Showing 66001 words to 69000 words out of 133328 words
ko ta kwanta bata bukatar irin wannan maganin, a kyaleta ta wuni da yunwa idan ta ji babu komai a cikinta zata karbi abincin idan an bata, da haka zata saba ta rika ci, amman a yanzu ai an hanata jin yunwa ne, kuma ace ana son ta ci abinci?”
“But he cant walk fa”
“That one is different, maybe damuwar ce ta haifar mata da hakan ko kuma wani matsalar dabam, amman rashin lafiyarta ba zai zama da matsala a cin abincin ta ba, indai ba wai tana kan wani magani da aka dorata ba ne, shi ma kuma sai dai ace ba zata ci wani ba wani zata ci”
Talba ya yunkura da zimmar tashi sai Kabir ya kalleshi ya ce.
“Ita ce yarinyar?”
Da ido Talba yai masa alamar question mark, sai ya karansa tambayarsa.
“Yarinyar da kake zargin Leila tana kokarin kashewa?”
Talba be ce masa komai ba ya fara tafiya.
“And do you really think Leila zata iya wannan abun?”
Tsayawa Talba yai ya juyo ya kalli Kabir.
“Amal ta baka labarin Baaba?”
“No amman Momy ta fada mana yan'uwanta sun zo sun dauke ta right?”
“Yes amman dazun nan jikanta ya zo nemanta, so kai tunani akai”
A take Kabir ya cika da tsananin mamaki, Talba kuma ya juya ya fice daga falon. Bangarensa ya nufo kamin a karasa ya cire agogon hannunsa, sannan ya kai hannunsa na hagu ya bude kofar ya shiga, tafiya yake kamar baya son taka kasa ya karasa bathroom dinsa ya jefar da wayarsa saman gado, ya cire tufafin jikinsa ya daura tawul. Samun kansa yai da karasawa gaban katon madubin dake dakin wanda ke nuna iya tsayin mutun. Tsaye yai yana kallon kansa kamin ya kai hannu ya shafa kirjinsa zuwa cikinsa sai kuma ya dawo da hannun saitin inda zanen kirjinsa yake yana tabawa.
Motsin shigowar mutum da yaji ne yasa shi juyowa da sauri domin ya san ba kasafai ake shigowa bangarensa ba, Momy ba tai musu wannan tarbiyar ba, ta shiga dakin juna barkaita sai dai idan da wani dalilin. Takawa ya fara yi kamin ya isa bakin kofar Bathroom din Leila ta shigo, tsaye tai cak tana kallonsa daga kasa zuwa sama, wani irin bugawa zuciyarta tai da karfi a lokacin da idanuwanta sukai arba da faffandan kirjinsa. Tun da take a rayuwarta bata taba ganin Talba babu riga ba sai yau, duk kuwa da kasancewar a gida daya suka tashi sai dai baya bayyana mata siraicinsa kamar yadda ita bata taba nuna masa nata ba sai dai dan abun da ba a rasa ba, kamar saka damammen kaya ko wando da riga, sai dai rika hannunsa ko taba shi ba wani abu ba ne a gurinta kamar yadda shi ma be dauke shi komai ba.
“Ya akai?”
Ya tambaya yana kallonta, ba karamin jihadi tai ba na ganin ta daidaita natsuwarta, sai dai hakan be hana numfashinsa yin nisan kiwo ba na tsawon dakiku, ta dauken kai tana kokarin dawo da numfashin a hankali.
“Yarinyar ta fada maka wanda yai mata haka?”
“Kina da wata maganar ne bayan wannan?”
Juyowa tai ta kalleshi.
“Ita wannan maganar ba mai muhimmanci ba ce?”
“Mai muhimmanci ce a lokacin da ta fada min cewar ke ce ko ba ke ba ce, and kuma idan na gane gaskiyar komai a game da Baaba”
“Duka biyun ban aikata ba, miyasa baka yarda da ni ba? And me zai saka ka zarge ni da kisan yarinyar da kai ma basan san ta ba”
“She can't walk she can't talk, depression yana damunta, and now idan na gano da hannunki a ciki, i swear ba zan raga miki ba, you have no idea what she's going through”
Ta kara matsowa kusa da shi tana kallon idonsa.
