Showing 72001 words to 75000 words out of 113608 words

Chapter 25 - TSINTAR_AYA

Start ads

09 Aug 2025

692

Middle Ads

ya zame baya, seda wata mota ta tashi bugun nashi sannan ya saisaita kansa, me napep kuwa zuwa yayi da azama ya wuceshi sunata sauri tamkar zasu tashi sama wannan ne ya k'arawa abun k'aimi a zuciyar sa yace lallai seyaga inda suka dosa!

      Sanda yabi ta d'ayan layin daya ajiye motarsa yayi parking wannan motar sannan yashiga tsakanin gutter's ya tsallaka ya b'ulla ta wannan layin dayayi parking acikin motarsa ta alfarma ya sauya kayan jikin sa nanma, seda yayi branching guest house nashi yashiga ya ajiye wannan motar sannan yafita da wata motar ta k'ofar baya ya nufi masarautar sa a sukwane tamkar zakin daya shekara beci namaba! Kai tsaye part d'in khairiyya ya nufa acen ya tarar ta dawo, kallon ta yayi sosai sannan ya haska mata wayar sa, sesa ta karanta abinda yake nuna mata sannan ta kawar dakai tare da cewa

"Anguwa naje" Cikin fusata ya kuma rubuta

"Yaushe kika isa kije unguwa batare da izinina ba? Kuma unguwar wurin wa? Wa kika sani a garin? Tana gama karantawa ta kallesa

"Ajiyeni kayi ne? Kokuma kaine raina yake hannunka kaga Hammood dan Allah ka shafawa lafiya ta lafiya, abinda ya isheni ya isheni" Fusata yanzu kam yayi ya matso kusa da ita a harzuk'e ita kanta tayi mamakin yanayin sa, tunda suke yaune rana ta farko data hango masifa haka a idansa, matseta yayi har jikin bango amma bece mata ci kanki ba kawai ya tsatsareta da manya manyan idanuwan sane dasuka sauya launi, runtse idanta tayi cike da tsoro, she really need a shoulder to cry on, mesa yake mata fad'a, gaba d'aya mahaifiyarta ta janyo mata mummunan tabon daze illata rayuwarta, menene amfanin wannan mugun aikin data aikata, akan me Bilal zeje wannan matakin a tonawa mahaifiyarta a siri, zuwa wannan lokacin gaba d'aya kukan datakeso tayi tun d'azu bezoba se yanzu ya wanke fuskarta dukda idanta a rufe yake, duk yanda taso ta had'iye kukan nata seda yazo da iyakacin k'arfin sa, kukan ta saka sosai wanda ya sanya yayi kasake kawai yana kallon ta cikin mamaki, maganar sace ta b'ata mata rai kome? Metakeyi tare dasu Baba Usman? Me suka ce mata? Is she alright? Janyota yayi zuwa jikinsa ya soma patting bayanta a hankali ziciyar sa tana harbawa ya tabbatar akwai wani abun dasuke shiryawa tare da khairiyya kuma yanzu ne suke so suyi trapping nata tun ita batasan asalin halayyar suba, meke shirin tasowa kuma, be hanata kukanba seda tayi me isarta sannan ya kwantar da ita kawa yabar d'akin dan kuwa hankalin sa yanakan waccen yarinyar dayabi bayan 'yan keke napep yaga sun kaita unguwar Shiyar fada cikin tsohon guest house d'in me martaba dayake k'ark'ashin kulawar Baba Usman a yanxu, mecece alak'ar dake tsakanin Baba Usman da khairiyya, mesa kuma ya sanya aka d'auke matar mutane zuwa shiyar fada danya tabbatar cewar shine ya sanya aka d'auketa, to Amma ina hafsa taje? Metajeyi a wannan gidan? Kai tsaye part d'in Bahar ya nufa dan yasan a k'a'ida yau akace zata tare agidan ta, koda yaje ya binciki bahar batanan, driver dasuka fita atare ya tambaya ita inda ya tabbatar masa da cewar ga unguwan daya kaita kuma tace k'arfe shida ya koma ya d'auketa, yaje ance tafita tin yamma bata dawo ba, yajira har bayan magrib bata dawo ba wannan ya sanya ya taho a tunanin sa ta koma gida! Kai tsaye gidan Hammood ya nufa inda yaje ya tarar da Baba me gadi dan tuni ya dawowa aikin sa agidan, seda ya waiga baya yaga ba kowa sannan yace

