Showing 39001 words to 42000 words out of 133328 words

Chapter 14 - BAKAR WASIKA complete

Start ads

24 Aug 2025

462

Middle Ads

manya a gobnati, amman kina ta kewaye kamar wanda bata da kowa”

“Ba haka bane, Leila na dade ina mafarkin aiki a kamfaninku Wallahi”

“Amman shi ne baki fada min ba? Haba dai Madina ina ganin kamar mun zama daya ni da ke?”

“Ai da nauyi, amman dai yanzu komai ya wuce na gode sosai zan kawo takardun anjima ko gobe Inshallah na gode sosai dear ina kaunarki”

Leila ta yi murmushi.

“Karki damu, i trust you”

“Bari na tafi kar na yi latti”

Ta fada tana daukar jakarta ta rataya, sai Leila ta rakota har gurin motarta sai da ta shiga ta bar gidan sannan Leila ta juya ta koma ciki.



BATURIYA POV.

Har ta huta ta ci abinci yayanta be dawo ba, daman idan ya fita gurin kasuwancinsa baya dawowa sai dare. Batan ta yi wanka ta fito ta tari Napep ta nufi family house dinsu.
Tana shiga cikin gidan kannenta da mahaifiyarta suka hau murna kamar su hade ta. Ko minti talati ba ta yi da zama ba, Sultan ya shigo cikin gidan da gudunsa, kanwarta ta fara tare shi ta daga shi sama yana dariya.

“Sultan kaga Mama ta dawo?”

“Tace a daina cewa Mama sai Mommy”

Ya fada da yar siriyar muryarsa yana kallon Baturiya dake zaune falon.

“Kai da wa ka zo nan?”

“Daddy yana waje”

Wani tsaki taja ta dauke kai.

“Zuwa zai yi ya fara min bakar masifar nan Ko?”

“Aa ya isa? Ai Raliya ta fada masa halin da kike ciki, ko ma haka be faru da ke ba tun da ya ga baki dawo gida ba ai ya san ba lafiya ba, dole ya daga miki kafa”

“Uhm Umma baki san halin Faruq ba, Wallahi ni da nake tare da shi kawai na san ukubar da nake sha a gidansa, zai iya zuwa a nan ya nuna babu komai sai mun koma gida ya fara min masifa”

“Bayan duk hakurin da kike da shi? Cikin yan'uwanki ke kadai ce baki dace da daki ba Rafi'a, ba mu yi zaton haka ba”

Wannan maganar da Umma tai sai ya saka Baturiya ta kara bata fuska.

“Wallahi Umma ni kadai na san azabar da nake sha a gidan Faruq, bayan yunwa ga rashin sutura da kwadayi, ga masifarsa kamar ni na dora masa talauci”

Umma ta sauke ajiyar zuciya tana kallon yarta cike da tausayawa.

“Shiyasa tun farko ni bana son auren nan na zumunci, mahaifinku ne ya dage sai an yi gashi nan ya tafi ya barki da wahala, haihuwa daya kenan nan gaba idan an tara yara me kike tunani”

“Ni ma tsorona kenan Umma, haihuwa daya, rayuwa tana ta mana haka balle nan gaba, kullum dai dai tai ta min karyar aikin zai fito amman shiru”

“Ni abun nasa har mamaki yake ba ni, wai ko dai be yi karatu mai kyau ba ne”

“Ni ina na sani, tun da ba fada zai yi ba, ni Wallahi makaranta ma nake son komawa, kar na bata nawa future na zama irinsa”

“Aiko da kin yi ma kanki abu mai kyau, sai ayi ma yayanku magana ya biya miki”

A take murmushi ya cika fuskarta.

“Da gaske Umma?”

“To miye a ciki idan ma be biya miki ba, ai ni zan biya miki”

Umma ta fi tausayin Baturiya fiye da kowa a cikin yayanta, domin ita kadai ce take auren matalauci talaucin da abun da zasu ci ma sai ya gagaresu wani lokacin. Ba wasu masu arziki ne can sosai ba sai dai suna da rufin asirin irin na yayan da suka dace da daki, domin kusan duk abun da ake ci a gidan yayyun Baturiya ne dake aure suke kawowa, sauran dawainiyar kuma babban yayansu ne yake yi, domin yana da rufin asiri irin na wanda kasuwanci yai ya aura.