“I don't care, she can't talk or walk is not my business, ta mutu ko ta rayu be dame ni ba, ina ta fito ina zata je me ya faru da ita duka ba matsala ta ba ce, all what i care is us....we... I mean us... Just us...”
Yanayin yadda tai maganar ya bayyana bacin ran dake tare da ita, shi ma kallonta yake ido cikin ido yana kokarin hana zuciyarsa tsanarta. Sai da ta gama yawo da idanuwanta a fuskarsa sannan ta juya ta fice daga dakin a fusace. Tana dawowa dakinta ta dauki wayarta ta kira Madina ta san is late amman tana son ta yi magana da ita mai muhimmanci.
“Hello Leila”
Madina ta yi picking.
“Madina fada yadda ake mantawa da mutum”
“Ban gane ba”
“So na ke na manta da Talba, na cire shi a raina gaba daya na manta da shi”
Wani irin murmushi ne ya kawata fuskar Madina, ta yi saurin aje kofin ruwan dake hannunta.
“Amman miyasa?”
“Na gaji ba zan iya ba, sai na nuna masa ni din mai tsada ce kuma na nuna masa he is nothing to me”
“Shikenan zan zo da safe, wannan maganar ba ta waya ba ce”
“Okay ina jiranki”
Leila ta katse wayar, sai Madina ta rike wayar tana kallo, rabuwar masoya ba abu ne mai kyau ko dadi ba, sai dai ita ya zo mata a dabam domin ta samu kanta cikin farincikin jin abun da Leila take kokarin aikatawa.
BATURIYA POV.
Kamar yadda Ramlee tai mata alkawarin kawo mata kayan mata da zata sha a jiya, ta kawo mata su cike kamar wanda zata sara ta kai su wani gurin, ita ma kanta ta yi mamakin tarin hakin mayen da Ramlee ta kawo mata, wanda za a hado da madara ko zuma a sha duka ta siyo mata madarar da zumar, yadda ta ware kudi ta siye mata kayan matan sai ka rantse da Allah yarta ce.
Hakan yasa ta bude wardrobe dinta ta saka su ta rufe da makulli, idan zata sha sai ta bude ta debo ta sha ta rufe, ko Sultan bata yarda ya gani ba balle kuma Faruq uban gayya.
Bayan ta gama gyara gidan yayi tsab ta dora girkinta da wuri, sannan ta shigo falonta ta dauki wayarta ta kunna data ta fara chat. Zata yi reply wani sako kiran Fahat ya shigo wayarta, da sauri tai picking ta kai wayar a kunnenta.
“Hello”
“Yan mata ya kike?”
“Lafiya kalau, sai marmarinka”
“Uhm mmn Marmari kamar gaske, ke da kin ki bari ma na zo mu gaisa, sai kwana kwana kike min”
“Ai na fada maka gidamu ba za a bar ni ba, ba a barin mu zance gaskiya”
“Amman ai kin yi girman da ya kamata ace ana barinki zance Fee'at”
Ta lumshe ido tana jindadin yadda ya kira sunanta, daman haka take so ba kamar yadda Faruq yake kiranta da Rafi'a ta yi complain har ta gaji, sai yace mata shi ba ba ta soyayya yake ba, ta neman kudi yake da abun da zasu ci.
“Ba zaka gane ba ne”
“Na gane, kuma suna da gaskiya, wasu iyayen basa barin yayansu su na kula samari barkatai, amman idan kin amince min zan iya sakawa a zo a nema min izinin magana da ke har mu fahimci juna”
“Da gaske?”
Ta tambaya tana tashi zaune daga kwance da take.
“Wallahi kuwa, Fee'at ni fa da gaske nake aurenki zan yi, ba da wasa na zo ba”
“Uhmm”
“Allah kuwa, Momyna ta dade tana min maganar aure, ansha kai ni gurin yan mata da yan'uwa amman wallahi ban taba jin wanda tai min ba, amman ke ina ganinki na ji wani abu akanki Fee'at you're different...”