"Ka shiga ciki Baba dan Allah ka sanar wai Hafsat ta fito inji mijinta zasuje gida" Jin wannan sak'on ya tilastawa Momy fotowa daga cikin gidan tazo suka gaisa da Hammood inda kallo d'aya yayi mata k'irjinsa ya doka da kamanceceniyar dake tsakanin ta da khairiyya, gayar da ita yayi sannan ya sake maimita abinda ya sanarwa Baba me gadi, da mamaki tace tana kallon sa

"Hafsa a charge tabar wayarta kuma k'arfe shida tacemun zata dawo,bansan inda ta tafi ba bankuma san meya tsareta a inda taje ba, ni kaina na shiga damuwa sosai" Nisawa yayi sannan yace

"Ba damuwa nagode sosai, inaga tayi yamma ne ta wuce gida" Cikin rashin kuzari tace

"Ze iya yiyuwa hakan ne, zekuma iya yiyuwa wani abin ne, koma menene dai i will keep u updated idan tazo idan ma batazo d'inba" Godiya yamata amma be karbi lambar wayarta ba a hanzarce ya juya shitar fada batare da wani tunani na biyu ba, ko shakka bayayi wannan matar Hafsa ce, she can go to any extend akan abinda takeso, yayi iyakar tunanin dazeyi akanta ya gagara gane wa tskewa aiki akansa, kome menene wannan al'amarin tabbas babbane a wurinta indai har zata iya amfani da wannan hanyar me cike da hatsarin gaske wurin cimma burin ta! Yana shiga gate ya kira masu gadin gaba d'aya da masu kula da shuke shuken furannin gidan gaba d'ayansu wayoyin hannunsu yanfara karb'a sannan yace yana kallon me gadin

"Its been long i cm here show me in" Ranka ya dad'e duk datti ga k'ura ba shiga ake ba" kallon masifa ya wurga masa kafin yace

"My friend will you do just as i say? Gyaran zaman rigarsa yayi jikinsa yana rawa sannan ya shiga gaba Hammood yabishi a baya ko ina seda suka shiga beganta ba, rik'e bakin sa yayi sannan ya juya da zummar barin gidan amma me freezer dake gefensa seta motsa kallon me gadin yayi daya gama cewa gidan duk datti ne ko ina fesfes yace

"Bani ruwa a wannan freezer nasha" Jikin me gadin yana rawa ya kuma cewa

"Ai basa amfani da ita yallab'ai sedai wancen fridge d'in" Hannu yakai ze bud'e danyaganta a kunne amma me se me gadin yayi azamar rik'o hannunsa d'agowa yayi suka kalli juna jikin me gadin dukda yanda yake mazari hakan be bashi damar sake hannun ba, jijiyar me gadin ta wuya me taken mukwana lafiya Hammood ya kalla sannan yayi wani malalacin murmushi sekuma ya daddage yakai mata wani lafiyayyen sara da gefen hannun sa, take agun me gadin ya zube a sume, shi kuwa ya bud'e deep freezer d'inda har lokacin bata dena motsi ba, da sauri yaja baya ganin mitum ga dakakken yaji a barbad'a ako ina shi kanshi yana bud'ewa sanyin k'ank'arewar datayi tare da tashin hayak'in yaji ya daki hancin sa abinda yayi saurin sanyashi atushawa, seda ya matsa sosai sannan ya kuma dubawa tabbas yaribyar d'azu ce ko mata zece be gane komai ba se kayan jikin ta, da azama ya cicib'ota, ab daire hannunta da k'afafuwanta a had'e ankuma tura mata wani abu a baki, abin bakin nata ya soma zarewa kafin take ta soma atishawa tana ruwan k'walla sannan ya warware hannunta da k'afa be b'ata lokaci ba yabar gidan baya ya sakata a mota, abinda yafi bashi mamaki shine dayawa daga cikin yaran daya wurga wayoyin su a mota basa nan, sun gudu kenan kome? Asibiti ya nufa da ita yana k'are mata kallo, ko shakka bayayi yanayin yanda zuciyar sa ke bugawa akan Hafsat yasan yanxu kam itace, tome ya kaita? Meye nata na zuwa ta wannan matakin, sanda suka asibiti tama fita a hayyacin ta, k'afafunta ya kalla da hannayenta atake ya k'ara tabbatar da zargin sa akan Hafsat ce, dake private hospital kuma sun masa farin sani hakan ya sanya dashi suka shiga bata taimakon gaggawa, gaba d'aya sanyin k'ank'ara ya gama da lafiyar ta, ta kwashe sama da sa'o'i hud'u acikin freezer me azabar sanyi da yattafin yajin barkono, mamaki yake yanda aketa yaga kayan dake jikinta da almakashi se yagawa ake basa k'arewa lallai yarinyar nan batada bankali, meya kaita? Haka har ta dawo iya pant be da bra ajikin ta, kallon likitan yayi yana yamutsa fuska kafin tace

