Showing 126001 words to 129000 words out of 133328 words
tsaye ya nufi bedroom dinsa, daga Talba har Momy binsa sukai da kallo sai da ya shige sannan Talba ya mike tsaye da zimmar tafiya sai Momy ta dakatar da shi ta hanyar tsayar kiran sunansa.
“Talba”
Mikewa tai tsaye ta karasawa gurinsa tana kallonsa fuska a hade.
“Karka kuskura ka bari Leila ta ji wannan maganar, domin akan 'ya'yana, bana da mutunci, bana da ragowa, bana son abun da zai daga musu hankali, idan ma ka fara son yarinyar nan ka bullo da maganar ta wannan hanyar to ka cireta a ranka tun wuri, kana gani ai, ni kadai nake a gidan mijina, haka ma yayana zasu zauna har karshen rayuwarsu, ko da wasa kar ka yi kuskuren hada soyayyar Leila da ta wata macen ko da ba wannan ba, balle kuma wannan kazamar da bandits suka gama wulakantawa, yarinyar da ingiyar aurena ta rabu saboda ita”
Kallonta kawai yake da mamaki, kamar ba ita ce ta gama fada masa cewar tana kaunarsa ba, and yanzu ya gane halin Momy tana sonsa but when it's comes to her children bata saurarawa kowa. She got lucky ita ce ta fada masa haka b Leila ba, da Leila ce zai iya fada mata bakar maganar da har ta mutu ba zata taba iya mantawa da ita ba, but Momy ce ya zai yi bayan ya saka mata ido. Har ta yi gaba sai kuma ta dawo ta sake kallonsa.
“And for the very last time karka sake shiga safgar yarinyar nan”
“Yar'uwata a yanzu, ko a da na taimake ta balle a yanzu da bata da kowa sai ni sai Kaka”
“I don't care, rayuwar kowa bata dame ni ba, ka haka rame ka binne maganar nan a inda aka yi ta, idan ba haka ba zan baka mugun mamaki Talba domin ba zan yarda a taba kimar yata ba...!!!”
A falon ta bar shi tsaye ta nufi babban falo cikin fushi ta karasa kofar fita falon wanda zata sadata da bangarenta, shi kam binta yai da kallo har ta shige ta turo kofar sannan ya fito babban falon ya zauna yana tunanin yadda zai fuskanci Kaka, anya zata fahimta kuwa? Idan ta fahimta falillahil hamdu, daman haka yake so, sai ya cigaba da daukar dawainiyar Aminatu, sai dai idan kuma bata fahimta ba fa? Ya zai yi? Ya shafa kansa yana sauke ajiyar zuciya.
Ya kusan awa daya a zaune, sannan ya tashi ya nufi bangarensa yana amsa wayar Ali, a tsanake ya labarta masa komai sannan ya nufi gadonsa ya kwanta ba dan yana jin bachi ba, sai dan ya rasa abun yi. Yana rufe ido wayarsa tai ringing sai ya kai hannu ya dauka ba tare daya bude idon ba, power button ya danna sai yai picking call din ya kara kunnensa.
“Na cilasta maka aurenta ne da zaka turo ubanta ya rufe ni da fada, yana kokarin nuna min cewar ina son yi maka auren dole ne? Lallai Mu'azu ka nuna min ban isa da kai ba, kuma yanzu na gane dalilinka na watsar da mu da kake, saboda mu talakawa ne ko? Toh na shata layi daga yau kowa ya tsaya matsayinsa, yarinyar da kake kyama har ubanka yana fada min akwai banbanci tsakaninka da ita gata can ana mata karin ruwa, idan ta mutu aikowa ya huta”
Sai a lokacin ya bude idonsa ya tashi zaune da sauri.
“Bata da lafiya ne Kaka? Zata iya magana?”