Ba karasa maganar da yake ba ta yanke wayar ta kasheta gaba daya sakamakon jin ana kwankwasar gidan. Fitowa tai ta isa gurin kofar ta bude sai tai arba da Faruq yana dauke da Sultan.
“Har kun dawo”
Sai da yai kamar kar ya amsa mata sai kuma ya amsa.
“Eh, Sultan shiga ciki”
Ya karasa yana sauke Sultan dake rike da ledar kifi kasa. Sannan ya juya ya
“Zan tafi shago”
“Allah ya tsare”
Ta fada kamar ba ita ba har sai da ya juyo ya kalleta, rabon da tai masa addu'a har ta manta.
“Ameen”
Ya amsa sannan ya juya ya cigaba da tafiyarsa, ita kuma ta maida kofar ta rufe taja hannun Sultan suka nufi cikin gidan tana tunanin maganar da Fahat yai mata.
‘Amman da gaske yake zai aure ni? Ko kuma dai wasa yake? Amman ai be san na taba aure ba, idan na fada masa gaskiya zai yarda ya auri bazawara?’
Ita kadai take ta haukanta ta saka wannan ta kwance wacan, gaba daya sai hankalinta ya tattara ya koma gurin Fahat tana ta ayyana irin rayuwar da zata yi, kasancewar sa mai kudi kuma dan masu kudin.
“Momy Mama tace a gaishe ki”
Sultan ya fada yana zaunawa ya bude ledar kifin.
“A hanya Dady ya siya min, yace na ci rabi na baki rabi”
Ba ta ma kula, gaba daya hankalinta yana gurin Fahat.
“Amman fa na masa karyar arziki, wata kila yana min kallon yar masu kudin ne”
Sultan ya kalleta.
“Momy waye?”
Sai a lokacin ta lura da a zahiri tai maganar ba a badini ba.
“Ba kowa ba ci kifinka, ga abinci can akan wuta idan yayi zaka ci kaji”
Ya fada mata kai ita kuma ta shiga uwar daka ta dauki wayar ta kunna, sai ga sakon Ramlee ya shigo mata.
‘Ki sha kayan nan da yawa, yace yana son ku hadu da gobe, na kira wayarki ban samu ba, idan kin gama karantawa ki goge sakon’
Dundundun ta ji gabanta yayi duka uku uku, ba dan bata saba haduwa da mazan da ba muharramanta ba, sai dai wata kila saboda wannan haduwar ta daban ce, saboda zata aikata sabo ne alhalin tana da aure da kuma da, ga kuma karamin ciki a jikinta.
Saurin goge sakon tai kamar yadda Ramlee ta bukata, sannan ta mike tsaye ta isa bakin kofar dakinta ta tsaya tana kallon Sultan dake ta aikin cin kifinsa hankali kwance, damuwa ce ta bayyana a fuskarta, duk wani dauki da take na son a bata kudi sai ta ji ya ragu, domin bata taba aikata alfasha ba, sai a wannan karon ne zata gwada. Juyawa tai ta koma cikin dakin tana busar da iskar bakinta.
18
*Khadeeja Candy*
Ko kin san kamshi na daga cikin abun da yake daga darajarki? Kamshi yana saka a ga kimar mutum a girmamashi musamman ma na Ramla incense, tana da turaruka kala ka kama daga na jiki dana daki da na tufafi, irin su Halud
Sandal flakes
Sandal wood
Signature
Kajiji
Damboun kajiji
Halud ball
Wardrobe ball
Coconut sandal
exclusive gowe
Black humra
Body milk
Kulaccam
Misik humra. Ramla Incense ta shirya tsab domin aika muku da turarenku har garin sa kuke, da kudinki kalila ki samu turare mai kyau mai dadin kamshi da sanyaya zuciya domin siye ko sari ku tuntu Ramla incense ta wannan number +234 703 839 2576 tana aikawa har wajen Nigeria. You can check her Instagram handle ramla_incense. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=1fl5k3wnc4opb&utm_content=43xtopa
*Dan girman Zatin Allah karki karanta idan baki biya ba. Masu sharing Allah yai muku yadda kuke min! Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci. Pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith bank, then send the evidence via 08036126660*
LEILA POV.