"Dr. Ba wani privacy cover her body please" kallon sa likitan yayi

"Yanzu zamu rufe ta karka damu" yana nan tsaue har suka sanya wani blue zani suka rufe ta, anan suka shiga dudduba ta kayan data tulawa jikinta sun taimaka wurin hanawa sanyin freezer shiga jikinta sosai amma idanta da mak'oshinta da komai ma ya gama shiga azabar sanyin da turirin yajin wannan ya sanya gaba d'aya wata azababbiyar mura ta taso mata ta lokaci guda tasamu taimako dai, an shafa mata mayukan rage azaba sabida zafin d'aurin datasha sannan akayi mata abinda ya dace tukunna sukace bazasu sallameta ba se zuwa safiya idan sunga dacewar hakan shima!

Wayar sa ya zaro ya kira Uncle Jay wanda yana d'auka yace dashi

"Mesa zaka sanya ta irin wannan aikin? Akan me duk a cikin mutane masu wayau da girman shekaru se ita kad'ai" Nisawa Uncle Jay yayi danyaso hana faruwar abinda ya samu hafsat amma besan ya akayi sukayi outsmarting nashi ba akanta

"Hammood magana ce wannan me tsayi bazatayiyu a phone ba ka bari idan mun had'u" Cikin takaici yace

"Your crossing the line Uncle Jay, she's my wife remember? Yaya zaka sakata aikin dani mijinta na kasayi? Kasan me suka mata yanzu? Nisawa Uncle Jay yayi cikin jimami

"I hope she's now safe" Tsaki gajere Hammood yayi kafin yace

"She's not and please count her out of this bullsh****t" Nisawa Jay yayi

"Ka saurareni mana Mood bawai da wani niyyan na sakata ba kawai naga ka d'aura zargi ne akanta shine nakeso nayi diggin meke k'asa ta b'angaren ta, am just trying to proove her innocence"

"What ever" ya furta sannan ya kashe wayar sa ya juya yana kallon ta, kowama indai akace sarauta ne kowa kansa hayak'i yake, meye wannan 'yar tatsutsuwar ta sani, wama yasan kalan shirmen dazata kwab'a idan ba sonkai ba kawai aikin da manya ma basuyi ba se ita taje tayi. Wayar sace ya kuma yin k'ara ya d'akko Uncle jay ne bayaso ya masa rashin kunya dan harga Allah ya shafe shekaru yana masa biyayya, ya gaza gane inda ya dosa akan harkar nan, me suka isa su masa idan sun gane yana maganar daze takurashi ya hanashi yi, lokaci yayi daze yiwa tufkar hanci tunda har aka soma had'awa da Hafsat abin ya zama jin dad'i ma kenan, zama yayi akusa da ita fatar fuskarta dake fara tayi kaman jikin gawa sabida sanyi daya dazk'arar da jini yayi bak'i, yanzu kam bacci take tana sauke numfashi a hankali, wacece Hafsat? Menene ainahin musababbin zuwanta a rayuwar sa, ya sani Hafsat bata kunya ko kad'an tanada tsiwa da sakin magaba yanda duk taso amma she's very honest, sam bata tsoron fad'ar gaskiyar komai d'acin ta, mesa yake zargin ta amma hakan baya rasa nasaba dak'in kareshi datayi da zargin da ake masa akanta tun farko, wayarsace ta kuma k'ara a karo na uku kuma duk Uncle Jay ne, d'aga wayar yayi yanxu kam amma beyi magana ba, Uncle Jay cikin mutuwar jiki yace

"Bani bane na sakata wannan aikin, Bahar ce da Maminka, naso in d'auki wannan blame d'in amma banaso yarda da amincin dake tsakanina dakai ya watse akan hakan, nayi k'ok'arin nusar dasu kuskuren yin hakan amma Mami ta kafe akan Hafsat zata iya tono sirrin b'oye ni me zanyi? Cikin tsananin b'acin rai yace