“Ban sani ba, na dai fada maka kar kaka sake turo min ubanka ya dame ni da wata maganar banza, idan abun da yake ganin yana bani ne yana daukar nauyina ban cilasta shi ba, kuma ba a yunwa ya gan ni ba”
“Kaka dan Allah ki kwantar da hankalinki, daman na yi magana da Daddy ne saboda ya fahimtar da ke, ban yi tsammanin abun zai kai ga haka ba, na yi alkawari zan aureta”
“Ba zan aura mata miji irinka ba, kaje can ka auri yar masu arziki, ai daman kishi yake taya yarsa, har yana nuna min cewar kuna da banbanci”
“Zan shigo garin Maradu yau ko gobe kuma Wallahi sai kin aura min ita”
Yana fadar haka ya ji ta mikawa wani wayar tana fadin.
“Karbi kashe min, waya sani ma ko zagina zai yi yanzu kuma, bayan ubansa ya gama nasa”
Dit... Ya ji ankashe wayar, sai ya mike tsaye ya fice daga dakin da zimmar zuwa bangaren Daddy, sai ya same shi waje direbansa ya bude masa mota yana kokarin shiga. Sai dai hangoshi da Daddy yai ya saka ya dan jinkintar yana jiransa. Ya karaso gaban Daddy a natse.
“Daddy aka yi magana da Kaka ne? Ta kira ni tana ta masifa”
“Na yi magana da ita, ina kokarin fahimtar da ita ta kasa fahimta, sai maganar take saboda anga ita talaka ce shiyasa nake mata haka, kuma wai ina taya yata kishi for god sake ya za'ayi na taya Leila kishi ni ba mace ba? Ba wai bana goyon bayan auren nan ba ne saboda Leila, Wallahi bana goyon bayan auren nan ne saboda baka so”
“Amman Daddy idan yin zai zama mafita why not...”
“No baka so ba za'ayi ba, that's it”
“Idan kuma ina so fa...”
“No baka saba yi min karya ba, ni kuma ban saba canja kalamaina ba, ba zan yarda kai abun da baka so ba, kuma ba zan bari ka yi abun da zaka zo kana nadamarsa ba, ba za'ayi auren ba karka sake yi min maganar nan”
Daddy na kaiwa nan ya shige motarsa, Direban ya zagayo ya rufe matsa sannan ya koma ya shiga driver side ya ja motar. Sai da Daddy ya fice daga gate din gaba daya sannan Talba ya koma bangarensa ya canja tufafin jikinsa ya dauki wallet dinsa da keys ya fito da sauri ya shiga motarsa sai da yai reverse sannan ya hango Momy dake tsaye a backyard tana kallonsa fuska a hade, dauke kai yai yaja motar yana danna horn da karfi kamar mai tsere. Sai da yai nisa da unguwar sannan ya kira Ali ya fada masa abun da ya faru.
“Yanzu miye abun yi?”
“Oho ni yanzu hankalina ma ya koma can gaba daya, saboda Kaka tace min gata nan ana mata karin ruwa waya sani ma ko wanda ke mata karin ruwan be wani kware ba, kuma wata kila ba a bincika ciwonta ba”
“If ka damu da ita da lafiyarta Talba, be kamata ka nunawa Daddy baka son aurenta ba, kasan Daddy ya fika son abun da kake so, kuma yafi ka tsanar abun da kake ki, yanzu ya zaka yi kenan?”
Talba yayi jimmm sai kuma ya sauke ajiyar zuciya.
“Aurenta zan yi, ba zan yarda zumuncin dake tsakanina da Kaka ya lalace ba akan abun da ina da iko da shi ba, kuma ba zan yarda Daddy ya samu matsala da Kaka ba”
“Then ya zaka yi convinced din Daddy ya yarda ka aurenta? Kasan ba zai taba yarda ba, aje maganar Daddy a gefe ma, ya zaka yi da Momy da Leila?”
“AUREN SIRRI no one would know, har sai komai ya daidaita, and i think Aminatu deserved a better life zan dawo da ita gidan nan”
Ali yayi saurin mikewa tsaye daga zaunen da yake yana girgiza kai.
“No karka yi haka Talba, zaka cutar da kanka kuma yarinyar zata cutu”
“Sai dai ni na cutar da kaina, amman ba zan bari a cutar da Aminatu ba, kuma ba zan cutar da ita ba”
“Maimakon haka, ai kara ka samo wani dabam ka aura masa Aminatu a matsayinta, saboda ba lallai ne ma idan a aureta ka iya zaman aure da ita yadda ya kamata ba”
Talba yayi murmushi yana tuna kalaman Momy na dazun.