Sam bachi ya gagari idonta saboda yunkurin da take a zuciyarta na naki da soyayyar Talba. Sai ta kasa samun hadin kan sassan jikinta ciki har da idanuwanta, da kuma zuciyar datai mata garkuwa da kaunar Talba. Sai yanzu ta gane ashe abun ba shi da sauki, daman taya zai zame mata mai sauki? Ta rayu da kaunarsa na tsawon lokaci a dare daya ta ce zata cireta?
A maimakon ta ji kuzarin cirewar ta karfafawa kanta guiwa, sai ta samu kasala tana jin kamar ba zata iya rayuwa idan babu Talba ba.
Sai dai tana jin ajinta da martaba da kimarta ta wuce Talba yai mata haka kuma ta cigaba da sonsa ko waye shi kuwa?
“Na girmi wannan... Amman why?”
Ta furta tana jin kamar ba zata samu hadin kan zuciyarta ba.
“Allah karka min jarawa da kaunar mutumen nan”
Ta furta ta saka hanayenta biyu ta share hawayen da suka zubo mata. Mikewa tai tsaye ta nufi gurin window ta bude window ta tsaya a gurin tana kallon taurarin da suka kawata samaniya.
“Do i deserve this? It's painful...”
Ta fada wasu hawayen na sauko mata, a rayuwarta bata san zafin rashin ba, bata san ta nemi wani abu ta rasa, wata wani abu painful irin na wannan daren ba, a damuwarta akan halin Talba ne, amman a yanzu abun ya ninku tana jin kamar ba zata iya yakar kaunarsa a zuciyarta ba, kuma ba zata iya barin kaunar ta zauna ba then me zata yi?
Ta yi kasa da kanta wasu hawaye na sauko mata, ta fashe da kuka marar sauti, sai kuma ta soma murmushi.
“Ni Leila ina kukan namiji? Wannan ba ajina ba ne, at least na san Talba be isa yace ba zai aureni ba, amman ni din ai be kamata na aure shi bayan duk wannan abun da yai min ba, be kamata na damu ba”
Ta share hawayenta, sai magana take da kanta tana kallon harabar gidan kamar wani bakonta. Can kuma ta rumgume hannayenta tana tuna kalaman Kabir cewar Talba yana son ta, sometimes akwai kamshin gaskiya maganarsa, amman idan har Talba baya son ta waye zai so? Dole dai ita din ce.
“Akwai maza da yawa da suka fi Talba komai a duniyar nan, kudi, kyau, aji da komai ma, idan zan ba wa maza da yawa dama zan samu wanda zan so fiye da Talba ma”
Wannan karon with full confidence tai maganarta tana jin cewar zata iya. Ba laifi ta dan samu karfin guiwa da dakiyar zuciya, hakan yasa ta rufe window ta dawo saman gadonta ta hau ta kwanta ya rumgume filo ta lumshe ido tana son bachi ya dauke ta.
A nan ne bachi ya ce mata fir ba dai shi ba a yanzu, tunanin abun da Talba yai mata sai ya dawo mata a rai ya zauna, idonta zuciyarta kuma a bude, har kusan karfi uku na dare, Leila ba mace ce ma'abociyar karatu ba balle ma har tai tunanin raya daren da nafila.
Bata yarda ta bude idon ba duk kuwa da kin bata hadin kai da bachin yai. Sai kusan asuba bachi yai gaba da ita.
Washe gari Sunday kamar jiya kowa ya hadu a gurin cin abinci ban da Leila, sai dai a yau bangaren Momy aka zauna ba kamar jiya ba da aka karya bangaren Daddy.
Daddy ya gama duba kowa be ga Leila, hakan ya saka ya kalli Momy.
“Doctor ina Leila?”
“Tana dakinta i think”
Daddy ya yi mata wani kallo da kyau.
“So you think? Lafiya take na lafiya tana dakin ma ko bata ciki baki da tabbaci?”