"Uncle daka sanar dani akan hakan, tasha wuya a hannuna, duka, mari,tsangwama dik akan ina zarginta, dakun sanar dani sena taimake ta" Yana gyaran murya yace "Hammood baka taimaki kanka ba akan mak'iyan ka kake tsammanin zaka taimaki macen dake shirin taimakon ka, kai bazaka iyaba ai" Tunawa yayi da kalmomin ta "Ur a coward!! Tabbas abinda kowa ke kallon sa kenan ciki hadda uncle jay

"But Uncle kaida kake cikin su meka tsinana? All these years ka taimakeni ne? Cikin jin zafin sa yace

"Nida kai duk d'ayane bazamu iya yin komai ba akan wannan abun" Dafe kansa yayi

"Fine then ku barsu su kasheni saime, amma dai wannan 'yar alhakin a zareta a wannan maganar zan gayawa ummi, kuma ka sanar a masarauta a taramun duk manyan fada daduk wanda ya dace ya sani inada magana da dukkansu gobe" cikin sauri yace

"Me kake shirin yi?

"Magana" ya bashi amsa a tak'aice

"Wace iri? A masife yace

"Da baki uncle irin wacce nakeyi dakai yanzu a wayar nan, gobe iwar haka kowa a duniyar Daulatul dinar ze tabbatar wa kansa harshen Hammood ba tattaura bane yana motsawa" Nisawa Jay yayi

"Son please calm down, yanzu gayamun me sukawa Hafsatun" kallon fuskarta yayi sabban yace

"Kasheta sukayi" yana kaiwa nan ya kashe wayar sa ya kira Barra, tana d'agawa yace

"Ki gayawa Bahar Hafsat tana wurina karta nemeta a yau, har mami ma"

"Kawun kane yace ka somayin magana da mutane? So yayi ya gaya mata magana amma kuma seya fasa kawai yace

"Bashi bane kamawa tayi"

"Daka aikon message kawai ai" Bece komai ba ya datse kiran yaje ya kuma rik'e hannun Hafsat yana mata wani kallon dabesan ma'anar saba.

****************
Aminulla kuwa yayita neman wancen layin dasuke waya amma be samu ba, wannan ya sanya gaba d'aya hankalin sa ta tashi, gashi dai komai datace yayi ya kammala amma baya samun wayarta, da wannan ya yanke shawarar kawai ya adana mata sirrinta har sanda tazo wannan itace amana, koda yake har yanzu hoton yarinyar da masu napep suka d'auke a bakin hotel d'in suna masa gizo, seyake ga kamar itace tayi basaja...........

Asaman kujera ya kwana yana rik'e da hannun ta, babu kiran da khairiyya batai masa dole ta hak'ura sabida dama tunda suka dawo basa kwana wuri d'aya sedai yakan zo idan yana buk'atar hakk'in sa daganan ya koma, ta masa magana yace tradition d'in kenan, tarasa gane wanne mahaukacin tradition ne wannan daze nesantata da mijinta, wuraren k'arfe hud'u hafsat ta farka da sambatun ta

"Karku sakani a freezer, sanyi baya bani lafiya kuyi hak'uri" daganan ta tuna sanda aka tura mata wani abu a baki kawai seta mik'e zaune a zabure, da sauri ya farka ya rik'eta dama be kashe fitilan d'akin ba, waige waige ta somayi kafin da azama taja baya a tana rirrike bargon daya rufeta dashi, matsawa yayi har saman gadon ya k'ara rik'ota

"Hafsah" ya furta yaba d'aura kanta asaman k'irjin sa

"Calm down ur safe now, ina tare dake ba abinda ze sameki" kallon sa tayi tana k'ok'arin yin magana attishawa ya taso mata gaba d'aya tayi ajere ajere yakai so goma sannan ta nemi langwab'ar dakai cikeda tsoro

"Wurin Bahar zaka kaini, sunce kasheni zasuyi, kuma ina abubuwana, banga wayana bafa, ina mayafina? Kallon ta yake

"Keda bakida lafiya me zakiyi da wad'annan abubuwan? Rik'o hannun sa tayi

"Wannan ne lokacin danake gaf da cimawa Bahar burinta, ka taimakeni ka baki wayana da mayafina akwai abu me muhimmanci a bayan mayafin nan nawa dan Allah karka hanani" Tausayinta yaji wato shi takeso ta k'watowa 'yancin sa amma yaketa shirme akaron banza, rungumarta sosai yayi sannan yace

