana dariya gami da sauke hannun rigarsa dake tattare,shima da alama alwala ya daura,da idanu ta masa nuni da mama dake wajen,dariyarsa ya gumtse yadan matso inda take
"Yaushe aka fara kunyar mama wai haka?,anya kuwa?,ba'a fara yi da danta ba?" Tabbas da zata iya duka zata kai masa,to amma saboda ba halin hakan saita bishi da harara shi kuma ya fice yana dariya,yayin data koma ciki itama ta soma haramar sallar.


Sai bayan sallar isha'i sannan ta shiga tayi wanka,ta dawo ta jawo jakar kayanta ta buda.


Da ɗaya da ɗaya take duba kayan da ilham ta hada mata,gaba daya haushin duniya ya cikata,tabbas da ilham na kusa saita mammaketa,gaba daya riga da skert dinta wanda bata sakasu saita dora after dress akai,sannan babu bra ko pant a ciki sai qwara daya,gefe daya taje ta debo mata kayan bacci cikin wadanda ta fara tarawa a baya,sanda take saka ran aurenta tare da 'yan uwanta
"Lallai yarinyar nan ta rainani....Allah saita raina kanta,bari muje gida" ta fada tana cire daya daga cikin kayan baccin doguwar riga ce wadda kadan ya rage ta isa idon sahunta,ita kadaice me dama dama,saita dauki aron hijabi daya cikin hijaban hajja ta zumbula bayan ta shafe jikinta da turaruka kamar yadda ta saba duk sanda zatayi shirin bacci.


Falo ta dawo ta iskesu suna hira,mama da umma su suka fara tashi,dama tuni abba babba suna waje,da suka shigo kuma sai suka musu sallama,don abba babba yace ya kama musu masauki acan zasu kwana,ya rage a falon daga hajja sai zahra sai musty,sai a sannan zahran ta samu sukunin zubo abinci ta zauna tanaci suna kwasar dariya,saboda wata drama da ake haskawa,hajja ta dage saita fahinta abinda akeyi,musty na fassara mata yana hadawa da yi mata tsiya suna kwasar dariya abunsu harta gama,ta maida farantin ta dawo sukaci gaba da hirarsu.


Qarfe goma na dare aka sake bude gate din mota ta shigo,zahra dake zaune daura hajja sai taji tasha jinin jikinta,dukkansu sunji shigowar motar,saboda haka babu damar tace zata waske ta tashi,tilas taci gaba da zama a wajen,har zuwa sanda muryarsa ta fara ratso falon yana amsa waya kafin isowar gangar jikinsa,hannunsa daya dafe da waya,dayar kuma baqar leda ce dauke da tambarin wani wajen saida abinciccika.


End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login