“Uhm wani lokacin kana bani mamaki Alhaji, yaran nan fada wayansu ya kamata idan muka gan su a wani yanayi da suke son kebancewa mu bar su a yanayin da suke ciki”
“Amman idan suna da damuwa fa? Har kullum wanda ka haifa kana masa kallon yaro ne ko da kuwa ya girmi duniyar nan, irin wannan abun shi yake haifa da depression mutum yana da damuwa kuma a kasa maganance masa ita ko a ki kula da shi, wannan be dace ba, ko jiya bata ci abinci safe tare da mu ba”
Momy ta tabe sannan ta kwalawa Mairo kira, Mairo dake kitchen tana wanke kayan da sukai amfani da su, ta amsa tana fitowa da sauri.
“Shiga dakin Leila ki kirata”
“Hajiya Wallahi ko dazun dana shiga gyara dakin fada tai tayi tace idan a sake shiga dakinta ba tare data fito ba ko kuma na tashe ta bachi sai ta mare ni”
Mairo ta fada a ladabce. Sai Daddy ya kalleta.
“Ta mare ki? Yarta ce ke?”
“Wata kila fada dakin ne ba sallama ko knocked”
Momy ta amsa.
“No wannan ba dalili ba ne, at least ai ta girmamasu sun gurme ta nesa ba kusa ba”
“Wallahi Daddy haka take musu, ko magana cikin tsawa take yi”
Amal ta dora da nata, sai Daddy ya kalleta sai dai be ce komai ba ya cigaba da cin abincinsa, Daddy mutum ne mai matukar son yayansa, ko kadan baya son ya ga wani abun bacin rai ko n damuwa ya same su, sai dai hakan be taba saka shi ya kyalesu a inda ya kamata ya gyara musu ba kuma ya saka musu ido.
Sai da Daddy yai rabin cin abinci sannan ya kalli Momy ya ce.
“Yawan fushi ko tsana yana nuna akwai abun da yake damun mutun ne, musamman a kwana biyun nan da bata fitowa cin abinci, idan akwai wani abu da yake damunta ki sama mata mafita, akwai abun da ke ya kamata ki yi a matsayinki na uwa, zata fi sakewa da ke kuma ta bude miki cikinta ta fada miki damuwarta, and to you my friends idan akwai wanda yake mata wani abu da zai sakata a damuwa ko bacin rai dan Allah ku daina, ya zama tsintsiya madaurinki daya, idan dayanku yana cikin damuwa ku yi kokarin ganin kun kawar masa Allah ya hada kanku yai muku albarka”
Duk suka amsa da Amin, sannan Daddy ya mike tsaye yana fadin.
“idan kin yi magana da ita, ki fada mata ina son ganinta”
“Okay”
Momy ta amsa tana watsawa Talba harara kasa kasa domin har ga Allah yanzu haushinsa take ji, saboda yana kokarin wuce gona da iri. Sai da Daddy ya fice daga falon sannan Momy ta dakawa Amal tsawa
“Amal... Wallahi idan na sake jin bakinki akan fadawa Daddy magana any how sai na baki mamaki, sai na miki hukuncin da baki taba mafarkin zan miki ba, cigaba karki fasa”
Momy ta karasa tana dukan burin dinning din sannan ta mike tsaye ta bar gurin a fusace. Amal ta bata fuska kamar zata fashe da kuka, Kabir ya saka mata dariya. Talba ya kalleshi.
“Kabir?”
Ya sake bushewa da dariya yana yi ma Amal gwalo.
“Sai a hana ni dariya? Yarinyar tafi kowa iya gulma, bata gidan amarya bata gidan ango ai maganinki kenan”
Dariyar ya cigaba da yi mata yana cin abincinsa, ita kuma ta kara bata fuska kamar zata fashe da kuka.
“Karki biye Kabir kin san halinsa ai, daman so yake ki yi kuka, karki yarda ki masa kuka”
“Ai ba zan masa kuka ba, na fi karfin na yi masa kuka”
Ta fada tana matse hawayen dake son fito mata. Kabir kam ban da