“Sultan je kace Daddy ya shigo kar ya ce an barshi a waje”

Baturiya na fadi hakan Sultan din ya sauka daga kafafuwan kanwar mamansa ya nufi kofa da saurinsa, ko da ya fito Faruq na tsaye bakin karamin gate din gidan rumgume da hannayensa.

“Daddy ance ka shigo”

Faruq ya sakar masa murmushi sannan ya kama hannun dansa suka shiga cikin gidan, cike da nauyi ya shiga kasancewar baya samun riko musu komai idan zai zo, ba kamar sauran surukan ba da har mararin zuwansu ake saboda suna da rufin asiri, Baturiya ma ta sha fada masa shi kadai ne baya kawo komai idan ya zo, hakan yasa idan ba da wani babban dalilin ba baya son shiga cikin gidan duk kuwa da kasancewarsa dan'uwa, shi kansa ya san baya samun sakin fuska a gurin mahaifiyarta yadda ya kamata.
A bakin kofar falon ma tsayawa yai sai da aka matsa iso, sannan ya shiga cike da kunya ya nemi guri kusa da matarsa ya zauna bayan ya gaishe da sarakuwarsa kuma matar Kawunsa.

“Yanzu kika iso ne? Na dauka gida zaki wuce ai”

“Ko naje gida me zan yi tun da ba abinci ke akwai ba, yunwa kawai zan sha”

Juyowa yai da kyau ya fuskance ta.

“Rafi'a wannan wane irin magana ce? Idan ma kasa kike ci naga ai gidan aurenki ne”

“To karya na fada? Ni yanzu ga shi na rasa waya da sauran canjina”

“Rashin jinki ne yaja miki ai”

“Kaji ba bakar fata kawai yake min, shiyasa ai baka ma damu ka san inda nake ba sai yanzu”

Uffan be sake cewa ba ya kama hannun dansa yana wasa da shi.

“Ya kira ni ai ya tambaye ni”

cewar Raliya kanwar Baturiya. Sai mahaifiyarsu ta tashi ta nufi dakinta tana fadin.

“Allah ya kyauta”

Bayan ta wuce, Faruq ya kalli Baturiya.

“Tashi muje gida”

“Yanzu yanzu fa na shigo, sai na huta zan tafi gida”

Ta fada tana turo baki gaba tana hararsa kasa kasa.

“Rafi'a me ke damunki, sai ki rika min abu kamar ba mijiki ba, danki ne ni?”

“To idan naje gidan me zan maka? Yanzu fa na dawo ai sai ka bar ni sai na huta sannan anjima zan koma ai ban ce nan zan zauna ba”

Sanin cewar idan ya biye mata za su siyar da hali ne a gidan da ba a ganin mutunsa da kimarsa ne yasa be sake ce mata komai ba ya saki hannun Sultan ya mike tsaye.

“Raliya ki fadawa Umma na wuce”

“Okay”

Raliya ta amsa tana kallon Baturiya cike da jin haushin abun da yar'uwarta take yi a gabanta. Sai da ya fice sannan ta kalli Baturiya ta ce.

“Wallahi Rafi'a baki kyautawa, talauci ba fa ba hauka ba ne, baki san budin da Allah zai masa nan gaba ba”

Baturiya taja wani shegen tsaki.

“Ki dauki arziki ki ba shi, idan mun zauna mu kadai kin san iya abun da yake min ne? Kin san yadda yunwa take halaka mutum kuwa? Dan Allah karki kara min da wata damuwar ki bar ni na ji da wanda nake ciki”

Tana fadar hakan ta mike tsaye ta nufi dakin mahaifiyarta, Sultan ya bi bayanta.