“Saboda me? Saboda wasu mazan sun wulakantata? Ali bari na tambaye ka, idan kanwarka zaka so wani aureta? Ita ta kaddarowa kanta wannan abun ya faru da ita? Miyasa ake kyara mutanen da irin wannan kaddarar ta fada musu? Wallahi wannan abun ya fara min tausayinta kuma ya karfafa min guiwar aurenta, saboda ta cancanci zama da namiji irina, bayan ni a yanzu ban san wanda zai aureta ya zauna da ita da zuciya daya ba, and ba zan iya yaudarar Kaka tana kallon ni na aureta sai kuma na saka wani yayi? Ita kanta Aminatu ba zata ji dadi ba, and idan hawayen yarinyar ya zuba saboda ni ba zan taba yafewa kaina ba”
Ali yayi murmushi.
“Na taba fada maka lokaci zai da idonka zai rufe ka taka kaya ka jita kamar lad'a, kana son yarinyar nan believe me, zaka iya yaudarar Daddy da Momy da Leila amman ba zaka iya yaudararta ba, and you are telling me idan hawayenta ya zuba saboda kai ba zaka yafewa kanka ba... This is Love Talba, Welcome To the club”
Talba ya natsu yana nazarin abun da ya fadawa Ali, did he say something wrong? No gaskiya ya fada masa ai abun da ke ransa. A hankali ya sauke wayar ya cigaba da tukin yana tunanin halin da Aminatu take ciki.
LEILA POV.
Tana fitowa daga dakin ta shiga dakin Momy, bata same ta a ciki ba, sai ta sauko kasa ta shiga kitchen nan ma bata ciki.
“Ke Mairo ina Momy”
Ta tambaya tana wani yatsinar fuska kamar wanda tai arba da kashi.
“Tana sama”
Mairo ta amsa mata ba tare da ta kalleta ba.
“Wai Mairo har wani ji kike da kanki a gidan nan, Wallahi idan baki yi hankali ba sai na karya ki, ba ki san halina ba ne”
Kallonta kawai Mairo ta yi ta dauke kai ta cigaba da abun da take, ita kuma ta juyo ta fito daga Kitchen, kai tsaye ta nufi upstairs kamin ta karasa Momy ta sauko rike da atamfa.
“Momy ina kika shiga ban ganki ba”
“Ina backyard”
“Gurin me?”
Leila ta tambaya da mamaki domin ba kasafai take shiga can ba.
“Gurin kallon Talba, ashe har yanzu yarinyar nan tana ransa?”
“Me yace ne?”
“Ba komai kawai na lura da yanayinsa ne”
“Yauwa Momy daman ina son na yi miki magana akanta, ki bincikar mana shi inda ya kaita dan Allah ko ma ki saka ya dawo da ita gidan nan if possible”
“Saboda me?”
“Madina ta ba ni shawarar mu samu wani mu biya shi ya aureta, kin ga ai mun huta, to na yi da bugun cikin Ali be fada min komai ba, sai ma ya nuna min kamar be san inda Talba ya kai yarinyar ba”
Momy ta yi shiru tana nazari.
“Indai haka ne, Madina ta kawo shawara mai kyau, amman akwai wani sirri da baki sani ba”
“Minene?”
“Wannan yarinyar da kakanta da kakar Talba yaya da kane ne”
Leila ta gwalo ido waje tana bude baki cike da mugun mamaki.
“What'? That's mean cousin dinsa ce kenan? How how Momy how? No ba gaskiya ba ne kina min wasa ne”
A take idonta ya cika da hawaye jikinta ya fara rawa, sai Momy ta rika hannun ta koma sama da ita.
“Shiiiiiiiiiii zo nan ki ji”
Momy taja hannunta har cikin dakinta, hawaye kam sai sallama yake yi ma idanuwan Leila tana amsa masa da gaggawa.