"Hafsat calm down naga jakar hannunki a inda na d'akkoki, nakuma d'auka miki, wayarki yana ciki, but banga mayafin kiba nidai" Tana dube dube tace "That is the most important thing ai, shi mayafin sa abayan sa akwai abun amfani ka bani wayar zan kira Aminu" Agogon wayarsa ya kalla

"K'arfe hud'u da kwata na asuba, bazan bari ki kira kowaba a wannan daren, ki bari gari ya waye, kanki yana ciwone? Kokuma kinajin yunwa" kwantar da kanta tayi akan k'irjinsa

"Menake anan to?

"Ki dena yawan surutu bakiji muryanki ba,mura ya kamaki da yawa" Wani yanayi yakeji mara misaltuwa, gaba d'aya jikinsa se k'aryata sa yake a wannan yanayin, jan jikinta tafarayi tanaso ta raba jikinta da nasa ta kula so yake ya soma sha'awar zama awurin, da sauri ya ya sake maidata k'irjinsa

"Hafsah please, stay still" Kasa yi masa musu tayi, why is he so cool today?he's acting so wired, is this real or is she dreaming? Ta tambayi kanta, lafewa tayi na wani lokaci seda yagaji dan kansa yace

"Mesa kika zab'i yin wannan aikin sayar daran? Am not even worth it, mesa zakimun irin wannan sadaukarwar" Janye kanta tayi suka kalli juna sannan tace

"Wanne irin aiki kake magana kenan? Ni in sayar daraina akanka? EHM Allah ya kiyaye" Murmushi yayi, she's still rude kodatake fama da kanta

"Sanda Bahar da Mamina suka sakaki mesa ke baki gaya munba" Yanzukam gaba d'aya tureshi tayi daga jikinta

"Ni bansan abinda kake magana akai ba" Allah sarki, wato dai bazata fallasa sirrin data d'aukarwa iyayen saba akan taimakon sa, lallai yanzu ya dace ya shirya ya d'auki d'amarar sanin wacece Hafsat donya saka mata da mafificin abinda tamar dukda bawai 100% zuciyarsa ta gama nutsuwa da itaba, mik'ewa yayi

"Zanje gida a babban masallacin fada nakeso inyi salla tare da sarki" batace masa komai ba harya wuce yabar d'akin, wayarta ta janyo akan gadon asibitin datake kwance bata fasa aikata abinda tasa agababa!!
Ganin ya fita yabar cikin d'akin ya sanya wad'anda dama fitarsa suke jira sukayi hanyar waje domin dawowa tare da wad'ansa ake jiran suzo domin gamawa da rayuwar Hafsat gaba d'aya kafin shima ya koma fad'a ya tarar da ajalinsa, tunda yaji sirrinsu bazasu barshi ya kara rayuwar koda 1 second bane har itama........Abin mamaki yau a babban masallacin fada Hammood ne ya bada sallah dakansa, inda mutane da dama sun ganshi yana bada sallan, be fitoba seda haske ya bud'e ko ina lokacin ya gama azkhar d'insa, tare suka jeru da muhseen daya masa dirar mikiya sabida yanayin dayaji muryan sa jiya dasuke waya wuraren 12 na dare, suna tsakiya da tafiya kawai sautin bindiga sukaji wanda atake suka zube k'asa atare shida muhseen, mutanen dasuke wurin kuwa wasu suma tsere wasu kuwa sukayo kan muhseen da kuma Hammood ciki kuwa hadda sarki, kafin wani yunk'uri se tashin wani harsashi sukaji atake sarki ya zube awurin shima!!!

*Readers kumun uzuri, yara nata fama wlh musamman Nu'aiym, ga kuma yanayin abubuwa, book yana gangarewa zamuce baze wuce mu 40pages dududu to mucigaba da hak'uri, wamda suka kira Nu'aiym da ayaan suna godiya sosai, nima ima godiya Allah yabar zumunci.

*Mom Nu'aiym.*


*TSINTAR AYA*  FREE BOOK

*BILLY GALADANCHI*

*SHAFI NA ASHIRIN DA HUD'U*
24.
Lokacin da Hammood ya fita gaba d'aya se hankalin Hafsat yak'i kwanciya, wanda suka mata

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login