Family house dinsu ya nufa cikin rashin jindadi, daman ta saba masa a gaban yan uwanta, yan'uwansa kam daman sun san irin zaman da suke, hakan yasa kanensa basa sha'awar zuwa gidan sai da wani babban dalili, domin bata musu tarbar arziki.
Mai achaba na sauke shi kofar gidan ya ciro kudinsa ya mika masa sannan yai sallama ya shiga cikin gidan, tun daga yanayin yadda ya ga gidan ya san ba su girka komai ba, domin murhunsu a bushe yake, a take ya ji ransa ya kara baci domin baya son ganin mahaifiyarsa a hali na yunwa, ga kuma damuwar halin da suke ciki na neman kudin aure. Da sallama ya shiga cikin dakin kanwarsa Aisha ta amsa ciki yanayi na damuwa. A bakin kofar dakin ya tsaya yana kallon mahaifiyarsa dake lullube da wani tsohon zanen gado tana ta rawar sanyi.

“Jikin ne?”

Ya tambaya da muryar dake bayyana tsananin damuwarsa.

“Haka ta kwana”

Aisha ta amsa.

“Miyasa ba a kira ni ba?”

“Ita ce kar a kiraka kar a tayar maka da hankali”

Runtse ido yai ya sauke ajiyar zuciya, ya dade a haka kamin ya bude idon ya nufi inda mahaifiyarsa take kwance ya zauna daf da ita, sai ta yaye mayafinta ta kalleshi da idanuwanta dake fassara irin tsananin zazzabin da take.

“Faruq”

“Mama damuwar nan ce kika dauka kika saka a ranki ko? Allah shi yake yin komai, kuma daman na yi tunani zamu hutar ta da kanmu da wani lefe ya bada kudin kawai a siya mata kayan daki da su”

“Ko ya bada kudin ai ba zai wuce 100k ba kuma ba zai isa a siye kayan daki ba, ko kujeru kanana yanzu sai an siye su 60k ko fiye ma”

“To ai sai a kara da wani abun idan Allah ya mana fatahi, dan Allah ki cire damuwa a ranki, Mama so kike ke ma mu rasa ki? Haba Mama”

“Damuwa dole ce Faruk bayan ta auren yaran nan akwai ta yau da kullum, yanzu ga shi abun da zamu karya ma ya gagaremu sai da na ba Asiya ta siyar da tufafina sannan zamu samu su karya, tun safe har la'asar ace bawa bai saka komai a bakinsa ba”

“Allah be manta da mu ba Mama, bayan wuya sai dadi, kuma idan ka ga tsanani yayi yawa sauki na tafe, Inshallah komai zai warware kamar ba a taba yi ba”

“Allah yasa muna da rabon jindadi ko kadan ne Faruq, lokaci tafiya yake baya jiran kowa”

Ta karasa tana runtse ido da karfi sakamakon bugawar da zuciyarta tai da karfi. Daga Aisha har Faruq hankalinsu tashi yai.

“Sannu Mama”

Kai ta daga musu cike da karfin hali har lokacin idonta na rufe saboda azabar ciwon da take ji. Ajiyar zuciya Faruq ya sauke ya mike tsaye ya bar dakin cikin damuwa, ji yake kamar ace yana da halin da zai magance damuwar mahaifiyarsa, kuma ya kaita asibiti a duba lafiyarta, amman ina? Talauci ya saka shi a gaba kamar wanda ya zagi arziki.



LEILA POV.

Rike da takardun Madina ta shiga dakin Momy ta zauna gefen gadonta.

“Momy Could you do me a favour?”

Momy ta aje plate din abincin dake hannunta ta kalli Leila dake sanye da doguwar rigar shadda ta sha aiki kamar sabuwar amarya.

“Minene?”

“Kin san kawata Madina ai...”

“Har sai kin sake gabatar min da ita? Madina ai ta zama yar gida”

“No Momy ina son ki gane cewar maganar da zan miki tana da muhimmanci ne, Wallahi ta min magana tana son aiki a kamfanin Daddy and i promise her zan saka a dauke ta”

“And....?”

Momy ta bukata tana tsattsage hakoranta na makka.

“So daman dazun na mata magana ta kawo takardunta shi ne ta kawo, da na zo naje na samu Daddy kai tsaye da maganar amman na san zai ce na bawa Talba ne, Talba kuma zai iya cewa ba zai dauke ta ba, kuma kin san be kamata na kasa yi mata haka ba, ko da ba ita ba ma a kamfanin mahaifina ya kamata ace zan iya yin komai ina da ikon yin komai”

Momy ta yi dariya.