34
*Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci. Pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith bank, then send the evidence via 08036126660*
AMINATU POV.
Tana jin muryar Talba sai ta bude ido da sauri, domin tabbatarwa idan kunnuwanta daidai suka jiyo mata, tsaye ta ganshi a kanta yana ta kallon kyakkyawar fuskarta cikin damuwa. A take ta zabura ta tashi zaune.
“Ina wuni”
Sai ya zauna kusa da ita yana kallonta cike da kulawa.
“Ya jikin?”
“Alhamdulillah”
Ta fada tana jin kamar an yaye mata ciwon an aje gefe daya. Hannunsa ya kai ya taba wuyanta sai ya ji shi da dan sauran zafi. A nan ya kalli Kaka.
“Wane irin magani aka bata?”
“Wanda ka kawo mata”
Kaka ta fada masa tana wani tsuke baki, ta dauke kai kamar wata yar yarinya wai ita ala dole fushi take da shi.
“Haba Kaka”
Sai kuma ya kalli Aminatu.
“Shalele wani irin magani aka baki?”
“Mai dacin nan na malaria da na ciwon kai, sai kuma ya saka min ruwa, kuma ta min allura”
Ta fada a shagwabe idonta na cika da kwalla ji take kamar ta fashe masa da kuka tunawa da zafin allurar da akai mata gashi kullum yake mata safe da yamma.
“Kin gani ko? Ba ma wani kwararen ba ne, taya zaka baka maganin malaria da allura a lokaci daya, kuma ba a tsaya an auna mutum ba? Maybe ma hawan jini ne tun...”
Kamin ya karasa Kaka ta daka matsa tsawa.
“Can can ga kanka, sai dai idan kai ka shafa mata hawan jinin, dan dai ina da shi ne shine kake son murdowa ta nan kace ni na saka mata? Daman tun da ka tafi take ciwo tana kuka na kira dan Asabe ya dubata yace malaria ce”
“Ba a auna mutun ba za a gano ciwonsa? Ni ban ce kin laka mata ba, daman ya za'ai wani ya saka ma wani hawan jini?”
“Wai idan ma manufar ka kenan ai na san ba so na kake ba”
Da gaske take maganar, a kokarin juya maganar zuwa wasa yai dariya ya amsa mata da.
“Me zan yi da tsohuwa ga sabon jini na samu”
Ya fada yana kallon Aminatu. Kaka ma kallonsa take.
“Ko Shalele?”
Aminatu ta yi kasa da kanta gabanta n bugawa da karfi. Sai yai murmushi
“Kin ci abinci?”
“Bata ci abincin ba ai gidan yan yunwa ka kawo ta ko?”
Kaka ta amsa masa a fusace. Be kula ta ba ya cigaba da kallon Aminatu.
“Bari na fita na bincika idan akwai inda ake siyar da abinci mai kyau sai na siyo miki, hankalina ya dauku shiyasa ban tsaya a hanya na siyo miki komai ba”
Magana yake mata a hankali kamar mai kokarin fahimtar da ita. Sai ta daga masa kai a hankali tana kai hannu ta share kwalla da suka tarar mata.
“Good Girl”
Ya mike tsaye sai ta bishi da kallo har ya fice, Kaka kuma ta bita da kallo mamaki zuciyarta na raya mata wani abun.
“Ke Auta...”
Aminatu ta kalli Kaka da sauri, sai Kaka ta matsa kusa da gadon da take zaune.
“Fada min lokacin da kuna can, yana miki wani abu?”
Aminatu ta yi shiru domin bata fahimci inda Kaka ta dosa ba.
“Yana tabaki ko ya rike hannunki ko ya dan shafa ki”
Aminatu ta yi shiru tana tunanin irin amsar da zata bawa Kaka.
“Karki ji tsoro ko kunya, kin ganshi nan jikana ne, duk yafi soyuwa a raina amman wacan kanen uban nasa da tsinanniyar matarsa da bata nuna masa son yan'uwan uwarsa ba, sun canja shi sun maida shi wani kala, ba san manufarsa a yanzu, na lura sai son shige miki yake kuma bayan ya nuna min shi ba zai aureki ba, har yana wani kiranki Shalele, wannan sunan yan iska ne, karki yarda ya sake ce miki haka kinji ko?”