“Leila kenan, kina abu kamar ke ce Amal, idan za a dauki wani aiki ta dalilinki har sai kin tsaya wani kame kame? Ki same yayanki Talba da maganar mana”

“No Momy ni fa bana son magana da shi sai idan wani babban abu ne, yadda yake jin kansa haka nakr jin kaina, kuma kin san zai iya amfani da wannan damar ya wulakanta ni ko ya fada min wata maganar marar dadi, idan kuma na rama ke da Daddy ni zamu dorawa laifi”

“Wannan ai da ne Leila, amman yanzu na fahimci halin da kike ciki, halin Talba sai mai hakuri da kai zuciya nesa ni kaina yanzu ya fara min ai”

“Shiyasa nake son ki saka shi ya dauke ta... ”

Tana rufe baki Talba ya kwankwasa kofar dakin sannan ya murda kofar ya turo ya shigo, juyowa tai ta kalleshi, a take annurin dake fuskarsa ya auri idanuwanta, duk yadda ta so ta dauke kai daga barin kallonsa sai ta kasa har ya karaso inda Momy take ya zauna a saman kujera, lumshe ido tai tana ta yaki da numfashinta dake ta kokarin sauya mata kamshin dakin Momy zuwa na turaren Talba da ya cika daki.

“Momy barka da dare”

“Yauwa”

Yanayin yadda Momy ta amsa masa ne yasa shi murmushi domin ya san har yanzu bata gama hucewa daga laifin da be aikata mata ba.

“Allah yasa dai ba fushi kike da ni ba har yanzu Momy?”

Uffan Momy bata ce masa ba, hakan ya saka shi kara yin Murmushi sai dai wannan karon be ce komai ba.

“Abun da kake dai ba abu ne mai kyau ba, mata aka sani da tsegumi ba maza ba”

“To ayi min afuwa ba zan sake ba, Leila...”

Ya karasa yana kiran sunanta, sai ta bude idonta a hankali ta kalleshi ba tare da ta amsa ba, daman shi ma he called her name ne kar Momy tace ta ganta be mata magana ba, duk kuwa da kasancewar ita ya kamata ta fara masa magana a lokacin daya shigo a matsayinta na kanwarsa kuma wacce zai aura, ko ba komai ai ita ce karama.
Mikewa yai tsaye sai Momy ta dauki takardun da Leila ta aje mata gefenta ta mikawa Talba. Sai da ya kalli takardun sannan ya mika hannu ya karba ya bude yana dubawa.

“Ba mu fara daukar ma'aikata ba, muna da enough”

Ya fada bayan ya dauke idonsa daga fararen takardun zuwa ga Momy.

“Na sani, saka iya replacement dinta da wani ai”

“Na dauka Madina tana aiki da ma'aikatar Alhazai ai”

“Tana yi, yanzu nan take so kuma umarni ne so nake ka dauke ta”

Ya hade yawun bakinsa, sannan ya kalli Leila da ita ma kallonsa take ya rufe takardun ya juya ba tare daya sake cewa komai ba ya fice, binsa Leila tai da kallo har ya fice sannan ta juyo ta kalli Momy.

“Thank Youu Momy”

“Karki damu, je ki samu abun da kika sakawa cikinki”

“Okay”

Ta mike tsaye ta fice daga dakin cikin jindadi. Ko da Talba ya fito Kabir na zaune kan center carpet tare da Amal suna shan kankana. Saman kofa Talba ya zauna rike da takardun yana kallon plasma.

“Malam bismilla karka ce mun maka rowa”

Kabir ya fada yana kallonshi, Talba kallonsa kawai yai ya dauke kai fuska ba yabo babu fallasa. Amal ta kalli Kabir sannan ya kalli Talba ta ce

“Ya Talba Momy ta maka fada dazun?”

Gira ya daga mata, wanda hakan yai daidai da saukowa Leila sai ya mike tsaye ya fice daga falon gaba daya.

“Strangers, ban taba ganin masoya irinku ba, wai a haka zaku yi aure?”

“Miye damuwarka ne Kabir? As long as yana so na miye ruwanka ne?”