Aminatu ta daga mata kai, alamar eh sannan tai kasa da kanta tana tauna maganar Kaka ba cewar yace ba zai aureta ba, wa yai masa tayin auren tun farko? Amman miyasa zai aurenta bayan ita da shi akwai banbanci da tazara mai girma?
‘A'uzubillahi’
Ta fada a ranta tare da lumshe ido tana jin kamar ta yi banban sabo saboda zuciyarta na kusanto mata da aurenta da mutumen da ko a mafarki yafi karfinta. Taya mutum mai daraja da tarin dukiya da kyau da iyali kamar Talba zai yarda ya hada jini da irinta? Amman miye manufarsa ta yi mata furucin da yai mata a lokacin da zai tafi? Ta daga idonta ta kalli Kaka.
“Tsohuwa ke kika ce masa ya aure?”
“Eh, saboda ki samu rayuwa mai kyau, kuma kin ga dan'uwanki ne zai rike ki da amana, sannan ni bana son yarinyar can da zai aura, uwarta sau biyu kawai ta taba zuwa garin nan, ita yarinyar ma ban santa ba, amman suka zaba masa ita saboda sun ga yana da dukiya, sai juya shi suke kamar waina, ni bana son ya aureta ma, kara ya auri yar'uwarsa idan ma a nan zai aje ki ai kin ga dole ya rika zuwa yana duba ki mu ma muna ganinsa, kuma sai na nunawa wannan bakar matar ni ma na isa da shi, amman sai ya juya min baya harbda turo wannan uban nasa a waya yana fada min kabli da ba-adi da shika shikan kin aurenki”
“Yana da wanda zai aura Kaka, kuma ba ki ga zubinsa ba? Akwai banbanci rayuwata da dasa, ni fa a kauye na tashi, sannan na rasa abubuwa da yawa da be zama lallai ma wani namijin ya so ni ba, balle kuma shi”
“Ai ba wannan za a duba ba, hadin gida da zumunci ba ruwansa da wannan dan haka ki daina ma duba wannan”
Kaka ta karasa tana mikewa tsaye ta gyara daurin zanenta.
“Bari na yi fitsari”
Aminatu ta yi kasa da kanta idonta na cika da hawaye. Kaka na shiga bandakin Talba yai sallama ya shigo, Aminatu ta kasa amsawa kuma ta kasa dago kai ta kalleshi, har ya zauna kusa da ita ya kai hannunsa ya dago kansa sai yai arba da hawayenta.
“Kaka ta miki wani abu?”
Ta girgiza masa kai alamar no.
“Toh miya faru ko kina jin ciwon ne?”
Wannan karon ta samu damar amsawa.
“Aa”
Sai ya saka hannunss biyu ya share mata hawayenta.
“Idan ina kusa da ke, hawaye basa da muhallin a fuskarki, ki daina kuka kin ji Shalele?”
“Ka daina ce min haka dan Allah”
Ya daga kansa sama yayi murmushi ya sauke.
“Idan Kaka ta zo ki fada mata ba zan daina ba”
Ya fada domin ya san ita ta kitsa mata wannan maganar, domin bata taba masa korafin kiran da yake da Shalele ba sai a yau.
“Na bawa wani ya siyo miki abinci mai kyau, yanzu fada min Kaka ta miki gulma ta?”
Ta yi shiru kanta a kasa.
“Kaka tana fushi da ni, saboda na ce ta aura min ke taki”
“Aa ba sai ka boye min ba, ni bana son aure a yanzu kuma na san akwai banbanci a tsakanina da kai...”
Bata karasa ba ya kai hannunsa ya rufe mata baki.
“Wallahi ban taba ganin wannan banbanci ba, kawai abun da nake tunani yadda zamu fuskanci juna ni da ke, kuma yanzu wannan zuwan da na yi ba zan tafi ba sai da igiyar aurenki”
Ta sakar masa ido sai kuma ta matsa baya