Yayi dariya ya mikawa Amal hannu suka taba.

“Hi five Baby”

Dinning ta nufa ta bude manyan kulolin tana duba abun da Momy ta dafa, wayar dake hannunta ta aje a gefe ta dauki karamin plate ta dauka ta fara zubawa, abun ka da wanda baya son cin abinci sai ta zuba kadan ta ja kujera ta zauna. Kamar zaman ake jira tai sai ga sako ya shigo wayarta.

‘Good Night Dear’

Wani irin kasaitaccen murmushi tai bayan ta gama karanta sakon dake dauke da hoton zuciya.

“I love you”

Ta furta a zahiri, sannan ta aje wayar ta juya ta kalli Kabir dake ta rigima da Amal akan waye zai karasa shanye watermelon din da suka raga mai tawa, sai kuma ta juyo ta kalli abinci.

“Talba kana da wuyar sha'ani, wannan girman kan naka yana bani mamaki, ban taba ganin mai tsoro ko jin nakasu akan nuna soyayya ba kamar kai... But i love you..”

Ta furta tana kara jin shaukin kaunarsa na ratsa zuciyarta.


________

Na zo muku da albishir guess what? A have alot of kayan mata masu kyau gaske, akwai na infection, akwai maida tsohuwa yarinya, akwai set din da ake hadawa for matan da basa gane kan mazajensu, akwai na mallaka kala kala, muna kaza mai magani, tantabaru, akwai kaza mai Yasin, akwai na mallaka sirrine mai karfin gaske. Ina masu son zama madubi a gurin mazanje su? Ina matan dake cewa na gwada ban dace ba? Muna da gumba da garin magani kala kala da na tsarki ga Humra da turarunka kala kala amman fa na kayan mata.
  Ga masu bukata za su iya tuntubar number na 08036126660 zan saka miki a mota na aika miki har inda kike da yarda Allah.

Serious Buyers please, idan ba ki shirya ba kar mu batawa juna lokaci.


12

Shin kin san Kamshi na daga cikin abun da yake daga darajarki? Kamshi yana saka a ga kimar mutum a girmamashi musamman ma na Ramla incense, tana da turaruka kala ka kama daga na jiki dana daki da na tufafi, irin su Halud
Sandal flakes
Sandal wood
Signature
Kajiji
Damboun kajiji
Halud ball
Wardrobe ball
Coconut sandal
exclusive gowe
Black humra
Body milk
Kulaccam
Misik humra. Ramla Incense ta shirya tsab domin aika muku da turarenku har garin da kuke, da kudinki kalila ki samu turare mai kyau mai dadin kamshi da sanyaya zuciya, domin siye ko sari ku tuntubi Ramla incense ta wannan number 07038392576 tana aikawa har wajen Nigeria. You can check her Instagram handle ramla_incense. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=1fl5k3wnc4opb&utm_content=43xtopa


_________


*Dan girman Zatin Allah karki karanta idan baki biya ba. Masu sharing Allah yai muku yadda kuke min! Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci. Pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith bank, then send the evidence via 08036126660*


Seven days later...

FARUQ POV.

A gabanta ya dire kofin dake dauke da koko ya dora mata suga a saman murfin.

“Ga abun da muka samu”

Wani banzan kallo tai ma kofin ta dauke ido tana turo baki gaba.

“Koko kuma? Ni bana son shan koko gaskiya”

Kallonta kawai yai ya dauke kai ya shiga dakin ya cire tufafin jikinsa ya daura wani tsohon tawul ya fito ya nufi inda ya jona ruwan zafi a electric a juye a karamin bokitin wanka ya fita waje ya sirka ruwan sannan ya dawo falon.

“Ni fa bana son koko”

“Wani yana can yana nema be samu ba”

“Wallahi babu, ba dai sa'ata ba, sai dai tsofafi sa'o'ina kyawawa kam suna can suna neman arziki”

Uffan be sake ce mata ba ya nufi hanyar dakin.

“Ni fa ba zan sha koko ba, waina nake so da nama”

Juyowa yai ya kalleta.

“Idan ina da halin siya miki ita kin sani, kuma babu abun da zai hana na siya miki,

End Ads

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login